gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Dr.bob Complete Hausa Novel by by Aysha Rano Chapter 32 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

samarinta ya fito da ita sbd batada hankali...ta zauna gaban motarshi tanata washe mashi baki sbd batasan ciwon kanta ba ga wani shegen riga da tasa da bai gamsheshi ba sam..gaba daya rigan ya bayyana surar jikinta instead of tasa hijab shine ta dakko wnn dan veil din tayi rolling sbd rashin nustuwa...ranshi yaji yayi wani irin 6aci baisan lokacinda ya hada kan nashi da starring motar ba...yana rantsuwa da Allah idan har yarinyar nan zata cigaba da abubuwa haka mutuwa zaiyi...yasan for sure ko wulakancin da take mashi bai kasheshi ba to duk ranar da aka daura mata aure da wani nashi ya kare...a yanda yakejin zuciyarshi tamkar tana dab da fashewa ne sbd ciwon da yakeji cikinta ya fara mishi yawa...kiri kiri wai kana son mutum shi kuma baya sonka wani yakeso...duk ya tunada wnn abu sai yaji kmr yayi commiting suicide ya huta...har ta karaso inda yake bai iya dago kanshi ba..ganin tanata knocking ko dagowa baiyi ba kawai ta bude motar ta shiga fuska daure kmr wanda tayi ido hudu da makiyinta...duk abunda take yana jinta amma ko dagowa baiyi dan shi kadai yasan what is taking place in his heart...addu'o'i yayita karantawa iri iri har yaji ya dan samu relieve snn ya dago kan nashi ba tareda ya kalleta ba ya tada motar suka tafi...a hankali ta dan saci kallonshi taga fuskan nan a dinke kaman na saniya dan haka ta shafawa kanta salama tayi kasa da kanta tareda cewa"ina yini"..ko kallon inda take baiyi ba balle tayi tunanin samun amsa daga wurinshi...ta tabe baki tana gyara zamanta dama ba gaisheshi tayi dan ya amsa ba dan rainin hankali kawai...haka suka cigaba da tafiya in silence har suka isa Malam Aminu Kano International Airport...mamaki ya cikata ganin airport ya kawota ko me zasuyi a nan kuma oho?..bata dai tambayeshi ba tanaji bayan ya gama parking ya dauki wayanshi yayi dialing number daddy...bayan ya dauka Bobby yace"mun iso airport din sir"..daga daya bangaren daddy yace"muma gamu nan shigowa ciki yanxun nan"..daga haka ya kashe wayarshi snn ya bude motar ya fita...itama ta bude daya side din ta fita...suna fita kuma motan daddy yazo yayi parking a kusada nasu...ta wani zare ido tana kallon motar kmr bata taba ganinta sbd mamaki...kenan daddy ne yace ya kawota airport zasuyi tafiya ne ko kuma yaya abun yake?..daddy ne ya fara fitowa daga motar sai Ammi sai Husna da Yusra suma suka fito a tare...da sauri ya karasa inda suke yana kokarin durkusawa daddy yayi saurin kama hannunshi ya hada da nashi sukayi musabiha yana fadin"bana hanaka durkuson nan bane Attahir"..murmushi kawai Bobby ya saki kanshi kasa yace"barka da isowa"..daddy yace"barka dai..ya aiyuka?.."kai a kasa yace"Alhamdulillah sir"..sake kama hannunshi daddy yayi yana nunawa Ammi yace"to Maimunatu yau dai gaki ga Attahir"..ya juya yana duban Bobbyn shima yace mishi"itace Maman Aysha"..kokarin durkusawa ya sakeyi still daddy ya hanashi...ba yanda ya iya haka nan ya mike saidai ko kusa ya kasa dago kanshi ya kalleta a hankali yace"Ina yini"..Ammi dake kallonshi tana murmushi tace"lafia