You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mama ta yi maganar a hasale.

"Mama biri kuma, ba amin ba gaskiya, dan Allah idan irin wannan addu'a ki yi mini ki daina, ni wallahi kyakykyawa na ke so"

"Kyan banza da na wofi, kyan Wan maciji ki auri kyan ya din ga gasaki ba gara mummuna na gari ba"

Ruma kamar za ta yi kuka ta ce "Ina wani abin arziki a muni"

Mama ta hau ruma da faWa, ruma ta yi shiru, amma a duk sa'ar da mama ta ce Allah ya bata miji nagari duk muninsa a zuciyarta za ta ce ba Amin ba.

Yau ruma Alla-Alla take gari ya waye, sai murmushi take ita kaWai.

Yasir ne ya lura da ta na fara'a, dan haka ya ce "Wai ke murmushin me ki ke yi ne haka?"
Ta gyara zama ta ce "Ka san tun da na shiga sakandare, ban yi faWa da kowa ba, so nake na zama 'yan mata, in din ga tsayawa a cacar baki, to ni cacar baki ba ta biya mini bu?ata, na fi son na haWawa yarinya malaman jikinta, muka yi faWa da wata yarinya, ka san ni ba na zagi, ta dinga zagina in gaya maka, amma ban yi kuka ba.
Kawai yau na ga babarta ta zo makarantar mu, da ?yar ta shiga ofishin principal saboda girmanta, ina ga ta yi rabin bangon Wakin mama.
Kai ina ga fa ta yi yakuzuna na jikin receiver girma, koma ta fishi, shi ya sa nake son Allah ya kaimu gobe, za ta gane ba ta da wayo, ba dai har da cewa babata tsohuwa ba ce, wallahi a jikin allo zan zana babarsu.




Ayshercool
08081012143
[19/07, 8:42 am] JAKADIYAR AREWA: ?ANWAR MAZA
? ? ? ? ? ? ? ??

Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing? YouTube channel Win
@Cool Hausa Novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro.







14

BuWe baki Abdallah ya yi ya na kallon ruma, bil ha??i take maganar har cikin zuciyarta.

"Ke fa hankali bai wadaci ?aramar ?wa?walwarki ba, sai ki je allo ki zana babar wasu, idan aka zana taki zaki ji daWi?"

"Ai ni na yi al?awarin na daina dambe, ta zageni na kasa ramawa, saboda ashar take yi, ni kuma bana zagi, gaba Waya ta cuceni ta Sata mini rai, ni kuwa ba ta san ba a taSani a ci bulus ba, wallahi sai ta gane kurenta"

Abdallah ya girgiza kai ya ce "No, ki nemi wata hanyar dai, amma ban da iyaye, ba abin wasa bane"

"Iyaye ba abin wasa bane, ta ce mini mara tarbiyya babata tsohuwa, sai na ci buhun ubanta, ranar ma a sanyi ta sameni, da sai na tayar mata da aljanu na yi mata dukan tsiya, to bana som daga shigata makarantar a tsaneni ne, ayi mini mummunar shaida". Duk yadda Abdallah ya so nusar da ruma, ta yi biris ta ?i fahimta ta yi alwashin ramuwar gayya a kan abin da aka yi mata.

*****
Nasihar da takawa yake yi mata, a hankali ta ji ta ratsata sosai da sosai, daga ita har shi suna fuskantar jarrabawa daban-daban, wanda hakan yake jefa Ammi cikin damuwa.

Nusaiba ta kalli Takawa da Iman ta ce "Iman 'yar gidan yaya, Ammi ta ki yayan ma naki"
Murmushi iman ta yi tana sake gyara zamanta.

Turo ?ofar falon aka yi, suka Waga kai gaba Wayansu suka kalli ?ofar. Jabir ne ya shigo, da sallama a bakinsa. Suka amsa masa gaba Waya, hankalinsa ya na kan Iman ya na ?are mata kallo. Hakan ya sanya ta haWe rai tana Wan kawar da kai gefe.

