You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

"Allah ya baki ha?uri, a cewa likita ya zo ya sallame ni, saboda ayi ta ?are a yau"

Mummy ba wanda ta kula sai mahmud, suma ba su kulata ba.

"Mahmud ina ka kai Jamil ne? Kana a wannan yanayin zaka je wani wuri? Ka sa matar nan ta tayar wa da mutane hankali, sai bala'i take yi. Ta shafa mini kashin kaji, wai ni na saka ka dake shi ka kulle shi. Ga wani zancen ma wai ko an kama Jamil gaske ne ko ?arya oho"

Ammi ta ce "Kenan maganar ruma gaskiya ce"

"Ba da ke nake ba, da Wana nake malama" Mummy ta yi maganar gatse-gatse ga giwa.

Ammi ta ce "Allah ya baki ha?uri"

***
Katafaren falon ya cika ga Wambai, ga turaki da wasu manya daga masarautar kano.
Ammi ta hallara, ga Mahmud dan ko gama warwarewa bai yi ba. Aka jima sai ga rumaisa da takawa, Bashir jami'an tsaro da wasu daga cikin yayyen rumaisa, ga Samha a wurin da mahaifiyar ta, ga Hajiya Lubabatu da duk wanda yakamata su halarci zaman.

Gaban Samha sai dukan uku-uku yake yi, dan bata san mai rumaisan za ta kwatsa ba.

Wambai ya ce "Su kuma waWan nan lafiya?" Yayi maganar yana nuna jami'an tsaro, da suka shigo da jabir, a wahale.

Bashir ya ce "Ranka ya daWe, zuwanmu wannan zaman yana da matu?ar muhimmanci, zaka ji dalilin zuwanmu in sha Allah. Zuwanmu nan ayi tattaunawar da mu, sai ya fi sirri, saboda wasu abubuwan da za a bayyana, akwai kunya ace wasu laifukan daga gidan girma da daraja suka fito"

Adam ya ce "Allah ya taimake ka, wannan ita ce rumaisa matata kamar yadda ka sani, waWan nan kuma ?an uwanta ne, wannan kuma abokan aikina ne"

Wambai ya kalli rumaisa ya ce "Ke! Ke ce mai haddasa mana husuma da tashin hankali a cikin family ko? Kafin ki zo lafiya lau mu ke zaune, amma daga zuwanki kin hargitsa komai, ki ce wancan yana asiri, ki ce wannan baya son wannan saboda me?" Ya fara yi wa ruma faWa, tayi shiru ta sunkuyar da kai.

Turaki ya ce "Ina ganin, a fara bari mu ji ta bakinta tukuna ranka ya daWe, kar a yanke mata hukunci kai tsaye"

Wambai ya kalleta ya ce muna saurarenki.

Ruma ta ?ulu, basarwa kawai ta yi, ta haWiye wani abu mai Waci sannan ta ce "Kafin na ce komai, zan fara da bawa babana ha?uri a kan abubuwan da zasu fito daga bakina, duk da ya san wasu, na san bai san wasu ba. Ina neman afuwarka babana mai girma turakin kano"

Turaki yayi murmushi mai ciwo, sannan ya ce "Kar ki damu yarinyar kirki, kamar yadda na ri?e miki al?awari a baya, ina umartar ki da ki faWi komai, dan fita daga zargi.

Ayshercool.
08081012143



Rumaisa ta ja numfashi, sannan ta fito da wata waya, duk ta sha jiki, screen Win ma duk ya tsage, ta ce "Wannan wayar, ita ta fara haWani da takawa, kafin ?addara ta sake haWa mu a karo na biyu.
Silar haWuwarmu na farko wannan abu ne da ya shafi rayuwarmu ni da shi, bai shafi abubuwan da suke faruwa a yanzu ba"

