You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wanka ta sauya kaya, sai dai ta kasa manta fuskar mai sunan baba, yau yayi kyau sosai, sai dai yanayin muzuransa ko tunawa ta yi sai ta ji gabanta ya faWi, dan har suka kawota gida, ban da kwatance, ko abokin nasa ba ta ji yana yi wa magana, balle ita ya kulata.

?angaren mai sunan baba ma, mamaki yake yi, yadda tsoronsa ke bayyana sosai a kan fuskar iman, ya san yana da kwarjini sosai, sai dai ita ya lura ba kwarjini kawai yake yi mata ba, tsoronsa take ji, tsoro kuma ba na wasa ba. TaSe baki yayi ya cigaba da sabgoginsa.

Washegari ya kama ranar da za ayi dinner, rumaisa ta tashi da ciwon kai, saboda kukan da ta sha jiya, idanunta duk sun yi ja.
Ta wuni a uwar Wakan mama, tun ?arfe uku yayyenta suka tafi fara nasu shirin, a ?arfe ukun kuma, aka aiko da motar kaita wurin kwalliya.
Ma?wabta na ta mamakin wani hamsha?in ne haka zai auri rumaisa, sai abu ake yi kamar wata babbar budurwa.

A wurin kwalliyar ma, kuka take ta yi, Habiba da su hauwwaliya suna ta rarrashin ta, amma ta ?i tsayawa.

Mai kwalliyar ?awar nusaiba ce, dan haka ta kirata ta sanar da ita halin da ake ciki. Nusaiba ta gaya wa takawa, ya din ga mitar shi ba ya son a tsaya wannan shafe-shafen aje a ajiye mutane su na jira.

?arshe dai da kansa ya tafi wurin kwalliyar da shi da bashir.
Ya je ya tarar duk an yi wa ?awayenta kwalliyar ban da ita.

Ya kalleta ya ce "Zaki tsaya ayi kwalliyar ne, ko kuma mu tafi a haka?".

"Ni bana son auren nan na fasa, mama ta ce wai barin gidanmu zan yi, ni na fasa" ta yi maganar cikin kuka.

Bashir ya ce "Haba rumaisa, an gama tara mutane, ki bari idan aka gama sai ayi duk maganar da za ayi".

Adam dai ya ?ule ?arshe, Bashir ne yayi ta bata ha?uri, sannan ta tsaya aka yi.

Mai kwalliyar ce ta fito da rumaisa reception, ta yi kyau kamar ba ita ba, kayanta iri Waya da na Adam.

Hauwwaliya har da tsalle, tana koWa rumaisa.

Bashir ne ya din ga yi musu hotuna, sai dai daga ita har adam babu wanda yake walwala.

A harabar wurin bikin, suka tarar da su Aliyu, sun haWe cikin shadda iri Waya, hatta huluna da agogo iri Waya suka saka, motar na tsayawa, ta buWe ta fice ta nufi wurin su Usman.

Abdallah ya din ga Waukar rumaisa a hoto.

Usman ya ce "Allah sarki lantarkin gidanmu, zaki tafi ki barmu a duhu, zaki barmu da Wan hasken da ba zai ishemu ba"

Rau-rau ta yi da ido, za ta yi kuka, ya girgiza mata kai ya ce "Yau ranar murna ce, da yi wa Allah godiya, ki bari mu je mu yi rawa mu ci kaji, idan an koma gidan kya yi kukan, dan kukanki ba zai hanani cin abinci ba na gaya miki"

Bisa ga al'ada, ?awayen amarya da ?an uwanta ne ke shigo da ita, sai dai wannan amaryar, yayyenta maza ne suka shigo da ita, ga ta ?ar mitsitsiya a gaban angon nata, kamar ?a da uba.
Abun ba ?aramin ?ayatar da mutane yayi ba, sai dai fa wasu surutu suka fara da raina wayon takawa, na auren ?ar mitsitsiyar yarinya.

Taken gidan sarauta aka saka wa shigowar ta su, ga maro?a da suka biyo su suna yi musu busa, tare da kirari.