Yayi murmushi ya kalli Adam ya ce "Ni zaka yiwa haka, ka dawo amma sai dai na ji a gari ko ka neme ni"

Takawa yayi murmushin gefen baki ya ce "Ai idan ka san na dawo, zaka dameni ne ka sani yawo a gari, shi ya sa na yi shiru so nake sai na huta, shi ya sanya ma ban zauna a gidana ba, na yo nan"

Nusaiba ta ce "Uncle J, ina wuni?"

"Lafiya lau Nussy, Iman ba magana ne? 'yar rigima"

Ba dan ta so ba ta ce gaishe shi, gaba Waya kwanan nan ba ta son abubuwan da Jabir yake mata, wanda ta kasa gane kan su.

Suna tsaka da hirar sai ga sallamar su Fauziyya da Ru?ayya, tare da Samha suka shigo falon.
Gaban Iman ya faWi da ta ga Samha, musamman wani irin kallo da take bin ta da shi, da Iman Win ta kasa gane wane irin kallo ne.
Jabir suka fara gaisarwa, sannan cikin girmamawa suka gaida Takawa. Cikin halinsa na ko in kula da kuma tsare gida ya amsa musu.

Fauziyya ce ta gyara zama ta ce "Yaya ashe ka dawo, bamu san ka dawo ba, sai Wazu Mummy ta ce mana, ai ka dawo"

"Eh na dawo" ya faWa a ta?aice.

"Masha Allah, ya ibada?"

Ya amsa da "Alhamdilillah"

"To Allah ya sa an yi karSaSiyya".

Samha ta gyara zama, ta na yiwa Adam wani irin shu'umin kallo, ta Wan murmusa sannan ta ce "Takawa, ni fa kwance jaka na zo yi, daga zuwa wurin su Fauziyy, na ji suna cewa za su shigo yi maka sannu da zuwa, na ce bari na biyo su in yi sannu da zuwa, kuma a bani tawa tsarabar"
A hankali ya Wago idonsa, ya kalli Samha, ya Wan yi murmushi tare da girgiza kai amma bai ce komai ba.

Jabir ya dubi Iman ya ce "Iman, duk kin ma?al?ale mana shi, kamar ke kaWai ki ka yi kewarsa, ki barmu mu ma mu gana da shi sosai mana" yayi maganar da sigar wasa.

No?e kafaWa ta yi kamar ?aramar yarinya, sai dai suna haWa ido da Samha, samhan ta sake yi mata wani mugun kallo, da ya tilasta mata sunkuyar da kai.

"Jama'a ya shirin bikin Jamilu Turaki, Takawa akwai kilisa fa ranar Juma'a"

Adam ya girgiza kai ya ce"Kai, ?yaleni da wata kilisa, duk na gaji, ni ban so ku ka san na dawo ba ma, ina bu?atar hutu sosai "

"Amma ba dai ka na nufin, ba zaka yi hawan ba, Jamil Win guda?"

"Sai na yi tunani tukuna, idan ina da time"

Jabir ya ce"Ba ruwana, kai da shi"

Tsarguwa da rashin sukunin da idanun Samha suka sanya Iman ne ya sanya ta mi?e ta ce "Ni dai sai an jimanku, zan je na huta"

Samha ma ta mi?e ta ce "Mu je, ina son na gaida Ammi kan na tafi " jikin Iman ya yi sanyi, dan ta san akwai wani abu a ran Samha data ce za ta bita ta gaida Ammi.

Suna shiga ?ofar da zata sada su da sashin Ammi, Samha ta ri?o hannun Iman, ta tsayar da ita suna fuskanta juna.

Cikin raunaniyyar muryarta kamar mai shirin yin kuka Iman ta ce "Me na yi miki?"

Samha ta ?arewa Iman kallo, sannan ta ce "Wai wace irin yarinya ce ke, kin manta kashedin da na yi miki ko sai na sake nanata miki?"