lau Attahir..ya aiki ya kuma akaji da fama da Aysha?.."murmushi kawai ya saki kanshi a kasa...daddy ya sake nuna mashi su Husna kafin yace"ga sisters dinta nan..wnn sunanta Asma'u karamar kuma Yusra"..kallonsu Bobby ya shiga yi yana murmushi..Husna ta fara gaisheshi snn Yusra duk ya amsa musu smilingly...yaji gaba daya ahalinta sun shiga ranshi don sunada karamci sosai...ita kuwa Aysha da tayi mutuwar tsaye tun daxun tana kallonsu sai yanxu ta samu sararin karasawa inda suke hankalinta duk ya tashi kar ace tafiya zasuyi ba tareda ita ba tac"daddy sannunku da zuwa"..daddy yace"yauwa..ya karatun?.."tace"fine daddy gobe zamu fara exams"..yace"Allah ya bada sa'a"..ta amsa da Ameen snn ta juya tana kallon Ammi jiki a sanyaye tace"Ammi ina yini"..itama ta amsa mata da"lafia lau..ya mkarantan?.."tace"fine..Ammi tafiya zamuyi?.."murmushi Ammi ta saki gamida girgiza kai tace"tafiya zamuyi dai..keda zaki fara exams waye zaiyi tafiya dake?.."nan ta marairaice tace"Ammi dan girman Allah zanje kinga ko last year ma da banje umrah ba..kuma ai Friday zamu gama exams din"..kafin Ammi tayi mgn daddy yace"yanxun ma ba cewa akayi bazaki jeba ai..zakije amma sai kin gama exams dinki zaku taho tareda Najeeb"..shiru tayi batace komai ba itadai Allah ya sani tafi son ta tafi tare dasu...Yusra ce ta matsa kusada ita kmr zatasa kuka tace"daddy nima zan zauna da Adda"..daddy yace"no itada take makaranta a ina zata ajiyeki"..da sauri ta sake cewa"daddy nidai zan..."bai bari ta karasa ba yace"stop it Yusra bazaki zauna nan ba"..ba musu tayi shiru tana turo baki Ammi dai kallonsu kawai take tana murmushi...hannun Bobby daddy ya kama yace"zo muyi mgn son"..ba musu ya bishi a baya...Aysha kmr jira takeyi su bar wurin ta matsa kusada Ammi kmr zatasa kuka tace"Ammi dan Allah ki cema daddy ku jira in gama exams plss"..harara mai kyau Ammi ta watsa mata kafin tace"sbd ke kika haifemu sai mu zauna zaman jiranki ki gama exams koh?..idan kika cigaba da damuna wlh gaba daya zan soke tafiyan naki saiki koma gida ki jiramu kafin mu dawo"..ta wani tale baki kmr zata sa kuka tace"kai Ammi dan Allah"..harara ta kuma watsa maka before tace"just dare me and see what will happen..keda har yanxu bazakiyi hankali kisan kin girma ba"...shiru tayi bata sake mgn ba sai turo baki da take...juyawa tayi taga yanda suke mgn cikin kwanciyar hankali har wani smiling taga sunayi duk su biyun cikin ranta tace"ai dole kayi daria tunda kana neman shiga tsakanin da mahaifina..mugu dakai kawai"...bayan kmr 5 mins suka dawo wurin...Bobby yayi sallama da Ammi dasu Husna snn ya bar wurin...itama Aysha sallamar tayi dasu idonta har ya ciko da hawaye ta juya zuwa inda yayi parking...tana bude motar ta shiga saita hada kai da guiwa ta shiga sauke numfashi...Bobby yayi shiru yana kallonta baidai ce komai ba...lumshe ido yayi ya jingina da kujera yana jin wani irin zafi na neman rufeshi...wai after duk wulaknci da ignoring dinshi da take still bayason ya ganta cikin damuwa...ya rasa wani irin al'amari ne wnn ace wai duk bata maka rai da mutun zaiyi even for once bazaka iya fita sabgarshi ba...ko kuka yaga tanayi sai yaji kaman da idanunshi takeyi...baya son jinshi ko kadan kuma