You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

takura
tsabar takaicinsa da yake dafa ni.
Ya zauna a kasa kusa da ni. Ya ce "Barka da gida Asiya Toro".
Na kasa bu'de baki na ce masa uffan.
Domin yadda zuciyata take tafasa sai na ji tamkar na yi ta k'unduma masa ashariya.
Yasa dukkan hannunsa ya ru'ko ni yana fa'din "Ba kya gajiya da kuka ne Asiyata?"
Ai kuwa ba zato na fara kai masa duka a ko'ina. Ya dinga fa'din"ki yi a hankali
kada siraran hannuwan ki su ji ciwo."
Na bar dukan domin tabbas hannuwana ne suke mini zafi tunda jikinsa a murd'e yake
k'warai da gaske.
Kawai sai na fashe da kuka tare da ce wa "Sai Allah ya bi mini hakkina da ka keta a
gaban jama'a. Baka da buri irin ace an kai k'arata gaban iyayena. Ka je na barka da
Allah ya bi mini kadin zaluncin da kake yi mini. Ban da ka mayar da ni banza ka yi
mini hakan? Bayan kwanaki akan idona ka saka aka yi maka girki. Idan tak'amar kicin
da kayan abincin naka ne. To kwanukan da tukwanen fa? Ai da sai ka siyo ka kawo
mata, ko ta debo na uwarta."
Da sauri ya ce "Amma Dada ai ta kashe wannan maganar. Na baki hakuri kuma."
Na ja tsaki mai tsananin gaske tare da ce wa "Ri'ke ha'kurin ka bana so. Tunda ka
nuna ba ni da iko a cikin gidan da ake ce wa wai nawa ne, sai ka fa'da mini inda
zan dinga zama da jama'ata, tunda ka sani a gidan ubana ma ina da inda aka ware
mini nake zama na yi sana'ata."
Ya koma gefe ya ce "Gidan ki ne ba wai ba ne".
Da rawar murya na ce "Wallahi ba nawa ba ne. Domin da nawa ne ba zaka tozarta ni
irin haka akan d'aki ba."
Ya nisa ya ce "Tsakanin ki da Allah sau nawa ina gargadinki akan dakin? Ai ba
sana'a na hana ki ba. Dakin ne ba zai yiwu ace mata suna shigar mini ba. Tunda dai
shine dakina zan yi iyakacin kokarina na ba shi kariya irin yadda ake bawa dakin
mijin da yake da daraja.
Ki zo ki yi anan dakin, ko a falo ba ni da matsala da hakan. Amma wancan dakin baki
isa ba, ba ki biyo hanyar da zai zama k'arkashin ikon ki ba Asiya".
Na ji tamkar na sharara masa mari. Amma da na tuna maganganun Hajiya. Da alwashin
da ta yi na zata fa'da wa su Gwaggo halin da nake ciki. Ya sanya na ha'diye dukkan
fishina na ce "Ai shike nan".
Ya mik'o mini ledar awara tare da ce wa "Ga shi na san baki ci abinci ba.".
Ban kula shi ba. Ya mike ya ce "Sai da safe, yau na gaji likis."
Kwana na yi, ina nadamar yadda zan dawo da Tijjani dakin nan alhalin bai nuna yana
son ya dawo ba".
Washagari bayan na idar da sallah barci me nauyi na yi. Sai wajen goma saura na
farka. Na tashi na ga ya ajiye mini burodi. Na ga kuma kusan duk kayansa har wanda
ban ga ya sa ba, ya wanke su, ya shanya su a igiya reras.
Ashe fitar da yake yi da asuba aiki ya samu a gidan burodi. Kullum ya je suka yi
aikin kwabi da d'aure wa. Za'a bashi babban burodi d'aya da donot guda hudu, da
ku'di dubu da dari biyar.
Idan ya dawo kuma ya huta sai ya fita gurin aikin saka tiles ko na gyaran setlite
ko had'awa. Duk abin da ya samu a ranar zai yi. Na burodin ne sau hudu a sati.