Rumaisa ta kalli yadda hall Win ya cika, dama tun daga haraba motoci ba a magana, manyan mata masu shiga ta alfarma, gaba Waya taga ido a kanta, ga takalmi mai tsini, take ta ji jiri na Wibarta.

Adam ne ya fuskanci haka, dan haka ya ri?e hannunta, sai da ta Wan waro ido, ta sake kallon mutane ta ga kowa sai ?o?arin Waukarsu a hoto yake yi, ta sake sunkuyar da kanta a cikin mayafi, tana ?o?arin ?wace hannunta daga na Adam amma ya ri?eta sosai.

Har kan high table suka raka rumaisa, suka zaunar da ita, kowa ya gansu sai ya ce Masha Allah, tare da jinjina rumaisa a matsayin ?anwar zaratan maza har bakwai.

Iman ce ta fito stage, ta karSi mic, tare da gabatar da addu'a, da fatan alkhairi ga amarya da ango.

Jabir ba ?aramin mamaki ya yi ba, ganin rumaisa ita ce matar da takawa zai aura, ya din ga tunanin yaya aka yi hakan ta kasance bai sani ba?. Me Adam zai yi da wannan yarinyar ?ar talakawa mara kunya.

Sai da aka yi kamu, kan a fara gabatar da dinner, duk wani abu da ?awayen amarya za su yi, yayyen rumaisa ne suka yi shi.

Dangin su Adam sun so su farfaWi maganganu, da yin rashin mutunci a wurin, mussaman da kusan kowa ya san Samha tana son shi bai aureta ba, amma kasancewar su Abubakar da mai sunan bab a wurin, suka cika wa mutane ido, kowa ya ri?e gulmarsa.

Jabir ya rasa nutsuwarsa, ga tunanin auren adam,ga iman ta Wau ado, sai shiga take yi tana fita, yayin da ita kuma hankalinta ke kan mai sunan baba, har fata take Allah ya sa ba kallonsa ake yi ba, dan dangin nan akwai tarin ?an mata.

'To sai me ina ruwanki?' wata zuciyar ta tambayeta.

Aliyu habiba ya saka a gaba, yana yi wa dariya ?awar amarya an sha Wauri, ?ar ba?a kyakykyawa.

Iman ta ?arasa ta cewa Usman "Yaya ban san sunanka ba, na san dai duk sunanku yaya, kuma duk kamarku Waya, koda yake na san yaya Aliyu"

Usman ya ce "Usman nake, ma'abocin haske, ?ar balarabiya ya aka yi ne?".

Ta yi murmushi ta ce "Dama ban sani ba ko kun zo da abokanku, ga in da aka yi muku reserving can, za a fara dinner ne, gara mu fita kunyar kowa".

Usman ya ce "Abokai kai, kin san mu yawa ne da mu, bari in tattaro su wuri Waya, dama zan zo mu zauna in baku amanar ?amwarmu, dan Allah a kula mana da ita, ayi ha?uri da ita, idan aka taSata zuciyar maza bakwai ce za ta girgiza "

Iman ta yi dariya ta ce "Wane mu mu yi mata ba dai-dai ba ma, ai sai mu sha duka" tun da suke zuwa gidansu rumaisa, maganar kirki ba ta taSa haWata da yayyen rumaisa ba, sai yau da Usman yake yi mata halin na sa.

Umar yana jin su, kasancewar yana kusa da su.

Jabir ya ?araso in da Iman ke tsaye a wurin usman ya ce "Sweetheart, ina son magana da ke fa, ina aka yi wa abokan aikinsa reserving, suna daf da ?arasowa, na ga ke ki ke ta arranging mutane".

"Uncle J, ina wani aikin ne, ga uncle bashir nan, da shi muka zo wurin nan Wazu, ya san yadda aka tsara komai fa" ta yi maganar cikin muryarta ta shagwaSa.

