gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Dr.bob Complete Hausa Novel by by Aysha Rano Chapter 24 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dan haka ta fada musu exactly yanda sukayi dashi...hankalin Billy ya tashi matuka dan ko ita Lamidon bazata gaya mata shiga tashin hankali ba dama yanda kasan farar kura haka take wajen tsoro...basuyi niyyan barin kd ranan sunday ba amma haka Sa’eed ya tattarosu suka wuce sbd yana guje musu matsalan da zasu iya fuskanta wajen proprietor dama kuma biki ya kare tunda ankai amarya...haka suka tafi ko sallama basuje sunma amaryan ba...karfe uku da wani abu suka dauki hanyan kano and basu suka shigo birnin dabo ba sai around six..suna ganin an dauki hanyan FCNM hankalinsu ya sake tashi musamman Aysha da cikinta har wani juyawa yake sbd tashin hankali...har tsoron kunna wayanta take sbd tasan tana kunnawa zai kira and hakan na nufin masifa da bala’i dan kuwa tasan idonta idon Dr Bobby saiya cinye mata mutunci tas tunda dama ba yanxu ya saba ba..kawai tsoronta kada ya hadata da babanta amma dan ta masifarshi mai sauki ne dan idan da sabo yaci ace ta saba dukda cewa yanxu sam bai cika mata ihu ba..wani lokaci ko abu ya kama na fadan ne da idan baiyiba bazaiji dadi ba sai yayi mata shi a nutse kaman ba fada yakeyi ba amma yau kam tasan idan akwai abunda ya wuce ihu ma zaiyi shi tunda ta gama kular dashi...har suka isa hostel babu mai kwarin guiwar yin mgn cikinsu shi kanshi Sa’eed din addu’a yakeyi Allah yasa bazasu samu matsala sbd shi ba tunda shine wanda ya daukesu zuwa kadunan and Allah ya sani da yasan basuyi informing parents dinsu ba ba dalilinda zaisa ya kwashesu har kd saidai rashin sani...kafin su rabu ya sake kwantar musu da hankali tareda assuring dinsu cewa inshaAllah komai zai tafi normal..sukam gaba dayansu jinshi kawai sukeyi amma gani suke dole fa sai wani abu ya faru either big or small.

The next day sukayi shirin school kowa tasa uniform dinta suna jiran school bus saidai ba wanda takeda walwala a cikinsu...baa jimaba bus dinsu yazo ya kwashesu sukayi cikin makarantan...ana ajiyesu suka fice yau har rige rigen fita daga bus din suke a takaninsu sbd gudun haduwa dashi dukda ma sunsan monday ba ranan shigowarshi bane...daga nan direct class dinsu suka wuce basu sake fitowa ba har suka fara lectures.
Karfe tara daidai yayima Bobby a college din dukda cewa Monday ne ga kuma jikinshi da bai gama sauki ba amma ko hospital ya kasa zuwa sbd yanaso ya ganta...kai tsaye sama ya haura zuwa class dinsu don yasan idan yace har saiya sameta a waya to bazai taba samunta ba dan ba kunna wayan zatayi ba...wani lecturer ya samu a class din yana musu lectures dan haka kai tsaye ya fada class din fuskan nan a tamke kamar baisan menene daria ba...hannu ya mikawa lecturer din suka gaisa snn ya maida hannun aljihu yana baza idanu yanaso ya hangosu amma ko daya daga cikinsu bai gani ba...hankalinshi ya maida kan ‘yan class din fuska ba fus yace"where is Lamido?.."da sauri suka nuna inda take can baya tana sunukuyar dakai..baice kala ba sai takawa da yayi har gaban seat din nata ya zuba mata idanunshi ko kadan bata sonsu snn a kausashe yace mata"mike.."ba musu ta mike tsaye kai a kasa..ya