Ta Wan yi shiru sannan ta cigaba da cewa, "Kamar yadda wasu suka sani, yayyena maza ne, nice ?arama da duk wanda ya sanni, aka yi mini shaidar rashin ji.
Wannan wayar na Wauke da wasu abubuwa da ka iya taimakawa jami'an tsaro, saboda a rashin ji na, bani da tsoro, kuma cikin ikon Allah ranar da mu ka tafi kai ziyara dangin mahaifina, muka haWa mota da ?an bindiga. A cikin wayar akwai hotunan wurare da abubuwa da na yi ta Wauka, ciki har da jakar bullet mai Wauke da wasu lambobi, da sunan SMOKE.
A rashin ji na, na tattauna da ?an bindigar, har shugaban su yake ce mini, ?asa ta san da zaman su, dan kuwa akwai kason su, a kasafin kuWi da ake duk shekara.
Kasancewar a lokacin bakomai nake ganewa ba, amma na fuskanci wasu abubuwan.

Zuwana garin su babana, wanda ?an bindiga kusan suke mulkar garin, nan ma nayi wata tattaunawar da wani dattijo da aka ?ona rigar su, sai shi kaWai, wanda shima yana da ala?a da ?an ta'adda.

Daga nan har zuwa lokacin da aka yi garkuwa da ni, abubuwan dai tamkar a mafarki, duk yadda za a bawa mutum labarin yadda abun yake, sai ya je ya gani. Na sha ba?ar wahala saboda ina da taurin kai da rashin jin magana, na daku kamar ba mutum ba, saboda ban daina rashin kunya ba.

Kwatsam! Aka kawo matar da silarta abubuwa da dama suka faru, mace da tsohon ciki, ta din ga magiyar a bari ta tafi, ko dan cikin jikinta, aka ce a kula wannan ajiyar wakili ce".

?iff Wakin yayi, Wambai ya ce "waye wakili, wane waikilin tukuna".

Turaki ya ce "A daina katse ta, mu bari ta kammala tukuna".

Rumaisa ta Wora da cewa "Lokacin da ta zo ina tsaka da rashin lafiya, halin da take ciki bai dameta ba kamar ni, ta kula da ni sosai da sosai, sai dai wasu lokutan sai tayi ta kuka, idan na bata ha?uri sai ta ce; ba sace ta da aka yi ne dameta ba, mijinta, ba yadda bai yi da ita ta fasa tafiya ba amma ta?i, sai kuma sanya hannun Wan uwanta a wurin saceta.

Ta bani labarin mijinta, iyayensa, yadda suke rayuwarsu, da kuma irin rayuwar da tayi a nasu gidan.

Ta gaya mini mahaifinta ya saka sunanta a kadararsa, kuma wasu kuWinsa na shiga account Win ta, saboda ita bai taSa mallaka mata wata kadara ba, saSanin ?an uwanta, da kowa yana da wani muhimmin abu da ya bashi.

Ta gaya mini matar mahaifin ta da yayyenta, sun uzzura mata sosai a kan hakan, kuma babu wanda ya san da zuwanta Nigeria, sai yayanta da ta gayawa, ta sanar masa ga ranar da zata je dubiya....

"?arya ne, me ki ke nufi, Jamil ne ya sanya aka yi garkuwa da aisha, wallahi ?arya ki ke yi, ni za a yi wa sharri, a cuci Wa na a Sata mana suna"

Wambai ya Wagawa babar su Jamil hannu, ya dubi ruma ya ce "Wani tabbaci zaki bamu a kan haka, ta yaya zamu yarda da ke?".

"Na yi wa anty aisha al?warurruka, bayan ta ce mini ta bani amanar mijinta da Wan ta, duk da ?arancin shekaruna, na fahimci abubuwa da dama a labarin da ta gaya mini" rumaisa ta basu labarin komai, har kan mutuwar aisha.

Ta kalli Abdallah ta ce "Bismillah"

Abdallah ya dawo tsakiya, ya zauna da kayan zanensa.

Ruma ta ce "Wannan yayana ne, kuma ?wararre ne wurin iya zana abubuwa, da shi nake koyi, ya sanya nima na iya zane-zane, amma kasancewata ?ar koyo, zan ba shi damar ya zana wani abu, kar ace na yi son zuciya ko sharri nake son yi wa wani, yana daga in da yake zaune, zan siffanta masa abun da zai zana Win, Abdallah ba ya nan aka sace ni, nikaWai aka sace, dan haka you should be good in judgment"

Kowa yayi shiru ya zuba musu ido, sannu a hankali take siffanta masa abubuwa yana zanawa, bai ja lokaci ba ya kammala zanen ya mi?a musu takardar da yayi zanen a kan ta.

