You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ce kwabo, sai ga samha ta shigo tare da Fauziyya, suna sashin Mummy, Mahmud ya gaya musu.

Samha na zuwa ta ganshi jikinta ya yi sanyi, ta na jin labarin rashin lafiyar sa, tun suna yara, wasu lokutan abun ya kan tayar masa, amma ba ta taSa tunanin abun ya kai haka ba.

Ya na cikin wannan halin, ya koma cewa "Rumaisa! Ammi a Waukkota daga makaranta, kar wani abu ya sameta. Rumaisa! Ammi Rumaisa".

Jamil ya ce "Ka kwnatar da hankalinka, wace makarantar ce, in je in Waukkota".

Mummy ta ce "Takawa ka na ta kanka, kana ta wata daban, ka yi addu'a, fatanmu ka samu lafiya"

"Ammi rumaisa" ya sake nanatawa.

Haushi ne ya ?ule Samha, kamar ta buWi baki, ta ce Allah ya tsinewa rumaisan.

Ammi ta gaya wa Jamil makarantar, ya fita da sauri ya Wau mota.

Mahmud kuwa ya kasa zaune ya kasa tsaye, atleast ya na son jin ya jikin Adam, a wani situation yake, abun da bai taSa ji ba sai yau.

Rumaisa kuwa tuni aka tashi, har ta fara ?uluwa, ta ce "Lallai papa, zaton sa ba zan iya tafiya ba kamar yadda na ce masa ko? To wallahi tafiyata zan yi, in bi hanyar da ba ta gida ba, in Sata sai ya nemo ni". Ta na cikin mitar, ta ga motar adam, sai dai ta ga jamil a ciki, dan haka ta tsaya ta na kallonsa.

Ya sauke glashin ya ce "Zo mu tafi"

"Mu je ina?".

"Can gida, takawa ba lafiya, ya ce na Waukkoki, ya na cikin gari wurin ammi".

"Sai ka ce ba ni da hankali zan hau motar da ka ke tu?awa, in je ka kasheni a banza, tun da na san ka tsaneni, saboda papa bai auri ?anwarka ba, to ba zan hau ba".

Ya kwantar da muryarsa ya ce "Da gaske nake yi miki, ni ba kasheki zan yi ba, ba dan shi ya ce na Waukko ki ba, ba abun da zai kawo ni".

"TaS, ka isa ka gaya mini magana in yadda, ai ni yadda mutum yayi mini a haWuwarmu ta farko da shi nake amfani. Ba Wazu papan? ya kawoni ba ka ce shi ya ce ya zo ya Wauke ni, bayan a gabana ranar ka ke yi masa rashin mutunci, ka ce wai bai gaya maka anty aisha an sace ta ba, to ba zan hau ka kasheni ba, ba kai ne yayan anty aisha ba, duk na san komai, da ku ka din ga cin zalinta, tun tana ?arama, sai da ta mutu za ku nuna kuna son ta. To wallahi ba zan hau ba, gara na tafi da ?afata".

Baki buWe yake kallon rumaisa, ita ba ta manta abu, waye ma ya gaya mata wannan zancen, ita aishan ce ko adam Win ne ya gaya mata? Kuma ai ba shi ne ya nuna wa aisha ?iyayya ba.

Ya dai-daita nutsuwarsa ya ce "?anwata ki na ji, shigo mota mu tafi, sai mu yi magana, duk wanda ya gaya miki zantukan nan ?arya yake yi, na san dai aisha ba zata gaya miki ba".

"Kai ni fa ba a lallaSani, kuma ba a hantarata ko ayi mini dole, ka tambayi mijina ka ji" ta juya tayi tafiyarta, kan ya kunna motar, ya bita, ta haye a dai-daita sahu, ta ce a kaita gidan tsohon galadima.

Ana zuwa ta sauka abun ta, sai masu gadi ne suka biya kuWin napep Win, ta nufi sashin Ammi, a ranta ta na raya idan ?arya Jamil yake, sai ya gane ba shi da wayo.