yasan ko yayi mata mgn ma zaiyi wahala ta dena..baisan meyasa ta tsaneshi to this extent ba...bude idonshi yayi a hankali tareda tada motar suka bar cikin airport din...driving yakeyi a hankali yanajin yanda har yanxun kukanta bai bar taba zuciyarshi ba...ganin abun nata bana kare bane sai ya gangara gefen titi yayi parking shima ya hada kanshi da starring motar yana sauke numfashi...duk duniyar sai yaji tayi mashi wani irin kunchi da zafi da baisan daga ina hakan ke fitowa ba...saida ya dauki lokaci mai tsayi a haka kafin ya dago kan nashi da kyar yana kallonta...cikin muryanshi da yaji ya disashe all of a sudden ya kira sunanta"Aysher"...banza tayi dashi bata amsa ba kuma bata dago kanta ba..ya sake kiran sunan nata still bata amsa ba baisan lokacinda cikin karaji yace"idan baki denamin kuka a mota ba saukeki zanyi wlh..are u small kid da zakisa mutum a gaba da kuka sbd an tafi an barki.."..shiru tayi still bata dago kan nata ba..da karfi yakai hannunshi ya dago fuskan nata sai yaga ko digon hawaye babu..iskanci ne kawai yasa tayi hakan ashe ba kuka take ba..kallon cute face din nata ya tsaya yi without blinking...rabonshi daya kalli face dinta haka har ya manta..a hankali yaji wani irin nutsuwa na sauko mishi sbd ganin fuskan nata...ya lumshe ido yana sake budeshi kan face din nata da har dunia ta nade yasan bazai taba gajiya da kallonta ba...sai ya nemi duk wani haushinta da yakeji ya rasa..baisan ko magic take using a kanshi da baya taba iya dogon fushi da ita ba..duk yanda zata kai da bata mashi rai yana kallon face dinta sai yaji ya yafe mata komai sbd tsabar farin cikin da kallon fuskan nata ke sanyashi musamman idan tana cikin farin ciki...lokaci daya kuma ya dauke idonshi daga kanta ya wani sake dinke fuska snn ta tada motar suka cigaba da tafia...wani babban super market taga yayi parking yace ta jirashi nan ciki snn ya fita daga motar...bayan few minutes ya dawo da babban leda a hannunshi yasa back seat snn ya shiga ya tada mota suka cigaba da tafia....ko a hanya bai iya cikakken minti uku ba tareda ya juyo ya kalleta ba...haka nan sai yakejin ganin nata na tafiya da duk wani kunchi da damuwarshi...babu wanda yayi mgn har suka isa FCNM Hostel...daidai gate dinsu yayi parking kafin ta bude motar ta fita yayi saurin dauko ledan daya ajiye a baya ya mika mata cikin wani irin kaushin murya yace"ina iya neman wani alfarma wurinki?.."juyawa tana kallonshi wai alfarma zai nema shine fuskanshi cunkus haka..kai kawai ta daga mashi alamar eh...ledan ya sake mika mata kafin yace"hijabai ne nan ciki..inaso ko dan darajar amanarki da mahaifinki ya bani ki dinga sawa idan zaki fita..ko cikin college zaki shiga ki dora akan uniform dinki idan kinje class sai ki cire tunda na fuskanci ke har yanxu bakisan ciwon kani ba"...kallonshi kawai takeyi kmr mai tunanin wani abu sai kuma can ta numfasa tareda karban ledan da yake miko mata tace"nagode"..da sauri yace"banji kince zaki na sawa ba"..a takaice tace"zan sa"..ya saki wani murmushi yana binta da ido yace"nagode"..komai bata sake cewa ba ta bude motar ta fita shi kuma yayi relaxing nan ciki yana kallonta har saida ta shiga ciki snn yaja motar yayi reverse ya wuce.

