You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na farko, tana neman rumaisa, ya gane lambar, kuma lambar take cikin kansa, ko da bai Waga ba ya san lambar iman ce, yana kallon wayar ta ?araci ringing Win ta, ta kaste ya?i Wagawa.

Lambar Usman ta yi trying, shi ma sai da ta kusa katsewa, sannan ya Waga yayi sallama.

"Saboda tsabar kun tsaneni, kun kawo ni, kun ajiye ni, ba wanda yake nemana mama ma ta?i zuwa ta gannu, kuma bani da lafiya ma"

"Iyee, ko amsa sallamar ma ba zaki yi ba, sai wassafo mini ?orafi?".

"Mama ta?i ta zo ta ganni, ni na gaji da zaman gidan nan, dan Allah ku zo ku tafi da ni, gida nake so, kuma bani da lafiya".

Usman ya ce "Ke ban son shirme, a hakan zamu zo gidan naki, ki na yi wa mutane kuka?? Meya sameki?".

"Fitsarin jinin da nake ne na kuma yi, a asibiti fa na kwana, cikina ya din ga ciwo, jini sai zuba yake mutuwa zan yi idan baku zo ba".

Maimakon usman ya tausaya mata, sai ya ?ya?yace da dariya, ya ce "Kin ci kai, Allah sarki girma ya zo".

Cikin kuka ta ce "Yaya usy da gaske nake, a asibiti na kwana wallahi"

Sai kuma ya daina dariyar ya ce "Ahha haba dai?".

"Tun da baka yadda ba, bani mama mu gaisa".

Usman ya ce "Maganar gaskiya mama ta tafi cikin gari, yi wa mutane bangajiya, amma idan ta dawo sai a kiraki".

"To ai ba wayata ba ce ba".

"Aliyu yana da lambar mijinki, zamu zo ma in sha Allah, Allah ya ?ara lafiya uwar gida sarautar mata" yayi maganar cikin zolaya. Ganin ba shi da niyyar Waukar maganar ta ta serious ya sanya ta katse wayar.

***
"Ya ake ciki da maganar yaron nan ne, kwana biyu na jika shiru, babu wani update a kan moves Win sa ne?".

"Ranka ya daWe, ai babu wani sabon abu, ka san yayi aure kwanan nan, kuma kamar ma hankalinsa ba ya kan aikin a kanka yanzu, ko cikin Abujanma, ya fi watanni rabonsa da zuwa".

"A'a fa, ka san yaron nan da wayon tsiya, kar in je lumbu-lumbu yake yi mini, yana wani binciken ta ?ar?ashin ?asa, ko shirya wani abu da ban sani ba".

"Babu abun da yake aiwatarwa, ba tare da na san motsinsa ba, a yanzu dai haka babu ranka ya dade".

Ya juya ya kalli wakili ya ce "Khalifa, kai wurinka babu wani update Win".

Khalifa ya Wan sauke numfashi ya ce "Babu Daddy, sai dai ina nan ina ta bin diddigin sa fiye da yadda ka ke tsammani, babu wani abu da yake yi s kanmu, sai dai wani ?ishin-?ishin da nake ji, wai yarinyar da ya aura, ita ta tserato da Wan sa daga wurin masu garkuwa da mutane, amma bani da tabbas, an ce in jira a samu tabbacin hakan".
Senator wakili ya jinjina kai ya ce "Duk yadda ake ciki ka sanar mini, idan har ita Win ce, ka samo mini tabbacin hakan, a kan lokaci".

"To shikenan, In sha Allah daddy"

***
A duk lokacin da rumaisa ta je canza pad, cikin ?yan?yami take yi, kuma a tsorace take da tunanin jininta zai ?are, har sai da iman ta fuskanci wani abu, amms ba ta takura mata da son sanin menene ba, tun da ba ta gaya mata ba.
Mai sunan baba kuwa wuni yayi yana kallon missed call Win, iman a wayarsa, yana tunanin me za ta ce masa haka, da har ta yi masa 3missed calls, ko tana nufin ta ce Haryanzu ba ta san wayarsa ba ce ba?.
Gashi dai yana sane yayi ignoring kiran, amma yana son sanin dalilin kiran.