Ta siffanta masa Mutanen da suka je suka Wauki gawar aisha ne, da motarsu, da yanayin da suka Wauki gawar.

A yadda rumaisa ta suffanta masa ya zana, Jamil ne a gaba cikin kayan ppe, amma yanayin tsayuwar da sashin da aka iya gani na fuskar sa, zai tabbatar maka da shi ne, idan har ka san shi.

A lokacin takawa ya tuna a tsukin lokacin yayi ta fama da faWuwar gaba, da fita hayyaci, kuma Jamil yayi balagro a lokacin.

Mahaifiyarsa ta cigaba da bala'i, da i?irarin wannan shegantakar banza ce ba Jamil ba ne ba.

Mahmud ya ce "Allah ya baku yawan rai, muna da shaida ta gaba, ban sani ba kafin ni, ko ta gaya wa wani, amma ta same ni da maganar, kuma da ni da wasu daga cikin ?an uwanta maza muka yi aikin nan.
Akwai lambar waya da ta bani, lokacin tana magiyar a kai aisha asibiti kan ta rasu, ita ce lambar da aka kira, na bayar an yi tracking Win ta, haka zalika Wan uwanta Yasir yayi tracking Win ta, an daina amfani da layin, amma Jamil ne yayi register da layin, Yasir na da tracking result Win sa, ni ma ina da nawa da police suka yi"

Wani daga cikin ?an sandan ya ce "Amma wannan ai aikin police ne, mu yakamata ace mun yi shi, ko shi Adam tun da jami'in tsaro ne".

"Ban ji na yarda da kowa ba da zan iya???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? Waukar shaidu, masu muhimmanci na bawa ?an sanda ba, dan a lokacin na ji takaicin ace ?asata da jami'an tsaro amma aka kasa kuSutar da ni, daga hannun ?an bindiga, kuma ?an bindiga da kansu, suka tabbatar mana da kun san da kune ku ke sau?a?a musu aiki, ku jami'an tsaro.
Takawa kuma ban gaya masa komai ba, saboda a wancan lokacin yana cikin damuwa da tashin hankali ne, da kuma fuskantar matsin lamba daga mutane, a yadda yake a zuciye zai iya Sata komai a wannan lokacin.

Maganar ina ?o?arin Sata zumunci ta hanyar haWa husuma kuma, ina da shaida babu wanda na yi wa sharri, ranka ya daWe wannan ledar ta gabana, cike take da kayan tsubbu da na sanya baba uwani tsohuwar hadimar ammi tonewa, kuma nayi amfani da wayar Waya daga cikin ma'aikatana, na naWi duk abubuwan da aka saka ta yi mini, suma suna cikin wannan wayar na tura a ciki".

Adam ya tashi jiki a matu?ar sanyaye, ya Wauki excuse ya fita amsa waya.

Tun da suka shiga ake kiran wayar, sai dai da ya duba ya ga private number na.

A yadda ruma suka tsara da Mahmud, shi ne zai faWi abubuwan da suka shafi Sangaren Mummy, kutungwilar da take shiryawa amma ya kasa.

Turaki ya sunkuyar da kai zuciyarsa na yi masa raWaWi, saboda abun duniya yana ciki Waya da aisha, ubansu Waya, ya sanya aka saceta, kuma yake ta ?o?arin sanyawa a Wora zargi a kan Adam, Adam Win da ya kasance abokinsa Wan uwansa da suka tashi tare.

Kuka matar turaki take yi, ta ce "Ita haryanzu ba ta yadda da cewa Jamil zai iya aikata mummunan abu irin haka ba sharri ake yi masa".

Bashir ya ce "Hajiya sai dai ki yi ha?uri, domin kuwa jami'anmu sun riga sun kama shi ma"

Mahmud kuwa ya dubi Jabir, sannan ya mayar da idonsa kan Hajiya Lubabatu ya ce "In faWi me Jabir yayi, ko kuma in bari ku faWa da kanku?"