Dan haka baya rasa yan k'udade hidimar yau da kullum tunda ya k'i jikinsa. Mafi
yawa kullum sai ya shigo da taliya daya ko macaroni. Wani lokacin kuma magi rabin
leda sai da na ga robar maggin ta sake cika duk da bamu cinye kayan abincin namu
ba.
Da na yi tsam sai na fahimci baya son kayan abincin su k'are ne.
Shi yasa kullum sai ya siyo wani abu ya ajiye akan kayan abincin, duk da har yanzu
girkinmu ba kankama ya yi ba, sai na ga dama nake dafa wa.
Jiya da garin rogo ya shigo rabin kwano. Ban ce masa komai ba, da na ga ni. Amma
har zuciyata na fara gamsuwa Tijjani ba zai bar ni da hidimar gidansa ba, kamar
yadda ake hasashe. Sai dai bazan yi saurin shaidar hakan ba sai nan gaba.
Shiru bai dawo ba, yan k'unshi suka zo. Na rasa yadda zan yi, rana ta take barandar
ba zata zaunu ba tunda inuwa bata zo wajen ba. Ni kuma ina k'yashin yi a falona.
Na kasa samun mafita. Kan dole na ce musu "Ba ni da lafiya bazan iya yi ba.
Suka tafi suna mini fatan samun lafiya, tunda sun san ni, sun ga kuma ramar da na
yi.
Suna fita yana shigo wa da alamu sun yi kicibus ma.
Na kalle shi na dauke kai. Ya zuba mini ido ya ce "Sai yaushe zaki fara yi mini
oyoyo da barka da dawowa ne?"
Na gatsina fuska na ce "Eh ai ka yi mini sallama da zaka fice, bare ka saka ran zan
yi maka sannu idan ka dawo".
Ya girgiza kai ya ce "kullum fa sai na yi miki sallama Asiya. Yau ma sai da na leko
na ga barcin na ki ya yi nauyi. Ni kuma wai kada na katse miki shi yasa na fita.
Amma ki yi ha'kuri".
Na dauke kai na ce "To".
Ya mik'o mini leda tare da ce wa "Ungo nasan ki da son gurjiya, ganin ta na yi
manya manya da ita. Shine na siyo, na taho na kawo miki".
Na kar'ba a hankali na ce "Na gode". Karon farko da na yaba masa har na yi godiya.
Da'di ya kama shi ya ce "Nima na gode miki. Ko na zauna na bare miki ne?"
Tausayinsa ya kama ni wanda nake kasa gane dalilin raunin da yake kama ni akan
sha'aninsa. A hankali na ce "Na hutar da kai"
Dadi ya sake kama shi, walwalarsa ta karu. Ya zauna kusa da ni ya ce "Fa'da mini
sunan turare mai k'amshi, kuma mai sau'kin ku'di."
Kamar bazan kula shi ba. Sai kuma na bu'de baki na ce Dagmar".
Ya zuba mini ido sosai sannan ya ce "Na tsani turaren nan, duk yadda yake da dadi
mai nutsar da zuciya Asiya. Ya mike ya girgiza kai ya ce "Na gode da wula'kanci! Ai
na sha ganin kwalin turaren a dakin Jabir. Shine kike son nima na saka saboda ki
dinga jin kamshinsa a tare da ni?"
Ba'kin cikin da yake zuciyarsa ya kasa boyuwa. Ya juya ya bar gidan gaba'daya.
Kafin na tashi, sai ga shi ya dawo ya kwashe kayansa ya shiga da su dakin ba tare
da ya tsaya ninke wa ba.
Ya fito a hanzarce ya fice tamkar kububuwa.
Abin mamaki sai na ji babu da'di. Yadda idonsa ya canja launi duk sai na damu
ainun.
Ga shi ban roke ki shi ya bar ni na dinga zama a dakin da yake yi mini tijara a
kansa ba.
Na tashi na shiga d'akin. Na ga ya zube su akan tabarmar da take shinfide a k'asa.