sake cewa"ina Bilkisu?.."da sauri itama ta nuna seat dinda Billy ke zaune itama kallon nata yayi tayi saurin dukar da nata kan snn ya juya still hands dinshi a aljihu yace musu"follow me"..sum sum suka bi bayanshi kaman marasa gaskia..yana gaba suna binshi dukda bai juyaba yanajin footsteps dinsu ta bayan nashi dan haka kai tsaye ya wuce office dinshi suna biye dashi..a hanya ya kusa cin karo da Nur ya wani wara ido yana kallonshi then su Lamido dake biye dashi sai kuma ya saki dan murmushi yana maida dubanshi gareshi yace"so ka warke knn?.."ko kallonshi Bobby baiyi ba ya wuce office dinshi...yana isa ya bude kofa da yake bai shigowa Monday so secretary dinshi bata zoba...shine ya fara shiga ciki snn sukabi bayanshi...a kan sofa ya zauna yana kallon yanda sukayi wani cirko cirko a gabanshi sai ya sauke idanunshi kan Billy da yake ganin kamar tafi hankali yace"Bilkisu hadda ke?.."da sauri Billy da kanta ke kasa tace"wlh sir ba laifina bane ba yanda banyi da ita akan mu fada a gida ba tace wai baza’a fada ba"..yace"then meya hanaki kirani ki fadamin?.."Billy da har ta fara hawaye tace"shima cewa tayi bazan fada ba wai sbd hanawa zakayi?..sir dan Allah kayi hakuri wlh bazai sake faruwa ba"..gyada kai yayi dan ya yadda da ita yace"next time kina ganin zatayi anything stupid just give me a call ai kinada number na"..gyada kai Billy tayi tace"inshaAllah sir"..yace"shknn u can leave"..Billy tayi godia snn ta juya zata fita Aysha tabi bayanta da sauri wai tunaninta ya sallamesu gaba daya amma sai taji cikin cunkushashen voice dinshi yace"who ask u to leave?.."juyowa tayi a hankali tana dubanshi kaman zatasa kuka tace"sir dan girman Allah in tafi"...ya sake hade rai yace"C’mon comeback here before i loose it with u"..juyawa tayi a hankali ta daw ciki idonta na cikowa da hawaye...kallon hawayen dake silalowa daga idon nata yayi nan take ya lumshe ido yanajin yanda hawayen ke sauka har cikin zuciyarshi...baisan meyasa these days ko tayi laifi tana fara kuka jikinshi ke mutuwa ba..so yake yayi mata masifa son ranshi amma yana ganin hawayen nan yaji zuciyrshi yayi waji weak...kujera ya nuna mata idanunshi a kanta yace"seat"...batayi musu ba ta zauna inda ya nuna mata tana hawaye na sake ambaliya akan face dinta...dafe goshi Bobby yayi hade da lumshe ido yanajin yanda takeso ta sake haddasa mishi ciwon kai da wnn kukan nata yace"For Gods sake me akayi makai na kuka ne wai?..nayi maki wani abun ne?.."girgiza mashi kai tayi still tana hawaye yace"then why are u crying?..nida kika haddasa ma rashin lafia banyi kuka ba saike zaki sani a gaba kinamin kuka?..kinama da hankali kuwa?.."turo baki tayi jin abunda ya fada wai ta haddasa masa rashin lafia..ta sake tale baki tana dan kallonshi ta gefen idonta tace"nidai dan Allah karka fadawa daddy plss"...kallonta yakeyi yace"naji I won’t tell him amma inaso ki dena kukan nan muyi mgn dake"..ba musu takai hannunta ta goge hawayen duk yana kallonta snn tace"na goge"..gyara zama yayi still idonshi kanta yace"tambaya nakeso inyi maki and i want u to be fair to yourself..idan da a Gombe kike gaban parents dinki would u do what u where doing now?.."girgiza mishi kai tayi a hankali alaman bazatayi ba...yace"then