Suka yi tsit babu wanda yayi magana, Mahmud ya ce "Dole ka cigaba da zama a hannun 'yan sanda su kammala bincike"

Wambai ya ce lallai a nemo masa baba uwani duk in da take, gaba Waya falon ya hargitse da hayaniya.

Rumaisa ta ce "Babban ro?on da zan yi muku shi ne, kar wanda yayi ?o?arin yin wani abu a kan wakili, saboda nikaWai ce shaida a kansa, sai dai in Jamil ne ya yi magana a kan sa, idan ba haka ba".

Bashir ya ce "Haka ne, amma ban taSa tsammanin wakili zai kai haka ba, saboda tsamar da ke tsakanin sa da Adam ba"

Adam ya Waga wayar tare da yin sallama "Na san ko ban yi magana ba, ka san da wanda ka ke magana, Senator mai wakili ne. Ina tayaka da ?an team Win ka murnar gano suwaye SMOKE. Sai dai nikaWai ka sani a SMOKE, amma ka sani gano smoke ba shi da wani amfani, saboda su kansu wanda ka ke tunanin zasu Waukar maka matakin suna cikin SMOKE.
ministan man fetur ke da shiyyar satar mai, ?angaren tsaro suna da kamasho a kasafin da ake yi, da wasu manyan mutane a ?asar nan.
Talakawan da ka ke yi domin su, basu isa su yi maka komai ba, duk wata shaida da kake tunanin kana da ita a kanmu, akwai gaSar da idan aka kai, kai ne zaka kwana a ciki, dan na san baka isa ka yi jayayya da shugabannin rundunar tsaro ba, ba ka da wata shaida a kan sa.
Dan haka kai zaka kwana a ciki, duk yaranmu da ku ka samu ku ka kama, babu wanda ya san suwaye SMOKE, kai kaWai ka yi nasarar gano suwaye, Wan uwanka Jamil yaron Khalifa ne, tare da shi suka yi aiki, sai dai shima bai san mune SMOKE ba, mun yi amfani da sace matarka, wurin Wauke hankalin ka daga kanmu, kuma cikin ikon Allah ta haihu ta rasa ranta. Abu Waya zuwa biyu nake son gaya maka. Ka bar al'amarin nan a iya haka, idan ba haka ba zaka yi ta ranka, ko kuma ran matarka da Wanka, dan kuwa? ita ce duk sanadin komai, dan kuwa duk motsin ku, da duk abun da take yi, muna samun labari ta Sangaren Jamil.
Dan haka sai ka zaSi Waya, fito na fito da masu ?asa, ko kuma ka rasa rayuwarka da na matarka, dan ka san ba abu ne mai wahala ba. Sai dai fa ka yi ha?uri, domin kuwa rayuwar matarka ta salwanta kamar ko wani karabutin Wan ?asa, duk da kasancewar ka mai kaki, kuma jinin babbar masarauta, ire-iren yaranmu ne kisan su baya tafiya a banza. Kuma duk wani abu da zai faru Jamil ba zai taSa furta sunana ko na Wa na ba. Dan haka gara ka watsar da duk wani yin?urinka, ka tattala abun da yayi saura a rayuwarka, kan mu gama WiaWaita ku" ya katse wayar.

Duk da hatsaniyar da ta kaure a falon, yanayin da takawa ya shigo, ya sanya kowa yin shiru, wani irin gumi yake yi, jikinsa yana tsuma, kuma aka rasa mai tambayarsa meyafaru, kowa ya zuba masa ido.

Ruma ce ta mi?e tsaye, ta ce "Papa lafiya kuwa?"