Sai dai ga mamakinta ta ga baba uwani a falon ammi, bayan a gida suka bar ta.

Ta na ganin rumaisa ta hau kuka, ta ce "Tun Wazu aka ce a zo a Waukko ki daga makaranta, yanzu aka kirani a waya, takawa babu lafiya".

Ruma ba ta amsa mata ba, ta fara laluben a ina adam ya ke.

Ta na kaiwa bedroom Win ammi, ta ji tsigar jikin ta ta tashi, kanta ya wani sara.
Kamar ?wai ya fashe mata a ciki, ta shiga Wakin.

Duk ga su Mummy a gefe, har da Samha da su Fauziyya su na kuka.

Rumaisa ta ?arasa kansa ta tsaya, sai fizge-fizge yake yi, kamar zai fita hayyacin sa.

Rumaisa ta waiwaya, ta ?urawa mummy ido, a take jikin Mummy ya hau rawa, ta fara kame-kame "Rumaisa ko?, kin ga takawa ba lafiya ko?? Dama yanzu yake ta kiran sunanki ya ce a Waukko ki".

Ammi ta ce "Rumaisa, ashe jamil Win ya Waukko ki?".

Rumaisa ta girgiza kai ta ce "Ni ba shi na biyo ba, saboda ya tsaneni, haka kawai in je ya kashe ni, ai haushina yake ji saboda takawa bai auri ?anwarsa ba, na zata ma ?arya yake yi, lafiyar papan ?alau, yaudarata zai yi na hau adaidaita sahu na taho".

"Yaya jamil Win ne yake yi miki ?arya?" Samha ta yi maganar a ?ufule.

"Waye shi da ba zai yi ?arya ba? Na faWa na zata ?arya yake yi, tun da a gabana yake yi wa papa rashin mutunci, wai bai gaya masa anty aisha ta Sata ba. Sai kuma ya zo ya ce mini papa bashi da lafiya na yarda? Ai ni a ganin farko nake gane mutum".

Ammi ta ce "Ruma ya isa haka, ki yi masa addu'a"

"Ammi ni fa rashin adalci ne da fuska biyu ba na so".

Kallonta duk suke yi, ba tare da gane in da zamcenta ya dosa ba.

"Ammi ki danne ni, ?asusuwana karyewa suke yi" maganar takawa ta sa suka mayar da hankalinsu kan shi".

Iman ce ta yi sallama a bedroom Win, jikinta a sanyaye ita ma.

Rumaisa ba tare da jin kunyar wani ba, ta zauna a gefensa, ta ri?o hannunsa da yake cikin na ammi, ta ce "Papa meye yake maka ciwo?"

Ya ri?e hannunta sosai, cikin tsananin ciwo ya ce, "komai ma, Allah idan mutuwa za ta zama hutu a gareni, Allah ka sanya na mutu, da wannan azabar da nake ji" yayi maganar yana sake ri?eta tare da yin ?ara.

Duk ta na jin azabar ri?on da ya yi mata, ta sunkuya dai-dai kunnensa ta ce "Papa ba kyau fatan mutuwa fa, idan ka mutu sabir fa, ammi fa? Dan Allah ka daina, ka bari in cikawa anty aisha al?awarin da na yi mata, zaka warke gaba Waya har abada" ta yi maganar tana zubar da hawaye.

Samha wani uban tsaki ta doka, ta tashi ta fita, abun da babu wani take gaya mata game da zamansu daban, abun da take gani yanzu daban.

Mummy ma tashi ta yi ta ce "Giwa, Allah ya bashi lafiya, amma akawai bu?atar ki din ga kwaSar sirikar ki, ta iya bakinta".

Ammi ta ce "To na gode".

Baba uwani ta kawo kai, suka haWu da Mummy, Mummy ta yi mata sigina da ido, sannan ta tafi.

"Ki yi mini Addu'a" ya faWa ya na sassauta ri?on da ya yi mata.