"Yes na ji, zo mu je dai, ko na Wagaki yanzu na yi waje da ke, idan ya so gobe a Waura auren da namu"

Usman dai murmushi kawai yake, iman kuwa ba a son ranta ba, ta bi bayan jabir.

Suna yin gaba ya hau ta da faWan, dan me za ta je wurin maza ta tsaya. Ba ta iya bashi amsa ba, ta tsaya tana kallon sa kamar za ta fashe da kuka, babu tsammani mai sunan baba ya gifta ta bayansu yana waya, ta Waga kai suka yi ido huWu, da sauri ta koma cikin wurin dinner.

KwaSe fuska rumaisa take yi, tana nema ta yi kuka, Adam ya Wan sunkuyar da kansa ya ce "Meye kuma?".

"Ni na gaji, sai kallona ake yi, kamar wata mara gaskiya, ni bana son kallo, kuma ma yunwa nake ji, ina jin bacci ma kaina ciwo yake yi, na gaji da hayaniyar nan" ta ?arasa maganar bilha??i za ta yi kuka.

"Yanzu a gaban mutanen zaki yi kuka ranar aurenki, salon ace auren dole za ayi miki, ko ki janyo mini zagi ko?"

Tura baki ta yi ta ce "Ba auren dolen bane, ni na ce na fasa, amma aka ?i fasawa, wayyo mama ni na gaji"

A ransa ya ce na shiga uku, wannan Yarinyar tana neman ta jaza mini abun faWa.

Mc kuwa koWasu kawai yake yi, saboda shagwaSa rumaisa take yi, da ya sake fito da yarintarta, ba shiri adam ya din ga ya?e, dan kar a fahimci wani abu.

Abdallah ya hango, yayi masa alama da ya je, adam ya ce masa ya samo abinci ya zo ya bawa rumaisa, kar ta yi masa kuka.

Sai da Abdallah ya dungure mata kai, ya ce "Wace amaryar ki ka ga tana cin abinci a wurin bikinta?"

"Ni yunwa nake ji, ga su hauwwaliya can suna cin abinci, bari na je mu ci tare"

"Dalla zauna na je na samo miki, wai yunwa ranar aurenki dan abun kunya" ya sauka yana mita, ta bi bayansa da harara.

Da ya samo abincin, sai da su Aliyu suka raka shi, suka yi mata rumfa, ba a iya ganinta, Aliyu ya Webi abinci a cokali ya kai bakinta, wai ita ba abinci za ta ci ba, naman za ta ci, gani ta yi an bawa kowa abinci ita ba a bata ba.

Suka din ga zaginta suna bata naman, shi dai adam jinjina kai kawai yayi, ya yi wa Allah godiya da babu wanda ya san wainar da ake toyawa.

An sha hotuna kamar babu gobe, rumaisa ta Waga kai ta kalli Iman da ta zauna a kusa da ita, mai sunan baba yana gefenta aka yi musu hoto.

Hatta ammi ta je wurin, an yi mata li?i sosai da sosai, an ci an sha, manyan mata sun yi rawa sun yi li?i.

Yayyen rumaisa ma da abokansu, haka suka din ga yi mata li?i, wannan ya ja ta nan ayi mata hoto, sai ka rasa waye angon ma a cikinsu.

Adam ma basarwa yayi, ya din ga yi mata li?i, kuWi ba kaWan ba, ta din ga kallonsa ta ga ko yana sane, amma ya?i kallonta kar ta yi wani shirmen. Babban abun da ya fi burgeta, shi ne fareti, da kuma crossing sword Win da abokan aikin su Adam suka yi musu.

Gajiya kam rumaisa ta yi ta, dan har gyangyaWi ta fara, da ?yar take iya buWe idonta, ga takalmi mai tsinin gaske a ?afarta.

Sai sha Waya da rabi na dare aka tashi, rumaisa tana ta sauri ta bi su yaya Abubakar, amma takawa ya sakata a gaba zuwa motar da suka zo.