Iman ta Wan Sata fuska, ta aro jarumta ta Soye tsoron ta ta ce "Anty Samha, ni babu komai a tsakanina da takawa, ki yarda da ni mana, ina jin sa kamar wanda muka fito daga ciki Waya, ni ba zan iya aurensa ba"

Samha ta ce "?arya ki ke yi, ba wani ki na jin sa kamar wanda ku ka kwanta ciki Waya, ai ba ki da kimar da zaki kwanta mahaifa Waya da Adam, ko kin manta wacece ke?"

Iman ta girgiza kai ta ce "Ban manta ba, 'yar karere ce ni, wadda ba ta da gado a gidan Galadima, wadda aka taimakawa aka ri?e, ina sane ba sai kin tuna mini ba".

Samha ta yi wani murmushi sannan ya kuma duban Iman ta ce "?warai kuwa kina sane, ban da Ammi ta nace da a cikin barorin gidan nan ya dace ki tashi ba 'yan gida ba, dan haka ki kiyayi shiga gonata"

"Amma ta yaya, a tare muka tashi da takawa, ta yaya za ki ce sai na nesanta da shi?"

Ta Wage kafaWa ta ce "Wannan matsalar ki ce, ba tawa ba, dan na ga alamar tun da ba ki samu wancan ba, wannan zaki hara ki shiga hankalinki".

Iman ta girgiza kai ta ce "Ni babu abin da ki ke tunani tsakanina da takawa, amma ke ma Anty Samha bana tunanin zaki samu abin da ki ke so, akwai katangar ?arfe a gabanki, kuma kin san takawa kin san halin sa sarai, ki bi a sannu" daga haka tayi gaba ta bar Samha a tsaye.

*****
Kamar yadda ruma ta yi alwashi, haka ta yi, ta je ajinsu ta zana wata shirgegiyar mata a kan allo, ta yi labelling Win ta. Gefe kuma ta zana ?arama wadda ba ta kai matar ba, ta yi labelling ta rubuta Asiya shu'aibu.
'yan ajin suka dinga tuntsira dariya, saboda yadda zanen ya yi.
Ita kuwa Asiya ba ta san me aka yi ba, sai dai tana shigowa ta ga 'yan aji suna kallonta suna dariya.
Saroro ta yi, tana son gane me suke yiwa dariya, ba ta kula ba ta je ta zauna, sai dai ta na zaman idonta ya sauka a kan allon, ta ga ta'asar da ruma ta yi.
A firgice ta tashi tsaye, tana zazzare ido "Uban waye ya yi mini wannan rashin mutuncin"

Ruma ta mi?e ta ce "I am madam"

"Saboda tsabar kin raina wa kan ki hankali, kina nufin wannan babata ki ka zana?"

"An zanata Win, ni ba cewa ki ka yi babata tsohuwa ce ba, ashe ma babata ta fi taki kyau"

Kan ruma ta farga, Asiya ta diro gaban ruma ta sha?e ruma da hijjabinta. Kan ruma ta farga Asiya ta rufeta da duka, ta kaita ?asa saboda ta rufe mata fuska da hijjabi. Kan ruma tayi wani yin?uri, Asiya tayi mata duka.
Da ?yar aka kirawo wani malami, ya janye Asiya daga kan ruma.

Malamin ya tasa su a gaba zuwa ofishin malamai, dan hukunta su, ruma ta shafa bakinta ta ji jini, tun da take a rayuwarta ko da za ta yi dambe a fitar mata da jini, to tabbas a duba wanda suka yi damben ta lallasa shi shi ma.
Gaba Waya Wani irin ba?in ciki ya mamaye ruma, gaba Waya ta rasa abin da yake mata daWi, tun da take ba a taSa galaba a kanta ba sai yau.

Ko da aka je staff room ana mayar da yadda aka yi, ruma ta?i magana, sai idonta da ya yi jawur, aka yo caaa a kan ruma, malamai suka din ga yi mata faWa a kan bata kyauta ba zana babar Asiya da ta yi, suna kiranta mara Wa'a.
Haryanzu malaman basu san wacece ruma ba, dan tun da Allah ya sanya ta zo makarantar ba ta taSa gwada musu halinta ba.
Aka ce sai ruma ta bawa Asiya ha?uri, sannan za ta yi wankin banWaki na sati guda, ita kuma Asiya zata yi sharar aji na kwana uku, saboda Waukar mataki da ta yi suka yi dambe da ruma.
Juyin duniya ruma ta yi magana ta?i, ?ememe ta?i bayar da ha?uri, dan haka aka sakata Kneel down har aka tashi a rana.
Babu abin da take tunani sai abin da za ta yiwa Asiya ta huce daga wannan ba?in cikin.

