You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

za?inta, kuma ta WanWana kuWarta, amma ki cigaba da ha?uri ai mun Wana tarko daban-daban".

Mummy ta jinjina kai ta ce "Shikenan, bari mu ga zuwa yaushe, na cigaba da sanya musu ido, duk wani motsinsu uwani na gaya mini, kuma na ce lallai ta kawo mini maganin da waccan 'yar tsintuwar ke shafa masa".

"To shikenan, to bari mu ga yadda abubuwa zasu kaya".
***
Har azahar babu wanda ya kula su ruma, masu kuka na yi masu addu'a na yi, ga yunwa ta addabeta a gida wataran ?arfe bakwai ta karya, amma har bayan azahar babu wanda ya kulasu balle ya basu wani abu.
Tashi ruma ta yi ta samu Waya daga cikin 'yan bindigar ta ce "Bawan Allah yunwa nake ji, ku bani abinci na ci"

Wani mugun kallo ya yi wa ruma ya ce "Zo ki cinyeni, an gaya miki nan wurin hutu ne da jin daWi?".

"Ai ni ba mayya bace da zan cinyeka, idan ma cin ne ban ga abin ci a nan ba, idan ba za a bamu abinci ba meyasa zaku kawo mu nan?" Ta na rufe baki yana hankaWeta sai dai faWi ?asa ya saita ta da bindiga "Idan ki ka yi mini hauka, yanzu na lahira zasu yi maraba da ke".

Ruma ta kalli yadda ta faWi ?asa, wata irin zuciya ta harzi?ota ta mi?e tsaye ta sake kallonsa ta ce "Na faWa a bani abinci yunwa nake ji, ai daWinta idan ka kasheni ba a wuta zaka sakani ko aljanna ba, hisabi na Allah ne, to na faWa a bani abinci yunwa nake ji, harbeni maza kai kuma a ?ara maka kwanakinka a duniya"
Babu alamar tsoro ko shakka a tare da ruma, kowa sai da ya Zubo mata ido, saboda ?arfin halinta.

A fusace ya tashi yayi kan ruma, amma wani ya ri?e shi, ya ce kar ka kuskura, ?yaleta idan ka yi mata wani abun za'a iya samun matsala, ka bari oga ya zo ya faWi ya za ayi".

Huci ya din ga yi yaso ya tattaka ruma, ko ya keta mata haddi a gaban mutanen wurin, ya kawo ?arshen harshenta.

"Ni baka kyauta mini ba da baka bari ya kasheni na huta ba"

"Wato ke dai bakinki ba zai mutu ba ko?"

"Idan har so ku ke na yi shiru, to ku kasheni ko ku mayar da ni gidanmu, wannan ai zalunci ne ni yunwa nake ji" tayi maganar tana share hawaye.

Dattijon nan ne dai na jiya ya ce "Yarinya ki yi shiru da bakinki, kar su citar da ke, wannan mutanen ba ayi musu haka".

"To ni yunwa nake ji" tayi maganar har cikin zuciyarta.

Duk wani kurari da zare ido ruma ta?i yin shiru, kamar ma da gayya take yi dan ta tunzurasu su yi mata abin da za su yi mata.

***
Har dare mama ba ta san abin da ya faru ba, kuma an rasa wanda zai gaya mata, sai mita take musu cewar ita fa ta kasa ha?uri ta kira gwaggo idan an dawo da ruma ta haWata da ita, amma wayar gwaggon ba ta shiga. Sun yi mamaki da duk jin rediyon mama ba ta ji batun kai harin ba.
Ganin tana ta surutu ita kaWai ba wanda ya tanka mata, ya sanya ta magantu "Wai ba zaku gaya mini meke faruwa ba ne? Duk cikinku fa yau babu wanda ya ci abinci, kun ?i walwala kun ?i magana, kuma kun ?i gaya mini menene?"

Usman ne ya tashi ya ce "Mama sai da safe, ni dai bana jin daWi ne".