Yau sai da takawa ya dawo, sannan iman ta fara shirin tafiya gida, rumaisa ta din ga yi mata magiya a kan ta kwana, amma ta ce ba ta gaya wa ammi ba, direba ya zo ya Wauketa ya mayar da ita.

Takawa ya dubi ruma da ta haWe rai saboda Iman ta tafi ya ce "Ya jikin naki?".

"Da sau?i"

"Kin sha magungunan ko kuwa?".

"Na sha" ta amsa masa a ta?aice, bai sake kulata ba ya ?yaleta, dan yanayin fuskarta ya nuna masa a fusace take, idan ya biye mata rashin kunya za ta yi masa.

Mai sunan baba kuwa, missed calls Win nan a ransa ya wani, zuciyarsa na ta raya masa ya bi kiran nan, ko ya manta ya cigaba da sabgoginsa, sai ya tuna, yayi iya ?o?arinsa ya manta, amma ya kasa, yana ta tunanin menene haka mai muhimmanci da ya sanya ta yi masa missed calls har uku.

Babban abun da ya Satawa iman rai, bai wuce yadda ta koma gida ta tarar da Jabir ba, ya kasa ya tsare a falo, suna hira da Ammi, yana ganinta ya hau rawa jiki, ya fara yi mata hira.
Iya ?o?arin ta take yi, kar ammi ta fuskanci wani abu, dan haka ta ke amsa masa hirar.

Ammi ta tashi ta bar musu falon, ta tafi Wakinta, iman na shirin tashi ita ma, wayarta ta fara ringing, ba ta duba ba ta Waga ta saka a kunnenta, tare da yin sallama.
Shiru yayi bai amsa ba, sai wani numfashi da yake saukewa a hankali, yana jin yadda murayar ta ta, ta daki zuciyarsa.

"Hello, ba a jina ne, Assalamu alaikum" ta yi maganar cikin Wabi'arta ta iyayi.

"Missed calls na gani" yayi maganar cikin dakakkiyar muryarsa da take razanata.

Sai da ta Wan ruWe, amma ta yi iya yin ta, ta haWa nutsuwar ta wuri guda ta ce "Yaya Umar ina wuni?".

"Lafiya ?alau".

"Dama Anty Rumaisa ce ta karSi aron wayata ta kiraka, kuma ba ka Waga ba, ba intentionally na kira ka ba, ai ka gaya mini na daina kiran wayar ba tata ba ce, ka yi ha?uri dan Allah" ta ?arasa maganar kamar za ta saka masa kuka.

Ji yayi jikinsa har wani rawa yake yi, dan shi a rayuwarsa, idan ba mama da rumaisa ba, babu wata ?a da yake keSewa yayi wata doguwar magana da ita, ko ita rumaisan ba shiga shirgin ta yake yi ba, amma ya tsinci kansa da jin daWin sauran muryarta.

Amma da yake namiji namiji ne, cikin basarwa ya ce "Ina rumaisan take?".

"?azu ne na je gidanta, ba ta jin daWi shi ne ta karSi wayata, ta kira ka, amma ta ji sau?i".

"Shikenan" ya katse wayar.

Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, duk da muryarsa na razanata, amma ta tsinci kanta da jin daWin kasancewa da shi ta waya. Wani guntun murmushi ta yi, tana Waga kai ta ga Jabir da Nusaiba duk ita suke kallo.

"Iman da wa ki ke waya?" Jabir yayi maganar a hasale.

"Kamar yaya? Yayan Anty rumaisa ne".

"To meye ala?arki da shi" ya sake yin maganar yana tsareta da ido.

Tashi ta yi tsaye ta ce "Yayan matar wa na ce, kuma ni babu wani abu tsakani na da shi, ta ari wayata ta kira shi ne kawai".

"Ina fa lura da yadda ya din ga bin ki da kallo lokacin bikin nan, idan ya ganni tare da ke ya din ga hararata".