Ko da aka kaWa ?ararrawa, ruma ba ta jira malaman su sallameta ba, ta tashi ta tafi aji ta Wauko jakarta, Asiya ta din ga yi mata dariya har da gwalo. Wata nutsuwa ce ta shigi ruma a lokacin, dan a lokacin ji take da da wani abin dukan a kusa da ita, to tabbas sai ta illata Asiya.
Ta Wau jakarta ta fice, har ta je gida kamar zararriya jikinta a sanyaye.

Tun da mama ta ga ruma ta shigo babu ko sallama, ga uniform Win ruma a du?un?une ga busashshen jini a gefen bakin ta, ta san yau ta yi halin na dambe, ga takalminta da jakarta a hannu ta shigo da su, gwiwar wandonta ta yi kaca-kaca da ?asa.
Ta zubar da su a tsakar gida ta shige Wakin mama kawai ta nemi wuri ta kwanta.
Ba ta tashi ba sai bayan azahar, ta tashi ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallar azahar, ta kuma neman wuri ta zauna a tsakar gida.

"Mutuniyar, wai ya aka yi ne? Zo ki sayo mana kifi mu ci Abinci, tun da na dawo nake cigiyarki" yayi maganar yana le?a fuskarta.
Maimakon ta amsa masa kawai ya ga hawaye a fuskarta.

"Ke, menene mama ce?"

"Yaya Usy"

"Na'am rumaisa"

"Ni za a daka a hana kuka? Zuciyata zata fashe" tayi maganar tana sake fashewa da kuka.

Rarrashinta ya shiga yi, yadda ya ga tana neman ta shiWe, idanunta duk suka yi ja.
Ya din ga lallaSata ta gaya masa abin da ya faru.

Mama da take jin su ta ce "Allah ya ?ara miki, Allah ya sa yau da ki ka samu wadda ta zane ki, ba zaki sake dambe ba, dama ban da iskanci meye na zana uwar wani, idan ke aka zana taki uwar zaki ji daWi?"

"Mama cewa fa ta yi babata tsohuwa"

"To sai me? Tsufa ai arziki ne, ruma ita duniya 'yar siyasa ce, ba komai ?arfi yake baka ba, amma kin kasa gane hakan"

Wani irin kallo take yi wa mama, wato ita mama ko a jikinta kenan.

Usman ya kawar da fuskar ruma daga kallon mama. Abu ne mawuyaci ruma ta yi fushi, ko an Sata mata rai sai dai ta yi kuka, idan ta gama kuma shikenan ya wuce sai a shirya, amma yadda idanunta suka yi yau ya tabattar masa da ta kai ma?ura a Sacin rai, ba a taSa defeating Win ta ba sai yau. Irin zuciyar mai sunan baba ce da ita, idan rai ya Saci silently suke fushi, sai dai suna shiga mawuyacin hali, har gara shi Umar yana shouting wasu lokutan, amma ruma gaba Waya kasa komai take idan tana cikin matsanancin Sacin rai. Wata irin ajiyar zuciya kawai take yi.

"Yaya ni raguwa ce ko? Aka zageni, a kan gaskiyata kuma aka hukunta ni, ni ko?"

Usman ya yi ?asa da muryarsa ya ce "Ke ba raguwa ba ce, kowa shaida ne, kamar yadda nake gaya miki, ki fuskanci duk wani abin da yake baki tsoro, gaba da gaba na tsaya miki"

Ta Waga kai ta kalli Usman, ya jinjina mata kai alamar ?warin gwiwa, ta jinjina kai ta mayar da kai ta kwanta a jikinsa, tana cigaba da ajiyar zuciya.