why kikeyi a nan sbd ba gabansu kike ba?..tsakaninki da Allah da ace wani abu ya sameki a hanya what do u want me to tell ur dad daya bani amanarki?..ko sbd kina ganin baki ta6a yin wani abu na sanar dashi ba?.."girgiza kai ta shigayi da sauri tace"sir wlh ba haka bane..gani nayi Lubna friend dinmu ce sosai and ko sbd besty bai kamata muki zuw..."bata karasa ba ya katseta cikin karaji yace"in your entire life karki sake mentioning min besty idan muna mgn..ina ruwana da wani besty ni ke na sani bashi ba and idan bakiji abunda na fada ba kuma you will see the other side of me"..ya karasa mgn har wani huci yake kaman tsohon zaki...Lamido dai kallonshi kawai take tana mamakin yanda yake changing forms within minutes..yanxun nan fa yake mata mgn a nutse kmr bashi ba within a second kuma ya dawo mata asalin proprietor data sani...kauda kanta tayi tana turo baki ita gara ma ya dingayi mata masifan kmr yanda ya saba ba yasata a gaba yanayi mata mgnr dake sa jikinta yana mutuwa ba...ganin yanda itama ta hade rai tana turo mishi baki ya danyi kasa da voice dinshi yace"wai meyasa bakijin mgn ne ke kam?..meyasa fitinanki yayi yawa?.."sake turo baki tayi tana gunguni kuma akan idonshi kawai sai ya rufe idanu tareda jingina jikin kujera yana karanta innalillahi a cikin ranshi...kamar yanda ya fada ne idan baiyi wasa ba yarinyar nan saita haifar mishi da ciwon zucia sbd abunda yakeji kanta is beyond his control...kawai yana ganin Allah ne ke jarabtarshi da ‘yar Gombe sbd tsananin kiyayyan da yakema ‘yan Gomben.









Rano✨






Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
29
Kallonshi Aysha keyi ganin yanda ya dafe goshi ya lumshe ido aikuwa ta daddage ta maka masa wani harara sai gashi karaf ya bude idon nashi...ta wani zaro ido hadda dora hannu a bakinta tace"sir i swear bada kai nakeba"..bai iya cewa komai ba sai kallonta da yakeyi nan kuma tayi kasa da idanunta tanajin idanun nashi har cikin brain dinta...ta rasa meyasa har yanxun ta kasa sabawa da idanun mutumin nan..sam bata kaunar ya zuba mata su sbd sawa suke tanajin wani iri wlh..sai su saka nutsuwar da baka shirya masa ba...shiko Bobby kallon nata yakeyi yana tattaro duk wani abu da yasan yanaji akanta yana dorasu cikin idon nashi wai ko Allah zaisa taga illar da take nemanyi mishi ta zubar da makamanta...sun dauki lokaci mai tsaho a haka har zaman wurin ya fara isanta kafin kuma taji yace"bani wayarki?.."juyawa tayi ta kalleshi sai kuma ta kwar da idon da sauri ta zaro wayan da aljihunta ta mika mashi..ya amsa ya duba sai yaga babu key a jiki dan haka kai tsaye whatsApp dinta ya shiga yayi deleting gaba daya status dinta daga nan ya shiga gallery nan ma yayi marking all pictures dinsu na kaduna yayi deleting snn ya shiga bin duk wani picture da sukayi itada besty yana deleting dinsu...a garin haka yaci karo da wani da sukayi itada Prof ya zuba mata ido yana kallonta da murmushi itama tana murmushin aka dauki picture din...wani abu mai daci yaji yazo ya tokareshi a makoshi..sai yayi zuru yana kallon pic din yana sakejin zuciyashi ma tafarfasa amma bai nuna mata ba yayi deleting pic din ya muma cigaba da abunda yake...bayan ya gama da wnn foldern ya fito ya shiga wani sai yaci