You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon
yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

Ta shiga ba shi ha'kuri, shi kuma ya dinga yi mata sababi. Yana fa'din "Da kam nan
da kwana biyu na yanke zata koma zan ha'da ta Mamarsu ta je ta zauna da ita ko na
sati ne kafin jikinta ya yi k'wari. Amma yanzu na fasa ba zata koma ba. Ki fa'da
masa na ri'ke ta, sai ta haihu tunda ba shi da kunya, ya banbanta, ya nuna uwarsa
ce ka'dai zata yi wa iyalinsa hidima.
Ai kuwa Babah ta dinga ba shi hakuri, ta lallaba ta zame kanta ta bar Tijjani
tsundum cikin maganar.
Ta shigo d'aki ta duba ni. Ta bani leda mai d'auke da soyayyun kaji. Da kuma
soyayyar awara da ta sha yaji mai da'di fal leda (K'ara'i).
Na fahimci duk yadda Babah bata shiga al'amarin Bulkachuwa Amma bata dauki abin da
ya shafe ni da sau'ki ba. Samuwar cikin jikina kuwa sai na fahimci k'arfin soyayyar
da take yi masa. Domin farin cikin da take ciki duk wanda ya rab'e ta sai ya gane
hakan. Kusan kullum sai na amsa k'iran abokan arzik'inta. Suna mini sannu da jiki.
Daga samuwar cikin zuwa yanzu na manta adadin da ta zo duba ni.
A dakin Gwaggo ta shigo ta same ta suka hau cakar juna, tunda k'anwar miji ce.
Gwaggo ta ce "Oh ni Asma'u ina ganin kananci a wajen Hauwa. Kina zazzame wa akan
sha'anin yara. Amma tunda kika ji zaki yi jika sai b'are b'are kike yi da sintiri a
hanya tamkar a kanki za'a fara yin jika".
Ta ce "kya yi kya gama. Y'ay'ana nawa ne suka haihu? Yanzu ina ce duk sa'anin
aurenta sun haihu dama wandanda suka riga ta auren. Duk ba jikokina ba ne?"
Gwaggo ta ce "wace ni na ce ba jikokin ki ba ne. Gani na yi Ummi yar hutun ki ma
baki ta'ba zuwa dubiya idan tana laulayi ba, sai idan haihuwa ta yi. Amma Yabi kin
zo ganin ta, sau ba adadi sabo..".
Ai bata jira saboda me Gwaggo zata ce ba. Ta sunkuci jakarta ta fice tana wani irin
murmushin farin-ciki. Tare da ce wa "sai ki yi da wata ai. Ke da ake ganin shirunki
da hak'urinki, nan kuwa ba'kinki fal zan ce da bita da k'ulli ne".
Washagari ta shiga mota ta juya ba tare da ta ce wa Tijjani komai ba.
Ai kuwa kwanaki biyu ya dinga wata irin zarya a cikin gidanmu ta ban mamaki. Baban
Marina ya share shi.
Rannan da daddare ya murje kunyar sa ya ce "Baba gobe zan zo na d'auki Asiya."
Baban ya gyara zama ya ce "Ai haba?"
Ya yi wani irin tare da sunkuyar da kansa k'asa ya kasa amsawa.
Baba ya numfasa ya ce "Ai k'ure rashin kunyar ka zan yi Tijjani. Wai kai magidanci
kada a ga gazawar ka. Shine ka turo mini uwarka dan ka nuna mini ita ce zata maka
hidima kai tsaye ko?"
Ya yi k'asa da kansa tare da ce wa "Ba haka ba ne Baba".
Ya ce "Ya ya ne? Fada mini ina jin ka".
Tsawon lokaci bai tanka ba.
Baban ya ga ji da shirun sa ya ce "To uwar taka ma da soyayyarka ta rude ta, ta zo
zata mini rashin kunya na fatattake ta, bare kuma kai karamin alhaki. Ai tunda ka
nuna mini da wajena da wajen Hauwa da banbanci, ni kuma zan nuna maka da kai da
Salisu d'aya ne a waje na. Bazan baka Asiya ba sai ta haihu ta yi arba'in".
Ya kalli Baban ya ce "Idan na baka hakuri fa Baba, zaka ha'kura ka bani ita?"