Babu wanda ya bawa mama amsa, a hankali duk suka watse daga tsakar gidan, mama ta sha jinin jikinta ta fara tunanin menene ya faru haka, da basa son gaya mata?.

Babu wanda ya saurari su ruma sai bayan la'asar, aka zo da wasu kuloli a kan babur, aka rarraba musu wata busashshiyar gurasa, gaya guda Wai-Wai, sai pure water Waya tamkar mabarata.
Ruma ta kalli gurasar nan, duk uwar yunwar da take ji, amma a rasa me za a bata sai wannan takurarriyar abar a bushe, babu mai babu komai a jiki.
Gashi duk ta bushe kamar ?anzo.

Ruma ta gasta ta fara ?o?arin haWiya, amma ta kasa haWiyewa, da ?yar ta dannata da ruwa, daga gutsura Wayar nan ba ta ?ara ba ta shanye ruwanta ta yar da ledar, sauran kuwa tuni kowa ya kama gurasar nan suka cinye.

***
Duk wata tattaunawa su Usman da sauran 'yan uwansa sun yi, amma sun rasa ta ina zasu Sullowa lamarin, duk in da zasu buga sun yi, amma babu wani labari game da in da su ruma suke, gashi da wani ya ce zai je katsinan mama za ta gano akwai abin da yake faruwa, dan a yanzu haka ma duk ta tsargu, mussaman yadda suka daina walwala ga kuma ta fara shiga damuwa rashin shigar wayar gwaggo.
Su huzaifa ma sun gano abin da yake faruwa, sai dai yanayin ruWewa da Huzaifa da Yasir suka yi, ya sanya mama cigaba da jefa musu zargi da kuma kokwanto.

Yau ?arfe tara na safe taga duk sun fito daga Wakinsu sun jeru a tsakar gida, kamae kullum babu wanda yake walwala a cikinsu, kuma babu mai sunan Baba a cikinsu.
Mama ta girgiza kai ta ce "Koma menene Allah yayi muku maganinss, tunda ni dai ina tsakaninku ba zaku gaya mini ba".

Ta fito daga banWaki kenan, Abubakar yayi sallama ya shigo da jakarsa ta makaranta, sai dai kallo Waya tayi masa shima ta ga tsananin tashin hankali a fuskarsa.

Mama tayi saroro tana kallonsa, cikin ?arfin hali ta ce masa "Kai kuma me ya dawo da kai yanzu?"

Suka haWa ido da Aliyu, Aliyu ya sunkuyar da kai, Yasir kuma ya hau goge hawaye.

"Saddi?u, dan Allah kai ka gaya mini menene? Ku daina Soye mini koma menene, na kasa nutsuwa sun ?i su gaya mini abin da yake faruwa, na rasa gane kansu, dama har akwai abin da ban cancanci in sani ba?"

Abubakar ya ajiye jakarsa ya kamo hannun mama ya ce "Mu je Waki mama sai mu yi magana"

Mama ta buge hannunsa ta ce "Ba in da zani, ku yi ta ri?e abin ku a cikinku nima bana son ji, idan abin da bana ?auna a rayuwata bai wuce ganin fuskokin da ba sa son damuwata in gansu cikin damuwa ba, ko ba zan maganta muku ba ai na yi addu'a" ta juya za ta wuce Wakinta.

"Mama ruma ce" ya furta a hankali, cak mama ta tsaya ta kasa gaba ta kasa baya, ta ji maganar ta sa kamar bai faWeta dai-dai ba.

Ba tare da ta waiwayo ba ta ce "Mutuwa ta yi?"

"An yi garkuwa da ita, a garin su Iya, a cikin harin da aka kai ?auyen har da ita aka Wauka".

