You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a rayuwarsa da ita akwai wani darasi da nake fatan ya koya, kuma kan ayi auren ai dolensa ya dinga zuwa wurinta su saba"

Iman ta yi murmushi ta ce "Akwai rikici kenan?"

Ammi ta ce "Ta bani tausayi Wazu da muka yi waya, wai an ce ta yi cikin shege, ana yi mata kallon ?ar iska, saboda ta zo da sabir, idan ban saka takawa ya aureta ba, shikenan an yi mata mummunan tambari, mutane Wa idan ba na su bane ba, sun din ga janyo masa jafa'i kenan"

Nusaiba ta ce "Haka ne, Allah ya shirya, ya tabbatar da alkhairi" suka amsa da amin.

Baba uwani da take laSe ta ji hirar ta su sama-sama, sannan bakomai ta ji ba, amma a abun da ta jin, ta ?udurce za ta je ta sanar da Mummy.


Rumaisa mita a cikinta, kamar an yi mata gori, yau wuni ta yi tana cigaba da mitar abubuwan da ake yi mata a unguwar nan, mama tun tana yi mata nasiha tana cewa ta bar wa Allah, har ta yi mata banza ta ?yaleta, Abdallah ya sakata a gaba yana cigaba da kunnata, tana mita. Bayan fitar Abdallah rumaisa ta shiga Wakinsu, ta duba wurin da yake ajiye fensiransa na zane kasancewar sa architect.

Ta zauna ta nutsu sosai, ta hau zane-zane.

Mama ta ce "Uban me ki ke yi musu a Waki, ki ka shiga ki ka yi shiru?"

Rumaisa ta ce "Bakomai"

"To fito musu daga Waki, tun basu dawo sun tarar da ke ba"

"Mama zan fito ina zuwa"

Sai da ta gama abun da Allah ya nufeta da yi, sannan ta fito ta fice ba tare da sanin mama ba.

Ma?wabciyarsu ta zana, kuma zanen ya fita sosai, ta yi headline da munafukar unguwa, a ?asa ta rubuta by Rumaisa Mahmud ?anwar maza. Ta je ta li?e a ?ofar gidan matar, ta nausa ta tafi gidansu Habiba, ba tare da mama ta san ta fita ba ma.


Ayshercool.

paid book ne, ? 500 via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143


*KANWAR MAZA*

*39*



*PAID BOOK NE, ? 500 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*




Jin shirun yayi yawa ya kuma sanyawa mama ta ?walawa rumaisa kira, amma har ta kira kusan sau uku shiru, ba ta amsa ba, mama ta kaste abun da take yi, ta fita domin duba me rumaisa take aikatawa ta ji shiru. Sai dai da ta fito tsakar gida babu rumaisa ba alamarta.
Mama ta le?a Wakin ?an maza, amma babu rumaisa ?arshe ma sai shiga Maman ta yi ta kwaso kwanukan ta, da suka kai Wakin suka bar su, ta fito ta duba banWaki da kitchen duk babu rumaisa, tsayawa ta yi tana tunanin ina rumaisan ta tafi ba ta gaya mata ba?.

Tana cikin jimamin in da rumaisa ta tafi babu izininta, shamsiyya ma?wabciyarsu ta yi sallama, ita da wata mata.
Mama ta amsa musu cikin sakin fuska, ba tare da nuna mata ta san ta yi wa ?arta ?age ba.

"Maman rumaisa ni ba zama zan yi ba, ki shiga tsakanina da yarinyar nan, kalli abun da ta yi mini jiya a fuskata, da Sarnar da ta yi mini a cikin gida, maigidana ya kawo ?ararta, ?arshe ba wani mataki da kuka Wauka, sai ma cin mutumci da ya biyo baya, yau kuma ta je ta yi zane ta li?e mini a ?ofar gidana ya ?i fita, wai munafukar unguwa, me na yi muku haka ne?"