Kai-tsaye ya ce "Bazan hakura ba."
Tijjani ya ce "To ka yi ha'kurin kuskuren da na yi".
Ya ce "To na ha'kura Allah ya yafe mana. Ku daina banbanta iyaye. Dukkanmu d'aya
ne."
Ya ce "To Baba zan kiyaye."
Suka yi shiru.
Can Tijjani ya ce "Baba ko zaka yi hakuri ka janye zancen sai ta haihu, nan gaba a
k'ara wata biyar fa, kafin ma ta haihun".
Ya ce "To na ha'kura Tijjani. Allah ya yi muku albarka. Allah ya k'ara ha'da
zuciyoyinku. Ya kuma hore maka ikon kula da iyalinka". Ya amw.sa da "Ameen Baba".
Washagari da yamma ya zo muka tafi, ni kuma sai fishi nake yi.
Muna isa gida ya rungume ni sosai yana ta sakin ajiyar zuciya.
Ni kuma na sha mur, na kawar da fuskata gefe guda.
Ya ce "Tunda mun dawo ai sai ki huce. Yau kwana uku ko hudu kina mini fishi. Gidan
fa gaba'daya zafi ya yi mini da ba kya nan."
Nan ma ban kula shi ba.
Sai da ya dinga rarrashi da ban baki sannan na bu'de baki na ce "Ai dan ka ga na
damu da kai ne shi ne kake musguna mini ta hanyar ce wa dan baka da abin duniya ne
nake yi maka wani abu. Tunda haka zaka dinga yi mini kawai ka k'yale ni, kowa ya yi
harkarsa".
Ya dinga fa'din "ki yi ha'kuri na daina, dan Allah ki huce haka nan". Ya shafa
cikina da ya fara tasa wa. Ya ce "Ya bebinmu?"
Kawai sai kunya ta kama ni na ture hannunsa na rufe fuskata da hannuwana.
Ya sani a jikinsa ya ce "Asiya ina son ki, ina son kasance wa tare da ke muddin
rai. Jikina ya yi sanyi na kasa ce wa komai. Amma kalaman sun yi matu'kar tasiri a
zuciya da gangar jikina gaba'daya.
Ban samu kaina ba sai da cikin ya shiga wata biyar. A lokacin kuma ya fito sosai
tamkar ba cikin fari ba.
A kan dole nake yin k'unshin, amma sai muka tak'aita iya mutum uku kawai nake yiwa
a rana.
Amma ina yiwa masu son bak'i da tunda shi babu durk'ushe sosai. Sannan ina yin
kitso. Ana kuma siyan lalle.
Dai-dai lokacin kuma Tijjani ya fara zuwa Bauchi cikin kasuwar Muda lawal. Ya samu
Alhaji Auta aminin mahaifinsa tare ma suke kasuwancin. Kawai dai da tafiyar ta yi
nisa sai bai cigaba da bibiyar iyalin marigayin ba. Amma hatta katon fiilin da ya
fito a gadon Tijjani a jere suka siye su. A yanzu hakan ma shima nasan filin yana
nan. Wajen ya rayu, ya yi daraja ainun.
Cikin cire girman kai Tijjani ya yi masa bayanin yana son ya zama cikin yaran
shagon ko da ciccire ribabbun kayan miya ne. Domin ya fahimci idan Yabi ta haihu ba
k'aramin nauyi ne zai sake hawa kansa ba. Ga shi kuma, kullum rayuwar k'ara
tsananta take yi ga talaka.
Da sakin fuska ya karb'e shi ya kuma babshi wani bangaren da zai dinga kula da shi.
Dan haka sai Tijjani ya zama sai bayan kwana uku yake zuwa Toro. Duk sadda zai je
kuma zai je da kayan miya, da kayan abinci.
Sannu a hankali yake bin kasuwar yana kuma yin biyayya.
Amma ba'a dauki lokaci mai yawa ba sai ya fahimci yadda *BAK'AR TA'ADAR* hassada ta
yi katutu a zuciyar jama'a. Mafi yawa yaran shagon sun ha'de masa a dalilin suna
ganin maigidan nasu ya daukake shi. Sannan ba ya yarda a yi aikin ha'inci da shi.
Domin mafi yawa suna satar kayan su siyar ba tare da sum saka ku'din a shagon ba.