Innalillahi wa Innalillahi raji'un, mama za ta iya cewa ko mutuwar iyayenta ba ta girgizata kamar wannan abu da ta ji yanzu ba, ji ta yi kamar ba a hayyacinta ta ji maganar ba, tamkar an mata yayyafin wuta, Rumaisa a hannun 'yan biniga, gara ace kashe mata ita suka yi, ta tura a Wauko mata gawarta, amma ruma 'ya mace ?arama a hannunsu a tsakiyar dajin Allah, Allah kaWai ya san me za su yi mata, ga halin ruma da ta sani na rashin kunya da surutun tsiya, tsaf za su illata ta.
Jikin mama ne ya hau rawa, ta sake ?are musu kallo, Huzaifa da Yasir suna ta kuka, Aliyu kuma ya sunkuyar da kai, haka Abdallah, Usmsn kuwa barin tsakar gidan ya yi, babu mai sunan Baba ko ba a gaya mata ba ya tafi katsinan ne.

Ta yin?ura da niyyar Waga ?afarta, ta tafi luuu gaba Waya suka yi kanta suna kiran sunanta

Ayshercool


*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*




Sosai suke girgiza mama, amma ko motsi ba ta yi, a gigice Abdallah ya Webo ruwa ya din ga shafa mata a fuskarta Usman ya Wauko mafici yana yi mata fifita.
Aliyu ya kalli Usman ya c "Usman wani ya je ya samo napep mu kaita asibiti da sauri".

Usman ya ce "Ko nan da zaure ba zan iya fita gani nake komai zai iya faruwa kan na dawo, sai dai ko su Yasir".

Yasir da yake ri?e da hannun mama ya ?ara ?an?ame hannun, ya ?i tashi yana kuka.

A hankali mama ta yi tari, ta fara motsawa tana Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Babban fatanta Allah ya sa idan ta buWe idanunta ace mata mafarki take yi.

Sai dai tana buWe ido ta kalli fuskokin su Huzaifa, hakan ya tabbatar mata a zahiri ne, ruma an yi garkuwa da ita.

Sannu suka din ga jerwa mama, amma ta kasa amsa musu, a hankali ta ce "Ku kira babana, dan Allah ya juyo gida kar ya je, mu bar wa Allah komai".

"Amma mama meyasa?"

"Kar yaje ya tayar musu da hankali ko shi ma wani abun ya same shi, zuwan nasa babu abin da zai ?ara ku kira mini shi a waya, ya dawo gida dan Allah".

Jiki a sanyaye Abubakar ya janyo wayarsa a aljihunsa ya kira lambar Umar.

Mai sunan Baba na Wagawa Abubakar ya ce "Akhi mama ta ce ka dawo gida, bata yarda ka je ba?"

A hasale Umar ya ce "A kan me zaku gaya mata, kun san ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba dan me za a gaya mata? Wannan ai ba yi ba ne, idan wani abu ya sameta fa?"

Shima Abubakar da zuciyarsa ke a kusa ya hayayy?o masa "Kai saurara ni ka ke wa shouting? Da wanne zan ji ne? Har zuwa yaushe zamu cigaba da Soye mata. zamu dawo mata da rumaisa ne idan bamu gaya mata ba? zaka din ga yi mini hayaniya kai kaWai kake cikin damuwar ne? Duk ta shiga damuwa ba mai cin abinci kowa baya walwala kuma an ?i sanar mata abin da ke faruwa, zuwa yaushe za a cigaba da Soye mata, idan ka ga dama ka dawo idan ba ka ga dama ka je ka yi abin da ka ga dama"
Umar yayi wa Wan uwansa uzuri, damuwa ce ta sanya ya sauke masa, dan Sadik ba dai ha?uri ba. Suna gama wayar Abubakar yayi cilli da wayar zai tashi mama ta ri?e shi.

Cikin tawakalli da ?arfin hali ta ce "Yi ha?uri, kar ka yi fushi dan Allah, ka lallaSo mini shi ya dawo ka san halinsa"

Abubakar yayi ajiyar zuciya zai yi magana wayar mama ta fara ringing a Waki, Yasir ya je ya Wauko, mai sunan Baba ne yake kira.
Mama ta karSa da sauri ta kara a kunnenta ta ce "Babana dan Allah ka dawo gida" tayi maganar muryarta na rawa.