Baba uwani sai jera masa sannu take yi, iman ta kawo maganinsa, a shafa masa, ya ce ba ya so.

Iya abun da Allah ya sa rumaisa ta iya, ta din ga karanta masa, sai dai ta fi nanata la'iila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin. Saboda tana da ya?inin duk wahalar da ta shiga, idan ta karanta ta na samun mafita.

Lumshe idanunsa ya yi, ya daina hargowar da yake yi, ta kalli ammi ta ce "Wallahi ammi asiri aka yi masa, wai ku ba kwa ganin abun da nake gani?".

Ammi ta ce "A'a rumaisa, Allah ne ya Wora masa, muna fatan Allah ya yaye masa".

"Ammi, wai baku ga matar da take zaune tare da su Mummy ba, tana kallonsa, wata ba?a, idonta ya na ci da wuta, haka fa wataran idonsa yake yi, idan ransa ya Saci, kuma wallahi ni ban yadda da babar mahmud Win nan ba...... Kamar daWi take ji abun da ya samu baban sabir, sai murmushi fa take yi ku.........

Hannun sa ya saka ya toshe mata baki, duk da idonsa ya na rufe.

Rumaisa baba uwani take kallo, idan har abun da Mahmud da kuma Asiya suka gaya mata a kan baba uwani gaske ne, to za ta yi amfani da shawarar yaya usman, dan ranar da suka je gida, ba abun da ba ta gaya masa ba, kuma shi ya bata shawarar ta faWi wata maganar a gaban baba uwani, wadda ta san za ta iya zuwa kunnen Mummy.

A zahiri rumaisa ta ga matar da take faWa, a tare da Mummy, sai dai a wannan karon ma, ta gane ita kaWai take ganin ta.

Bacci ne ya Wauke Adam, rumaisa ta tashi ta ce za ta yi salla.

Ammi sai sannu take yi mata, saboda ta san idan har ciwon adam ya tashi, duk wanda ya yi wa wannan ri?on sai ya ji jiki, amma ta ga rumaisa ras da ita.

Maimakon ta je ta yi sallar, sai ta fice harabar gidan.
Lelle?awa take yi, ko za ta gano Mahmud, dan ta na da labarin gaya masa.

Bisa sa'a, ta ga yana tahowa daga waje, da alama masallaci ya je.

"Daddy" ta ?wala masa kira.

Yana hangota ya yi murmushi, ya ce "Daughter, ina takwarana?".

"Ya na wurin ammi, dama kai nake nema, Allah ya sa na ganka".

"To gani ya aka yi? Amma ba kya tsoron kar mijinki ya ganki, ya kuma hantararki?".

Ruma ta tura baki ta ce "Bashi da lafiya fa, kuma ko??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????wa ya zo duba shi, har da mamanka amma kai ba ka zo ba"

"To ai kin san ba shiri muke yi ba"

"Daddy meyasa?".

Mahmud ya numfasa ya ce "Manta kawai, ya aka yi?".

"Ka san maganar da muka yi ai ranar ko?, kuma ka ce zaka taimaka mini".

Mahmud ya ce "Ko zan yi wa kowa ?arya, ban da ?a ta".

Rumaisa ta ce "To ni fa na ce mamanka ce ta ke yi wa mijina asiri a gaban baba uwani".

Ya Wan yi shiru ya ce "Ke waye ya gaya miki haka?"

"Haka nake tunani, kuma nake son tabattarwa, amma so nake na kama baba Uwani, yaya usman ne ya bani shawara. Ni fa ban yadda matar nan mamanka ba ce, jiya mafarki na yi tana tura papa rami, yau kuma na ganta da wata mata, ba wanda yake iya ganinta sai ni, ba?a mummuna, idonta sai wuta yake yi, abar tsoro kawai dai ni ba ta tsorata ni ba. Papa sai ihu yake yi, abun tausayi"

Yayi zuru da ido yana kallon rumaisa, sai kuma ya ce "Da gaske ki ke ko da wasa?".