Zuwansa sai k'udaden shiga suka karu dan haka Alhaji yake bud'a masa yake yi masa
Ihisani.
A yanzu da ya wadata su da abinci sai ya koma siyan kayan haihuwa. Duk sadda zai
tafi sai ya sayi riguna unisex guda biyu, baya damuwa ko da iri daya ne matu'kar
dai kala ta banbanta su. Da ya tara riguna da yawa sai ya koma sayan ragowan kaya.
Yau ma Sai da ya biya ya siyi setin robar wanka mai sau'kin ku'di. Ya kalli rukunin
masu tsada mother care. Ya ji sun ba shi sha'awa. A fili ya ce "Allah ka hore mini
wata haihuwar na siya wa Asiya irin wadannan".
Ya kara da setin mai na Nycil. Ya tafi ya hau mota. Bayan ya siya mata tarkacen su
fruits dangin mangwaro da su abarba.
Sannu a hankali muke rayuwa, har cikina ya shiga watan haihuwa, zuwa lokacin kuma
ya canja mini gidan, amma shima na rabin shekara ya kama tunda ya fara tunanin mu
koma Bauchi da zama, amma ya ce sai na haihu tukun.
Kowa ya kalle ni sai ya yi maganr girman cikina. Har rinjaya ta yake yi.
Idan ya tafi Bauchi sai Iklima ta dawo gidana. Sai ya dawo sannan ta tafi.
Cikin sa'a haihuwa ta kama ni yana gari, kuma da daddare. Dan haka ya samo abin
hawa, muka tafi, sai da aka karb'e ni, aka bani gado. Sannan ya tafi gida ya fa'da.
Take Baban Marina ya ha'do shi da Mama akan ta zauna da ni.
Har asuba ban haihu ba ina shan azabar duniya. Na yiwa Gwaggo addu'a yafi cikin
carbi. Sai da na gama galabaita sannan aka fahimci bazan iya haihuwa da kaina ba.
Nan da nan aka shirya ni zuwa d'akin tiyata. Amma muna shiga ciwo ya sake tasowa
fiye da ko wanne. Na dinga kururuwa ina salati, tare da fa'din a ce wa "Gwaggo ta
yafe mini."
Likitocin da zasu yi mini aikin suka rufu a kaina. Ai kuwa sai ga haihuwa gadan
gadan. Suka taimaka wajen zaro jinjiri. Yana fito wa ya xika dakin da kuka mai
tsananin gaske tamkar gyare. Na fara maida numfashin wahala da gajiya. Ai sai wani
sabon ciwon ya taso, gaba'daya na rasa karfina. Take kuma likitocin suka tabbatar
ba mabiya ce kawai a cikin ba, akwai sauran halitta.
Na fara kuka domin na tabbatar bazan iya sake haihuwa a yanzu ba. Ina kuka ina
fa'din "Summa sabila yassara".
Daga haka ciwo ya tsananta, na birkice, ga shi na kasa nishi mai tsanani. Da
taimakon Allah da na likitocin na biyun ya iso duniya bayan sun k'ara ni. Wahala
kan wahala na yi kafin na rabu da cikin da na kwashe watanni tara ina tiriri da shi
cikin kalubale kashi kashi.
Ban gama wartsake waccar azabar ba, aka shiga yi mini dinki tamkar k'warya. Duk
yadda aka yi mini allura kashe rad'ad'i sai da na dinga jin ciwon har cikin kaina.
Sai da suka gyaramu sannan aka karbo kayan Bebi a wajen Mama sannan aka fito da mu.
Sai hamdala nake yi a zuciyata. Ina sake girmama sha'anin Ubangiji. Ba a taba ce
mini tagwaye ne a cikina ba.
Na tarar y'anuwa sun zo asibitin da yawa.
Na dan ji da'di domin kaf y'ay'an Babanmu da aka aurar da su. Ba wacce ban ga ni
ba, har Ubaida kuwa. Ko Yaya Indo da bata sake taka gidana tun ranar da aka kai ni
ba, na ganta a wajen. Idona ya cika da k'walla ina ayyana duk yadda shaidan yake
shiga cikin al'amarin zumuncin yau, jini yana da tasiri k'warai da gaske.