"Ki yi ha?uri mama, daga sallar asuba na wuce, ina Katsina yanzu haka na kusa ?arasawa ki yi ha?uri ba abin da za zan aikata, zan je wurin jami'an tsaro ne, ki kwantar da hankalinki in sha Allah za ta dawo lafiya ".

"To" kawai mama ta ce ta saki wayar, tana wata irin ajiyar zuciya, zuciyarta sai wani irin zafi take yi mata, amma idonta ya bushe babu hawaye.

Su ruma kuwa yau kwana na huWu kenan suna hannun 'yan bindiga, ba wanka ba wanki, ga azabar yunwa ruma ba ta iya cin abin da ake bata, ruwan nan Waya idan an basu da shi take sha idan tana jin fitsari ta yi. Duk azabar kashi irin na ruma, ta matse abin ta ba ta yi.
Tun da ruma take ba ta taSa kawo tsintar kanta a irin wannan halin ba.
Ga duka da wasu lokutan ake yi wa wasu, duk da ita babu wanda ya taSa dukanta, amma ana dukan wasu ciki har da mata, 'yan bindiga su dake su su taka su da ?afa.
Wani tarihi ruma ta tuna da aka taSa basu a islamiyya, a rayuwarta tana son malaman da suke basu tarihi, dan duk abin da take zata nutsu ta saurara.
Akwai ranar da malamin yayi musu tarihin Annabi yunus da kifi ya haWiye shi, ya karanta *La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*
Har ruma ta ce "Kai malam amma kifin da ya haWiye annabi yunus, dai yayi girman duniyar nan?"

Malamin ya yi murmushi ya ce "Meyasa ki ka ce haka? Kin san girman duniya kuwa?"

"To ai malam kifin da inuwa mai kifi yake sayarwa, da wanda ake talla ko Wan tsako ba zasu iya haWiya ba, amma na ji ka ce kifi ya haWiye mutum"

"Kifi ne dai babba ruma, amma ba kamar girman duniya ba, kuma ba a gaya mana girman kifin ba a Alqur'ani, abin da nake son ki ri?e yanzu shi ne, falalar wannan addu'a da annabi yunus Alaihissalam ya karanta, a duk lokacin da kika shiga wani mawuyacin hali, ko ki ka shiga hannun wasu azzalumai to kema ki karanta Addu'ar da Annabi yunus Alaihissalam ya karanta *La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*"

"To malam, in Allah ya yarda zan din ga yi, to wace addu'a zan yi idan na yi wa mama laifi kar ta yi mini faWa ko ta saka mai sunan Baba ya sakani kama kunne?" Jik tambayar da ta yi, ya sanya 'yan ajin suka kwashe da dariya.

"A'a ai dole idan ki ka yi laifi ayi miki faWa ko a hukunta ki, amma a duk lokacin da kike fargabar haWuwa da wani, mugu ko ma?iyi sai ki karanta *Allahumma inni as'aluka min nuhurihim, wa'auzubika min shuriruhim*"

Ko da ruma ta tuna da wannan tarihin da malaminsu ya yi musu sai ta fara nanata "*La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin*"

Ihun wata mata ne ya sanya ruma waiwayawa taga ko dukan na ta ake, amma taga Waya daga ci???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?kin mutanen yana jan ta tana ihu, tana a taimaka mata. Babu wanda ya tanka mata mutumin yayi cikin dajin da ita.

?aya daga cikin 'yan bindigar ya ce "Ai gara hakan, tun da 'yar matsiyata ce ba za su biyan kuWin da aka ce su karSeta ba".

Kusan awa biyu mutumin ya dawo ba tare da ita ba.

Ta ji wasu a kusa da ita suna magana ?asa-?asa "Innalillahi, ita ma sun mata fyaWe sun kasheta" Ruma ji tayi kamar ta tambayesu meye fyaWe, tunowa tayi lokacin da take tambayar mama meye fyaWe su Aliyu suka din ga hantararta.