Cikin dattaku mama ta ce "Dan Allah ki yi ha?uri, yaran zamani ne sai godiyar Allah, wallahi da kaina na yi niyyar shigowa na baki ha?uri, wallahi ban san ta yi ba, kin san dai ni ba zan goyi bayan ta yi wannan rashin kyautawar ba, ban san ta yi miki ba, dan Allah dan annabi ki yi ha?uri, bari ta shigo gidan, zan hukunta ta kuma zan sanya ta je ta cire, dan Allah ki yi ha?uri"

"Wallahi banda ina jin nauyinki, Allah da sai na kama rumaisa na yi mata shegen duka".

Mama ta ce "Ashsha, ba za ayi haka ba, ai ke ma ?arki ce, yanzu kina taSata komai zai Saci, yayyenta ba sa ganin laifinta, amma dai ina baki ha?uri, da kaina zan hukunta ta, kuma zan aikota ta baki ha?uri".

Haka Jamila ta yi ta farfaWar maganganu, mama tana bata ha?uri, da alwashin hukunta rumaisa, bayan tafiyarta mama ta dafe kai, haryanzu rumaisa babu alamar hankali a tare da ita, tuno damben da suka sha da ?ar ajinsu ta yi, abu har wurin ?an sanda saboda wannan shegen zane-zanen da take yi, shi kansa Abdallah dan ba yadda za ta yi da shi ne, abun da yake karanta kenan, ga rumaisa na neman gadarsa, in dai zane-zanen banza da na wofi ne, a litattafan makarantar ta ma yi take.

Mama ta rasa mai ma yakamata ta yi, ba ta san ta ina zata fara neman rumaisa ba.

Rumaisa kuwa gidansu habiba ta tafi, suka shantake suna ta hira, ta bawa habiba labarin abun da ta yi wa ma?wabciyarsu.
Habiba ta ce "Kin mini daidai, da nice ba zan iya ba, tsoro nake ji, kin ji yadda matar nan ta din ga yayata maganar nan a cikin unguwar nan, ummanmu ce ta fara taka mata burki ta ce ?arya take yi, daga nan ta je ta gayawa mamanku"

Rumaisa ta ce "Hmm, ai sai ta gane ba ta da wayo kan ma bar unguwar nan, da ina mutunta ita da mijinta, amma tun da ta taSo ni, za ta gane bata da wayo"

Cikin rashin fahimta habiba ta ce "Ki bar unguwar nan ki koma ina?"

Rumaisa ta Wan yi jimm, sannan ta ce "Ke share kawai, na san zuwa yanzu wata?ila ta je ta kai ?arata gidanmu"

"Me ki ka yi mata?"

Cikin ?warin gwiwa rumaisa ta ce "Zanata na yi, na rubuta munafukar unguwa, na li?e mata a ?ofar gida, na san yau za a azabtar da ni a gida, amma ba zan koma yanzu ba"

Habiba ta ce "Wai ruma ba kya jin tsoro ke? Mama ba ta san kin zo nan ba?"

"Ba ta sani ba, idan aka kai ?arata ina gidan, a gabanta mama zata bani rashin gaskiya, duk da abun da ta yi mini, zuwa yanzu kuwa na san ta tafi, in koma gida a haWani da mai sunan baba, ya bani gwale-gwale"

Dariya habiba ta yi ta ce "Wato ke har ma kin san me za ayi miki, ina yaya Aliyu?"

Rumaisa ta yi mata kallon ?asan ido ta ce "Yana makaranta, in ce kina nemansa ne?"

Habiba ta waro ido ta ce "Ke a'a, kawai dai tambayarsa na yi"

"Meyasa duk cikin yayyena shi ki ka sani?"

Habiba ta ce "Bakomai, ya na da kirki ne"

Rumaisa kawai ta yi dariya, tana lissafa yadda zata wanye da mama idan ta je gida.

Mama kuwa sai kallon agogo take yi, tana lissafa, ina rumaisa ta tafi haka? Ta ?i dawowa, zuciyarta ta bata saboda abun da ta aikata ne ya sanya ta fece.

Kasancewar azahar ta yi, kuma juma'a ce ya sanya ?an samarin mama dawowa gida, domin shirin masallaci, kuma aka yi sa'a ana public holiday, rumaisa ba makaranta ta je ba.