Ranan Thursday suna kwance hostel bayan sun fito daga exams kowa tana fama da azuminta musamman Lamido da sai juyi takeyi kan gado wai tanajin yunwa...sbd tsabar haushi Billy ko tanka maka tabayi ba har ta gama surutunta ta hakura...tana nan kwance har bacci ya fara daukanta taji wayanta na ringing...hannu ta mika ta dauko wayan daga kan study table dinta tareda dagawa takai kunne...muryan Sa'eed taji na fadin"my bestyyyyyy"...wani irin mikewa zaune tayi da sauri tana zare idanu tace"besty is this really you?.."full of excitement yace mata"its me besty...ur very own best friend"..tun kafin ya rufe baki ta wani turo baki tace"ba wani my very own best friend..yanzu tsakani da Allah haka ake rayuwa besty?..tunda ka tafi ba hello ba hy kaman dama ka gaji damu"...tana rufe baki shima yace"dadina da besty rigima wlh..to yanxu dai ku fito gani bakin gate ina jiranku".. sake zare idanuwanta tayi tamkar wanda tayi gamo da aljani tace"are u serious besty?."yace"come outside mana zaki gani ai"..daga haka ya kashe wayar ita kuma ta diro daga kan gadon ta rarumi hijab dinta ta zura snn ta karasa gadon Billy ta fara tashinta daga bacci...a fusace ta mike zaune tana cewa"Lamido wai meye baka plss?..meyasa bakyaso kiga nayi bacci a hostel din nan"..kama hannunta Aysha tayi ta mikar da ita tsaye ta dauko mata hijab ta mika mata snn tace"wai besty ne yazo yana bakin gate..kinji dan rainin hankali zaizo ko fada mana baiyi ba"...tabe baki Billy tayi tana kokarin momawa gadonta don sake kwanciya tace"kuma shine zaki tasheni daga bacci sai kace besty na ne yazo?.."sake kamata Aysha tayi ta shiga turata waje tana cewa"ai wlh baki isaba sai kinje"..daga haka ta ja hannunta suka fita daga dakin bayan Billy ta zura hijab dinta itama...suna fita suka hangoshi daidai inda ya saba tsayuwa idan yazo dan haka suka nufi wurin da sauri...har suka karaso inda yake kallonsu yakeyi yana murmushi...bai taba sanin da akwai friendship irin wanda yake tsakaninshi da su biyun nan ba...jinsu yake a jikinshi tamkar sun zama family...suna karasowa Lamido data wano hade girar sama dana kasa tace"nidai ba kulaka zanyi ba wlh"..murmushi ya saki kafin yace"idan besty taki kulani kuma ai sai in samu matsala..yanxun kiyi hakuri mu zauna sai in fada maku uzuri na nasan kema idan kikaji zaki hakura ki dena fushi"...ba musu gaba daya suka nufi inda suka saba zama nan cikin hostel din as usual...bayan sun zauna ya shiga musu bayanin tafiya sukayi zuwa Canada tareda Dad dinshi shine dalilinda yasa basu samunshi a waya...shima kuma bai samu yayi roaming ba and bai hau social media ba har suka dawo shiyasa sukajishi tsit kmr baya existing...kmr yanda ya fada kuwa nan da nan ta sauko daga fushin nata sai kuma aka hau labari na yaushe gamo..hatta Billy da ba wani dasawa sukeyi ba yau labari na musamman sukeyi dashi sbd missing juna da sukayi...bashi yabar hostel din ba sai around 4 yace su shirya kafin magrib zaizo ya daukesu su fita don akwai special iftar daya hada masu for the three of them...murna wajensu kmr ba gobe haka suka koma hostel kowa ta fara shirin fita tunda yace before magrib din zaizo yayi picking dinsu.

6 nayi kuma yazo yayi picking dinsu sai Cilantro...wurin har wani decoration yasa akayi mashi specially for them dama already yayi reserving so daga su sai su zasuyi iftar dinsu...tun kafin asha ruwa aka cika masu gabansu da kayan ciye ciye iri iri...sunata hiransu abunsu har aka kira sallah Sa'eed ruwa kadai yasha ya wuce masallacin dake nan ciki yayinda su kuma suka gabatar da sallahrsu a inda suke...yana dawowa suka shiga iftar dinsu hankali kwance kowa ka gani cikinsu is full of happiness and excitemet sbd kada cewa tareda junansu after a long period of time...Sa'eed sai snapping dinsu yakeyi wani su biyu kadai wani kuma yayi musu selfie gaba daya..a takaice sunyi having fun dinsu yanda ya kamata suna barin wurin kuma ya kaisu gidan Hajia nan ma taji dadin gani su sosai daga nan kuma yayi musu siyayyan kayan kwalam snn yayi dropping nasu a hostel as usual.