Duk wanda ya shigo ya ga ruma a haka, sai ya tambayi ba'asin meyafaru, ko ba ta da lafiya ne?
Mama ta ce "Ina fa, lafiyarta ?alau, yau bori ne ya kar boka, ta tsokano wadda ta fi ?arfinta, aka naWa mata duka, shi ne take nema ta suma ki cigaba kar ki fasa halinki"

Aliyu ya tsaya a kan ruma ya ce "Ke, ki na wani sokwancin ki ka yadda aka dake ki har ki ke wa mutane kuka?" Ruma ta yi shiru ba ta amsa ba.

"Ina fatan dai ba a gaban wadda ta dake kin ki ka yi kukan ba? Wallahi da ina gidan nan sai kin fita kin rama, dan ubanki yaushe ki ka koma shashasha har aka dakeki aka fitar miki da jini, 'yar uban waye da baki taka mini ita ba"

BuWe baki mama ta yi, ta kalli Aliyu ta ce "Gadanga, maimakon ku tayani yi mata faWa, ku ke mara mata baya? Ba sai ku ce Allah ya sa hakan ya zama silar shiriyarta ba"

Aliyu ya girgiza kai ya ce "A'a Addu'a ce kawai za ta shiryata, amma ba a daketa a waje ta tsaya tana kuka ba, babu rago a gidan nan, ko Wan uban waye ta daka zamu bada ha?uri, amma wallahi aka kuma dukanki a waje, ki ka zo mana gida ki na kuka, sai na ?ara miki wallahi, idan mazane kawai ban yadda ki yi faWa da maza ba, ki zo ki gaya mini, amma mace dai 'yar uwakki, ki tattaka mini kowacece"

Aikuwa mama ta haWasu gaba Waya ta din ga faWa kamar ta ari baki.

"Kaf cikinku babu wanda na sha wahalr rainonsa kamar ruma, amma kuna zigata ta Wauko magana, rainonta dai-dai yake da rainon fitinannun yara maza huWu, maimakon ku tayani dawo da ita hanya, amma ku ke ingizata"

Gaba daya suka yi wa mama shiru, ta yi ta banbaminta ta yi ta gama.

*****
Karkarwa jikinsa yake yi, tamkar zai hau bori, jikinsa sai wani ?a??amewa yake yi, tamkar ba jikin Wan Adam ba.
Wata matashiyar mace ce zaune a kan gadon, tana kallonsa, ido fal hawaye, ya yin da shi kuma ya cigaba da tunkararta.
Girgiza masa kai take yi, amma ta kasa motsawa balle ta gudu.
Yana zuwa ya zauna a gabanta ya tsura mata ido, ya mi?a hannunsa kan cikinta, take jikinta ya hau rawa ta rintse idanuwanta, tana zubar da hawaye. Sautin muryarta ne ya dakatar da shi ga aikata abin da yake ?o?arin yi
*Sarki ka ganni, ya na ga sarki da ?ananan kaya, sarki ka kalleni* tamkar a zahiri haka yake jin muryartata a cikin kunnuwansa, a hankali ya buWe ido ya na ?arewa Wakinsa kallo. Sai a lokacin ya gane mafarki yake yi, ba zahiri bane.
A hankali ya tashi ya zauna, ya yaye bargon da ya rufa da shi, ya kalli agogon da ke kafe a jikin bangon Wakin. ?arfe tara da rabi.
?an guntun tsaki ya ja, me yasa yake yawan jin muryarta ne? Anya ba aljana ba ce ita ma?. Gabansa ne ya faWi da yayi wannan tunanin, da kuma tuna matsalar da yake ciki, yake ta neman mafita a kanta.
Saurin girgiza kai ya yi, ya sauka daga kan gadon, ya wuce banWaki.

****
Cikin matsanancin razani ta ?wala ihu "Wayyo Allah mama" a gigice mama tayi kanta tana faWin "Ke lafiyar ki kuwa?"

Tashi ta yi zaune ta na rarraba ido, tana kallon Wakin.

"Lafiya menene?"

