You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mini fishin da ya
wuce na kwana d'aya. Ni ce dai nake jarumtar share shi na lokaci mai yawa.
Duk da ni din ma karfin hali nake yi.
Yanzu haka Tijjani yana da nasa teburin a cikin kasuwar ma'ana ba k'arkashin Alhaji
yake ba. Watanni uku ya karbi ku'dina ya mallaki wajen flda zai ajiye teburinsa.
Zobena daya muka siyar. Yanzu haka jiya ya kai ni na zabi wanda nake so ya siya
mini a madadin nawa.
Na sani ba dan ya samu damar biyan ba ne, sai dan yana son ya biya ni ne.
Hakan kuma bai sa sun rabu da Alhaji Auta ba.
Ana cikin haka guda cikin kamfanin sadarwa ya nemi kafa turakan ayyuknasu cikin
unguwar da filin Tijjani yake. Gaba'daya mutanan da suke da fili a wajen kowa fata
yake a ce su karbi nasa, tunda haya zasu kar'ba.
Alhaji Auta har addu'a ya baza a yi masa ko ya samu ya d'an farfado.
Kamfani har yanzu zagaye yake tare da wakilinsu da suka san ilimin kimiyya suna ta
auna inda zasu fi samun sabis.
Gaba'daya Tijjani bai sa hankalinsa a wajen ba. Gara ma jiya ya ce mini ku'din da
mutum zai samu a shekara d'aya kacal ba k'ananu ba ne.
Ina bu'de baki na ce "Idan akwai alheri a cikin samun da za'a yi, Allah ya saukar a
kan filinmu".
Ya ce "Kayya! Amma tunda Allah kika ce ai magana ta k'are. Ameen".
Muka bar magana a hakan.
A wannan tsukun auren su Yaya Ammar da na Yaya Rabiu da su Kaltume ya zo.
Muka shirya muka tafi tare. A can muka tarar da Babah da y'an yayenta. Hamim na
ganina ya cakume ni, ya cukuikuiye hijabina wai bazan gudu na bar shi ba. Hanif
kuwa kawai kwantar da kansa ya yi a jikina. Tijjani ya kalle shi ya ce "Kai ma ka
bi bayan d'anuwan ka, baka ta tawa ko?" Ya kalle shi kawai. Ya yafice shi tare da
ce wa "zo mana Babana".
Ya kuwa isa gare shi ya kwanta. Yayin da Hamim ya rikice sai ya sha nono. Da k'yar
Tijjani ya yane shi suka fice.
Babah ta ce "Ai ban yi zaton darun d'anuwana ya kai haka ba sai yanzu".
Na ce "Ai ba shi da sau'ki Babah. Hanif ya fi sassauci". Ta ce "Babu hadi ma. Allah
ya musu albarka ya tsare su. Ki yawaita yi musu addu'ar tsari da kuma kambun baka".
Cikin na ce "To".
Duk inda na shiga sai an kalle ni. Da na juya baya za a hau zancena. Haka Ikilima
ta jiyo mini gulmar da sa'anina da muka taso tare su Saratu su Maijida. Suna fa'din
",Ai gaba'daya Bulkachuwa tsorona yake ji saboda ina da ku'di. Duk kafafar da nake
yi da burgar kwalliya da yadikan yan gayu na Umm Nihla collection. Ni nake yiwa
kaina ba shi ba ne. Su kuwa sun gode Allah mazajensu ne suke dawainiya da su yadda
Allah ya hukunta. Barin Maijidda da a yanzu suke Kaduna. A dalilin Yaya J ya samu
aiki a kwalejin kimiyya ta kaduna(Kad-poly).
Gaskiya ne duk ta fimu d'aukar ido. Amma kuma ba wai ta fi kowa kwanciyar hankali
ba ne. Ko wacce ita tasan yadda take zaune a gidanta.
Nasiba tuni ta sake dawowa gidanmu gaban Dada. A yanzu da bata da aure ma tafi
walwala da kwanciyar hankali. Tunda yayanta Ammar na kula da ita daidai gwagwado.