A daren ranar Dr Bobby yana parlonshi yana karatun Qur'ani kiran daddy ya shigo wayanshi...ajiye alqur'anin yayi tareda dagan wayan da sallama..bayan sun gaisa daddy yace"wani nauyin dai zan sake dora maka son Allah yasa bazaka gaji dani ba"..da murmushi Bobby yace"not at all sir..ka fadi kome kakeso zaayi inshaAllah"..cikeda jin dadin amsan daya bashi daddy yace"nagode sosai Attahir...mgnr Aysha ne dama gobe zasu gama exams koh?."yace"yeah gobe zasu gama"...daddy yace"so nake if it's ok by you ka kaita wajen mahaifiyarka ta kwana biyu zuwa sunday wanda zasu tafi dashi ne har yanxun Passport dinshi bai zama ready ba amma yacemin zuwa sunday komai zai zama ready inshaAllah..banson ta koma Gombe ne snn ta sake dawowa Kano tunda dole ta kano flight dinsu zai tashi"...da sauri Bobby yace"no problem sir..zan kawota inshaAllah"..daddy yace"i hope dai ba wani matsala koh?.."yana gyada kanshi yace"babu wani matsala inshaAllah"..murmushi daddy ya kara saki kafin yace"to nagode sosai Attahir..zuwa sunday din komai inshaAllah zai zama ready ita dama passport da visa dinta duk basuda matsala so ticket kawai zaa sai mata"...gyada kai kawai yakeyi yama rasa abunda ya kamata yace...sallama sukayi snn daddy ya kashe waya..shima ya ajiye nashi yana sakin wani numfashi da karfi gamida dafe kanshi...farin ciki ya kamata yayi sbd zata dawo kusa dashi amma what he's feeling is not close to farin ciki at all...yasan zamanta a kusa dashi din ba abunda zai amfaneshi dashi saima karin damuwa da zai sanya mishi tunda yasan ba sonshi takeyi ba...duk sai yaji damuwan da ya fara raguwa a tare dashi yana neman dawowa sabo...dunia yanxu babu abunda ke bata ranshi kmr idan ya tuna yarinyar nan bata daukeshi a bakin komai ba bata kaunarshi...dukda har yanzun ba bai furta mata yana sonta ba yasan ko a can kasan zuciyarta babu wani abu makamancin sonshi shiyasa idan ya tuna haka yakejin kmr zai hadiye zucia ya mutu...ganin damuwan na nema yi mishi yawa sai ya dauki alqur'aninshi yacigaba da karatun da yakeyi...nan take kuma yaji ya samu saukin damuwar daya fara rufeshi.

Washegari bayan ya gama shiryawa kafin ya fita ya nufi Flat din Mummy dan sanar da ita yanda sukayi da daddy jiya...tana zaune itama tana karatu ya shigo dakin..ya karasa kusada ita ya zauna har takai aya snn ta rufe Qur'an din tana dubashi tace"har ka fito?.."yace"na fito Mummy..dama wata mgn ce nazo muyi dake"..Mummy tace"to ina jinka"..saida ya lumshe ido ya bude kafin a hankali yace"baban Aysher ne dama yace in kawota tayi kwana biyu a nan wai wanda zasu wuce Saudi dashi passport dinshi bai gama zama ready ba"..full of excitement Mummy ta wara idanu tana cewa"da gaske?..to Allah ya kawota lfy yaushe zasu gama exam din?.."a takaice yace mata"yau"..sake wara idanu tayi tana murmushi tace"to Allah ya kawota lfy kace mishi babu wani matsala zatayi zamanta tare damu a nan"...kallonta kawai yakeyi ganin how happy she is kawai sbd zatazo gidan tayi kwana biyu...baisan meyasa ba shidai tun jiya da aka fadi mgnr nan yakejin jikinshi wani iri kmr dai ba nashi ba...Mummy ta kamo hannunshi tana dubanshi da kyau tace"wnn damuwan kuma na menene Bobby?.."dan matsala yayi ya dora kanshi kan shoulder dinta murya can kasan makoshinshi yace"bata sona Mummy..har yanxun bata kaunata dan Allah Mummy me zanyi mata ta soni..ko bai kai yanda nake sonta ba at least itama ta soni"...Mummy dake rikeda hannunshi tace"inaji a jikina zaka auri yarinyar nan kawai ka kwantar da hankalinka"..sake lafewa yayi a jikinta yace"na gaji ne Mummy..na gaji da chasing dinta tana nuna banida muhimmanci a wurinta..Allah kadai yasan halin da nake ciki these days ko bacci wahala yakemin..ji nake idan abubuwa suka cigaba da tafia a haka mutuwa zanyi"..girgiza kai Mummy ta shiga yi tace"nace maka ka dena fadin haka amma ba kaji..ajiye duk wani pride and ego dinka zakayi a gefe ka fada mata how feel..tell her that you love her and you can die for her amma ba kazo kana tambaya yanda zakayi ba"..lumshe ido kawai yayi yana sauke numfashi da kyar..baisan meyasa when it comes to love yakejin brain dinshi na toshewa ba..gaba daya sai yaji ya rasa me ya kamata yayi...abu daya daya sani shine ya dena chasing dinta infact yama dena nuna yana son nata tunda batasan yanayi ba.