"Mafarki na yi na tsorata"

Mama ta ja tsaki ta ce "Ba dole ki dinga mafarki kina tsorata ba, tun da ba kya Addu'a kwanciya bacci".

"Wallahi mama na yi"

"Ke ki ka sani dai, ko a garin neman maganar ki ruma, kya tsokano abin da zai dinga tsorata ki, ya hana ki bacci tashi ki je ki yo alwala, yanzu za a kira sallar asuba.
Haka nan jiki babu ?wari, ta tashi ta yi alwala ta gabatar da raka'atanul fajr, sannan ta yi sallar asuba.
Jikinta duk yayi sanyi da mafarkin da ta yi, amma ta kasa tuna me ta gani a mafarkin ya tsorata ta.


Babu wanda Ruma ta kula a ajinsu, ta nemi wuri ta yi zamanta ta yi shiru, tana ta takura ?wa?walwarta, ta tuna mafarkin da ta yi ya bata tsoro, amma ta kasa har aka kusa tashi, hankalinta baya tare da ita.

Asiya ce ta zo kan ruma ta tsaya, ta ri?e ?ugu ta ce "Ki je ki wanke banWakin da aka saka ki, ko na je na faWa" tamkar ruma na jin tsoron Asiya, haka ta tashi jiki na rawa zata fita daga ajin, sai dai ta yi burki a gaban allo, ta Waukko chalk a aljihun rigarta, ta sake zana wata shirgegiyar matar, wadda tafi ta jiya, ta yi labelling Win ta.
Ta waiwayo kuma tana kallon Asiya, tare da jiran ko ta kwana.

Aikuwa kamar ruma ta san a rina, Asiya ta kuma nufo ruma, tana zuba ashar, kan ta ?araso ruma ta yi ciki da ita, suka faWa kan wasu Walibai.
Hannun Asiya Waya ta samu, ta din ga duka kamar ta samu Sarawo, sai da ta tabattar da ba zata iya kai duka da hannun ba, sannan ta koma fuskarta.

An kai ruwa rana kan a ?waci Asiya daga hannun ruma, sai a lokacin ruma ta ji hankalinta ya kwanta, ba?in cikin da ya tokare mata zuciya ya sauka.
Babu wata-wata, malamin su ruma ya saka su kneeldown a rana, ba tare da ya tsaya ya ji ba'asin ma meyafaru ba.

Tun a lokacin Asiya ta ji ba ta iya motsa hannun da ruma ta din ga jibga, ta din ga jin kamar ba a jikinta yake ba.

Suna Kneeldown ruma ta ri?e ?ugu ta ce "Ke kin isa ki dakeni na ?yaleki, hmm baki sanni bane, kuma wallahi ban huce ba, zaki ga abin da zan yi miki, ki dakeni ki zageni, sannan ki zaci kin ci bulus, ai faWa ni da ke daga yau har ranar busa ?aho, ba dai uwata ce tsohuwar banza ba sai ka ce babata sa'arki ce ba? Ai ki yi mini komai ban da taSa uwata, ban taSa zagin uwar wani ba, kema babarki? jibgegiyar bayerabiya masu kashi a leda"

Gigicewa Asiya ta yi, tana kuka tana son kaiwa ruma duka, amma ta kasa sarrafa hannunta ga ciwon da jikinta yake yi mata.
Ruma ta dur?usa ta dinga dumbuzar ?asa hannu bibbiyu tana watsawa Asiya a fuska. Ban da kuka babu abin da Asiya take yi.

Ranar ma sai da aka tashi sannan aka sallame su, aka ce gobe da safe za su cigaba da punishment.

Rumaisa ta riga Asiya tafiya, ta je ta samu hanya, ta tattara duwatsu, ta tara su a cikin jakarta. Ta kuma datsar Asiya a hanya, ta dinga kabbara tana jifanta. "SheWaniya gara na jefeki na huta, na ga haka ake yi idan an je makka a jefi sheiWan, gobe ko cewa aka yi ki kalleni, ba zaki sake ba balle ki dakeni"

Sai da ruma ta gama abin da Allah ya nufeta da yi, sannan ta wuce gida. Yau kam bakinta har kunne, jin ta take wasai ba ta da wata damuwa ko banza ta rama abin da aka yi mata har da riba, malamai kuwa ko zasu kwaWata su cinye bai dameta ba.