Sannan iyayen mijinta suna ri'ke da Muhsin cikin kulawa, Maryam din da take shan
nono ma sukan yi mata aike lokaci zuwa lokaci. Gaba'daya ta murmure ta dawo da
jikinta da ta rasa a baya. Sai daga baya aka gane komai na d'akinta ashe ya siyar
tunda mashayi ne kuma dan caca. Da ace wata a k'ofarmu hakan ta same ta da anyi
yamididin halin d atake ciki. Amma wannan shiru ake ji.
Tallafin da take samu ya sanya take figa take yin y'an sitturu da kayan kwalliya
dan haka fes take bata da makusa.
Na yi tsuka na ce "Basu da abin yi ne, koma a ya ya na ke rayuwa ai babu ruwansu,
tagayyara da ake mana fata kuwa ba zamu shige ta ba in sha Allah."
Amma a tunzure nake kwarai da Maijidda. Na kuma ku'dire indai ta sake ta mini
maganganun banza yadda ta saba yi mini, idan mun hadu a taro, to a wannan karon
zamu sake gwada yar kwanji dan na tuna mata baya.
Ta fitine ni da yawa. Nazira da take gefe ta ce "Sanin kina da daraja ne a wajen
mijinta ya sanya ta washe ki, ban da haka kina matar wani, ta shafa miki lafiya
mana, tunda tasan a musulunci mace bata auren miji biyu. Da a ce Nasiba ce ke, ai
da tuni Maijidda ta kusa zama gawa, domin ba abin da zai hana mijinta fitowa neman
auren ki, tunda har gobe yana son ki".
Da hanzari na ce "Allah suturi bukui. Ai sai yanzu na fahimci tun asali ba wani
sonsa na yi ba, shak'uwa ce da soyayyar k'uruciya. Yanzu da na saba mua'amalantar
barden namiji irin Baban 2, mai zan yi da dan karamin sauron mijinta? Su je can su
k'arata har abada ba zai sake burge ni ba."
Dadi ya kama Adda Nazira ta fashe da dariya ta ce "Ina komawa zan fa'dawa Baban su
Abid tun yanzu Yabi ta fara fa'din madallah da auren Yaya Bulkachuwa".
Kunya ta dan rufar mini na ce "eh ki fa'da masa".
Haka aka yi bikin aka gama lafiya. Baba Maryo da kanta wani gani gani take yi mini
da ban san dalilinsa ba. Ba dama ta ga Babah ta yi mini wani abu sai ta ce "Ba
hakan aka barki ba, da aka tashi kame mata Tijjani har da uwarsa aka ha'da ban da
hakan irin wannan gudun zuciyrta da kike yi har ina? Yara na son zuwa wajen uwarsu
kin kanekane kin rikesu kina fa'din ta je ta yi hidimar jama'a. Ke kuma kin zama
mai raino'.
A lokacin da take fa'din haka ina tsaye, wata irin fargaba ta kama ni, domin na
hango kishina ke cinta ba ka'dan ba. Na laluba ko na yi mata laifi ne, amma ban ga
na yi mata komai ba. Wata'kila zamana lafiya a gidan aurena ne yake mintsinarsu.
Tunda da safen nan ma sai da Baban Tsakiya da na kasuwa suka tambaye ni, wai na
fa'di irin zaman da nake yi, idan babu dama sai a ha'kura ramar da nake yi ta yi
yawa.
A dakin Dada a gaban kuma Babah.
Na kalle su ina mamakin manufarsu. Domin ni dai jefi jefi Tijjani na matsa mini na
kira na gaishe su, ina kuma yi tunda tisa ni yake yi a gaba. Amma su kam tunda na
yi aure ba wanda ya ta'ba kirana ya ji lafiyata, ko ya ji ya ya na ke? Baban Marina
ne kawai yake mini hakan a cikinsu.
Amma abin mamaki sune da fa'din wai na rame tsabar sun saka mini ido suna kuma
adawar sun jimu k'alau ni da Tijjani.
Na bu'de baki cikin nutsuwa na ce "Satin jiya na yaye yara, na yi fama da zazzabi a
dalilin haka. Sannan ni ba ni da matsalar komai ina cikin rufin asiri mai yawa.