Rano✨





Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ta fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
39
The next day which is Friday tunda suka fito daga exams Lamido keta trying number din Hamma amma bai shiga...duk ha kalinta yabi ya tashi kada dai ace shima wucewa yayi ba tareda ita ba...ta dubi Billy dake zaune kusada ita kmr zatayi kuka tace"Billy anya kuwa ba binku zanyi mu tafi ba?..kinga fa wayar Hamma har yanxun bai shiga ba"..Billy tace"tunda kika ga bai shiga ba kilan wani abun ne ya faru shiyasa nace ki kwantar da hankalinki kinsan Hamma bazai iya wucewa ya barki ba"..ta bude baki zata sake mgn wayarta ya shiga ringing ta duba da sauri don a tunaninta ko Hamman ne amma sai taga proprietor..dan bata rai tayi tana turo baki tayi picking call din ba tareda tace komai ba...shima sai yayi shiru na dan wani lokaci kafin yace"are u done with the exams?.."a hankali tace"eh.."yace"am coming right away to pick u up..if u like kije ki shiga motan saurayi kiga abunda zan maki"..yana gama mgn ya kashe wayarshi..itama ta ajiye nata tana 'yan mitocinta..Billy dake sauraronta tace"me yace wai?.."rai a bace tace"wani wai he's coming to pick me up ko gidan ubanwa zai kaini oho?..na fara gajia da halin mutumin nan wlh..mutum sai shegen zafin rai"...murmushi Billy ta saki kafin tace"ni salon love dinshi nema yake burgeni"..da sauri Aysha ta juya tana kallonta fuska a daure tace"what do u mean?.."girgiza kai Billy take tana cigaba da murmushi tace"aah ba abunda nake nufi nikam..kidai cigaba da rainama kanki hankali"...sake dinke fuska tayi ta cika tayi fam tace"kinga Billy bana son irin wnn abun da kikemin..na meye zaki dinga hadani da mutuminda kinfi kowa sanin yanda na tsaneshi"..har yanxu Hajia Billy bata bar smiling ba tace"shine nace kici gaba da rainama kanki hankali ai..kiri kiri kinsan mutumin nan sonki yake amma kina wani nuna baki saniba kina raina mana hankali kawai..continue deceiving yourself"..kallonta Aysha keyi fuskan nan ba sarari kmr zatasa kuka...dunia ba abunda ta tsana kmr wani ya bude baki yace proprietor sonta yake hakan ba karamin bata mata rai yakeyi ba...ita kuma Billy da gayya ma take mata haka sbd tasan yanda ta tsaneshi..idan ma ba wulakanci ba ta ya za'a kalli tsabar idonta ace wnn mutumin wai yana sonta..bayan duk wulakancin da yake mata shine mutane har suke da bakin cewa yana sonta?..ita bata taba ganin inda akayi soyayya haka ba..a iya saninta dai idan mutum na sonka baison bata ranka amma fa shi ko yanxu daya kirata a wani tsatstsaye ya fada mata mgn babu irin tausasa murya amma still sukeda bakin cewa yana sonta sbd basuda hankali...wnn dalilin ne yasa shi kanshi take dauke mashi wuta dan sai tayi sati bataje inda yakeba sbd kwata kwata bata son yanda mutane ke tunanin soyayya sukeyi...Billy kuwa kallonta kawai takeyi tana kunshe daria..al'amarin Lamido ba karamin daria yake bata ba wlh..ai ko makaho zuwa yanxun ya kamata ace yasan Dr Bobby sonta yakeyi amma ita kullum sai taita wani nuna batasan me yake faruwa ba...haka sukaita