Ta girgiza kai ta ce "Gaskiya kai ne ka ga haka, amma ba hakan bane" ta wuce ta nufi Wakinta.

Jabir zai kuma magana, Nusaiba ta ce "Uncle J, ka bi ta a hankali, fushi da tashin hankali ba naka bane ba, ba abun da yake tsakaninta da mutumin nan, na riga na baka shawara, ka je wurin ammi kawai, ko ka gaya wa turaki, na san komai zai zo da sau?i" sauke numfashi ya yi, ya tashi ya fice.

***
Tun da Adam ya fara hawo wa step Win bene, yake jin ?auri, yana hawa falon saman, ya tarar da ya turnu?e da haya?i, kuma haya?in daga kitchen yake fitowa.
A sukwane ya nufi kitchen Win, ya na zuwa ya tarar da rumaisa tana suyar wainar fulawa tana tari, Saboda ?aurin manja.

"Ke meye haka? Me ki ke yi?"

Ta waiwaya ta ce "Girki nake yi"

Da sauri ya ?arasa yana ?o?arin kashe gas Win, dan tuni suka haWa baki da iman, direbanta ya Wuro mata.

Tarewa ta yi ta ce "Girki fa nake yi na iya"

"Matsa, ban ce kar ki kuskura ki ce zaki yi girki ba?" BuWe masa flask ta yi ta ce "Ka ga fa, na iya" wainar fulawa ce ta yi sa?a mai kyau, sai ?amshin attaruhu take.
Ba ?aramin mamaki ta bashi ba, amma a fili ya ce "Idan ki ka yi mini gobara a gida, sai na casaki".

Ta ce "Eh na yadda" ya gyaWa kai ya fice.

Kusan awa guda, ya ma manta da batun rumaisa ya tuna kar ta yi wata aika-aikar, ya le?a falo, ya hangota tana ta suWar baki tana cin yaji.

Ganin tana lafiya, ba wani abu da ya faru, ya sanya ya nemi wuri ya kwanta, dan a gajiye yake sosai.

Sai dai bacci ya gagare shi, tunani daban-daban ya addabi kwanyarsa, ya rungume pillown sa, ya rintse idanunsa, ba ya son tuna yana da tarin matsalolin da ya kasa soloving Win su. Ga wani abu da yake bijiro masa ba gaira babu dalili.

Tashi ya yi ya kunna fitilar Wakinsa, ya tafi kitchen, sai dai ya tarar da rumaisa ba ta yi bacci ba, tana ta gyara abubuwan da ta Sata, tana tsaye a gaban sink tana wanke-wanke.

Bai ce mata uffan ba, ya Wauki heater, ya zuba ruwa ya jona, ita ma ba ta kula shi ba, ta cigaba da aikinta.

A ransa yake yabawa mahaifiyar rumaisa da yayyenta, dan a ?an kwanakin da suka yi, ya fuskanci tana da ?o?arin tsafta.

Tea yake son haWawa, ga ruwa ya tafasa amma sai duru-duru yake yi.

Ta kalleshi ta ce "Rumaisa, dan Allah tun da na ga kin iya girki, dafa mini tea, zan sha. Shi ne abu mai wahala a wurin ka, bari dai na taimaka maka, ai tun da na ga ka Wauko kofi na san shayi zaka sha, a gida ma kusan kullum sai su Yaya Aliyu sun sha shayi da daddare".

Ta taka kujera, ta buWe wata drower, ta Wauko Lipton, da kayan shayi, wanda bai san a in da ta same su ba.

Ta zuba a cikin ruwan zafin, ta sake tafasawa, ta Wauki ?aramin flask ta juye masa, ta haWa masa da kofi a kan tray, sannan ta ce "Gashi nan, kar ka damu ba sai ka yi mini godiya ba, dan na san ba za ka yi ba, muna da irinka a gidanmu. Idan ka gama shan shayin, ga omo da soso, ka wanke kofunan, kar ka bar mini kwanuka wani abun ya bi".