karo da pictures din ‘yan Manchester rututu musamman Pogba dan nashi sunfi na kowa yawa a matsayinshi na best player dinta...tsayawa kawai yayi yana kallon pics din kaman gunki..yana yin minimizing ya sake cin karo da hoton pogba akan screen din wayan nata datayi making as wallpaper ai baisan lokacin da yayi wurgi da wayan nata ya fadi kasa ba...Lamido ta wara ido tana kallonshi idonta kmr zasu fado don mamaki kawai sai taga ya mike ya fada bathroom ya wani buga kofan da mugun karfinda saida ya tsorata ta...jiki na rawa ta mike ta fita daga office din ko takan wayanta da yayi rugu rugu a kasa batabi ba...shiko yana shiga samun wuri yayi ya zauna yana dafe head dinshi wani azababben kunchi na sake rufar mishi...ya tabbata da yaci gaba da zama a wurin nan ita kanta yana iya yin ball da ita sbd kuncin da yakeji...ashe rashin hankalin nata har yakai ta ringa tsayawa tana hoto da ko wane banza and to top it all har tara hotunan ‘yan kwallo takeyi a wayarta kaman ta hada wani abu dasu?..hadda wani sanya picture din namiji a wall paper dinta wai meke damun yarinyar nan ne kam?..waye wani Pogba da take mugun sonshi haka?..me akai akayishi ma gaba daya..anya kuwa yarinyar nan bata samu ta6in kwakwalwa ba?..idan ba haka ba why zatana abubuwanda ba kowace mace ce keyi ba..meya hada mace da kallon ball idan ba tsabar rashin hankali ba...saida ya dauki lokaci mai tsaho nan cikin bathroom kafin ya fito..bai sameta a office din ba amma wayanta na nan inda yayi wurgi dashi sai yanxu kuma yaga bai kamata ya fasa mata waya ba..kaman yayi overreacting amma shi kanshi ba laifinshi bane baisan meyasa yake kasa controlling abuna yakeji akanta ba...gaba daya ma sai yaji dana sanin zuwa college din yake at the first place kawai sai ya juya ya fita daga office ba tareda yabi takan wayan daya farfasa mata ba.

Karfe hudu da kusan rabi ya baro hospital kai tsaye yacema driver ya kaishi FCNM zai shiga hostel yayi wani abu...driver ya dauki hanyan college din shi kuma Bobby yayi relaxing a back seat idanunshi lumshe yana sake sake cikin ranshi...tun daxu yasa aka kawo mashi sabon waya irin nata sak shine yakeso yakai mata tun kafin taje ta fara yamadidi dashi cewar ya fasa mata waya...bakin kokarinshi kawai yake na ganin abunda yakeji bai kwantar dashi ba amma ko Allah yasan ba karamin mawuyacin hali yake ciki ba...suna isa cikin hostel din yasa akayi mishi mgn da daya daga cikin matrons dinsu ya bata wayan bayan yace mata ta bada a kaiwa Lamido...daga haka gida ya koma dan ko ganinta bai sonyi ballantana ta sakeyin wani abun zuciyarshi tazo tana bugawa...koda ya koma gida yaki kwanciya kokari yakeyi sosai ya yaki abunda yakeji gameda ita yasan yana bari ya kwanta shknn ciwo zai samu galaba a kanshi.