Ina ta waige waige domin zuciyata so take ta ga jariraina, so take kuma ta ga uban
y'ay'an.
Amma ban gansu ba gaba'daya.
Na ha'diye na yi shiru na cigaba da kallonsu d'aya bayan d'aya.
Tare da amsa sannun da suke ta faman yi mini.
Na jima kafin barci ya sure ni. Na dai farka na tarar da Babah ta Bulkachuwa zaune
a gefena tare da Mama.
Sannan Inna da Yaya Ummi suna ri'ke da jariran da aka nad'e su da zani iri d'aya.
Dada na gefe tana mulmular goro a bakinta, tana kuma jan tasbaha.
Da suka ga na farka, suka hau fa'din "sannu, sannu Yabi".
Dai-dai lokacin kuma ruwan da ake k'ara mini ya k'are.
Wata jamiar kiwon lafiya ta shigo a daidai ta cire mini, tana mini sannu.
Da walwala ta ce "Mrs Bulkachuwa ina taya ki murnan samun wad'annan kyawawan
jariran. Allah ya rayasu ya baki lafiya".
Na yi shiru su kuma ahalina suka amsa da fa'din "Ameen mun gode".
Ta kalli Mama ta ce "Zo ki ri'ke ta, ki taimaka mini mu zaunar da ita.
Yaranta suna bu'katar nono".
Da dabara suka zaunar da ni. Sai da ta tambayi na ji da'din zaman ko na takura a
gyara ni?"
A hankali na ce "Ya yi".
Dada tana ganin malamar asibitin ta karbi yaron hannun Inna. Ta zabura ta ce
"Dakata dafta".
Kowa ya mayar da hankalinsa kan Dada da ta jawo ledar da ta zo da ita, ta fito da
k'ok'o tare da gorar mirinda da kuma wani ruwan maganin a wata gorar daban.
Ta yun'kura da k'yar tana dunduk'e ta nufo gadon.
Ta kalli jami'ar kiwon lafiyar da take shirin kwantar da jaririri a jikina ta ce
"gafara ka'dan".
Cike da girmamawa ta kauce tana ce wa "Sannu tare da mamakin me zata yi.
Sai dai su yan d'akin sun san me zata yi.
Ta saka k'ok'o a cinyata, ta d'aga rigata. Duk da y'an k'ananun nono gare ni, amma
tunda cikina ya fara girma suka ciko. Yau kuwa da ruwan nono ya zo sai suka yi
girma suka tsaya k'yam tamkar kwakwa.
Karon farko da aka bu'de mini nono a bainar jama'a ban kuma ji nauyi mai yawa ba.
Ta daidaita ta dinga zuba ruwan robar ta kuma saka hannu tana wanke mini su.
Sai kuma ta fara k'ok'arin matsesu tana fa'din sai an cire mataccen nonon da yake
lalata jinjirai kafin a basu su sha. Dukkansu babu wanda ya yi inkarin hakan domin
suma akan wannan Ta'adar suke.
Nan da nan malamar asibitin ta ce "kin wanke Dada ya isa haka".
Ta d'ago ta ce "Yarinya me kike fa'da ne? Kina son ki ce wai dak'ashin za'a bari su
sha?".
Cikin girmama wa ta ce "Eh Dada. Domin alfanunsa mai yawa ne a jikin jariri. Shine
rigakafi na farko da Allah subhanahu wa ta'ala ya fara yiwa dan-adam da shi."
Dada ta bar komai ta kafe ta da manyan idanuwanta ta ce "To sannun ki, amma su
wadannan baza su sha datti ba. Kullum a cikin yiwa Allah da ma'aiki k'arya ku ke.
Allah dai ya shiryeku idan zaku shiryu".

*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA
BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.

Ta sake rank'wafawa da nufin yin abin da ta yi niyya. Ma'aikaciyar ta ce "A a Dada
daure ki yi hakuri. A yanzu Asiya ba a hannunku take ba. Tana hannun gwamnati ne da
kuma hukumar lafiya. Dan haka duk abin da za'a yi mata dole zai kasance k'arkashin
kulawar hukumar asibiti ne. Bijire wa hakan kuma yana iya sawa mu gurfanar da mutum
gaban kuliya. Dan haka ki yi ha'kuri ki bar hukuma ta yi aikinta.