Allah ya saka muku da alheri bisa bawa Tijjani aurena da kuka yi. Bana fatan sauyi
ko a aljannah ne".
Baban Kasuwa ya ce "To ya isa zabiya! Mun ji, mun ga ne ba sai kin zarce da rashin
kunyar da kika saba ba."
Baban Tsakiya kuwa ya ce "Na tashi na basu waje sun sallame ni, dama sun nuna
kulawa ne dan sun gane muna zaginsu a bayan idonsu akan basa kula da sha'anin yan
k'ofarmu. Amma zan fara yi musu rashin kunya da iyashege."
Na fito zan shige Babah da take bawa tagwaye koko da kosai.
Suka fashe da kuka wannan karon kukan har da Hanif.
Murya babu amo ta ce "Zo ki zauna, yunwa suke ji".
Na dawo na zauna shi ke nan kuma suka yi shiru. Suka ci gaba da cin abincinsu.
Muna haka Tijjani ya shigo dan haka na sid'ad'a na fice tunda suna ganinsa.
Washagari muka koma, daga ni har Tijjani so muke mu tafi da yaranmu. Tunda sun yi
sati biyu. Amma kowa ya kasa fa'dawa Babah da ta daure fuska bayan ta fahimci take
takenmu.
Sai da zamu tafi ta biyo ni har zaure tana fa'din "Zan dawo muku da su, amma sai
kin warware kin murje. Kina ganin dai yadda ramar ta ki ta janyo cece kuce. Ki
kwantar da hankalinki, nan da wata ma zasu dawo."
Kunya ta kama ni, na shagwabe fuska na cuna baki na ce "Ni fa Babah ban damu da su
ba, su zauna ma gaba'daya a wajen ki, ba ni da matsalar komai".
Ina rufe baki Tijjani ya yi maza ya ce "Bilhiillazi karya take yi miki Babah."
Ta gwale shi da ce wa "ko k'arya take yi, ai ta saya, kai da baka da kunya ai ka
bu'de ka nuna na baku yaranku".
Nan da nan ya yi shiru, ni kuma na yi dariya tare da yi masa gwalo.
Da hakan muka rabu, ta koma cikin gida, mu kuma muka tafi.


✍️.

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered,
Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan
farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon
yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta
sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar
taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi
muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun
san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa,
mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai
soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan
littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan
numbers*
*Tuni labarin ya fara nisa, yana kuma da dadi da darasi*.
*08089965176*
*07084653262*

Da wuri muka shiga Bauchi. Ya taimake ni muka gyara gidan, muka yi girikin abin da
zamu ci.
Dai da yamma ya fita.
Kwanci tashi asarar mai rai, kwanaki suka yi ta shud'ewa har muka samu sati da
dawowa daga Toro.
Daga ni har Tijjani bama jin da'din rashin yaranmu a tare da mu. Kewarsu muke yi
sosai. Amma dukkanmu kowa ya bar abin a ransa, mun bisu da addu'a.
Muna cikin hakan ba zato sai aka kira Tijjani tare da albishir din filinsa kamfanin
sadarwa yake bu'kata. Zasu karbi hayar wajen na shekaru uku. Idan wa'adin ya cika,
wata'kila su siya gaba'daya ma, matu'kar mutane sun karbi sabon kamfanin da hannu
biyu.
Farincikin da muke ciki ba ka'dan ba ne. Mussaman da Tijjani ya tabbatar mini
ku'din ya isa ya sayi gidan da muke ciki da kuma mota golf da ake yin sufuri da
ita.
Cikin Ikon Allah kuwa bayan cike cike, da kai komo suka tura masa ku'dinsa cas ta
asusunsa na banki. Hassada da bak'in-cikin a wajen masu filaye a wajen tamkar su
jefa shi wuta. Hatta Alh Auta bai iya boye ba'kin cikin da ya ji ba.duk da Tijjani
ya bashi kyautar dubu dari a cikin ku'din amma hakan bai sa ya gode ya ha'diye
ba'kin cikinsa ba.