Kamar na ninke sai kuma na fasa.
Na janyo na rufe masa.
Da yamma sai ga shi ya dawo da cakwal da gawayinsa a leda. A tsakar gidan ya yi
shimfida. Ya fita ban san inda ya samo rushi ba. Na ga dai ya zo ya zuba gawayi
akai.
Tunda ya fara gugar nan bai tashi ba, sai da ya kammala tsab.
Ya kalle ni ya ce "kin dafa abincin, ko baki yi ba?"
Ba walwala na ce "Na dafa". Ya ce "To a dan bani".
Ya fa'da fuskarsa a tamke.
Na tashi na zubo masa, na rufe sannan na kawo. A wajen ya ci. Sannan ya kwashe
kayansa ya yi dakinsa da su.
Zuciyata ta yi nauyi tabbacin da gaske ba zai bar mini dakin ba.
Ya fito, ya shiga wanka. Ina zaune a barandar ya fito cikin farar shaddarsa wani
irin kamshi sai dukan hancina yake yi. Kamshin da ban ta'ba jin irinsa ba, mai
matu'kar da'di.
Ya yi kyau tamkar wani hamshakin attajiri.
Zuciyata ta buga da irin haduwarsa, ya taje sumar kan nasa da take cike. Gashi bai
sanya hula ba. Shaddar ta gogu.
Kuma babu dying tunda ya sake waccar mai cibiri cibiri lokacin bikinmu, bai sake
b'ata ta ba. Ya dai tara amma babu rini ko murde wa.
Na kasa gane me nake ji. Na gan shi a yadda nake son ganinsa.
Bai wani tsaya ba ya ce "Sai na dawo ya fice da alama masallaci za shi.
Amma ga mamakina bai dawo ba sai da tara ta gota.
Sannan da ya shigo ina jinsa da Rafia a zaure da alamu ita ma unguwa ta je a
lokacin ta dawo. Da k'arfi ta ce "Ka gaida amarya kwana biyu bana zama ne shi yasa
ban shigo ba".
Ban ji me ya ce mata, tunda bai daga tasa muryar ba.
Wani irin abu mai tsananin gaske ya tokare ni. Shaidan ya shiga zuciyata ya ayyana
mini tare suka dawo. Shashanci suka je suka yi abunsu.
Hawaye ya b'alle mini. Ya tarar da ni ina matsar k'walla.
A rikice ya zauna kusa da ni ya ru'ko ni.
Na fizge cikin kuka sosai na ce "Ka je kun gama iskancin kun dawo shine zaka ri'ke
ni?"
Ya zauna ya ri'ke kansa. Ya kasa ce wa komai. Amma ba k'aramin kidima ya shiga ba.



*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA
BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.
✍️

*BAKAR TA'ADA*

*47&48*


*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered,
Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan
farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon
yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.


*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin
register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*

Tsawon lokaci ina kuka shi kuma ya kasa ce wa komai. Da k'yar ya nisa ya ce "Asiya
Toro son ki ya zame mini jarabta mai girma. Daga ranar da aka ambata mini za'a bani
ke daga ranar ban sake samun y'ancin zuciyata akan lamarin ki ba. Me yasa zaki yi
mini irin wannan mummunan zaton?"
Ya fa'da cikin b'acin rai matsananci dan har wani haki yake yi.
Na cigaba da kuka ban kula shi ba.
Ya damk'e ni sosai cikin tsawa ya ce "Ina miki kallon yarinya k'arama kina mini
kallon biri boko.
Gaba'daya shekarun ki nawa ne a duniya. Ina tausayin k'ank'antar ki, amma ke abin
da kika sani ya zarce na manyan y'anmata masu shekaru ashirin da biyar.
Kin ture dukkan ka'idojin shari'a, kina ta musguna mini. Babu ragayya a tsakaninmu.