A take ta fashe da kuka, saboda yadda take kewar gida, duk suka juyo suka kalleta.

"Ke meye haka?"

"Mama" ta faWa cikin kuka.

"Yi mana shiru ko in taka ruwan cikinki"

"Wallahi ba zan yi shiru ba, wayyo Allah mama yaya Aliyu yaya usy dan Allah ku zo ku Waukeni zan mutu, wayyo Allahna" kuka take sosai kamar wadda wani iftila'in ya afkawa.

Wata mata ce ta din ga rarrashin ruma tana bata ha?uri da ?yar ta yi shiru, ta cigaba da nanata addu'ar nan.

Mai sunan Baba kuwa yadda yaje ya tarar da gwaggo ne ya sanya jikinsa yin sanyi, ya tarar iya ma tana asibitin ita da mijinta, gwaggo sai kuka take ba ta ko cin abinci, likitoci na ta fama jininta ya sauka abu ya gagara, saboda yadda ta addabi kanta.
Tana ganin mai sunan Baba ta sake rushewa da kuka, "Dan girman Allah ku yi ha?uri, ku yafe mini umaru ban zaci abin zai kasance a haka ba, tsananin ?aunar da nake yi wa Wan uwana ce na mayar kanku, ban yi hakan dan ba?anta muku ba, son da nake wa ruma ya sanya na hanata, da na san haka za ta faru da ba zan ce ma azo da ita ba, ku yafe mini dan Allah" gaba Waya suka fashe da kuka, har su iya da su Lawisa da aka sace ruma a gabansu.

Ganin yadda dattijuwar ke cikin tashin hankali ita da iyalanta ya sanya ya ji duk jikinsa yayi sanyi, idan ya ce zai Waga musu hankali bai yi musu adalci ba, tun da suma ba da son ransu hakan ya faru ba.

Ya ?arasa ya zauna a gefen gadon gwaggo sannan ya ce "Ki daina kuka, ko dan saboda a samu jininki ya sauka, yanzu ya ake ciki an sanar da jami'an tsaro ne ko kuwa ya ake ciki?"

Dagaci ya ce "Ka san garin namu, jami'an tsaro ba su fiye bamu agaji ba, mu da su mutanen muke yin sulhu, duk abin da muka saka jami'an tsaro wata Sarnar suke yi mana, amma dai saboda ita rumaisan mun sanar da jami'an tsaro, amma sun ce mu jira abin da 'yan bindigar suka ce sai a sanar musu, muna nan muna jira haryanzu dai ba su yi mana aike ba".

Mai sunan Baba yayi shiru ya ma rasa abin da zai ce, ?arshe ya yanke shawarar a kai shi wurin 'yan sandan domin ya ji meye abin yi.

?anlami ya Wauki mai sunan Baba suka tafi, sai dai daga ?auyen da aka sace su ruma zuwa wurin 'yan sandan uwar tafiya ce mai zaman kanta, da ko menene zai samu 'yan garin ba lallai su samu Waukin jami'an tsaro.

Ganin girma da kwarjini da kuma ganin cewa Umar ba Wan garin bame ya sanya DPO garin tsayawa ya saurare shi.

"To Wan uwa idan zan baka shawara ka koma gida kawai ku yi addu'a, bin bayan mutanen nan aikin sojoji ne bana 'yan sanda ba, mu mun yi iya namu ?o?arin, sai dai mun bar sallahun idan sun yi wata magana a sanar mana, haryanzu dai ba su ce komai ba"

Shiru kawai mai sunan Baba yayi, ba zaka ?ara sanin lamarin tsaron ?asarmu ya taSarSare ba sai wani iftila'i ya afka maka.

Ba tare da samo wata mafita ba, mai sunan Baba ya kamo hanyar kano.