Haka kwanaki sukaita tafiya suna zama weeks..weeks kuma suna zama watanni har suka fara second semester exams...zuwa yanxu Bobby ya tabbata ko ba sonta yakeba to definitely he’s attracted to her and tunanin hakan kadai yana iya samai zazza6i sbd tsabar takaici...zuciyarshi kwata kwata bata mai adalci ba amma alqawari ne ya daukan ma kanshi bazai bari koma me yakeji a kanta yayi tasiri a zuciyarshi ba...da wnn alkawari ya samu yake yaqar abunda yakeji dukda cewa ba karamin wahala bane yake bawa kanshi...har suka gama exam suka tafi hutu bai sata a idanunshi ba hakan kuma ba karamin tada hankalinshi yayi ba abun har mamaki ya bashi...da farko gani yake kaman rashin ganin nata shine mafi a’ala amma zuwa yanxu ya tabbatar idan ba ganin nata yayi ba yana iya samun gagarumin problem...haka a daddafe suka cinye two weeks dinsu na holidays zasu dawo school Sunday..Monday kuma kowa ta fara zuwa Clinical Area...baisan hospital da za’ayi posting nata ba dan haka yau Saturday yana barin Hospital ya kira Nur yace yanaso su hadu a College that yanada mgnr da yakeso suyi dashi..Nur baiyi masa musu ba yace su hadu a college din...karfe biyar saura ya shiga cikin makarantan a lokacin ma ko Nur din bai karaso ba dan haka ya jirashi nan cikin mota ya karaso snn suka wuce office din Nur din gaba daya...bayan sun zauna Nur yace"to Dr Bobby ina sauraronka"...ajiyar zucia Bobby ya sauke yana tunanin ta inda ya kamata ya fara dan bayason iskancin Nur ko kadan dan haka ya dinke fuskanshi tsaf yana wani babbasarwa snn kai tsaye yace mishi"wane Hospital akayi posting Lamido?.."Nur yayi kuri da ido yana kallonshi yana daria cikin zuciyarshi yana tausayi abokin nashi amma bai nuna mishi komai ba a fili yace"well ina tunanin bazai wuce General Hospital ba..kasan rural posting ne"...da sauri Bobby yace"inaso a dawo da ita Freedom"...kallonshi dai Nur yacigaba dayi yana tuno ranan da tazo tace a canxa mata posting amma yace baza’a canxa ba yanxu kuma gashi da kanshi yakeso a canxa mata posting din..kamar zai tsokaneshi sai ya tuna yanda sukayi dasu Mummy dan haka ya basar tareda fadin"shknn zanyi mgn da isaac zaa canxa mata inshaAllah"...wani ajiyar zucia Bobby ya saki sai yaji kaman an sauke mashi wani nauyi...yanada reasons da yasa yace a kawota Freedom sbd yasan ba hankali ta cika ba kilan zuwa zatayi taita kule kulen maza tana abunda bai kamata ba shiyasa yake sonta a kusa dashi yanda zaisa mata ido...Nur dai nata kallonshi yana kunshe daria a haka sukayi sallama kowa ya shiga motarshi ya wuce.

Washegari misalin 12 suka iso makaranta tareda Hamma daya dawo dasu as usual...kowa taje ta duba posting dinta suna murna zasuje rural posting amma sai sukaga an sake posting dinsu Freedom again...aikuwa gaba daya murnan da suke ciki sai ya koma ciki musamman Lamido da ko kadan last posting da tayi a Freedom din bataji dadinshi ba infact that was the most difficult and boring posting data ta6ayi a rayuwarta..lokaci daya duk wnn farin cikin na tafi rural ya koma ciki...kallon Billy tayi tana wani misti misti da ido sbd 6acin rai tace"zo muje mu samu provost mu fada mashi wlh..kan me za’a wani sake kaimu Freedom bayan ko last time can mukaje"...girgiza kai Billy tayi tace"nidai babu inda zanje and ina bakin shawaran kema ki hakura kawai..if u could remember last time ma kinje a canxa maki posting din hakan bai yiwu ba so yanxun ma ba canxa maki zasuyi ba"..sake hade rai Aysha tayi tace"amma nidai an cuceni wlh..dukma wanda ya bada shawaran a barmu a Freedom Allah ya isa tsakanina dashi wlh"...dan murmushi Bily ta saki kafin tace"nasan bazai wuce proprietor ba"..Aysha dai batace komai ba haka suka karasa cikin hostel kowa rai a 6ace.