FaWan Abdallah mama ta jiyo, yana faWin "Uban waye ya taSa mini kayan zanena, bana son rashin mutunci, Huzaifa ban hanaku taSa mini kaya ba?"
Huzaifa ya ce "Ni na iya amfani da wannan abubuwan naka ne? Sai dai ko Yasir"

Yasir ya tari numfashin Huzaifa ta hanyar cewa "Saboda ni ka raina ba, yaushe na zauna a gidan balle na taSa masa kaya".

Mama ta fita tsakar gida ta ce "Ba aikin kowa bane, rumaisa ce ta taSa maka, ita ta shiga Wakin ta yi shiru, ita ce ba wani ba".

"Tana ina, sai ta ci ubanta yau sai na zaneta, har da gum Wina ta buWe ta bar mini a buWe"

"Hmm, wannan yarinyar ai sai fatan shiriya, ina fatan Allah ya sanya auren nan ne mafi alkhairi, ko yau aka ce za ayi zance a Waura su tafi da ita"

Abdallah ya ce "Tana ina?"

Mama ta ce "Ina na sani, ta yi wata aika-aikar ta gudu, ban ma san ta fita ba".

Yasir ya ce "Kai wannan yarinya, Allah ya yi mata maganin abun da yake damunta yake sanyata rashin ji".

Rumaisa ba ta tashi tafiya gida ba, sai da unguwa ta yi tsit, duk an tafi masallaci, sannan ta nufo gida, cikin shirin karSar kowane irin hukunci za a yanke mata.

Da sallama ta shiga gidan, ta yi sa'a mama tana salla, ta lallaSa ta shiga Wakin ta zauna, tana jiran mama ta idar, ta shirga mata ?aryar da zata kare kanta.

Mama tana jin motsin rumaisa, amma ta shareta, ko da ta idar da sallar ma ta yi lazumi, ba ta tankawa rumaisa ba.

Cikin tsoro rumaisa ta ce "Mama" banza tayi da ita ta shige uwar Waki ta bar rumaisa.

Tun rumaisa tana War-War har ta Wan saki jikinta, da ta ga mama ba ta da niyyar kulata.
Sai dai ba ta ankara ba, mama ta shammaceta, ta janyota ta din ga Wirka mata dundu.

Ihu rumaisa take yi, tana neman agaji rabon da mama ta daketa har ta manta.

Tun daga waje Yaya Abubakar ya jiyo ihun rumaisa, a soro ya yasar da sallaya, ya shiga da gudu, ya tarar da mama ta samu mafici, tana jibgar rumaisa tana yi tana haWawa da hannunta.

Ai da hanzari ya ?waci rumaisa yana faWin mama lafiya.

"Rabu da ni, yau yarinyar nan ta kaini bango, rumaisa a rayuwarta ba zata bari na huta ba, daga wannan sai wancan, gidan ubanwa ki ka tafi?"

Cikin kuka rumaisa ta ce "Gidansu habiba"

"Gidansu habiba gidan ubanki ne? Wato kin san abun da ki ka aikata ko?, To fita ki je ki bata ha?uri, ki cire takardar da ki ka li?e mata a ?ofar gida, tun kan na murWe miki wuya ki mutu in huta, da Waukar maganar da ki ke yi, kullum nike nan cikin bayar da ha?uri da faWa da mutane saboda ke?
Bari na kira babar adam Win a waya, idan sun shirya ko jibi su zo a Waura auren nan na huta na gaji" Rumaisa ta yi fici-fici da ido tana kuka.

"Ba zaki fice ki je ki bata ha?uri, ki cire abun da ki ka li?a mata ba?" Ruma ta fita da sauri, tana jin haushin sake kai ?ararta da matar ta yi.

Ta je ta yi iya ?o?arin ta, wurin cire cardboard paper da ta yi zanen a jiki, amma gum Win da ta yi amfani da shi ya kama sosai, dan haka ta samo wata ?usa, ta dinga durzawa takardar, ta haWa da sabon fentin da aka yi wa ?ofar duk ta kankare abun ta, sannan ta shiga cikin gidan matar.