Ai ko ban ci darajar aure ba ya kamata na ci na jini. Wallahi na yi zaton ko wani
kika ji ya jefe ni da wannan al'amarin sai inda k'arfin ki ya k'are. Amma har da
ke a cikin jerin wadanda suke mini yarfe dan na tozarta na yi ba'kin ciki.!
Ya numfasa yana maida numfashi tamkar mai mura.
Jikina sai bari yake yi a dalilin na shiga zullumin irin damk'e ni da ya yi.
Nasan dalilin da ya sanya kike iya kallon idona kike jingina mini wannan Bak'ar
TA'ADA. Saboda ban nemi hakkina ba.
Ashe tunda ke ba yarinya ba ce kamar yadda nake miki kallo kuskure na yi, da na
dauke kai.
Tunda kin san kishi kin kuma iya har a kaina da ba sona kike yi ba shike nan,
magana ta k'are zan d'ora miki girman da zai sanya ki dinga jin nauyin fa'da mini
duk abin da ya zo bakin ki."
Na yi muk'us ban da b'ari ba abin da jikina yake yi.
Ya sake ni, ya fita. Ai ina ganin ya fita, na zabura na rufe k'ofar da sakata.
Na yi shiru ina ta zare ido domin har lokacin zuciya ta bugawa take yi da tsananin
gaske.
Can na ji yana kwankwasa k'ofar. Na yi bakam a zuwan barci nake yi.
Bai tsananta ba, ya juya ya tafi.
Da asuba ban yarda na fita ba duk yadda fitsari ya matse ni, sai da na ji fitarsa
masallaci sannan na yarda na bu'de k'ofar.
Har ya je gidan burodi ya dawo barci bai dauke ni ba.
Kamar daga sama na ji muryar Baban Marina a tsakar gidan.
Zuciyata ta tsinke sosai. Gumi ya dinga yanko mini. Gaba'daya na tsorata na
tabbatar Tijjani ne ya kai k'arata.
A sanyaye na bu'de k'ofar, na taya Tijjani marabtarsa.
A falo muka sauke shi. Ya amsa gaisuwa ta da walwala na d'an samu kuzari. Domin na
lura babu bacin rai a tare da shi.
Ganin hakan ya k'arfafa mini guiwa na mike na bu'de firij na d'auko ragowan k'wai
uku da ya ragu.
Na soya masa a gurguje tunda nasan da burodi.
Kafin na gama shirya kofina a tray har shayin ya kusa juyawa.
Na dauka na kai gaban Baban.
Ina dawowa kuwa shayin har ya tafaso na juye a flask na kai masa.
Cikin soyayyar da na kwana biyu ban ga ni ba a dalilin fishin da ya yi da ni akan
auren Tijjani.
Ya ce "Sannu Yabi. Allah ya yi miki albarka. Na ji da'din yadda na tarar da ku,
kuna cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Allah ya dauwamar da aurenku, ya baibayeku
da albarka ta inda kuka zata da ta inda baku zata ba. Wanzuwar aurenku na cikin
burina a wannan duniyar. Ki zauna lafiya, ki yi ha'kuri da kawaici irin na uwarki."
Kaina na k'asa amma hawaye nake yi. Tabbas idan da Tijjani zai bu'de baki ya yi
masa bayanin yadda muke zaune da bai yi wannan farin-cikin ba. Da bai sanya mini
albarka irin hakan ba.
Tijjani ya ha'da masa shayi ya ce "Bismillah Baba ka ci abincin Asiya".
Da murmushi ya ce "Na riga da na karya, amma tunda Ubangiji ya nufe ni da zuwa
gidanku zan ci abin da kuka ba ni. Ina fatan Ubangiji ya buda maka k'ofofin ciyar
da iyali cikin sau'ki Tijjani".
Nan da nan ya masa da "Ameen Baba".
Yana kurb'an shayin Tijjani na yankar biredin yana cusa masa k'wai a ciki, yana
mik'a masa.
Ba wani sosai ya ci ba. Amma ya shanye shayin. Ya yi hamdala ya ci gaba da sanya
albarka cikin marari.