Kamar soko haka yake kallonta, ta Wauki wani Wan bowl, ta zuba uban cabin da madara da sugar, ta fice.

Washegari ta tashi da safe, tana aikace-aikacen ta, barira Waya daga cikin hadimanta, ta kawo abinci ta ce na takawa ne.
Ta karSa ta ajiye masa, dan da baba uwani ta gaya masa rumaisa ta ce a daina kawo abinci, cewa yayi su ?yaleta su cigaba da kaiwa.

?akinsa ta shiga da kayan mopping, ta tarar yana banWaki yana wanka, ta karkaWe masa gadon, ta gyara ta kalli gadon bai gyaru sosai yadda yakamata ba, ta ce "Oho, ni a gidanmu babu gado sai katifa, hakan ma na yi ?o?ari ai".

Idonta ne ya sauka a kan side bed, in da ya sha shayin, nan ya bar kwanukan, "Kam bala'i, Wa ya bar wa kwanukan nan a nan?" Ja ta yi ta tsaya tana jiran fitowarsa.

Rigar wanka ce a jikinsa, sai dai gaban rigar a buWe yake, gashin ?irjinsa ya kwanta saboda ruwa, da sauri ta kawar da kanta gefe.

"Ya aka yi?".

Ba ta kalleshi ba ta ce "Eh kwanukan da na ce idan ka gama shan shayin ka wanke na gani a nan".

Ya ce "Eh, idan kin gama ki fita da su ki wanke"

"Ni na sha maka da zan fita da su in wanke?"

Ya kalleta ya ce "Me ki ka ce?" Ta girgiza kai ta ce 'Bakomai".

"Oya kwashe su ki fita da su, ki je ki wanke, sannan kan na gama karyawa, ki shirya, zamu je gidan turaki".

Ta ji daWi za su fita, amma babban abun da ya bata haushi, bai wuce sakata fita da kwanukan da shi ya mora ba ita ba.

Wata turkey abaya ta saka, blueblack fuskar nan fayau babu ko kwalli, ta yi ta shafa turare, dan akwaisu available a kan mudubinta, dan ko a gida ta saba, dan Abdallah har Sarauniyar turare yake ce mata.

Suna tafe a hanya, tana kallon titi, tana son gane hanya, dan so take wataran ta Salle ta tafi gida.

A gidan turaki suka tarar da Jabir, da shi da Jamil ga kuma Zainab da Mummy, Samha ce ba ta nan.

Rumaisa ta gaishe su, sai dai ba wanda ya amsa mata da mutunci sai Zainab.

Adam ya ce "Zainab nema mana iso wurin mai girma turaki" ba musu Zainab ta tashi.

Rumaisa da sun haWa ido da Jabir take galla masa harara, haka Jamil da yake ta kallonta a wula?ance.

Aka yi musu izinin shiga wurin turaki, turaki yana ganin rumaisa ya fara murmushi.

Ita ma Murmushin ta yi ta ce "Barka da wannan lokaci ranka ya daWe".

"Barkanmu dai ?ar albarka, ya gidan ya ?o?ari?"

Ta amsa da "Alhamdilillah"

Adam har le?a fuskarta yake, ya ga ko ita ce ta nutsu haka.

Shi ma suka gaisa da Adam, Adam ya ce masa sun zo su yi godiya ne, tare da yi musu bangajiya na hidima da aka yi.

Turaki ya yi musu nasiha sosai, mussaman ma Adam, a nasihar rumisa ba komai take fahimta ba, mussaman da ta ga da Adam ake.

Bayan turaki ya gama, yayi musu addu'a sosai, Adam yayi ta godiya, ya ce masa za su je wani wurin daga nan.

Rumaisa ta ce "Babana, yaushe zaka zo gidanmu, na iya abinci in dafa maka duk abun da ka ke so?" Yayi murmushi ya ce "Za a zo ne in sha Allah".