Ta tsaya daga soro ta yi sallama, matar ta amsa sannan ta fito, ta sakawa bakinta da goshinta shanshanbale, in da rumaisa ta fasa mata da dutse.

"Kin kai ?arata, mama ta ce sai na zo na baki ha?uri, na cire takardar da na saka miki, na cire takarda, idan ki ka kuma kai ?arata zan yi miki abun da baki zata ba, kuma wallahi ban yafe miki ba sharrin da ki ka yi mini, wuta balbalin bala'i, idan baki nemi yafiyata ba, sai kin ga abun da Allah zai yi miki, kayan da ki ke sayarwa ma sai an daina siya" tana gama maganar ta juya ta tafi.

Da sauri ta biyo bayan rumaisa, sai dai tana zuwa ta tarar da sabuwar ta'asar da rumaisa ta ?yan?yasa mata a ?ofar gida, ta kankare tsakiyar ?ofar da ?usa, duk fentin ya fita ga sauran takardar ba ta gama fita ba, gaba Waya ta sauya fasalin ?ofar.

"Na shiga uku ni Jamila, wace irin masifa ce wannan, fentin ?ofar da bai fi sati da yi ba ki ka dirje?".

Rumaisa ta waiwayo ta kalleta ta ce "Idan baki gaji ba, yanzu ma ki je ki kai ?arata, zaki sha mamakin abun da zan yi miki next"

Ta shige gida tana sunkuyar da kai, mama ta kalleta a fusace ta ce "Kin bata ha?urin ko kuwa?"

"Na bata" ta amsa tana sunkuyar da kai.

Aliyu ya kalli rumaisa ya ce "Allah ya shiryeki ruma, ke ko gajiya da Waukar magana ba kya yi, kullum ayi ta yi miki faWa, daWi yake yi miki ko?" Ta girgiza kai alamar a'a.

"Zo ki karSi kuWin nan ki sayo mini milo a kantin malam lawan, zan sha shayi bana son cin abinci" kallon yaya Aliyu ta yi, kamar tana hararsa ya ce "Ni ki ke yi wa wannan kallon, ko ba zaki ba?" Ta dur?usa ta Wauki kuWin, ya ce "Ki taho da manja kwalba Waya, na ga wanda muke da shi ya kusa ?arewa".

Ita dai ba ta amsa masa ba, ta fice ko da ta fita a ?ofar gida ta hangi shamsiyya da mijinta, suna duba ?ofarsu da ta dirje, ba ta kula su ba ta tafi shagon.

Malam lawan mai kanti, yana ta yi mata wasa yana tsokanarta, amma ta share shi, ya auna mata manjanta, ta fito. Sai dai tana fitowa ta yi karo da wani tantirin Wan daba da ya addabi unguwarsu, wanda har kisan kai yayi, amma aka sake shi.

Ya kalli rumaisa ya ce "Ke, karSo mini sigari a cikin shagon nan"

Tsaki ta yi, zata wuce, ya sake daka mata tsawa ya ce "Ke, na ce ki karSo mini sigari a cikin shagon nan"

"Na yi maka kama da ?ar iska, ni ce ma zan taSa sigari saboda wula?anci, to ba zan karSo ba" ware jajayen idanunsa ya yi a kan rumaisa, a hargitse malam lawan ya ce "Yi ha?uri bari na mi?o maka".

Cikin muryar mashaya, Wan daban da ake cewa Wan kada ya ce "Ni ki ke gayawa haka?".

Fitowa ta yi zata wuce shi, ta tafi, amma ya sanya ?afarsa ya kwashe na rumaisa, a take kuwa ta faWi ?asa, manjan hannunta ya fashe, ta datse goshi.

Idan da abun da rumaisa ta tsana, bai wuce ganin jini a jikinta ba, jiki na rawa ta tashi ta kalleshi, ya kalleta ya ce "Sai na tsarge hanjinki da wu?a, na kashe banza ni zaki nemi ki zaga wata jagwal da ke"

Cikin hanzari malam lawan da sauran mutane suka fara lallaSa Wan kada suna bashi ha?uri, rumaisa ta shiga cikin shagon, ta dumbuzo ?wan da ke kan teburi, ta fito ta shiga jifan Wan kada da shi.