Ya ce "Tijjani ina fatan dai lafiya kuke zaune babu damuwa?"
Jikina ya d'auki rawa.
Amma ga mamakina sai ya ce "Lafiya k'alau muke zaune Baba. Ai Asiya har bayan
idonka tana kiyaye tare da girmama umarninka".
Da'di ya k'ara kama shi. Ya ce "Alhamdulillah! Allah ka so Asiya, ka sanya
soyayyarta da tausayinta a zuciyar mijinta. Shi kuma ka bashi lafiya da jarumta da
arziki mai gudana. Àllah ka zaunar da su lafiya, ka basu zuri'a dayyiba."
Daga haka ya mik'e ya gyara rigarsa ya ce "Nurun ala nurun a dukkan rayuwar da zaku
yi".
Tijjani ya bishi suka fita, yayin da na bisu Ina fa'din "A gaida mutanan gidan,
Allah ya k'ara lafiya mun gode".
K'aran mashin din Tijjani ya tabbatar mini ya tafi mayar da shi ne.
Bai dawo ba sai wajen k'arfe d'aya da rabi na tabbatar kuma sai da ya yi sallah.
Kai tsaye wanka ya yi, ya sanya jallabiya ya shigo falon, k'amshin turaren da ya
tsiri sawa ya bugi hancina.
Ya zauna. Na yi kokarin kyautata fuskata na ce "Sannu da dawo wa."
Ya kalle ni ya ga na yi kwalliya cikin wani fitinan material.
*Wanda Umm Nihla mazauniyar Malaysia take odarsu.*
Tuntube ta akan wannan lambar ta *manhajar Whatsapp dan ganin JERIN gwanon
yadinanta da basa kode wa ko jeme wa.*07020695644*

Ya ce "Wow Asiya kin yi kyau tamkar yar tsana. Na murmusa na ce "Na gode".
Ya numfasa ya ce "Wannan sannun ta ki nasan kin yi saboda rufin asirin da na yi
miki ne".
Na cuna baki na ce "Yo kai ma ai na rufa maka naka asirin ai".
Ya matso kusa da ni ya ce "Fa'da mini rufin asirin da kika yi mini, ni da kin
fallasa da ba hakan ba".
Na dauke kai ina hura hanci irin na ta'bara da shagwaba.
Ya sake susucewa ya ce "Saboda Allah me zaki ce masa ina yi miki na musguna wa?"
Cikin yanayin tab'ara na ce "Abubuwa masu yawa, yo ni abubuwan da ka yi mini ban da
dai ni din mai hankali ce, da tuni ba'a yi b'atacciya ba".

*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a
kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu,
nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*

Ya maze ya ce "Ni nasan hankalin ki yawa ne da shi ai".
Na sake ce wa "Ban da dai ina tsoron fishin Baba ai da tun ranar da ka sanya aka
shigar mini kicin da tun ranar zan bar maka gidan, ita sai ta zauna kawai a
madadina".
Da sauri ya bar kan kujerar ya gurfana a gabana, ya ru'ko dukkan hannuwana ya
sassauta murya ya ce "Asiya" cikin wani irin yanayi.
Na kasa amsa wa, karon farko da ya ri'ke ni ban fizge ba. Domin gaba'daya
maganganun Baba ya dagargaza ni, ya fahimtar da ni zama da Tijjani tilas ne.
Zamana lafiya a gidan aurena yana nufin farin-cikin mahaifina na tabbatar Gwaggo ma
ba zata so ta gan ni a gabanta da sunan mutuwar aure ba.
Na zum'bura baki na ce "Uum".
Ya yi kasa da murya ya ce "kalle ni".
Na sake juyar da fuskata ba tare da na kalle shi ba.
Da wata irin murya ya ce "Pls mana Asiya Toro".
Na zakuda da sauri, na fara kokarin cire hannuna a nasa. Ina ce wa "Ai dai kasan
bana son gatsa mini sunana da kake yi."