Wani k'aramin gida da yake gabanmu ka'dan, Tijjani ya siya. Sabon gini ne, fenti ne
kawai ba'a yi ba.
Mai gidan ya d'aga gidan xai siyar a dalilin ya samu wnada ya fishi yalea zai siya.
Da yamma muka je na ga gidan.
Karamin guda ne ainun. Sai dai kuma an tsara shinda kyau. Kafin udan an shiga daga
farkon akwai daki mai dauke da band'aki. Wanda tsarinsa yafi dace wa da na
maigidan.
Daga ciki kuwa k'aramin tsakar gida ne, sai falo mai dauke da dakuna biyu, ko wanne
da bandakinsa.
A tsakar gidan akwai kicin da kuma wani band'akin daga gefe.
Gidan ya sake kawatuwa a dalilin an zuba masa tayal ta ko'ina. Ta bayan dakunan
kuma akwai doguwar hanya, bata bille wa, amma dakuna zasu sami iska, sannan za'a
iya daura igiyar shanya a wajen.
Farin ciki ya mamaye ni. Yau ga ni zan yi d'aki mai dauke da band'aki a cikinsa.
Lallai komai lokaci ne.
Ya kalle ni da murmushi ya ce "Ya yi miki?"
Na bu'de baki na ce "sosai ma kuwa Baban 2. Ubangiji ya k'ara arziki, yasa rabo
ne."
Da walwala ya ce "Ameen, tunda ya yi miki bari na je wajen dillalan, mu nemi shaidu
a je a biya".
Na fa'da jikinsa ina jin farin ciki na walagigi da ni. Na dinga jera masa fararen
addu'oin da suke sanya shi farin ciki.
Ba'a dauki lokaci mai yawa ba, ciniki ya fa'da ya yi fentin da ba'a yi ba.
Ya sayi katifa ya saka a d'akinsa.
Dakina kuwa aka shirya kayan gadona bayan an musu kwaskwarima, katifar gadon muka
bari a tsohon gidan kafin mu tare. D'akin yaran kuwa aka saka musu katifarsu da ya
siya musu yun suna jarirai.
Kujera ya canja mini, tawa ta tsufa da yawa, tunda ba mai tsada ba ce dama. Yanzun
ma mai L ce amma mai daraja sosai. Aka makala tibinmu a bango shike nan, domin a
kicin a saka firij tunda da fili.
Gida ya fito ras. Na dan yi siyayyar kayan kicin wanda zan iya. Na sayi kafet da
labule kalar kujerar.
Muka ja gida muka rufe. Da kansa ya je Bulkachuwa ya taho da Babah da yara. Ta zo
ta ga gidan da Ubangiji ya mallakawa Tijjani cikin sau'ki.
Ta dinga hawayen farinciki, tare da addu'ar Ubangiji yasa likkafa ta cigaba. A fili
ta ce "Da ikon Allah sai kun yi arzikin da kowa sai ya ci arzikinsa. Ina da yakinin
Ubangiji ba zai juyar da addu'ar da nake yi muku ba".
A ranar ta tafi, duk yadda muka so ta kwana tare da mu, amma fir ta ki. Ta bar
yara, tare da zolayata wai gasu nan su mini sati biyu, zata turo Nasiru ya dauke
su.
Haka ya je Toro ya sanarwa da iyayenmu alherin da ya samemu, tare da basu Ihisani.
Mota guda suka taho ganin gidan da su Baban Tsakiya nasu gasgata Tijjani ya siya
ba.
Tun wuri ya kawo mini kayan miya da nama ya ce "Ki yi abinci da yawa Asiya. Yau
mutanan Toro sun taho ganin gidanmu. Nasiba ta ce mini har da Dada".
Na dan ji babu da'din yadda ya ce Nasiba ta fa'da masa. To waya suke yi ko kuwa ya
ya?
Na daure na ha'diye ban tuhume shi ba.
Na hau hidimar aikina. Shi kuma ya ri'ke hannun yara suka tafi siyo ruwa da lemo.