Gudun kar ta fara sakin layi kamar yadda ta saba, ya sanya adam sakata a gaba suka fita, sai dai a wannan karon sai suka fita ta ?ofar da zasu fita haraba kai tsaye, ba tare da bi ta falon gidan ba, sai dai suna fita suka yi kiciSis da Samha!

Ayshercool.
08081012143

*Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please =?O?




Adam yayi ta maza ya ce "Au dama kina nan? Mun wuce su mama a falo ban ganki ba ai".

Cikin matsanancin takaici ta ce "Meye na borin kunya kuma? Ai ba ka so ka ganni Win ba ne? Tun da har ka shiga ta falo, ka biyo ta nan za ka tafi".

Rumaisa ba ta kula Samha ba, dan ba zata manta fuskar ta ba, ta mayar da hankali wurin tsinkar furanni da ke wurin, sai dai tana jin duk abun da suke faWa.

"Yanzu da ma adam a kan wannan abar ka wula?anta ni, ka ?i ka aureni? Yanzu wannan abar wani abu ta fi ni da shi, yarinyar da ba ta kai a kirata mace ba ma, an ya ka yi mini adalci kenan? Soyayyar da na nuna maka tsawon shekaru shikenan ba ni da wata makoma?"

"To ni idan ba mace ba mace ba ce, namiji ce ni?" Rumaisa ta yi maganar tana ri?e ?ugunta.

Adam ya kalli rumaisa ya ce "Wuce ki je mota ki jirani"

"To saman motar zan hau ko ?ar?ashin tayoyi? Tun da a rufe take".

"Duk in da ya yi miki" kallon banza ta yi wa samha ta wuce.

Samha tana ta tunanin a ina ta san fuskar rumaisa ma, ta kasa tunawa, ta ma fi cika ido a hotunan bikinsu, a zahiri kuwa ?waila ce ta gaske.

"Yanzu abun da ki ka yi kin kyauta Samha? Da auren wuri aka yi miki, ko baki haifeta ba kin kusa, wannan ai salon ki janyo wa kanki raini ne".

"Ban damu ba adam, ba raini ne a gabana ko akasin haka ba, ni batun soyayyaya ta ce a gabana, wallahi ka cutar da ni Adam".

Adam ya Wan yi shiru, sannan ya ce "B???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?an cutar da ke ba Samha, abun da nake son ki gane shi ne, komai mu?adarri ne na Allah. Daga haWuwata da rumaisa, zuwa lokacin da na aureta, da zan gaya miki zaki gane aurena da ita ?addarar Allah ce".

"Ba ka son ta kenan?"

"Ba zan ce eh ba, kuma ba zan ce a'a ba, ki yi ha?uri ki cigaba da addu'a, idan da rabo sai in aureki, idan kuma babu ko yi ha?uri, ki auri wani, kar ki ce zaki cigaba da zaman jirana samha".

Rumaisa kuwa ranta a Sace, ta ?arasa in da motarsu take, tana zuwa ta ga Jamil da Jabir a tsaye a wurin suna magana, ba ta kula su ba ta tsaya, tana hura hanci.

Jamil ya ?arewa rumaisa kallo ya ce "Lallai, Adam sai ka ce makaho, dan Allah ina mamora a tare da wannan yarinyar? Me wanna za ta tsinana masa a zaman aure? Yanzu wannan ya zaSa ya bar Samha? Saboda wannan abar?".

Jabir ya ce "Kai ba ka san komai ba ai, ba ta da kunya ne yarinyar nake gaya maka, kai ka ga wahalar da ta din ga bashi, ka san ita ta dawo da jaririn fulani, kan ta faWi fulanin ma ta rasu, sai da aka kai ruwa rana, ba ta da kunya"

Zabura Jamil ya yi ya ce "Kana nufin da gaske wannan yarinyar ce, ta dawo da yaron wurin aisha?".

Jabir ya ce "Tambayeta ka ji"

Juya musu ?eya rumaisa ta yi, tana wasa da ?asa da ?afarta.