Rikicewa malam lawan yayi, dan yanzu aka sauke ?wan ko lissafawa ba ayi ba, ji ta yi zuciyarta na tafasa, ta juya da gudu ta tafi gida.

Aliyu na ganinta ya ?are mata kallo ya ce "Meye haka?" Cikin kuka ta kwashe komai ta gaya masa, nan da nan ransa ya Saci ya ce "Mu je" mama na banWaki tana gyaran murya, amma Aliyu ya ja rumaisa suka yi waje.

A ?ofar shagon suka tarar da Wan kada, har ya karSi sigarinsa ya fara sha, malam lawan kuma yana ta masifa, yana sai ya je gidansu rumaisa an biya shi, shi kansa Wan kada yayi alwashin sai ya kashe rumaisa, saboda wula?ancin da ta yi masa,ta din ga jifansa da ?wai.

Idan da abun da samarin gidan maman suka tsana, bai wuce taSa Wannan tilon yarinyar ba, dan haka a zafafe Aliyu ya ?arasa, yana zuwa ba tambayar ba'asi ya ci kwalar Wan kada, ya shiga kifa masa mari.

Kokawa ta kacame, ga Wan kada a buge, dan haka ya kasa wani abun arziki, Aliyu ya din ga haWa masa naushi.

Da ?yar mutane suka shiga tsakani, ana rirri?e Wan kada yana rantsuwa sai ya kashe Aliyu.

Mama kuwa a gigice ta fito daga banWaki, jin wanda rumaisa ta tsokano, dan babu wanda bai san yadda ya addabi unguwarsu ba.
Mama ta kira mai sunan baba a waya, ta ce masa duk abun da yake ya bari ya tafi shagon malam lawan, Aliyu ya fita ba ta san mai zai aikata ba.

Aliyu kuwa ya kalli Wan kada ya ce "Jinina da na zuriyar gidanmu ya fi ?arfin mutum irinka,? duk wani hauka da iskanci da kake ji da shi a unguwar nan ?yaleka aka yi, ?anwata ta fi ?arfin wawan mutum irinka su cutar da ita"

Malam lawan ya ce "Wai Meye haka ne Aliyu, ina nan aka sace ?anwar ta ku me ku ka yi, sai yanzu zaku haddasa mana masifa a cikin unguwa"

"Wallahi malam lawan, duk shekarun da muka yi tare a unguwar nan, idan ka taSa rumaisa sai na tuSe na yi maka bugun sakwara, saceta kuma da aka yi wannan ?addararta ce, ba yadda muka iya"

Rumaisa ta ri?e hannun Aliyu ta ce "Yaya mu tafi gida"

Da ?yar rumaisa ta ri?e hannunsa, suka juya suka fara tafiya, sai dai ana sakin mai kada, ya zare wu?a ya nufi Aliyu da ita gadan-gadan yana ihu.

Ihu rumaisa ta saka ganin wu?a tsirarata, wu?a ba ta wasa ba an nufo yaya Aliyunta da ita, wanda ba da tabbacin ita aka nufo ko shi. Aliyu ya hankaWeta, ya kuma ri?e mai kada suka hau kokawa ga wu?a tsirarta.

Aliyu ya danne mai kada a ?asa, ya Wau wu?ar ya ce sai ya yankashi da ita a wurin.

Nan aka din ga kokowa da Aliyu, aka kasa ?wace wu?a.

Rumaisa ta ce "Yaya Aliyu kar ka yi kisan kai, amma dai ka yi masa dukan tsiya".

Cikin takunsa na isa da ta?ama, ya din ga ture dandazon mutane, ya ?arasa in da Aliyu yake kan mai kada ana fama da shi, ya ri?e hannun Aliyu mai wu?ar ya murWa, ya jefar da wu?ar, sannan ya Wago shi daga kan mai kada ya tsayar da shi a kan ?afafuwan sa ya Kalleshi ya ce "Meya haka? Shaye-shayen kai ma ka fara ne?" Ya kalli rumaisa ya ce "Duk saboda ke ko? Sai ku wuce mu tafi ai".