Gidansu ruma kuwa tamkar an yi mutuwa, ko magana mai sauti ba sa iya yi, tun da mama ta Wan samu ?warin jikinta ta hau sallaya, canza alwala ce kawai take Wagata, yunwa kuwa ko jinta ba ta yi.

Ba yadda ba su yi da mama ba a kan ta ci abinci, ta ce su ?yaleta kawai.

Ko da ta ji sallamar mai sunan Baba, ji ta yi kamar zai ce mata ga ruma nan ya dawo mata da ita, amma ko da ya shiga Wakinta ta kalleshi ta ganshi shikaWai, sai ta sunkuyar da kanta ?asa, ta ji zuciyarta ne neman karyewa.

Ya ?arasa gaban mama ya zauna, su Abdallah duk suka zubo masa ido, amma ya rasa ta ina zai fara yi musu bayani.
Mama ta sake Waga kai ta kalli ta mai sunan Baba, ya girgiza mata kai ya ce "A dage a cigaba da Addu'a kawai"

Wata irin wahalalliyar ajiyar zuciya mama ta sauke, ta sake sunkuyar da kanta ?asa.

Huzaifa ya fashe da kuka, Yasir ma ya taya shi.

Cikin dakiya mai sunan Baba ya haWe rai ya ce "Meye haka kamar wanda ba su je islamiyya ba, ba ku yi imani da ?addara bane? Yanzu kuka ne ya kamace ku ko kuma addu'a?" Haka ya din ga yi musu faWa alhalin shima da zai samu space kukan zai yi. Ya tashi fuuu ya tafi Wakinsu, yana zuwa ya tarar da Abubakar a zaune yayi shiru ya lula duniyar tunani.

Mai sunan Baba ya zauna a kusa da shi, ya ce "Akhi na dawo?"

Banza yaya Abubakar ya yi masa bai kula shi ba.

"Na san na yi maka laifi, amma yakamata ka yi mini uzuri, ba a hayyacina nake ba, idan ka gama fushin sai mu yi magana" ya yin?ura zai tashi Abubakar ya ce "Yaya ku ka yi da ka je, an samu labarinsu?"

"Babu wani labari mai daWin ji, sai ma kayan takaici, ance mu saurara idan sun kiramu sun ce mana wani abu shikenan sai mu sanar".

"Idan kuma ba su kira ba a haka zata cigaba da zama a hannunsu?"

"I have no idea" mai sunan Baba ya faWa cikin damuwa.

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Aki meye abin yi?"

"Addu'a" ya bashi amsa a ta?aice.

Dare ya tsala, wasu daga cikin al'umma sun kwanta suna hutawa, yayin da wasu daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da iyalansu suke kwanan zaune, ciki har da mama da yaranta maza yayyen ruma gaba Waya mama ta manta da wani abu wai bacci a wannan halin da take ciki, a zaune take tamkar an dasata tun tana iya lazimin da addu'a har ta kasa ta rasa abin da ma zata ja.
Zuciyarta sai zafi take mata, da tunanin a wani hali ruma take ciki.

Wurin baccin ruma ta kalla, da yanzu tana nan mama tana faman gyara mata kwanciya ko tashinta fitsari, da yanzu ta yi Wai-Wai sauro na cizonta mama tana mita tana sake gyarata, ko ta ?aro fanka idan ta fuskanci zafi yayi mata yawa, ko ta kashe fanka ta lulluSeta idan sanyi yayi yawa.

"Ruma ko a wani hali kike? Ko kina raye? Ko kin ci abinci? Ya in da ki ke kwance? Sanin gaibu sai Allah, ya rabbilarshil azim, dan girmanka Allah ka tsare mini 'ya ta da sauran 'ya'yan musulmi, Allah ka dawo mini da ita cikin aminci" ta ?arasa addu'ar kuka yana kufce mata, sai a lokacin ta Wan ji nutsuwa da ta samu hawayen idonta ya zuba.

?akin 'yan mazan ma gaba Waya idonsu biyu, wasu da Alqur'ani wasu a kan sallaya, wasu suna kuka, dan basu taSa tsintar kansu a cikin mummunan tashin hankali kamar wannan ba.