Tana shiga ta zauna ce "Wayyo Allahana, na gaji"

Ya kalleta yayi shiru, basu je ko ina ba ta hau bacci, gaba Waya ta kife masa a jiki, kai da jin yadda take sauke numfashi ka san ta gaji da yawa.

Sidi ya ce "Sir amarya ta gaji da yawa"

Adam ya ce "Gashi har ta yi bacci"

Sidi ya ce "Allah mai iko, ba zan manta scene Win da ku ka yi making, ranar da ku ka fara haWuwa ba, and she's now your wife"

Adam ya ce "Shhhhh, a daina tayar da wannan maganar"

"Sorry sir"

Adam ya gyara mata kwanciyarta, ya Waukar pose Win ta, ya buWe, ga sababbin kuWi nan a ciki, fal. Ya girgiza kai ya ri?eta a hannun sa.
Rumaisa kuwa jin ta take kamar a kan katifarta, har da gyara kwanciya.

A ?ofar gida ya tarar da yayyenta, suna jiran su ga ta ina za su ?araso, ya sauke glass Win motar, gaba Waya suka ?araso.

"Ta yi bacci fa" ya faWa yana kallon Usman.

Usman ya ce "Ai haka take, da yin magariba take bin bango, a bata ta ci ta yi bacci, kamar ?ar kaza".

Adam ya Wagata zaune da niyyar ya tasheta, amma ina baccinta kawai take yi.

Mai sunan baba daga in da yake tsaye, yana hango cikin motar, rumaisa ba ta san ma me ake yi ba. Haka nan ya ji wani irin kishi ya taso masa, ?anwarsa a kwance a jikin wani ?ato. Takawa ya Waga kai suka haWa ido da shi, ya wani cukule fuska.

Aliyu ya zura hannunsa, ya Wauko rumaisa gaba Waya, ya nufi gida da ita,, da gayya Adam ya fito daga motar, ya ce "Kai Ali ka yi a hankali, kar ka yi mata rauni fa, a kawo mini nakasashshiyar amarya gobe, ba zan karSa ba, da na san bacci za ta yi daga nan ai gida zamu wuce kawai"
Aliyu ya ce "Tuba nake, zan kula sosai"

Juyawa mai sunan baba ya yi, ya shiga gida, ?asan zuciyarsa istigfari, da tunanin meye nasa na jin haushi kuma, bayan komai daWewa dole wataran ta zama matar wani.

Aliyu ya shimfiWe rumaisa a katifar mama, Gwaggo cewa take "Wannan an yi shashasha amarya, haka take da wannan nauyin bacci haka, ta bar mutane da dakonta".

Mama ta ce a tasheta ta yi sallar isha'i, lawisa ta ce sun yi salla a gidan kwalliya, kafin su tafi.

Tana magagin, mama ta dafa ruwa, ta kaita banWaki ta wanke mata fuska, ta yi mata wanka tas, ta lulluSota ta kawota Waki, ?an biki na ta yi mata dariya, sai dai har a cikin ranta ji take ruman ba ta wuce wankan ba, ?addarar aure zata rabata da ?ar da take matu?ar ?auna.

?akin samarin nan kuwa, kusan kwana suka yi babu bacci, suna ta Wan tattaunawa, a kan biki, da kuma jajanta rabuwa da tilon ?anwarsu, kuma kallabi a cikin rawunansu.

Mai sunan baba kuwa ya naWe, ya lumshe idanunsa ya yi shiru, ba abun da yake ganowa sai kai wa da komowar iman a wurin nan, da yadda suke yawan haWa ido. Tsaki ya ja???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? ya nemi wuri ya kwanta, sai dai tunanin gobe dai-dai lokacin, rumaisa na gidan wani, ya hana shi bacci, ya din ga yi mata addu'ar shiga gidan miji a sa'a.


Bayan idar da sallar juma'a, aka Waura auren rumaisa da adam, ?an unguwar da basu san waye mijin ba a ranar suka ji.
Unguwar ta cika da dawakai, da manyan motoci na alfarma, duk in da ka kalla, jami'an tsaro da kuma masu rawuna ne.