Gabanta ya ?arasa, jiki a matu?ar sanyaye ya zube a kan gwiwoyinsa ya furta "Na gaza, dama kin gaya mini, na gaza rumaisa ba laifina bane, na yi iya yina, abun ya fi ?arfin yadda nake tunani, na barwa Allah, tun da a cikin gidanmu ma aka kware mini baya, ba ni da saurin ?warin gwiwa. Da izzar da tawa da sarautar tawa da komai na zube su a kan gwiwoyina, na gode rumaisa, na gode. Ke alkhairi ce ga rayuwata da ahalina, wata?ila ba dan ke ba, ba zan gane bara gurbin da suke rayuwata ba" Hawaye yake zubarwa kamar ?aramin yaro, cike da ?unar zuciya. Lallai faWa da aljani ba daWi, shiya san bai isa cigaba da fito na fito da wannan mutanen ba, in dai a Nigeria ne, mutane sun san ta'addancin Smoke, sai dai basu san suwaye ba, kuma wani abun shaidar rumaisa kawai ba zata wadatar ba, hakazalika da rayuwar rumaisa ta salwanta gara ko menene ya ha?ura da shi, yarinyar tayi sacrificing alot".

Rumaisa ta dur?usa ta ce "Papa dan Allah ka tashi, ka sakani a duhu, ni ban gane me ka ke nufi ba, ka tashi dan Allah, a gaban mutane ne fa"

Mahmud ne ya tashi ya kama Adam, ya mi?ar da shi tsaye, ya ja hannunsa ya cewa rumaisa su tafi.

?an sanda suka tattara duk wasu bayanai da suka kamata, wanda rumaisa ta bayar, da zanen Abdallah da aikin da Yasir yayi, Bashir ya karSe ya ce sai sun kammala na su binciken tukuna, zasu gani idan da yiwuwar ba wa ?an sanda.

Wambai kansa ya girgiza da jin lamarin, tausayin Wan uwansa turaki ya kama shi.

Sosai babar Jamil ke kuka, tana cewa turaki ya saka baki, ya ?aryata abun da suka faWa, ya sanya a saki Jamil.

Wambai yayi mata tsawa, ya ce su tashi su tafi sai ya sake nemansu.

Mummy godiya ta yi wa Allah, da ba a faWi komai a kanta ba, Hajiya Lubabatu ta zube tana yi wa wambai magiya ita ma a kan a taimaka a sanya baki, a saki Jabir.

Mummy ta ce "Wallahi ba ta isa ba, ba zai lalata mata ?a ya ci bulus ba" jin abubuwa babu Allah a ciki, dagulewar lamuran yayi yawa, ya sanya wambai cewa su tafi su je su ?arata a wurin ?an sanda.

Sai da ya rage daga shi sai turaki, sannan turaki ya samu zubar da hawaye, ya daWe matar nan tana citar da shi da Aisha, amma ba ya iya Waukar mataki, dama tun a farko rumaisa ta gaya masa komai, sai dai bai tabattar ba sai a yanzu.
Wambai ya dafa kafaWarsa ya ce "Ina neman afuwarka Wan uwana, na rashin tsayawa in fuskance ka a abubuwa da dama. Dama na san biyayya ce ta sanya ka auri Sa'adatu, sai dai wannan abu ba kai kaWai ya shafa ba, zan yi iya ?o?arin ganin cewa maganar nan ba ta fita ba"

"Kar ka yi haka, ko kayi hakan, ko ba kayi hakan ba, dole sai maganar ta fita, Allah ya ji?an fulani da mahaifiyarta, rumaisa kuma Allah ya yi mata kyakykyawan tukuici da ita da iyayenta.

Mahmud kai tsaye har gida ya kai Adam da rumaisa.

Adam na kwance a jikin rumaisa kamar uwa da Wa, sai aikin rarrashin sa take yi, tana bashi ha?uri.

"Rumaisa, ni wakili yake gayawa sai in dai in yi ha?uri, ran matata ya salwanta a banza, saboda wautata da rashin hankali, kuma wai ba wani abu da zan iya yi a kai"

"Ban gaya maka ba? Na ce zaka iya bincike ne kawai, amma in dai a ?asar nan ne, kar ka yi tsammanin samun adalci, mu bar wa Allah papa, you try your best, Allah shaida ne"

Mahmud ya ce "Takawa dan Allah ka daina kukan nan haka, kar ka tayar mata da hankali, ga ciki tana fama da shi".