"Ni ba kullum nake yin ?arya ba" ta bashi amsa.

"So, you want expose my mother daughter?".

Ta yi shiru, tare da zuba masa ido.

Ya ce "Shikenan, ni na yi al?awari ai kuma zan cika in sha Allah, duk wani support da ki ke nema, i will assist in sha Allah, zan taimaka miki, ki cika al?awarin da ki ka yi wa fulani, amma yaushe zaki bashi bayani a kan abun da yake nema na binciken? Ya na son aisha sosai, a yanzu ba shi da burin da ya wuce, ya gano wanda suka saceta".

Rumaisa ta ce "Kamar ka na son takawa? Tun da har ka san abubuwa a kan sa, amma meyasa ba kwa shiri?"

Jiki a sanyaye ya ce "Kar ki damu, lambar wayata na nan, na rubuta miki, a bayan sashin su mijinki, duk lokacin da ki ke bu?ata ki kirani, idan har ina Nigeria" yana gama faWa ya juya zai tafi ta ce "Idan kuma na gane ka zaSi uwar ri?on ka, ka yaudareni, zan yi maka abun da ba ka zata ba, zan iya yin komai a kan uban Wa na"

Cak ya tsaya, ya waiwaya ya kalleta, kawai ta kwashe da dariya, ta ce "Kamar a film ko? Zan iya acting ashe, ai na san ba zaka yi mini haka ba"

Tun da ya dawo ?asar nan, suka haWu da rumaisa, suka yi magana, yake jin kamar wani abu ya sauya a tare da shi, sosai yake jin tausayin Adam, kuma a jikinsa yake jin, lokaci ya yi, da yakamata Mummy ta tuba, shekaru sun fara ja, ko ba komai ta mutu ta samu rahamar Allah, sarautar da take yi masa ?uzu kuma, shi ba a gabansa take ba ma.

A Wakin Iman rumaisa ta yi salla, iman ta baya doguwar rigarta ta saka, suka zauna su na Wan taSa hira, iman ta Wan bata labarin, irin wahalar da yake sha, idan yana ciwon nan, da kuma wahalar neman magani da ammi take yi, ba yau ba gobe".

Iman ta Wora da cewa? "Anty rumaisa, da kin sani ba ki faWi maganar nan ta Wazu a gaban mutane ba, ba zan musa miki mummy ba ta asiri ba, amma idan maganar ta koma kunnenta fa? Zai iya haddasa wata rigimar".

"Ai na ga duk wanda yake wurin, amintacce ne. Waye zai je ya faWa? Ammi ce za ta gaya mata, ko kuma ke? Ko kuma baba uwani, da dama dan ita na faWa"

Iman ta kalli rumaisa da mamaki, rumaisa ta yi dariya, ta ce "Iman, ina da wayo fa, kawai dai ba na ji ne, amma dan Allah Meyasa papa suke gaba da daddyna? Ko da ba ammi ce ta haifesu duka ba, amma ai ?an uwa ne"

Iman ta ce "Duk ?a?an ammi ne"

Rumaisa ta ce "Ai na zata kema zaki raina mini hankali ne, ai na sani, na san duk ammi ce ta haifesu, amma daddy ya dage wai waccan matar ce babarsa, amma dan Allah meyasa gaba Waya gidan nan naku, a hargitse yake? Kowa ba shi da gaskiya".

Iman ta rausayar da kai ta ce "Ai ba abun da ki ka gani, family ne mai cike da rikici da ?ulla-?ulla".