Wannan karon kam a zabure ta ce "ke yarinya kar ki mini iyashege kin ji. Dan Allah
falfala da gudu ki kirawo mini hukumar mu yi arangama domin mutuwa ce ka'dai zata
hana ni matse wa Yabi mataccen nono marar amfani, ba ku da kuke yiwa masu jajayen
kunne bauta ba."
Ta murmusa ka'dan ganin Dada ta kufula da yawa. Ta ce "Dada abin bana b'acin rai ba
ne. Ki Fahimci bayanina. A da an rayu cikin duhun kan cewar nonon farko mai kalar
rawaya matacce ne kuma mai illah. A yanzu da ilimi ya cika duniya masana kimiyya
sun gano d'inbin amfanin da Allah ya ajiye a nonon uwa. Mussaman na awannin farko
da haihuwa. Yana rigakafin ciwon hanta, k'oda, huhu. Yana hana tasirin ciwon
k'yanda da tarin fuka, da shawara. Yana k'arawa jariri kaifin k'wak'walwa, yana
kuma daidaita k'asusuwansu".
Dada ta dauki salati tare da cewa "Ni Binta ina ga ni da sauraron kinaya. To da
kunsan da hakan amma kuka sake k'ak'alo allaurar da ake daukar watanni ana yiwa
yara babu tausayi bare imani da sunan rigakafi ce. Yanzu wanne ne gaskiyar magana
kenan?"
Malamar ta yi murmushi ta ce ko wanne gaskiya ne Dada".
Ta ce "To ku ri'ke gaskiyarku, amma ni ban yarda da ita ba, bare kuma na yi muku
biyayya"
Da walwala ta ce "Shike nan Dada ki ri'ke fahimtarki. Amma tunda har aka kawo Asiya
asibiti to wajibi ne abi ka'idojin hukumar lafiya. Idan ba hakan ba zamu sallame ku
ne. Komai ya biyo baya kuma babu ruwanmu. Kafin haka kuma, zan rubuta tirjiyar da
kuka yi, idan abu marar da'di ya biyo baya ke ce da d'aukar alhakin komai. Domin na
tabbatar za ki ga ni".
Nan da nan Dada ta d'auki salati tare da fashe wa da kuka ta koma gefe tana ce wa
"Yau ko da wa kike tak'ama sai na yi sharia da ke tunda kika ce zan ga ni."
Ita kuwa bata damu ba, da alamu ma dariya Dadan ta bata. Domin sai guntse bakinta
take yi. Ta kuma d'ora mini yaron tana nuna mini yadda zan tallafe shi a duk sadda
zan shayar da su gudun kada su dinga kware wa ko su kasa samun iska.
A lokacin da yaron ya fara tsotso wani irin rad'ad'i ya ratsa ni. Na zabura ta ce
"Sannu".
Na kasa amasawa, kunyar idon su Babah ya hana na yi kwarmato. A daddafe ya sha. Ta
dauke shi, ta dauko d'ayan.
Ya fara sha ke nan Tijjani ya iso da kayayyaki a hannunsa. Ya ci birki ya tsaya
yana kallon yadda take rurrufe ido tana cije wa ga yaro yana sha. Farin cikin Asiya
ta zama uwar y'ay'ansa har biyu tashi guda yana matu'kar saka shi tsumaye.
Amma ganin Dada na kuka ya takaita masa murnar da yake ciki.
Ya ajiye kayan a gefe ya isa kusa da da ita.
Yasa hannu ya ru'ko hannunta da take share hawaye. A tausashe ya ce "Dada kukan me
kike yi haka ne? Ina ce d'azu kika dinga rangwad'a murnar alherin da ya samu a
cikin alhalinki na samun tagwaye?"
Cikin kuka mai yawa ta ce "Ayyah mai sunan manya ai wannan ja'irar yarinya tana
neman mayar mini da murnar tawa ciki. Ba yadda ban yi ba kada ta bawa yaran nan
dattin nono amma sai da ta kafe ta basu suka shanye. Idan an yi sa'a sun rayu, to
tabbas zasu tashi da kukan da baya jin rarrashi ga yawan kumburin ciki, sannan mafi
muni suna iya samun tawaya a hankalinsu". Ta ke ce da kuka mai tsananin gaske.