Da azama ya ce "Indai zaki daina yi mini rashin kunya ai daga yanzu na daina fa'da
miki. Kwanaki kin ce mini bana goge kaya, bana saka turare. Yanzu na fara yi dan
kisan ba abin da bazan yi dan na samu aminci da nutsuwar ki ba. Amma ko ki nuna kin
gane na canja, balle ki yaba mini na ji dadi".
Na bata rai na ce "Akan me zan yaba? Bayan ba dan ni ka yi ba. Ina ce jiyan da ka
fita sai da dare ya raba kana zan ce, idan ta yaba maka ai shike nan"
Ya kame baki ya ce "Tabdi jam!
Ya bar maganar ya canja da ce wa "Yanzu zan sake ba ki hakuri, ki manta maganar
shiga kicin din ki. Na yarda na yi kuskure, dan Allah ki shafe ta a zuciyar ki.
Nima na yafe miki zargina da kika yi jiya. Kin ga dai murna da addu'ar da Baban
Marina ya yi. Kamata ya yi mu ha'da kanmu mu zauna lafiya".
Na bata rai na ce "To ai kai abin haushin ka yawa ne da shi Tijjani. Bana son na ga
namiji ya cika kule kulen mata, kai kuma kana tafiya a mashin ma kana iya tsayawa
ka yiwa mata magana ko baka sansu ba".
Ya sake ru'ko hannuna sosai ya ce "Billahillazi a da ne Asiya. Tunda muka yi aure
bana yi, na rantse miki da Allah. Mussaman da kika ce mini mai kamun kai kike so,
sai na sake kame wa sosai".
Na yi shiru ya ce "shike nan komai ya wuce zamu zauna lafiya, zaki yarda na zama
mijin gaske ba na wai ba?"
Na ce "Sai ka yarda wanccan dakin ya zama zan yi yadda nake so a cikinsa".
Ya ce "Kin san ban iya yaudara ba. Idan kin yarda na zama mijinki na sosai, ai
gaba'daya ma ya zama naki, to me zan yi da shi?"
Na ce "Ban gane ba?"
Ya jima yana kallona har sai da jikina ya amsa sannan murya a dashe tabbacin ya
shiga cikin shauki sosai.
Ya ce "Idan dakinki ya zama shine nawa, kayana sun koma ciki, kin adanasu tamkar
yadda kika adana na ki, sannan a ciki zan dinga kwana, a ciki zan yi komai. Shike
nan dakin ya zama na lallen ki da duk bak'on kwana da zamu yi".
Gabana ya yanke ya fa'di tamkar yanzu na fara jin ya kamata ya dawo dakina".
Na yi k'asa da kaina na kasa ce wa komai.
Ya marairaice fuska ya ce "Ki ce to Asiya, na matsu ki zama matar aure ta sosai, na
k'osa ki zama babba."
Kunya ta kama ni, na rasa yadda zan yi, sai kawai na fara kananun kukan shagwaba
tare da ce wa "Ai yanzun ban girma ba kake nufi?"
Da sauri ya ce "kin girma mana, shi yasa nake son na sake mayar da ke babba sosai".
Na sunkuyar da kai na k'asa domin kunya ce ta sosai ta yi mini k'awanya.
Ya dinga murza mini tafin hannuna wanda hakan ba k'aramin abu ya haifar mini a
gangar jikina ba.
Haka shima gaba'daya ya yi sanyi ido ya canja.
Kunya ta sake kama ni. Kan dole sai da ya sake wanka kafin ya tafi sallar la'asar.
Nima dai abin da na gani na kasa gane wanka zan yi ko tsarki. Dan haka sai na yi
wankan gudun kokwanto.
Na dinga mamakin lokacin da muka cinye bamu nemi ko abinci ba.
Na shiga kicin na dauko plask din abincin wanda jallof din shinkafa ne.
Na koma na dauko plates da cokula.
Ya dawo ya tarar da abinci. Ya ce "Kamata ya yi muci a plate daya Asiya".