Daga kwance mai kada ya ce "Na rantse da girman Allah, idan har ina yawo kana yawo a unguwar nan, sai na kasheka na kashe matsiyaciyar yarinyar nan, na ga uban waye gatanku"

Aliyu ya sake tunzura, jijiyoyin kansa suka kumbura, mai sunan baba ya kalli mai kada ya ce "Idan kana zubar da jini a unguwar nan kai da yaranka, ana tsoronku, kar ka ratso ta gidanmu, wallahi duk wanda ka zubarwa da jini in dai Wan gidanmu ne, kaima sai na zubar da naka, ka kiyaye"
Ya ri?e rigar Aliyu, hannu Waya ya tankaWa ?eyar rumaisa zuwa gida.

Mutane wasu har da shewa, abun ya burgesu, kaf unguwar nan babu gidan da suke da haWin kai da nunawa juna soyayya kamar gidansu rumaisa.

A gigice mama ta tashi da suka shigo, ta ga jikin Aliyu duk ?asa, rumaisa kuma da fasashshen goshi, duk da ba ta zubar da jini da yawa ba.

"Mai sunan baba, maiyafaru?"

"Kar ki damu, ba abun da ya faru"

Mama ta ri?e Aliyu da yake huci ta ce "Ina fatan dai ba abun da ya sameka ko?" Ya girgiza mata kai alamar a'a.

Mama ta ce "Duk saboda wannan jairar yarinyar ne, da ba zata bari a zauna lafiya ba? Ina ke ina faWa da gagararren Wan daba saboda Worawa kai bala'i" Mama ta yi maganar tana ?o?arin kai mata duka, amma mai sunan baba ya tare ya ce "Ki ?yaleta please, baki ga ta ji rauni a goshi ba, ki yi ha?uri"

Mai sunan baba ya sakata a gaba, ya kai ta chemist, aka duba goshin, Allah ya taimaketa babu Winki, suka dawo gida.

Mama ta kai ?arshen ?ulewa da rumaisa yau, ta din ga yi wa ?an mazan faWa a kan biye mata wurin tare mata faWa.

Kasancewar ma?wabcin su rumaisa malam shamsu, yana cikin ?an kwamitin unguwa, shi ne mataimakin ?an ?ato da gora, yana dawowa aka sanar masa da abun da ya faru a unguwar, nan da ya ji ya samu damar rama wula?ancin da rumaisa da yayyenta suka yi masa, kai tsaye ya je ya sanar da ?an sanda abun da ya faru.

Mama har ta bar sallahun a rufe gida, ?an sanda suka yi sallama, suka ce sun zo tafiya da Aliyu.

Duk yadda aka so sasanta lamarin, abu ya gagara, ga Abubakar ya koma makaranta, Mai sunan baba da Usman suka bi bayansu, amma har wurin sha Wayan dare, ?an sanda suka ?i bayar da Aliyu, ?arshe ma suka sanar da su cewa sashin kula da manyan laifuka na bamfai zasu turasu, tun da Aliyu ya yi i?rarin kisan kai.

Haka mai sunan baba suka koma gida, jiki a sanyaye, mama ta rasa in da zata saka kanta saboda tsananin damuwa da tashin hankali, tare da Wora zargin komai a kan rumaisa.

Adam kuwa bayan ya kammala cin abinci, ya tashi ya yi wa ammi sallama, ammi ta ce "Yauwwa, na ce ba" Adam ya Wan tsaya yana kallon ammi.

"Dan Allah gobe in Allah ya kaimu, tun da da wuri zaka fita, kuma ka ce zaka je gidan gona, dama unguwar su matarka ne, zan baka sa?o ka kai wa rumaisa"

Adam ya kalli Ammi ya ce "Matata kuma? Kuma ni zan kai ss?on?"

"Ban isa ba kenan?"