Fargaba ta shige shi ainun. A ki'dime ya ce "jariran aka yiwa sanadin raunin
k'wak'walwa Dada?"
Ta kad'a masa kai tabbacin eh. Tare da ce wa "Kuma Wallahi tunda ta ce mini zan ga
ni, sai na yi shari'a da ita ko da me take tak'ama kuwa. Ba zata lahanta mini
tattaba kunne, sannan ta bini da mugun k'ulli na kuma ha'kura ba. Ko waye ubanta a
garin Toro da kewaye sai mun je gaban gatan marar gata wato kuliya".
Ya sake ta ya isa gaban su yana leka yadda a ke bawa yaron nono. A gigice ya ce
"Baiwar Allah ya zaki dage sai sun sha abin da zai zame musu illah?"
Ya fara k'ok'arin karb'e yaron.
Babah ta Bulkachuwa ta yi wani irin tari mai kama da kashedi. Nan da nan ya ankara
ya fahimci gargadi ta yi masa.
Ya d'aure ya saki yaron. Ya koma gefe amma zuciyarsa ta dinga wani irin tsalle.
Dada kuma ta sake tsananta kukan tana fa'din "Duk wannan iyakacin da aka nuna mini
akan y'ay'an nan baki ji ciwo ba ashe? Ba ki hana ta ci mutuncin uwarki ba, baki
hana ta nakasa rayuwar y'an mala'ikun Lillahi ba. Shi ya zo zai kwatar mana
yancinmu ni da su shine zaki hana shi?
Eh lallai! To ki je na barwa hukumar asibitin ke, ranar da zamu yi shari'a da su ki
zame musu shaida ki kwaye wa uwarki da jikokinki baya".
Ta juya ta fice tana kuka bilhakki.
Yayin da Babah da Inna da kuma Mama suka bita da nufin lallashi da ban baki a gare
ta.
D'akin ya yi saura daga mu sai Yaya Ummi.
Ya d'auki yaron ya rungume shi tsam tsam. Yana ta tofa masa addu'ar da ta zo
bakinsa. Ya kalle ni ya ce "Sannu Asiya! Ubangiji ya yi miki albarka, ya baki
lafiya, ya baki hakuri da kuma juriyar raino da tarbiya".
Na kalle shi ina jin wata irin soyayyarsa na kekketa ni fiye da ko wanne lokaci.
Wata'kila kuma kasancewar sa uban y'ay'an da nake jin kaunarsu har a cikin b'argona
yana da alak'a da sake jin ninkin soyayyar sa.
Na murmusa na masa ameen a zuciyata.
Ya mik'awa Yaya Ummi wanda yake hannunsa ya karbi d'aya yaron da ya kammala sha
yanzu a hannun malamar.
Cikin nutsuwa ta kalle shi ta ce "Mr Tijjani kada Kaka ta rikita ka." Ta shiga fado
masa muhimmancin fara bawa yaro nonon uwa a farkon awanninsa a duniya. Ta sake ce
wa "Tunda mu musulmai ne mun yi sa'a kuma muna d'abbaka sunnar manzo. Da zarar uwa
ko uba sun tauna dabino sun guntsawa yaronsu a baki bayan sun yi Bismillah. Ba abin
da zai fi dace wa da lafiyarsa illah wannan nono da mutanan jiya suka tafi a
fahimtar ce wa cuta ce. Babban sirrika ne da Ubangiji ya zuba a ciki".
Ya gyada kai cike da gamsuwa. Ya yi mata godiya sosai tare da bata ha'kuri akan
maganganun Dada. Ta murmusa ta ce "Ai babu komai nima kafin na fito sai da muka
haura da tawa kakar. Sai ana yi musu uzziri. Da zarar sun kai shekarun girma irin
haka, sai an sake yin hakuri da sha'aninsu ana mayar da komai zasu ce a matsayin
girma ne. Shi kuwa tsufa ba k'aramin nauyi ne da shi ba. Domin Allah da kansa sai
da ya yi ta jan kunnenmu a cikin kura'aninsa mai girma akan idan iyayenmu suka kai
shekarun girma kada mu fa'da musu munanan kalamai, komai zasu yi mana, kada mu ce
musu uffan, balle a yi sa'insa da su".
Ya sake ce wa "Haka ne. Na gode sosai".