Na kammala abincin na yi wanka. Ina cikin shiryawa na ji tsayuwar mota, a gaggauce
na gama shirina.
Na fito ina marabtasu.
Na ri'ke hannun Dada ina yi mata maraba ta mussaman. Tuni su Baban Marina, da Baban
Tsakiya har da Baban kasuwa suka isa falo. Baba Maryo na cikinsu.
Tare da Tijjani muke ta ajiye musu kwanukan abinci da abin sha.
Yadda muke shige da fice muna hidimarsu tare, abin ya yi matu'kar burge Dada da
Baban Marina. Domin sai addu'ar alheri suke bin mu da ita. Su kuwa ragowar wani
irin kallo suke bin mu da shi wanda na rasa gane inda suka dosa. Domin ba wanda ya
taya Dada da Baban Marina albarkar da suke sanya mana.
Sai da suka ci, suka gyatse. Suka je masallaci suka yi azahar. Sannan muka d'unguma
ganin sabon gida.
Dada sai hamdala take yi, yau Ubangiji ya gwada mata ta ga gidan mai sunan manya.
Baba Maryo kuwa da ta shiga falon ta leka ta ga dakuna biyu, ko wanne da bayi a
ciki. Tana bude baki sai ce wa ta yi "Gida kuwa a yalwace. Ban da wuyar zama irin
ta y'ay'an yau. Mace biyu ma sai su yi zamansu wata bata takura wata ba. Tunda
akwai turakar maigidan".
Zuciyata ta yi matu'kar bugawa, domin na fahimci akwai k'ulli a zuciyarta game da
ni, tunda muka je biki na ga tana rawar jiki wajen Babah tare da bagarar da ni,
nasan akwai abin da take nufi da ni.
Maganar da Tijjani ya fa'da mini dazu na ce wa Nasiba ta ce tare da Dada suka taho,
ta sake dawo wa ta rib'anya zullumin da na shiga.
Na daure ban ce komai ba illah yak'e da nake yi. Gaba'daya Dada da Baban Marina ne
suke yin murna ta fisabidillahi a cikinsu. Baban kasuwa da ya bu'de baki sai ce wa
ya yi "To Tijjani gida ya yi kyau. Amma ku shiga a hankalinku, ku dinga jin tsoron
Allah. Harkar nan ta neman maza ta zama ruwan dare a tsakanin matasa. Kada ku bari
manyanku su rude ku su dinga baku kudade kuna b'ata gobenku".
Na kalli Tijjani na ga ya yi kasa da kansa yana fa'din"Da ikon Ubangiji zamu kiyaye
iyakokon Ubangiji."
Zuciyata ta dinga tsallen na mayar masa da martani. Amma idon Baban Marina, da na
Tijjani suka mini cikas. Domin na sani dukkansu baza su mini ta da'di ba, idan na
yi masa rashin kunya a gabansu.
Ban gama jimamin isgilancin Baban kasuwa ba, sai kuwa Baban Tsakiya ya ce "Haka
KUMA a kiyaye cin riba, da shiga kungiyar masu daukar bindiga suna kwace wa jama'a
rayukansu da dukiyoyinsu suna azurta kansu. Wannan zamani da wuya ya ke."
Dada ta ce "Ina addu'a akan duk rintsi kada a jarrabi iyalina da aikata kaba'ira.
Ban san me ya hana Baba Maryo sakin nata bakaken ba. Tunda ita ma bata nufinmu da
alheri.
Shi dai Baban Marina bai ce musu kala kanzil ba. Sai da suka gama. Ya nisa ya ce
"Ubangiji ya yiwa neman ka albarka, ya tsare ka, ya baka arzikin halali mai yawa.
Ubangiji ya saukar da farinciki a kanka da iyalinka. Allah ya tsareku gaba'daya, ya
shirya muku zuri'a."
Na daddage da k'arfi na ce "Ameen Babanmu. Ameen dattijon arziki, uban marayu, har
masu uban ma.."
Baban Marina ya faki idonsu ya galla mini harara. Gane nufinsa ya sanya na ha'diye
sauran maganar da na yi nufin zubarwa.