"Mahmud baka san me nake a zuciyata ba, ba zaka gane ba"

"Na sani mana, saboda sau?a?a maka raWaWin da ni da rumaisa muka yi aiki tare dan sau?a?a maka aiki. Ina mai baku ha?urin rashin exposing Mummy, amma ita ma very soon in sha Allah, ka yi ha?uri dan Allah"

Cikin kuka ya sake cewa "Jamil fa mahmud, a Wakin Ammi muka yi wasa tare muka faWi muka tashi, amma ni Jamil zai din ga yi wa wannan cin dunduniyar? Me nayi masa? An kashe mini mata kuma ya cigaba da bibiyata da ?o?arin Wora mini sharri? Me nayi masa ne?"

"Baka yi masa komai ba Papa, hassadar ka fi shi komai ne kawai da kwaWayin abun duniya ya sanya shi haWa kai da ma?iyanka, gashi wanda ka ke yi wa kallon ma?iyin, shi ne ya taimake ka, duk lalacewar Wan uwa naka ne papa".

"Na gode mimi na gode sosai"

"Dan Allah ka daina yi mini wannan godiyar, ni ba abun da na yi "

Mahmud ya mi?e ya ce "Daughter, ki kula mini da shi sosai dan Allah, zan je gida wurin ammi, na san tana cikin damuwa ita ma"

Ruma ta ce "Wait, wai ba daga gadon asibiti ka taso ba?"

"Rabu da ni na warware "

"Amma ka yadda maman jabir tayi maka wani abu?"

Ya ce "Na yarda, Kamar yadda muka saka Yasir bibiyar wayar Mummy, ya kunna mini wayar da Mummy tayi da Hajiya Lubabatu. Na karSi duk wata shaida ta hannunsa, jibi in Allah ya kaimu zai tafi wurin Anty laila, kar ma a samu wata matsala saboda aikin da ya yi mana"

Ruma ta ce "When are you exposing her?"

"Soon in sha Allah"

"Idan ba zaka yi ba, allow me to do it"

"I will in sha Allah" ya juya ya fita.

Haka ruma tayi ta aikin rarrashin Adam, dan abun ya dake shi sosai da sosai, duk iya tunaninsa bai ga ta ina zai iya jayayya da SMOKE ba.

Kuma dolensa ya ha?ura da cigaba da duk wani yin?uri a kan garkuwa da aisha, saboda rayuwar rumaisa.

***
Kwanaki uku kenan, gidajen sarautar suka shiga Wimbin tashin hankali, komai ya damalmale, ba kama hannun yaro, aka gaza samo bakin zaren abubuwan da suka riga suka dagule, Kodayake ba komai ne zai gyaru ba, kasancewar wata Sarakar ta samo asali ne tun shekarun da suka gabata, ba tare da an mayar da hankali an gyara su ba.
Kodaye rumaisa ta kawo gagarumin cigaba da kuma gyara wasu abubuwan.

Ba tare da wani cikakken shiri ba, Mahmud ya ce lallai sai Yasir ya tafi canada, Yasir ya so ayi bikin yaya Abubakar yana nan, amma ba dama, aikuwa sai da yayi kuka saboda rabuwa da mama da ?an uwansa. Mahmud kuma ya ?arfafa yin hakan ne, kar wani abu ya samu Yasir, saboda aikin da yayi musu, dan a wata fuskar laifi ne abun da ya aikata Win, kutse da satar bayanan mutane ba tare da izinin su ba.
Haka ya tsallaka ya tafi ya bar Nigeria.

Abdallah kuwa Bashir ya ce sai sun tafi da shi Abuja, mama ta tashi hankalinta ganin kamar ana yi wa yaranta Wauki Waya-Waya, amma ya bata tabbacin babu wata damuwa, a kan Jamil ne ita ma rumaisa Adam ne zai wakilce ta, saboda tsohon cikinta.

Ranar da zasu tafi Abuja, takawa yayi ta rarrashin ruma, tare da bata tabbacin, Abdallah zai dawo lafiya, tun da har da shi zasu tafi.