"Ke, da gaske kin ga fulani, kin ganta a hannun ?an bindiga, suwaye? Ya aka yi suka kasheta?" Yayi maganar cikin rikicewa yana kallon rumaisa,ya na jin tamkar yanzu A'isha ta rasu.

?aga kai Rumaisa ta yi ta kalleshi, ta yi guntun tsaki.

"Magana nake yi miki, aisha ?anwata ce, jami'in tsaro ne ni, ki gaya mini abun da ya faru, ko kuma ?arya ne kawai haWin baki ne?" Yayi maganar kamar zai kaiwa rumaisa duka.

She?e?e rumaisa ta ce "To mijinta ma shi Adam Win ban gaya masa komai ba, balle wani kai, ba ruwanka da ni kuma, wallahi ka sake ce mini wannan abar, sai na yi maka rashin mutunci, mai na yi muku, ni na ce kar ya auretan? Wannan masifaffiyar matar na na Wauka ma babar wasu ce".

Daga nesa da ya tunkaro su, ya hangi rumaisa tana zazzaga masifa, Jabir ya ri?e hannun Jamil, ya ce kar ya yi magana.

Adam ya ?araso ya ce "Lafiya kuwa?"

Rumaisa ta ce "Ce mini yayi wai wannan abar, ni na ce kar ka auri waccan matar, da za su din ga ce mini wai wannan abar, shi kuma wannan har da ce mini mara kunya, me na yi masa na rashin kunya".

Adam ya buWe motar, ya ce wa rumaisa "Shiga ki jirani"

BuWe motar ta yi ta shiga ta zauna, tana cigaba da tura baki.

Adam ya kalli Jamil ya ce "Sannu Jamil, kirkin ka har ya yi yawa, shikenan ita rayuwa ba za a karSi ?addara ba, ka ?i halartar Waurin aurena, kuma ka ?i yi mini Allah ya sanya alkhairi".

"Allah sanya alkhairi saboda ka auri wannan abar?" Yayi maganar yana nuna motar adam.

Adam ya sauke hannun Jamil ya ce "Ko dan albarkacina, yakamata ka tausasa harshe a kan ta, matata ce, kuma bana son zumuncinmu ya samu matsala saboda son zukatanmu".

Jamil ya ce "Adam ka na da ?warin gwiwar yin wannan maganar? Dama yarinyar nan ita ce ta zo da jaririn aisha, ka ce aisha a hannun 'yan bindiga ta mutu, ya aka yi ita ta kuSuta, wani mataki ka Wauka, na san dole ba za a rasa wani information daga bakinta ba, menene dalilinka na Soye mana?".

Nan da nan Adam ya hasala ya ce "Kai ma kana zargin ni na kashe fulani na yi tsafi da gawarta ko? To na yi, idan wani bayani ka ke da bu?atar ji daga bakinta, ka je ka tambayi mai girma turaki".

Cikin sauri Jabir ya ce "Jamil, bai kamata ka faWi irin wannan maganganun ba, da na san haka abun zai zama, da ban gaya maka ba, takawa dan Allah ka yi ha?uri"

Bai ko tsaya ba, ya wuce mota, ya buWe ya shiga, zuciyarsa na yi masa wani irin zafi.

Sai da suka Wan yi nisa sannan ya cewa rumaisa me suka ce miki?.

"Su wa?" Kallonta yayi, ta ga alamar babu wasa a idonsa, ta ce "Tambayata yayi, wai ya aka yi na san anty aisha, ni kuma na ce ban sani ba"

Jinjina kai kawai ya yi, ya cigaba da tu?insa.

Wani store yayi parking, ya ce ta fito su shiga. Ta fita ta bishi tana kallon wurin.

Suka je Sangaren jakunkuna ya ce ta zaSi jakar makaranta.
Haushi ne ya kamata, dan ko zancen makaranta ba ta so.

Ya sai mata kayan karatu da rubutu, da takalma, jakar ma uku ya saya mata, sannan ya sakata a mota suka tafi.