Ya ce "A'a tare da sunkuyar da kai"

"A yanzu kana da wata matar da ta wuce rumaisa ne? Zaka kai mata sa?o, kallonka kawai nake yi, har na je wurin turaki na dawo ba ka tambayi yaya muka yi ba, kuma ya zama dole ka din ga zuwa wurinta, saboda ta saki jiki da kai, kuma ka daina yi mata wannan muzuran"

Adam ya jinjina kai yana wasa da yastun hannunsa.

"Je ka, da safe in Allah ya kaimu kan ka wuce, ka biyo"

Bai ce komai ba ya fice.

Ayshercool.

Chat me on what's app, to subscribes yours
08081012143

*PAID BOOK NE, ? 500 NE VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA, 08081012143*



Gaba Waya ji yake duk wani girma da mutuncinsa sun zube, kamar shi ace wai zai je wurin wata ?ar yayyiyar yarinya yayi zance da ita, wai zai aureta, ko aurensa na fari aisha ta kammala deegree ya aureta, wannan shi ba ya tunanin ko primary ma ta gama.

Mama kuwa kwana ta yi ba barci, sai addu'a kawai da take yi, ji take tamkar ta rufe rumaisan da duka, dan bayan gama ?an koke-kokenta tuntsirewa ta yi ta hau bacci.
Mama ta kalleta ta girgiza kai ta ce "Allah ya shiryeki, ya ganar da ke"

Da asubar fari, bayan rumaisa ta idar salla, ta tafi Wakin su mai sunan baba ta yi sallama, suka amsa mata.
Ta le?a ta ce "Yaya usy jiya kun dawo da yaya aliyun?"

Abdallah ya ce "Wuce ki bawa mutane wuri, duk ba ke ki ka janyo ba, karfa kawai"

Mai sunan baba ya kalli Abdallah ya ce "Kar ka kuma gaya mata haka, bai dawo ba a can ya kwana, duk saboda ke, gaba idan ki ka sake, ke zan kai musu in karSo shi, dan mun fi son sa a kan ki, mara kai kawai"

Sumi-sumi ta juyo za ta fito, ta fuskanci kowa haushinta yake ji yau.

Usman ya ce "Wallahi yau da na ga malam shamsun nan a masallacin asuba, ji na yi kamar na Waga shi na wurga shi cikin kwalbati, shi ne babban munafukin da ya je ya kai wa ?an sanda"

Mai sunan baba ya ce "Ba ruwanka da shi, ku bari mu kashe wannan case Win tukuna".

Abdallah ya ce "Ni malam lawan mai shago na kusa kifawa mari, ya biyo ni wai rumaisa ta yi masa asarar ?wai cret huWu, wai in zo in biya, na ce masa sai dai mu yi kokowa ya Wiba, gaba Waya mutane fuska biyu ce da su".

Rumaisa da take tsaye tana jin su da sauri ta ce "Wallahi ko kret Waya bai yi ba, bai fi guda shida ba fa"

"Au laSe ki ke yi mana ko?" Abdallah ya faWa yana nemo abun duka.

Da gudu ta shige Wakin mama, sai dai irin kallon da maman ta yi mata, ya sanya ta rasa in da zata saka ranta.

Haka ta tsuguna ta takure, da duku-dukun mama ta shiga kitchen, ta girka abinci, gari na yin haske, ta ce lallai mai sunan baba ya taso su tafi station Win.

Mai sunan baba ya ce "Mama, idan kin je wurin nan babu abun da zaki iya a kai, ki bari zan je ni da Usman"

Mama ta ce "Ni dai ka ?yaleni na je na ga a yaya ya kwana?"

"Lafiya ?alau ya kwana, kuma in sha Allah zamu dawo miki da shi, ki yi ha?uri" da ?yar mama ta yadda, ta basu abincin suka tafi.

Rumaisa ta ce ita ba zata tafi makaranta ba, sai yaya Aliyu ya dawo.

Mama ta ce "Aikuwa ba ki isa ba, sai kin shirya kin tafi, wata?ila kan ki dawo na huce, dan da

Please Login or Register in order to submit comment