Rumaisa suna ta shirin fara Waec, sai dai fa nauyin ciki ya hanata sukuni sosai, tun da ta dawo daga makaranta, mararta take yi mata ciwo da ?afafuwanta, kuma takawa ya riga ya tafi, dama ya ce mata idan ba zata iya zaman gidan ba, ta tafi gida wurin mama ko ammi.

Jin ciwo ya?i ?arewa, ta kira Usman a waya, ta ce ya zo zata mutu.

Ya je ya tarar da ita duk a firgice, ta bashi mukullin Waya daga motocin takawa, ta ce ya kaita asibiti.

Suna tafe a hanya ya ce "Ko dai haihuwa zaki yi?"

"Edd Win bai cika ba fa"

Ya ce "Ikon Allah, muna zaune yarinyar da muka goya, muka yi wa wanka za ta haihu, haryanzu muna gararamba, bakomai akwai lokaci"

Bakin rumaisa bai mutu ba, sai da aka ce mata haihuwa ce a asibiti, ita dai ta san lokacin haihuwa da saura, aka ce usman ya je ya kwaso kayanta.
Maimakon ya kira mama a waya, ko ammi, kawai sai ya kira Aliyu da Huzaifa, sannan ya ?arasa gidanta, ya Waukko akwatin da ta kwatanta masa, dan tuni takawa ya gama sayen komai na jariri.

Mamaki ya kama nurses Win, suka ce babu wata mace wadda za ta zauna da ita duk sai maza.
Huzaifa ya ce "Hajiya gidanmu ita kaWai ce mace, babarmu kuma tsohuwa ce ba ta da cikakkiyar lafiya, duk abun da mata zasu yi, mu ma zamu yi"

Nurse Win ta ce "A dai duba dangi a samo wata"

Usman ya ce "Hajjaju, wallahi zamu iya komai, ki ?yalemu kawai".

"To ina mijinta?"

Aliyu ya ce "Tafiya ce ta kama shi Wazu"

Ta jinjina kai ta ce "Lallai ?ANWAR MAZA"

Rumaisa ta sare da al'amarin, saboda tun da mama ta haifeta ba ta taSa jin masifaffen ciwo kamar wannan ba.

Mai sunan baba kuwa, ganin hankalin Adam yayi wani wurin, mahmud kuma ya warware, ya sanya ya yi wa mahmud zancen, mahmud ya din ga murna, ya ce dole su je Lagos tare, dan tabattar da wannan lamari, dan haka ya ce zai yi musu booking Flight su je, su yi abun da za su yi, saboda su koma bakin aiki.

Mai sunan baba ya kira Huzaifa a waya, yana masa faWan duk suna ina, gida ba kowa sai mama itakaWai a gidan.

Mama ta ce "To yarinya ce ni, da lallai sai sun zauna a gida?".

Huzaifa ya gaya masa in suka tafi, ba tare da ya gaya wa mama abun da ake ciki ba, ya tafi asibitin.

?arshe sai da suka cika asibitin, Abdallah da Yasir ne kawai babu.

Gaba Waya suka zama abun kallo a asibitin, wai sun kawo ?anwarsu haihuwa a asibiti.

Ruma ba ta haihu ba sai bayan magariba, babyn pre term ne, watanni bakwai da sati biyu.

Nurse ta fito ta ce "Kun ga ga mahaifa, ga kayan jini, dan girman Allah ku nemo mace"

"Sai kuma ki yi, karSar haihuwar ma da kin matsa sai mu karSa, ko abun da ya fi kayan jini ne zamu gyara, babarmu tsohuwa ce, bamu da ?ar uwa mace, dangi ba kowa ke son ka katse masa hidimomin sa ba, dan haka ba jini ba, ko menene zamu iya"

Mai sunan baba ya ce "Ina jaririn?".

"Nursery zamu kai shi, sa an saka shi a kwalba"

Sai da suka jira aka basu damar shiga su ga ruma, tana kwance kai da ganin idonta ka san an sha gwagwarmaya.

Nurses suka ce a kawo mata abinci, sai a lokacin mai sunan baba ya tafi

Please Login or Register in order to submit comment