"Ai shi ne wannan yayan anty aishan, zai raina mini hankali, ni kuma wallahi yadda mutum ya mu'amalance ni a farko, haka nake tafiya da shi, kin ga rashin mutuncin da suka yi mini ranar da muka je gidan su, da shi, da wannan masifaffiyar mai jan kaya ta Wazu, da wannan jabir Win, shi ma jabir Win da babarsa, wadda ta riga Mummy tafiya Wazu.
Wai takawa ya turo shi ya Wauke ni daga makaranta, na ce ba zan hau motarsa ya kashe ni ba, dan na san haushina yake ji, saboda takawa bai auri ?anwarsa ba, wai ni zai yi wa dabara, a gabana fa ya yi wa papan wula?anci, wai an sace ?anwarsa bai gaya masa ba, shi a wa? Sai ka ce son anty aishar suke yi".

Iman ta ce "Ke dai kawai ki ce, an taSa miki miji kin ji haushi. In dai yaya jamil ne sun saba, faWa da takawa kuma daga baya su zo su shirya. Amma duk da haka na yi mamakin yadda ki ka iya kawo, yaya Mahmud sashen nan, ba ya son ammi da abun da ya shafe ta, balle adam. Lokaci na ?arshe da ya zo, shi ne lokacin da aka fasa aurena, saboda rashin asali, ammi ta ro?e shi ya aureni, har da kukanta, ya ce ba ya so na, ba zai aureni ba". Ta yi maganar hawaye fal idonta.

Rumaisa ta yi shiru, ta ce "Wane irin abu ne wannan kuma? To duk saboda me? Ban gane ba ki da asali ba"

Iman ta share hawayen da ya zubo mata, ta ce "Zan yi miki bayani, yanzu mu cigaba da addu'a papan mimi ya warke" ta yi maganar cikin ?arfin hali tana murmushi.

"Shikenan, ara mini wayarki, na kira gida na gaya musu papa ba lafiya".

Iman ta ce "Amma idan mai sunan baba zaki kira, ki yi masa magana ta what's app, ya hana ni kiransa a waya".

Ruma ta ce "Au kuna waya ne dama?" Ta yi maganar tana dariya.

Da sauri Iman ta ce "A'a, ba waya muke yi ba, ke ce da ki ka kira rannan bai Waga ba".

Ruma ta yi dariya ta ce "BuWe mini data mu yi magana da shi".

Iman ta karSa ta kunna mata data, ta ba ta, yaya umar ta ga iman ta yi saving number.
Ruma ba ta ce komai ba, ta yi masa voice message "Mai sunan baba, ni ce, ka gaya wa mama mijina ba shi da lafiya, mu na gidan ammi, idan ka ga message Win dan Allah ka yi mini magana, rumaisa ce".

Iman ta zare ido ta ce "Ba kya jin kunya, ki ke cewa ace da ammi mijinki babu lafiya"

Rumaisa ta mi?e tsaye ta ce "To me zan ce? Ai maman ma mijina take ce masa, bari na je na gani ko ya tashi, idan mai sunan baba ya yi magana, sai ki kira ni" ta fita daga Wakin, ta tafi na ammi.

Ammi ba ta Wakin, ta tarar da adam a zaune, sai dai ta ga samha a zaune a gefen sa, da flask Win abinci.

Wani abu ne mai nauyi, ya daki zuciyar rumaisa, da ba za ta iya tantance ko menene ba.

Iman kuwa ta cigaba da chatting Win ta, sai ga video call na mai sunan baba.

Gudun kar ta yi laifi, kan ta kai wa ruma wayar ta katse, ya sanya ta Waga, gabanta ya na faWuwa.

Maimakon ya ga rumaisa, ya ga kyakywar fuskar iman, ta bayyana a kan screen Win wayarsa.

Ta Wan sunkuyar da kai ta ce "Barka da yamma yaya umar"

Sunkuyar da kanta da ta yi ne, ya bashi damar ?are mata kallo, ya na jin releif na abun da yake damun ruhinsa.



Ayshercool
08081012143
What's app only please, ban da kira please =?O?.
? 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank.

Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please =?O?



Jin shirun ya yi yawa, sai da ta yi zaton, ko wayar ya katse, ta sake Waga kanta, ta ce "Ina wuni yaya umar?".