Ga mamakinsa sai ya ji na ce "To."
Na zuba mana, muna ci yana yi mini hira kala kala.
Muna gamawa ya kalli agogo ya ce kwaso kayan ki na wanke miki".
Na girgiza kai na ce "Bar shi zan wanke da kaina".
Ya mike ya na ce wa "Bari na debo da kaina.
Kan dole na bar masa wankin nan ya yi, ina baranda yana ta faman zuba mini hira. Ni
kuma na kasa tanka masa, sai dai eh ko a a.
Da daddare yana tafiya sallar isha na rufe k'ofata. Da ya dawo ya ga na rufe. A
hankali ya dinga buga mini tare da kiran sunana, amma na kasa bu'de masa. Wata irin
fargaba ta dinga ratsa ni. Kan dole ya hakura ya bar ni.
Da safe da na fito ya amsa sallamar da na yi masa, kansa na kan doguwar rigata da
yake goge wa.
Tausayinsa ya tsirga mini, duk yadda na rufe masa k'ofa, kuma ban yarda na bu'de
masa ba, bai sanya ya fasa goge mini kayana ba.
Gasu nan birjik a gabansa da alamu ya jima yana yi. Tunda rigar da yake kan yi ne
ta k'arshe. Sai da na yo brush na ce masa "Ina kwana?".
Ya amsa babu yabo babu fallasa"
Da ya gama zai fita na ce "Zaka dawo ne da rana?"
Ya girgiza kai tare da ce wa "To me zan dawo na yi?"
Na yi shiru sai na ce "To idan an zo k'unshi zamu shiga d'akin, kada ka zo ka dizga
ni."
Ya girgiza kai alamun bai yarda ba.
Ya bu'de baki ya ce "Ban yarda ba. Kada ki fara, idan kuma kin ki ji, to ki
tabbatar zaki ga abin da baza ki so ba".
Na Kwakkabe fuska tare da fa'din "Amma dai kai ne ka ce zai koma nawa".
"Na fa'da tabbas. Amma ai na fa'di sharadina. Baki yi abin da na ce ba, dan haka
kada ki sake ki kai mini mutane d'aki".
Daga hakan ya fita. Ina gama abun da zan yi. Na fara tunanin yau laraba, zan samu
masu kunshi sosai har zuwa gobe. Ina matu'kar son sana'a ta, ina samun nisha'di da
walwala a cikinta. Sannan ina son na dinga aika wa iyayena wani abu. Idan bana
sana'a kuma bazan samu wannan alherin ba.
Na tabbatar kuwa matu'kar da kayan Tijjani a dakin da nake son ya zama na zaman
sana'ata, to kuwa da sannu zai kore mini jama'a.
Na zabura na shiga dakin na dauko jakar kayansa. Na kai ta d'akina. Na sake dauko
kwalin makorinin da ya zuba takalmansa a ciki.
Na fito da shi tsakar gida na bu'de. Kafa hudu ne da alamu biyu a lokacin aurenmu
ya siyesu tunda sabbi ne.
Na goge su na kai su daki.
Jallabiya da tawul din da suke rataye, na fito da su na shanya tunda da danshin
ruwan wanka a tare da su.
Bargo da filon kawai na ninke na barsu gefe daya.
Na dauko kaskon turaren wuta da yake ci a dakina na saka na sakayo k'ofar.
Cikin sauri na d'ora shinkafa da wake.
Na kammala na ji almajiri yana bara.
Na kira shi na bashi naira dari ya siyo mini salak da kokomba, domin kayan ganye
sau'ki ne da su a Toro tunda muna kusa da Jos.
Nan da nan ya siyo mini, na bashi guntun burodin jiya.
Ina tsaye na yanka na wanke na rufe shi.
Na ha'da kwanukan da na bata na wanke.
Na shiga wanka. Na shirya cikin doguwar riga cotton mai gajeran hannu.
Na saka

Please Login or Register in order to submit comment