Sai dai tun da aka Waura auren nan, rumaisa jikinta yayi sanyi, take ta uban kuka, duk yadda aka so rarrashinta abun ya gagara.


Tuni hotunan biki suka zaga duniya, kowa da abun da yake tofawa, na alkhairi da akasin haka.


Samha kuwa kaiwa take ta yi tana komowa a Wakinta, tana fatan aikin da ta bayar ayi mata, ya yiwu ba tare da samun wata matsala ko akasi ba, dan ta riga ta ?udirce wa kan ta Waukar fansa, ko da tsiya ko da arziki.

Ammi a wani event center, ta shirya taron wunin bikin, sai dai abu ya so ya zama rigima, in da facalolinta da masu goya wa mummy baya, suka din ga ci mata mutunci, wai saboda Aisha ba ?ar ta ba ce, ta shirya irin wannan biki haka, kuma aka samo yarinya mara galihu ta aurawa mahaukacin Wan ta.
Duk yadda ammi ta so jurewa sai da ta kusa zubar da hawaye, Nusaiba ba ta da hayaniya, balle iman, Laila ce masifaffiya dama, kuma ba ta ?asar da ita kaWai ta ishi duk wani mai bakin magana.

Da la'asar mama ta kira ammi, ta ce mata za a kawo rumaisa nan wurinta, ta gaisheta ta yi mata faWa, sannan a wuce da ita gidanta, ammi ta ce ba sai an kawota ba, saboda wasu dalilai, zuwa magariba zata turo da waWanda zasu Wauki rumaisa.

A yammacin aka yi kilisar dawakai, takawa ya haWe cikin kayan sarauta, rumaisa ma aka yi mata ado da alkyabba, aka yi ta musu hotuna.



Da magariba rumaisa ta yi wanka, ido duk ya kumbura saboda kuka, Yasir da ya shiga ya fita ya ga tana kuka, shi ma sai ya fashe da kuka, ta tashi ta saka kaya ma abu ya gagara mama sai daurewa take yi, amma hawaye ya cika mata ido.

Jiki a sanyaye mai sunan baba ya shiga Wakin, ya tarar da ita a zaune, tana kuka mai taSa zuciya.

"Rumaisa" ya kira sunanta, ta Waga kai ta kalleshi.

"Tashi ki saka kayanki, kar dare yayi sosai".

"Dan Allah mai sunan baba ku yi ha?uri, wallahi na fasa ni ba zan tafi na barku ba, mama dan Allah ku yafe mini ku barni na zauna a gida, ni ba zan iya rayuwa babu ku ba" tayi maganar cikin kuka.

"Tom, mun ji, amma fara saka kayan" da ?yar ya saka kaya, ya ciro turare a aljihunsa ya fesheta da shi, mata sai rangaWa guWa ake yi.

Ta ri?e mama tana wani irin kuka.

Ya saka hannu ya cire nata daga jikin mama, ya ja hannunta yayi waje da ita.

Suna fita mama ta shiga Waki, ta fashe da kuka, dan an kai in da ba zata iya jurewa ba.

Suna tafe a mota tana kwamce a jikin mai sunan baba, tana ta kuka, kamar ta shiWe.

"Am sorry, kiyi ha?uri haka lamarin aure yake, da haka kowace mace take tara nata iyalin, Ubangiji Allah ya baku zaman lafiya, ya sanya alkhairi. Ban da rashin kunya da raina miji, mijinki ne ibada zaki je ki yi, ki nemi aljanna na san duk an gaya miki, ki girmama mahaifiyarsa, matar nan ina ganin mutuncinta saboda son da take yi miki. Sannan kuma Sabir ko Allah ya baki naki Wan, kar ki canza soyayyar da ki ke yi masa, ki yi ha?uri ki saka a ranki, ?ofar sabon ?alubale zaki buWe ki shiga. Duk da ?an?antarki nauyin aure ya hau kanki sai ha?uri, kiyi ha?uri, ki yi ha?uri, ki jure ki daure duk ?alubalen da zaki fuskanta wataran sai labari, ina yi miki addu'a Allah ya sassauta miki jarrabawar gidan aure, don babu auren da babu jarrabawa"
Haka ya din ga yi mata nasiha, har suka je gidan, gida ya tsaru kamar ba na rumaisa ba, ko ina ya ji kaya.