Wata Soyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke, ya ce "Lafiya ?alau, ya mutan gidan?".

Cikin jin daWi ta ce "Suna nan lafiya, ya mama da su Yaya Aliyu"

"Lafiya ?alau, na ga message Win wannan Yarinyar ne, na mijinta ba shi da lafiya". Yayi maganar yana sake fatan iman ta Wago kanta ya kalleta, ko ya cigaba da jin nutsuwa a zuciyarsa.

Ba tare da ta Wago Win ba ta ce "Eh, ba shi da lafiya, su na gida ita da shi".

"Za su koma gidansu yau ne, ko su na nan?"

"Wallahi yaya ban sani ba, amma dai ba na tunanin su koma yau, bari na kai mata wayar, yanzun nan ta tashi".

"No ?yaleta, idan ta dawo ki ce mu na yi masa sannu, Allah ya bashi lafiya, a gaida sabir".

Murmushi ta yi ta Wan Wago ta ce "To in sha Allah zan gaya musu, mun gode sosai".

"Zan shigo zuwa an jima, sai na duba shi".

"To yaya umar, Allah ya kawo ka lafiya"

Ji yake tamkar kar ya katse wayar, wata irin narkewa zuciyarsa take yi, da jin iya muryarta kawai. Mussman idan ta kira shi da yaya umar, ji yake tamkar ta fi kowa iya faWar sunan.

Kamar wanda aka yi wa dole, haka ya kaste kiran wayar, ya lumshe idonsa ya na haki, ya na gazgata zuciyarsa da babu tantama wannan shi ne so.

Girgiza kansa ya yi ya ce "Ya salam, why? Why? Abun da ban taSa yi ba, ni ko shirin aure ba ni da shi, ina zaman zamana meya aikeni" ya tambayi kansa. Gashi Abubakar ne abokin hirar sa, Abubakar baya nan, kuma duk da haka ma, ya san idan ya gaya masa dariya zai ta yi masa, abun da ba ya so, dan haka yake jin, zai iya jure koma menene.

A ?asan zuciyarsa ya ji kamar dama ce, da zai yi amfani da zuwa duba Adam, ko zai samu ya ga iman.

Rumaisa kuwa, takawa ya ga reaction Win ta, ta ?arasa wurinsa ta ce masa "Wai dama ka tashi, ina ammin?".

"Ta fita ita da Nusaiba" ya bata amsa.

Ta je ta zauna a kusa da shi, ta ce "To meyasa baka ce a kirawo ni ka tashi ba?"

"To yanzu ba ga shi kin zo na tashi ba".

"Ammi zan mutu, ki zuba mini ruwan sanyi, idan mutuwa ce hutu a gareni Allah ya sa na mutu, to ba in da za ka mutu ka tafi, sai na gama makaranta mai lilo" ta yi maganar farko tana kwaikwayon sa.

Murmushi ya yi, da sai da ha?oransa suka bayyana, ya ce "Rashin lafiyar ta wa ce, ta zama abun tsokana kuma".

"Wane irin wula?anci ne, ina magana da Wan uwana zaki zo ki zauna ki na wasu surutan banza?"

Rumaisa ta kalli Samha ta ce "Au dama Wan uwanku ne? To ni kuma ?arewar ?an uwantaka gidansa a kai ni na zauna, ke meyasa ba a kai ki ba? Me Wan uwa?"

"Shut up" yayi maganar yana matse mata baki.

"To ina ruwanta da ni, ba bu kyau wata ta kula mijin wata ba?" Kallonta kawai yake yi.

"To ina ruwana. ka ci abinci ne?"

Ya numfasa ya ce"Ammi ta bani, tun da tafiyarki ki ka yi, ki ka barni".

?an shiru samha ta yi, abun da take gani yanzu, ya sha ban-ban da wanda baba uwani take gaya mata, ?arya take yi mata kenan ko kuwa? Ta ce mata ba sa wani jituwa, amma alamu sun nuna mata, kamar sha?uwa a tsakanin su, babban tashin hankalin ta da fatanta, Allah ya sa wani abu bai taSa faruwa tsakanin su ba, ta kuma fuskanci rumaisan tantiriyar fitsararriya ce.