Ranan Monday tun seven Bobby ya bar gida zuwa Hospital ko breakfast bai iya tsayawa yayi ba duk yanda Mummy taso yayi hakan kuwa...so kawai yake ya sanyata idonshi ko zai samu ya cike wasu gurabe da yakejinsu so empty a cikin zuciyarshi...su kuma basu karaso Hospital ba sai after eight...bus dinsu na gama parking duk suka firfito zuwa cikin asibitin kowa sanyefa uniform dinshi...daga bakin office dinshi ya hangosu suna tafia and duk yawan nan nasu idanunshi basu sauka kan kowa ba sai ita..nan take kuma yaji wani irin sanyi mai hade da zafi yana mamaye zuciyarshi..shi sanyin dai na ganinta da yayi ne after a long period of time while shi kuma zafin na jin ciwon yanda tazo asibitin ne daga ita sai dan hijab dinsu na uniform da ko chest dinsu bai gama rufewa ba...wasu sukan dora hijab ko mayafi akai idan anzo makaranta ko asibiti sai a cire amma Lamido koda wasa bai ta6a ganin tayi irin wnn ba...haka take yawonta a college da hospital tana tallata surar jikinta kowanne jick and jerk yana kallo...gashi ya kasa dauke idanun a kanta tunda yake bai ta6a jin ciwon kananun hijabs din nan nasu ba sai yau..gaba daya jikinta a waje yake sararin Allah...har sukazo suka wuceshi bai dena kallonta ba saida suka shiga office din da za’a yi musu posting...already yayi mgn da CNO yace ayi posting dinta theatre yanda zai dinga samun ganinta sosai..idan basuda aiki kuma ta tafi Office dinshi dan yasan tsaf zai iya zuwa ya samu tana hira da doc Gabriel ko doc Vivian...kaman yanda ya tsara din kuwa haka akayi..tanaji anyi posting dinta theatre hankalinta yakai kololuwar tashi dan har yanxu bata mance suman da tayi last time da suka shiga theater ba..sbd tsabar wulakanci duk fadin asibitin nan a rasa inda za’ayi posting dinta sai theater?..aiko billahillazhi bazata zauna a theater ba saidai duk abunda za’ayi ayi...suna barin office din kowa ya nufi various post dinshi including Billy dake maternity...ita kuma sai ta nufi office dinshi da nufin ta hadashi Allah annabi yasa a canxa mata posting...da sallama ta shiga ciki kanta a kasa ta gaisheshi...ya shiga binta da kallo sama da kasa yana wani 6ata rai kaman baiji dadin ganinya ba ya nuna hijab din jikinta yace"shi wnn mezai hana ki cireshi sai ki dinga yawonki a haka kawai"..kallonshi takeyi kallo irin na mamaki jin mgnr daya fada kafin tace"sir in cire hijab dina fa kake nufi"..a fusace yace"to meye amfaninshi tunda dama jikin naki kikeso a gani ai saiki cireshi kawai yanda zaa samu daman kallon jikin naki da kyau"...daure fuska tayi tana turo jin inda zancen nashi ya dosa tace"nidai bazan iya yawo babu hijab ba"...yace"if u are referring wnn abun dake jikinki to a hijab then you are deceiving yourself..ke ko irin asa babban hijab akan uniform baki iyaba..u always come out like this kamar dai tallan jikin naki kike"...sake daure fuska tayi jin maganganun da yake fada..indirectly fa zaginta yakeyi knn?..ita batasan ma tsautsayin daya kawota office dinshi ba tunda tasan halinshi and bazai ta6a canxawa ba...juyawa tayi zata fita a fusace yace"come back here"..ba yanda ta iya haka ta juyo ta dawo tana tutturo baki...mikewa yayi ya shiga wani kofa dake office din can sai gashi ya dawo da coffee hijab mai girma a hannunshi yana zuwa ya mika mata...batayi musu ba ta kar6a saidai fuskan nan har yanxu ba fus...komawa seat dinshi yayi ya zauna ita kuma ta sake juyawa zata fita yace"dawo kisa hijab din nan"...kaman zatayi kuka ta dawo ta zura hijabin..shi kuma yana zaune yana kallonta har wani dan murmushi ya saki ganin hijab din yayi covering dinta yanda yakeso yace"perfect...now seat saiki fadi meke tafe dake?.."zaunawa tayi tana sake marairaicewa tace"Sir dan Allah so nake kayi mgn CNO a