Baban Tsakiya ya kalle ni cikin fishi ya ce "Shi ka'dai ne Ubanku?'
Da azama na ce "Duk nan ina da uban da ya fika ne Baba? Kai ne ka d'aura mini aure
fa".
Ya furzar da iskar baki ya ce "Na dauka kin manta saboda kina ganin kun fara shigo
wa gari ai"
Kan dole na yi shiru. Ban sake ce wa komai ba. Amma dai kam zuciyata a tunzure take
ainun.
Muna dawowa suka shiga mota suka tafi. Bayan Tijjani ya saka musu kwanduka kayan
miya, ya kuma biya ku'din man da suka zubo a motar.
Kan dole nabi bayansa wajen yi musu godiya da addu'ar sauka lafiya. Dan kuwa ba dan
tsoron Baban Marina ba da iya shi da Dada zan ware na yi musu godiya da fatan su
sauka lafiya.
Tunda abin nasu babu arziki. Ban da fitina daga zuwa ganin abin arziki, babu saka
albarka, babu fatan alheri, babu nasiha mai da'di. Sai mugun k'ulli ya biyo baya.
Har da jinginawa mutum mafi munin zunubi irin luwadi. Kaico ga mutanan da basa
furta alheri. Hasara da tabe wa ga masu hassada da k'yashi. Àllah ka shirye masu
shiryuwa kawai.
Tunda suka tafi Tijjani ya kasa tafiya kasuwa. Kwanciya ya yi har dare, sallah
kawai ke fitar da shi. Na sani kuma maganganunsu ne suke dafa shi. Duk da bai yarda
ya biye ni mun yi zancensu ba.
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA
BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.

Kwananki ka'dan muka tare sabon gidanmu mallakinmu ba wai haya ba.
Cikin dare mun gama mua'amalarmu, mun yi wankanmu a cikin d'akinmu. Munana kwance
ya kankame ni, a kunne ya rad'a mini "little kamar yau kike mini kukan band'aki a
daki kike so. Na ce miki da sannu zan miki, a wanccan lokacin baki gasgata ni ba,
sai kika ce wasikar jaki nake yi. Tun daga waccan rana ban sake yin sujjada ban
ro'ki Ubangiji ya bani damar da zan miki band'aki a cikin d'aki. Sai ga shi a kusa
na samu damar ba tare da zato ko iyawa ta ba."
A hankali na ce "Baban 2 kana da tashin tashina Wallahi".
Ya yi dariya ya ce "Indai ba sharri ne da ni ba ai da sau'ki Maman 2".
Ban gama wartsake wa daga kunyar da ya saka ni a ciki ba. Ya sake baro wata
maganar. Ta hanyar ce wa "Na k'osa ki yi ciki little kada ki fara yi mini borin
idan ban miki ciki ba zaki tafi ki bar ni".
Na kai masa duka a k'irjinsa ina kukan shagwaba tare da fa'din "Bana son irin hakan
da ka ke yi mini Baban 2".
Ya ri'ke ni yana dariya ya ce "Ba gaskiya na fa'da ba? Kin ga twins sun yi wayo,
suna gudunsu ko ina, idan kin samu ciki yanzu babu damuwa, kafin ki haihu sun sake
girma. Na ga kuma Babah so take ta rabamu da su. Idan kina da wani a hannun ki ba
zaki wani damu ba".
Ban ce komai ba. Domin kunya ta yi mini k'awanya.
A wannan tsukun da'din da Baban 2 ya jiyar da mu ba ka'dan ba ne. Domin suturun da
baya samun sukunin yi mini sai da ya mini matsakaita kala biyar. Kusan karamin lefe
ya yi mini. Tunda komai sai da ya siya mini daidai misali. Haka yara ma ya yi musu
siyayyar kayan sawa da kayan wasa.
Cikin nutsuwa muke rayuwa, ina mutunta shi tare da girmama shi. Haka shima yake
kaffa kaffa da ni. Idan ya ga zan rikice masa, zai bar komai ya rarrashe ni, ya
kwantar mini da hankali. Domin budin da ya samu, ya sanya shima ya sabunta
suturunsa, ya sake zama hadadden gaye. Tunda yanzu ne ya cika shekaru talatin.