✍️.
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin
register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.

*Masu fitarwa bazance muku komai ba. Kowa ya yi mai kyau kansa.*
*Wacce ta karanta mini labarin nan bata biya ba tabbas ina binta bashi*.
*Masu jiran na kammala su had'a mini document, kada ku yi hakan, na ro'ke ki a
littafaina na baya amma still baku ji ba.*
*Bana son a had'a mini document*
*Bana son a had'a mini document*
*Wacce kuwa ta hada na kai ta k'ara wajen Ubangiji*.

Ta tattara kayanta ta fice ta bamu waje.
Ya matso ya zauna a gefen gadon da nake kai. Ya zuba mini ido tare da ce wa "Sannu
little. Ban zaci zaki iya haihuwa da kanki ba. Mussaman da na ga Ubaida da Nasiba
masu garin jiki sun gaza haihuwar da kansu".
A hankali na ce "Haihuwa ikon Allah ke sawa a yi ta lafiya ban da haka kam da
iyayenmu basu taramu da yawa haka ba".
Ummi da take gefe ta murmusa ta ce "Yabi an je kusa da lahira an dawo."
Ya ce "Ummi ai ni da kaina na tausaya mata, haihuwar yara biyu tashi guda, sannan
ki gansu manya tamkar ba tagwaye ba? Wani ikon Allah bamu yi zaton yan biyu ba ne,
Ubangiji ya boye su ko sikanin din da aka yi bai nuna ba."
"Ikon Allah ya fi ga hakan ai" Yaya Ummi ta fa'da a hankali.
Ya sake kallona ya ce "Asiya kin ga yaran nan kuwa, kina ganin yadda Ubangiji ya
mana kyautar da ba kowa yake yiwa irinta tashi guda ba?"
A hankali na ce "Ai ban gansu ba, ba'a bani na ga ni ba, kunya kuma ta hana ni
na tambaya".
Ya yi hanzarin sake matso wa kusa da ni tare da d'ora mini yaron akan cinya a
hankali. Cikin nutsuwa yake ce wa "kalle shi da kyau Asiyata. Kalli ki ga yadda
suke kama da ni. Kalle shi, ki masa addu'a, ki kuma gode wa Ubangiji bisa d'inbin
baiwar da ya yi mana".
Na zuba wa yaron ido. Ina son ga ne kammannin da Tijjani yake fa'da. Amma na kasa
tantance wa, domin ni kam bana ga ne kammannin jarirai. Na tsananta kallonsa, ina
jin wata irin nutsuwa da kaunar yaron na shigata sannu a hankali. Na saka hannu ina
duba yatsun hannunsa da na tabbatar irin nawa ne.
A hankali Tijjani ya ce "Yusuf ke nan (Baban Bulkachuwa) ki masa addu'a, shi ne
babban".
A fili na furta "Allah ya raya shi, ya saka shi cikin bayinsa da yake sonsu. Allah
ya masa kyakkawar rayuwa. Allah ya bashi basira da azanci, ya saukaka al'amarinsa,
ya kuma ba shi kyakkawan rabo a lahira".
"Ameen ameen" Tijjani yake fa'da cikin wani irin yanayi.
Da azama ya ce "Ummilolo kawo shi, shi ma ya samu tabararakin addu'ar uwa."
Ya dauke wanda ya kira da Yusuf. Yaya Ummi ta d'ora mini na hannunta ta koma gefe.
Ya gyara rikon na hannunsa ya ce "Kin ga yadda suke kama da juna ko? Tagwaye ne
masu kama da juna kwabo da kwabo(Identical twins)".
Na gasgata shi, domin ni kaina idan aka jere mini su bazan iya banbanta su ba a
yanzu.
Na zuba masa ido tamkar yadda na yiwa d'anuwan sa. A hankali Tijjani ya ce
"Muhammad Sani ne wannan(Baban Marina)."
Haka kawai na ji tausayi yaron ya shige ni. Kaunar sa ta shiga mamayata.
Cikin rauni na ce "Allah ya raya shi, ya sanya shi cikin bayinsa da yake kar'ba
daga garesu. Allah ya saukaka al'amarinsa, ya kimsa masa ilimi da azancin sarrafa
harshe.

Please Login or Register in order to submit comment