Ana kai rumaisa wata ?anwar ammi, ta sake saka mata alkyabba a kan kayanta, suka din ga yi mata guWa a ka, amarya ?anwar maza, dan su suka kawota Wakin ma.

Sun daWe tare da rumaisa, kowa da irin faWan da yake yi mata. Sai da kowa ya watse, Tawagar angwaye suka ?araso, gida ba kowa sai tsirarin mutane da zabga-zabgan ?arti.

Suna zuwa mai sunan baba ya tashi ya ce su tafi.
Rumaisa ta ri?e rigarsa ta tashi tana kuka "Dan Allah yaya umar, kar ku tafi ku barni, ku tafi da ni, ko ku zauna da ni a nan Win, dan Allah yaya. Yaya usy, yaya Abubakar, dan Allah duk ku zauna, Abdallah kar ku tafi, Yasir dan Allah" mai sunan baba duk ya kaWa musu kai alamar su tafi.

Iman tana cikin waWanda suka rage, gaba Waya tausayin rumaisa ya cika mata zuciya.

A hankali ya fincike rigarsa daga hannunta, ya juya, ta sake ri?o rigarsa.

Ya juya a kausashe ya ce "Wuce ki je ki zauna" a razane ta saki rigar ta sa tana kuka.
Yana juyawa sai hawaye, karo na farko da abu ya daki zuciyarsa ya saka shi kuka. Ya saka hanky ya goge, ya kalli Adam ya ce "Ga ta nan amana ce, marainiya ce, ko ka ci, ko kula da ita" yayi maganar wasu hawayen na cika masa ido.

Adam har mamaki yake, wace irin soyayya suke nuna wa rumaisa haka.

Bashir ya ce "Za a ri?e amana in sha Allah. YallaSai aje a rarrasheta dan Allah, tana cikin damuwa".

Adam ya ce "Sai ma ka faWa? Ba daga ni sai ita zaku tafi ku bari, wannan kuma ya rage nawa" dariya abokansa suka yi, suka yi musu addu'a sannan suka watse.

Ya koma ya shiga Wakin na ta, tana tsaye tana ta kuka, ya ?are mata kallo sannan ya ce
"Yau sarki mai koriyar alkyabba, ya baki alkyabba saura Wana ki a kan doki. Sannan ke kuma ki cika al?awarin sanya shi dur?usa miki a kan gwiwoyinsa".


What's app only please =?O?
Ayshercool.
08081012143

*Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*


Wani mugun kallo rumaisa ta yi masa, ta ture hannunsa da yake gyara mata zaman alkyabbar jikinta, ta ce "Ba ruwanka da ni, kuma ka zo ka mayar da ni gidanmu".

"Ni na kawo ki? Sai ki fita ki koma ai, tun da bani na Wauko ki ba".

"Kuma wallahi sai na tafi, ko ka sani ko ba ka sani ba".

Hannunsa ya saka, ya matse mata kumatu, ta saka hannunta ta ri?e hannunsa, saboda azabar zafin da ta ji.
Ya sake kallonta ya ce "You better behave yourself, a gidana ki ke, fita ki bar mini Waki, wancan Wakunan zaki Wauki Waya, da safe zan saka a kwashe miki tarkacenki, a mayar miki can" ya ?arasa maganar yana sakar mata baki.

"Ba in da zani, tun da dai na ga kayan da aka sai mini ne a ciki"

"Kayanki ne, amma gidana ne, sai na kwashi kayan naki na mayar haraba, ki je can ki ?arata" ya yi maganar yana wucewa cikin bedroom Win.

Ya rage kayan jikinsa, ya shiga banWaki.
Har yayi abun da zai yi ya fito, rumaisa tana tsaye, tana kuka.