Ma'ana yana cikin shekarun samartaka da k'arfi. A lokacin ni kuma nake shirin shiga
shekaru ashirin.
Gaba'daya na kwarzabi raina, domin ina ganin zai iya samo zabgegiya ya aura.
Ban ta'ba bu'de baki na yi masa k'orafi ba. Amma a ankare nake matu'ka da gaske.
Ba a jima ba motar da ya siya ta golf ta iso.
Ya zaunar da ni ya fa'da mini zai fara kai kayan miya garuwa ranakun kasuwanni.
Tunda zaman kasuwar yana neman gagarar sa. A dalilin yadda Alh Auta da sauran
wadanda suke ganin ya je ya same su a wajen amma ya kere su. Sun ki fahimtar
Ubangiji ne yake raba arziki a sadda ya so.
Cikin nutsuwa na ce "Wai filin nan naka babba ne da suka karbe shi da ku'di masu
nauyi irin hakan?".
Shima a nutse ya ce "Babba ne ainun. Idan raba shi za'a yi zai yi fuloti uku manya.
Sannan wajen ya yi daraja baya ga hakan a bakin titi wajen yake. Kar kuma ki manta
tsawon shekaru biyu suka biya.
Shiyasa nake son na juya ku'din da ya yi saura mu dinga samun na abinci da sauran
bu'katun yau da kullum.
Yaranmu gaba ka'dan makaranta za'a sasu, boko da Islamiya, kin ga duk hidimar ku'di
ce. Ga yadda kullum rayuwar take sake tsananta. Akwai bu'katar na yi aiki tuk'uru.
Sai na barwa Allah ya taimake ni a inda zan gaza".
A sanyaye na ce "Da ikon Allah na zaka gaza ba Baban 2. Ubangiji ya yiwa kokarinka
albarka. Ya tsare ka da dukkan sharrin masu sharri. Allah ya raba ka da sharrin
karfe da titi."
Ya rungume ni sosai ya ce "Ameen Maman 2. Ina son ki, ina alfahari da ke. Allah ya
barmu tare cikin aminci".
Da rauni na ce "Ameen. Amma kasan ina shiga zullumin kada wata ta zo ta k'wace mini
kai?"
Na fa'da hawaye na ziraro mini. Ya tsananta rik'on da ya yi mini ya tausasa harshe
ya ce "me yasa kika karaya haka Asiya? Ban ji akwai wata mace da zata firgita ki
ai. Ni naki ne, a hannunki na ke. Ki daina damuwa da abin da yake gaibu ne.
Al'kawarin da zan miki d'aya ne. Har abada kin wuce wula'kancina. Kina da alfarmomi
masu yawa da babu wata macen da zata samu irin alfarmomin ki a waje na."
Bai bar ni ba. Sai da na samu nutsuwa. Can kuma ya ke ce da dariya ya ce "Ubangiji
yana ta kama mini Asiyata. Kamar yau take fa'din me zata yi da Basamude irina. Kin
tuna amsar da na baki a ranar?"
Na k'yale shi domin yanzu ya riga da ya lakanci tuno mini abubuwan da suke kunyata
ni.
Bai bar maganar kamar yadda na barta ba sai da ya ce "A lokacin na ce miki akwai
ranar da zaki yi kuka akan son basamuden nan. Sannu a hankali komai na fa'da a
kanki Ubangiji yana zartarwa. Na share ban yarda na tanka shi ba.
Cikin Ikon Allah Tijjani ya fara safarar kai kayan miya kasuwanni daban daban na
cikin jahar Bauchi da makwabtanta irin su Jigawa.
Da wuri yake fita. Ya je ya kai. Idan zai dawo kuma sai ya lodo mutane. Gaba'daya
ya ajiye girman kai, da tunanin yana da kwalin digiri.
Ba'a dauki lokaci mai yawa ba, muka rabu da matsalar babu. Domin sosai yake samun
ku'di

Please Login or Register in order to submit comment