Gidajen ?an uwansu ya din ga zagayawa da ita, suna gaishe su, sai dai rumaisa ta ?ule da yadda wasu suke karSarta, tare da nuna ita yarinya ce, ta yi masa ?arama da aure.
Babu wanda ya sake ?ona mata rai, kamar hajiya Lubabatu, wato mahaifiyar Jabir, matar Galadima mai ci a yanzu.

Ban da tana ganin girman matar, ta yi sa'ar mama, da babu abun da zai hana ta zageta, dan ma Adam yana ta kareta, amma matar ta ci zarafinta, duk da bakomai take fahimta ba.

"Ragowar ?an bindiga aka kawo mini kenan, lallai takawa, ka yi jihadi sai fatan Allah ya biya ka".

Adam ya ce "Ba ragowa ba ce ba, kuma aurenta ba ni na yi jihadi ba, ita ta yi, tun da kun san waye Wanku, amma ta amince da aurensa".

Hajiya Lubabatu ta yi dariya ta ce "Yo ba dole ba, ai ko a turu kake Wan mu yana da arziki da sarautar da za a aure shi domin sa, kuma a zauna da shi, kwaWayin abun duniya ne kawai".
Ba dan Ammi ta matsa, lallai ya zagaya da rumaisa, ya nuna mata familynsa ba, ya kuma yi musu bangajiya ba, da babu abun da zai sanya ya zo gidansu Jabir, wurin mahaifiyarsa.

Adam ya ce "To Hajiya, ina ga bari mu koma, akwai in da zamu je".

"Ahh haba dai, na saka a Wora muku girki ai".

"A'a Alhamdilillah, a ?oshe muke".

Hajiya Lubabatu ta ce "Gaskiya ban ji daWin wannan zuwan ba, yakamata a kawo mana ita ta wuni, da haka tana shiga cikinmu, za ta san yadda matan sarakai suke rayuwa, dan na san ba sani ta yi ba".

Adam ya ce "Bakomai ana koya mata"

Wata hadimar Hajiya Lubabatu ta ?araso, ta bawa hajiyar wata leda. Ta karSa ta mi?awa rumaisa ta ce "Amarya ga wannan ba yawa, kya sai tsintsiya, sai na sake kawo ziyara, tun da rabona da gidan, tun washegarin kai ki, mun ce a bamu ?yalle mu tabattar da abun da aka auro mana, an yi mana wala wala".

Rumaisa ta sha kunu, ta ?i karSar ledar.

"Ki karSa mana" rumaisa ta girgiza kai ta ce "A'a"

Hajiya Lubabatu ta ce "Takawa, ba ka gaya mata, masarauta ba ma kyauta ace a'a ba, rayuwar masarauta, ba kamar ta sauran gama garin mutane ba ce".

Ya kalli rumaisa da ke kusa da shi ya ce "Ki karSa, ba a mayar da kyautar matan sarakai".

"Bana so" ta faWa yadda shi kawai zai ji.

Ya saka hannu ya karSi ledar ya ce "Godiya take, kin san amaryat ta wa akwai jan aji, da gudun raini, kyauta ko da ga ni take, sai ta tantance, gaku sarakai, amma ta fi ku sarauta" yayi maganar a baibai, cike da mayarwa da Hajiya Lubabatu martani.

"Ikon Allah, da alama auren haWi zai koma na soyayya, ai labarin zuciya a tambayi fuska takawa".

Adam ya ce "Eh to, ba zan musa miki ba, amma hausawa suka ce Wan hakin da ka raina.."

Murmushi kawai hajiya Lubabatu ta yi, tana yi musu su gaida gida. Rumaisa tuni ta yi waje, dan idan ta cigaba da tsayuwa, matar nan tana washe baki, tana gaya mata magana, ba abun da zai hana ta zageta.

Shi kansa adam mood Win rumaisa ya gani, ya san a ?ule take kamar ta fashe dan takaici, la'asar ta riga ta yi sosai, ya ga idan suka koma gida, shi ficewa zai yi, ya san zama za ta yi, tayi ta ?unci a gidan, dan haka ya wuce da ita da

Please Login or Register in order to submit comment