Ya je yayi salla, ya wuce ta ya je kitchen, ya dawo amma tana tsaye. Nan ya sake sarawa taurin kan rumaisa.

Har ya gama cin abun da zai ci, tana tsaye ?yam, ta juya masa baya, ya kashe fitila, ya kunna A.C, ya kwanta, gajiyar biki da zirga-zirga ya sanya yana kwanciya bacci mai nauyi ya Wauke shi.

Rumaisa gajiya ta yi da tsayuwa, ga tsoro da ta fara ji saboda duhu, ga sanyin A.C yayi mata yawa, dan ba ta saba ba, ta nemi wuri ta kwanta a ?asa, ta du?un?une a cikin alkyabbar ta hau bacci.


Mama kuwa yadda ta ga rana, haka ta ga dare, dan babu wani abu mai kama da barci da yayi shirin Waukar ta.
Haka ma ?an mazan nan, Aliyu cewa yake "Allah ka rufa mana asiri, Allah ya sa kar yayi mata wani, abu yarinya ce ?arama wallahi".

Usman ya ce "To yanzu mu kake gaya wa ko yaya?"

"A'a addu'a kawai nake yi"

Mai sunan baba duk da yana cikin damuwa, amma jin abun da suka faWa da ya haWa ido da Abubakar, kawai Abubakar ya tuntsire da dariya, mai sunan baba kuwa murmusawa yayi, tare da basarwa kamar bai ji me suke faWa ba, haka suka kai har wurin ?arfe biyu, suna hira yadda biki ya gudana, da kuma jimamin ya rumaisa za ta kasance a gidan aure.


Samha ma haka daren nan yayi, ta kasa rintsawa, duk da sun yi chatting da Fauziyya, tana ta rarrashinta, ta tura mata hoton bikinsu Adam.
Amma kasa tsayawa ta yi ta kalla, saboda yadda zuciyarta ke matu?ar tafasa da wani irin masifaffen kishi.
Ko lokacin da ya auri Aisha, ba ta shiga wannan yanayin da take ciki a yanzu ba.



Sai da aka kusa idar da sallar asuba, sannan Adam ya farka, a gaggauce ya shiga banWaki, yayi alwala, sai da ya ga ba zai samu salla ba ko ya fita, dan haka ya ce bari kawai yayi sallarsa a Waki.
Ba tare da ya kunna fitilar ba, ya tayar da salla, bayan ya idar ya din ga jin kamar numfashin mutum, har gabansa ya faWi, dan ya Wauka irin razana shin da aka saba yi ne, ya tashi ya kunna swtich Win Wakin, mai zai gani, madiga ce a kwance take ta uban baccinta, abun ka da a gajiye take dama, duk ta cukuikuye alkyabbarta.


"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ke wai a nan ki ka kwana?" Yayi maganar yana taSa ta.

Oho bata san yana yi ba, bacci kawai take yi.

"Tashi, ki je ki yi salla" nan ma bata tashi ba.

Toilet ya shiga ya Webo ruwa, ya dawo ya zuba mata a fuska.

A rikice ta tashi tana faWin "Huzaifa meye haka wai?".

"Na hauzaifa bane Adam ne, ban ce miki ki bar mini Waki ki tafi ga naki can ba"

Maimakon ta yi magana, sai ta haWe rai tana kallonsa, kamar mafarki take yi ma ba a zahiri ba.

Ganin ta tsareshi da ido, ya sanya ya tashi, ya ri?e hannunta ya yi waje da ita, Waya bedroom Win ya kai ta, ya juya ya tafi ya barta.

Kallon Wakin ta yi, wasu furnitures Win ne a ciki ba nata ba, amma sun yi kyau sosai da sosai.

Ta cire Alkyabbar, ta shiga ta yi alwala, ta fito babu hijjabi. Ta koma Wakin da aka fara kai ta, wato Wakin da Adam ya ce nasa ne, ta buWe drower ya Wau

Please Login or Register in order to submit comment