daukeni daga theatre..tsoro nakeji wlh"...murmushi sosai ya saki wanda har ya bata mamaki dan zaiyi wahala kaga murmushinshi shiyasa idan yayi ma sai ta ganshi wani daban kmr ba proprietor data sani ba...saida ya gama smiling dinshi snn ya sake relaxing kan seat dinshi yana kallonta kamar ba gobe yace"yanxu me kikeso inyi Lamido?.."da sauri ta sake dagowa tana kallonshi dan ita wlh bata ta6aji ya kirata da Lamido ba..ko sunanta ma ita baya kira saidai yace ke ko wani abu amma yau shine da kiranta Lamido?..duk yau sai taga kaman bashi ba..kaman canxashi akayi sbd yanda yake behaving is so unlike him...ganin yanda tayi wani zuru tana kallonshi sai yadan hade rai yace"meye?.."da sauri tace"sir cewa fa kayi Lamido"...ya sake hade ran yace"eh ba hakane sunanki ba?..ko kinfi so kiji nace Aysher?.."wani mamakin ya sake kamata da alama yau dai Dr Bobby na cikin farin ciki...saita dan saki smile itama kafin tace"sir you are in a good mood today"..yana cigaba da smiling dinshi yace"of course..rabona da jin farin ciki kaman na yau har na mance"..dan wara idanu tayi irin abun mamakin nan sai kuma tacigaba da smile dinta tana gyada kanta tace"to sir albarkacin farin cikin da kake ciki kayi mgn a canxa min posting dan Allah"...girgiza mata kanshi yayi in a serious tone yace"no..kawai kiyi hakuri kije tunda can aka kaiki"...kaman zatasa kuka tace"sir suma fa nakeyi idan naga ana yayyanka mutum"...murmushi ya kara saki before yace"zaki dena inshaAllah..kuma I promise idan naga kin maida hankali kin nutsu sosai da kaina zanyi posting naki inda kikeso?.."nan da nan face dinta ya washe da fara’a tace"dan Allah da gaske?.."yace"yea i mean it..kawai so nake inga kin nutsu"...yana rufe baki kuwa ta hau gyada kanta tana fadin"nama nutsu tun yanxu wlh..i will be behaving gently"...yace"ni kuma zanyi posting naki inda kikeso"...sake gyada mashi kai tayi tana murmushi sai kallon yanda shima ya kasa dena murmushin take...mamaki take ashe haka murmushi ke bala’in mishi kyau amma baya yi?..kam ai da itace ta gane murmushi nayi mata irin kyan da yake mishi da kullum cikin murmushi zata kasance wlh koda cikin bacci ne kuwa...shi kuma kallonta kawai yake yanajin yanda yau ta ware dashi ba tsoro ba fargaba ko 6acin rai a tattare da ita...shi kanshi so yake ya gina kyakyawan alaqa tsakaninshi da ita yanda ko sun koma college bazata na gudunshi ba snn bazata na daure mashi fuska ba...yayi na’am da wnn shawara na zuciyarshi dan haka ya daura damarar gina shakuwa tsakaninshi da ita.

Cikin lokaci qanqani sai shakuwa ya shiga tsakaninsu kamar dai yanda Bobby ya daura damara a farko...sam yanxu basu fiya fada ba dan tanabin kusan duk abunda yace tayi sbd ya canza mata posting...ranan da farko da aka sake shiga theater da ita saida tayi wnn suman saura kadan ta fadi Bobby yayi saurin tareta ta fada jikinshi...gaba daya hankalinshi dama yana gareta sbd yasan something like this might happen...dole sai fita sukayi da ita suka kira wata tayi replacing dinta amma daga baya a hankali sai ta fara sabawa...gaba daya tsoron sai ta dena jinshi tunda gashi za’a shiga theatre da ita har ayi a gama bata ji jiri kota suma ba saidai dan wanda baza’a rasa ba...a zaman kuma ta koyi abubuwa da dama dan sai yanxu take gane ashe zama a theater din yanada amfani...a haka ta cinyeshi two weeks dinta a theatre.

Yana zaune office dinshi yana duba patients wayanshi ya fara ringing bai daga ba saida ya sallami matar ta fita..ya saki dan murmushi ganin wanda yake kira snn yayi picking ya gaidashi with respect...a daya 6angaren daddy yace"Attahir kana lafia?.."yace"ina lafia sir..ya aiki?.."daddy yace"Alhamdulillah..kana

Please Login or Register in order to submit comment