Abdallah ne yake ta shiri, ruma sai tambayarsa take ina zashi?.

"Ke wai kin aikeni ne?"

"A'a, amma dan Allah ka gaya mini"

"Cikin gari zani ziyara"

Ta haWa hannayenta biyu ta ce "Dan annabin rahama ka tafi da ni" hararta ya yi ya cigaba da shirinsa.
Ta dinga bin sa tana lallaSa shi, har ya amince zai tafi da ita.
Mama ta ce "Hmm in dai ruma ce zata baka kunya, Allah ya sa kar ta Wauko maka magana"

"Ta Wauko ma, dakuwa zata yi wallahi"

Ruma ba ?aramin daWi ta ji ba, ganin ta a cikin gari cikin 'yan uwa, akwai 'yan uwan mama sosai a cikin gari, sai dai mama ba ta zuwa da ita, saboda ta din ga neman magana da dukan 'ya'yan mutane kenan.

Akwai wata 'yar cousin Win mama, da rashin jin su ya kusa zuwa Waya da na ruma, duk da ruma ta fita. Ta ce "Ruma, zo mu je yakasai, akwai ?awata a gidan Turakin Kano, jikarsa ce biki ake a gidan, kuma za ayi kilisa, kan Abdallah ya dawo mun je mun dawo, mu je mu ciyo banza"

Ruma ta ce "yauwwa hauwwaliya, yi sauri ki shirya mu tafi kan ya dawo ya hana ni zuwa"

"Ke har da babbar leda zan Wauko, idan mun ci mu ?ullo sauran"

Haka suka shirya, suka yi sallama a kan zasu je biki su dawo.

Suna tafe a hanya suka sai masara, suna tafe suna ci suna hira.

Tabbas idan ka ji wane ba ?arya ba, gidan ya tsaru yayi kyau sosai da sosai, gini ne na sarauta da aka ?awata da kayan alatu, ruma sai rarraba ido take yi.

?awar hawwaliya ta din ga murna da ta gansu, ta kai su wani falo suka zauna.

Ruma kuwa hankalinta na kan wata mata, da ta sha ado sai kai wa take tana komowa tana wani hura hanci, tana dakawa mutane tsawa.

Ruma ta ce "TaS, wai wacece waccan?"

Yarinyar ta kalli wadda Ruma ta nuna ta ce "Laa Anty Samha ce, ?anwar mama ce, ba mata bace ba ta da aure".

Ruma ta ce "too na ganta wata gwabjejiya, sai masifa take yiwa mutane, ni na zaci matar sarki ce ma, yakamata a samu mai kwaWeta ya zata din ga hantarar mutane?"

Hauwwaliya ta daki cinyar ruma ta ce "Ke, ?anwar mamanta cefa"

Yarinyar ta yi murmushin ya?e ta ce "Bari a kawo muku Abinci, sai mu je wurin kiWan ?warya da kilisa"

Ruma ta mi?e ta ce "Hauwwaliya, ni dai zan je wurin da na ga an Waure dokuna na kallesu, idan an kawo Abincin ki ?ulle mini nawa a ledar da ki ka zo da ita" buWe baki Hauwwaliya ta yi, da jin hansfreen da ruma ta yi musu.

Kai tsaye ruma ta fito tana cigaba da kallon gidan, da yadda manyan mata ke shiga suna fita, da shiga kala-kala.

"Ke ba kya gani ne, meye haka?" Ruma ta Waga kai ta kalli wadda ta daka mata tsawar. Matar da take ta hantarar mutane ce.

"Eh bana gani, sandata na fito nema, ke da ki ke gani meya hana ki kauce?" Ruma ta yi maganar tana tsare Samha da ido.

Wata mummunar faWuwar gaba ta ziyarci Samha, da ta

Please Login or Register in order to submit comment