Ruma ta ce "To yanzu ya ka ke ji, da sau?i jikin?"

"Eh, Alhamdilillah"

"To sannu, ka tashi mu tafi gida"

Adam ya ce "Mu je gida ki yi yaya da ni, ba iya jinyata za ki yi ba"

Mi?ewa Samha ta yi, ta fice zuciyarta na zafi, a gabanta adam ya sakarwa wannan shegiyar yarinyar baki, wata banza da ita mara aji, balle mamora.

"Kuma duk mai kula mijin wata, Wan wuta ne, kuma sai ya daina magana" ta yi maganar cikin Waga murya.
Samha ba ta ko juyo ba, ta yi gaba tana ?wafa, ba dan Adam ya auri rumaisa ba, da duk hakan ba ta faru ba, ta Wora zargin komai a kan sa, kuma ya kasa tsawatar mata.

Samha na fita, ya rungumo rumaisa jikinsa, tare da kwantar da kansa a jikin na ta.

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, meye haka kuma, dan Allah ka cikani"

Bai ce uffan ba, ya ?ara lafewa, yana sauke numfashi.

Shiru ta yi, ba ta kuma ko motsawa ba, ta na jin bugun zuciyarsa a jikinta.

"Ita ma haka ka yi mata ko?"

"Ita wa?"

"Wannan matar da ta fita yanzu".

"Eh, tun da ba kya jin magana, ba zaki saita bakinki ba, idan ta zaneki shikenan" ya sake rungumeta sosai.

Cikin tsoro ta ce "Ba kyau fa"

Yayi ?ar guntuwar dariya, yanzu abubuwanta sun daina bashi haushi, akwai wayo wasu lokutan, wasu lokutan kuwa kanta a kwano yake, gashi dai ta fara girma, amma kamar ba mutum ba, har mamaki take bashi".

Ya kalleta ya ce "Wani al?awarin ki ka yi wa fulani?"

Ta numfasa ta ce "Ba yanzu zan faWa ba. Kuma gaskiya ka Wagani, ka yi mini nauyi, na ji da matsar hannun da ka din ga yi mini Wazu, ?asusuwana sai ciwo suke yi".

Bai Wagata ba, ya kwanta sosai a kan cinyarta, ya lumshe idanunsa.

***
A fusace Jamil yake sosai, ya dubi Jabir ya ce "Jabir, har ni wannan Yarinyar za ta yi wa fitsara, wai ba son fulani muke ba, kenan adam zuwa ya yi yana Sata mu a wurinta, abun da ya wuce ba ya riga ya wuce ba? Shikenan ba ni da zarafin bincike a kan ?ar uwata, ni da a tunanina, na lallaSata na samu wani abun daga bakinta, yadda ka san na harbeta na huta, ka ga iskancin da ta din ga yi mini?"

Jabir ya ce "Wai kai da na gaya maka halinta baka yadda ba? Kai ka ga zaryar da jami'an tsaro suka din ga yi tana asibiti, amma ta ?i magana, sai da aka kai ruwa rana, sannan ta yi".

"Ni anya ba fulanin ce ta gaya mata wani abun ba?"

Jabir ya ce "Ba tabbas, ka san halin Aisha bana tunanin ita ce, bari dai a yi sallar magariba, zan shiga na duba shi"

"Ka dai yi a hankali, ciwon nan nasa ne, ya tashi, ka san kuma sha?e mutane yake yi".

Jabir yayi murmushi bai kuma cewa komai ba.

Tamkar mai comedy, haka rumaisa take ta zuba, tana yi wa Adam shirme samfur -samfur.

Can kuma ta ce "Tashi, in Wauko maka filo, cimyata ta gaji, zan kuma

Please Login or Register in order to submit comment