zaune a wurin babu mai cewa kowa komai ita Aysha na daure fuska yayinda Billy kuma ke daria kasa kasa...bayan wani dan lokaci akazo daukan Billy daga Bauchi nan kuma hankalin Lamido gaba daya ya tashi da taga da gaske Billy tafia zatayi ta barta..to ita ina zata zauna ne wai?..yaushe ne kuma zasu wuce Saudi don har yanxu bata samu mgn da Hamma ba...haka ta rakata har mota sukayi sallama snn suka wuce ita kuma ta koma ciki idonta na cikowa da hawaye...tana kokarin haurawa sama zuwa class dinsu wayanta ya sake daukan ringing...ta dakata da hawa stairs da takeyi snn ta dauka still batace mishi komai ba...a takaice taji yace"where are u?.."tace"Sir ina class"..a dan fusace yace"ni kike jira inzo in sauko dake knn?.."tayi shiru tana turo baki..yace"if u like ki fito nan premises ina jiranki and don't waste my time"..kmr zatasa kuka tace"wai ina zamuje?.."baice mata kala ba ya kashe wayarshi ita kuma ta sauka kasa zuwa premises din tanata banbami cikin ranta...can inda ta hango motarshi ta nufa kai tsaye ta bude front seat zata shiga taji ya daka mata wani tsawa yana cewa"ba nan akace ki shiga ba"..rufewa tayi snn ta bude na baya ta zauna nan kusa dashi driver ya tada motar suka tafi...shiru cikin motar babu wanda ke cewa wani abu a cikinsu...Bobby ya jingina kanshi da kujera tareda lumshe ido yana sauraran heart beat dinshi yayinda ita kuma ta rakube can karshen mota tana kallon window fuskan nan a tamke...kawai tunanin inda zai kaita takeyi..ita batasan meyasa ma Allah ya hadata dashi ba at the first place..kawai gashi nan yasa mutane na tunanin suna soyayya...maimakon gida sai taga hanyar Hospital dinshi ya dauka..ta tabe baki bata dai ce komai ba har suka isa Freedom Specialist Hospital...kafin driver ya bude mashi kofa ya bude ya fito da kanshi...itama ta fito suka shiga ciki..office dinshi ya bude suka shiga ya nuna mata seat yace ta zauna nan ta jirashi theater zai shiga..batace mishi komai ba har ya fita daga office din sai a snn ta bishi da harara tana fadin"da azumin ma mutum bazai dena bakin hali ba..wani wai zai shiga theatre sai kace dai a kanshi aka fara zama doctor bashida aikin daya wuce theatre"...haka tayita zaune nan office din tana jiranshi har kusan magrib bai dawoba duk ranta yabi ya gama 6aci..knn a asibiti yakeso tasha ruwa ko a ina?..kawai yazo ya wani ajiyeta office dinshi kmr wata gantalalliya...har ta cire ran dawowarshita gama sadakarwa yau a nan cikin asibitin zatayi iftar dinta sai kuma gashi ya dawo hajaram majaram dashi kmr wanda ya kwana yana theatre😂bai tsaya wasting anymore time ba yace ta tashi su wuce...su A'i ba musu ta mike tabi bayanshi...suna shiga mota driver ya tayar da ita suka tafi...har suka isa gida ba wanda yayi mgn cikinsu..driver na gama parking ya bude mota ya fita ya rage su biyu a cikin motan..har ya bude shima zai fita sai yaga hankalinta na wani wajen..kallonta ya tsaya yi for like 5 mins kafin ya dauke kanshi a hankali ya bude motar ya fita..ga mamakinshi har ya kama hanyar entrance bata fito

Please Login or Register in order to submit comment