Ruma ta yi rigingine a filin Allah, wani irin sanyi yana ratsata ga cikinta kamar ya haWe da bayanta saboda azabar yunwar da take ji, ga ?ai?ayi da jikinta yake mata saboda rashin wanka, ga wani irin sauro na bala'i da ?wari suna gasa mata cizo.

A hankali ta furta "Mama, mai sunan Baba" sai kuma ta yi shiru hawaye ya fara zirarowa ta gefen idonta.

Tana tsaka da tunanin, wurin yayi tsit, mutanen sai kewayasu suke yi da manyan bindigogi.

Wani irin sauti ruma ta din ga jiyowa na motoci ?asa-?asa, daga bayan dutsen da ke nesa da su.

"Sha tara ga motocin smoke can suna aiki fa" cewar Waya daga cikin 'yan bindigar.

" 'yan wahala ba, ni mamaki nake yadda suke iya fitar da sabgar nan ba wata matsala" Wayan ya bashi amsa.

"Haba, sun gama sai ta komai nake gaya maka, babu wanda ya isa ya tare musu hanya, babban controller na ?asa ma fa nasu ne, kuma akwai na sa kason a ciki mu suka mayar 'yan iska kawai".

Sha tara ya ce "Aikuwa sai mu yi tawaye, ko dai su yi wani abu a kai ko mu bujure, haba ma'adanan nan fa da suke kwasa ba dan muna gyara musu aikin nan ba da ba zai yiwu ba, amma kura da shan bugu gardi da kwashe kuWi".

"Kai ni ba wannan ba ma, oga nake jira ya zo ayi wadda za ayi a san yadda za ayi da mutanen nan"

"Eh gobe zasu shigo ai"

Haka suka cigaba da hirarsu, amma kan ruma ya Waure, wasu ma'adanai ake kwasa meye ma ma'adanan?

"Zan yi fitsari" ta faWa cikin rawar murya".

"Yi a nan" Wayan ya bata amsa.

"Ina jin yunwa ma"

"Idan ki ka kuma magana sai na taka ruwan cikinki"

Guntun tsaki ruma ta yi, tayi juyi wani abu da ba ta san menene ba gasa mata cizo, wata uwar ?ara ta saki, ta mi?e tana kuka.

"Wai wannan wace irin iblishiyar yarinya ce meye kuma?"

"Wani abu ne ya cijeni" ta yi maganar a gigice tana soshe-soshe.

"Nemi wuri ki zauna ki rufewa mutane baki, ni wallahi da oga ya zo da na daWe da harbe wannan shegiyar yarinyar da ba ta rasa matsala".

"To ku mayar da ni in da kuka Wauko ni mana, meyasa zaku kawo ni nan" tayi maganar a sangarce

Hasketa Wayan yayi da hasken fitila, ta saka hannu ta kare tana motsa baki, saukar wani abu ta ji a goshinta mai nauyin tsiya, daga haka ba ta sake sanin in da kanta yake ba.

Bayan sallar asuba, su Abdallah suka sanar da abin da yake faruwa a masallaci, tare da ro?on bayin Allah su taya su da addu'a, Allah ya fito da rumaisa cikin aminci da ?oshin lafiya.
Mutane da yawa sun kaWu da jin abun da ya samu ruma, dan ruma ta mutane ce, da yawan mutane sun santa, kan gari ya gama haske unguwar su ta cika da labarin yin garkuwa da ruma.

Gari na gama yin haske aka din ga sintirin zuwa yi wa mama jaje, tare da addu'ar Allah ya bayyana ta.

Mama duk yadda ta so ta jure, ta kasa haka ta dinga share hawaye, masu cewa ta daina kuka kuwa kallonsu kawai take yi, gani take ba su san a cikin tashin hankalin da take ba ne.
Hatta daga islamiyya su ruma haka aka yi tawaga

Please Login or Register in order to submit comment