You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gode"" ya jinjina mata kai ya fice."

"Iya tana kallonsa daga tagar Wakin ta, yanayin yadda yake shishshigewa ummi, abun ya fara ™ular da ita, dan haka"

"tayi ™wafa, tare da aniyar Waukar mataki a kansa."

"Sai dai can ™asan ranta, ta ji babu daWi ganin kuWin da aka yi, gashi ta riga ta saka an zane ummin, an rufeta a Waki"

"kwana da wuni, ba tare da hakkinta ba. Haka nan abun ya din ga damunta, da safe ummi ta je har Waki ta gaisheta, da uniform za ta tafi makaranta."

"""Kin karya ne zaki tafi makaranta?"""

"Ummi ta ce ""A'a"""

"""Ki je wurin sa'adatu ta zuba miki kunu idan ta dama"" ummi ta Wan yi shiru ta tuna yadda sa'adatun ke haWe rai idan"

ta je karSar kunun.

"Ummi ta ce ""Na san idan na je ya ™are"""

"Iya ta bankaWa Wan tofinta, ta ciro naira Wari, ta ajiye wa ummi ta ce ""Gashi nan ki sai waina a hanya ki ci"""

"Ummi ta kalli kuWin, tana wani irin murmushi da ita kaWai ta san ma'anarsa, ta mi™e tsaye idonta fal hawaye ta ce ""Ki"

"bar shi iya, idan na dawo na ci abincin"" tayi waje."

"Tana jin Iya na zazzaga mata masifa, tana zaginta, amma tayi waje tana share hawaye."

"""³ar ™an™anuwarki da ke, kin san munafunci, to kin yi wa kanki, halin uwar taki da nake ta gudu sai da ki ka kwaso shi? To ki ci kanki, da ke da mugun halin naki"" Haka iya ta cigaba da sababi da kame-kamen borin kunya."

"Ummi na tafe a hanya tana kuka, haka ta ™arasa makaranta, suna ta shirye-shiryen shiga sakandare, sun kusa zana"

"jarrabawar common entrance, shi ma kuWin jarrabawar da ™yar, ta biya, shi ma Naima ce ta zo gida, ta sa aka kirawo ta, take ta yi mata tambayoyi da ™yar ta gaya mata batun kuWin jarrabawar."

***

"Manema na ta zuwar wa mariya, duk da ba fita take yi ba, amma mariya tayi burus, mahaifinta ya kaWa ya raya, amma ta™i tsayar da kowa, da yayi mata zancen auren ma sai ta hau koke-koke."

"Yayi ta rarrashin ta, a tunanin sa ko saboda tsohon mijinta ya sanya take jin ba zata sake yin aure ba, yayi nasihar, yayi rarrashin saboda kusan shekaru huWu kenan rabonta da aure."

"Kuma shekarun nan huWu cif, ita ba mai lafiya ba ita ba mara lafiya ba."

"Takura mata da maganar aure, ya sanya ta daina cin abinci ma, ta ™ara tsananta kaWaice kanta, ga rashin barcci da ya sar™afe ta, ta wuni ciwon kai dare yayi ta kasa bacci."

"Tsananin ciwon kai ya sakata a gaba, gashi tayi shiru ba wanda ta gayawa, abu kamar wasa tun tana daurewa har ta"

"kasa, ta din ga burgima a ™asa tana wayyo kanta."

"Sai a lokacin suka san ba ta da lafiya, aka kaita asibiti, sai dai babu cigaba, idan an kaita asibitin sai an tursasata shan"

"magani, idan ta sha Win ma babu cigaba, wasu lokutan haka zata ri™e kanta tana ihu, tana kuka saboda rashin iya bacci, idan aka kaita asibiti sai dai su yi ta yi mata allurai."

"˜arshe aka tura su ganin likitan ™wa™walwa, hankalin mahaifin mariya ya tashi da ´an uwanta, jin an tura su"

Sangaren likitan ™wa™walwa.

"Likita ya duba ta sosai da sosai, ya basu shawarar a kula da ita sosai, saboda depression ne ya kamata, idam ba a"

"kula da ita sosai ba, za a rasa hankalinta gaba Waya."

"Karo na farko da iyalan su mariya suka ji mahaifinsu yayi wa wani Wan adam Allah ya isa, wanda sai da ya zubar da"

"hawaye, yana matu™ar tausaya wa mariya, dan haka bai gaza ba, ya sake tashin yaya magaji, tare da Maryam, ya ce su je su bawa uwar mijin mariya ha™uri, ko sau Waya ta bayar da ummi, ta zo ta kwana biyu tare da mariya, ko a samu hankalinta ya kwanta."

"Yaya magaji ya ce ""Baba, ka san matar nan ba zata bayar da yarinyar nan ba, sai dai a tafi da mariyar, ta je ta ganta"

"mu dawo"""

"Maryam ta ce ""A hakan zamu tafi da ita? Ba zai yiwu ba ai, kana kallon abun da take yi, ai salon ta sake jin daWi ne,"

"dan matar nan ba mutunci ne da ita ba, kuma muddin aka bawa mariya ummi, ba zata bari a sake rabata da ita ba, a ganina kawai mu mayar da hankali a kan nema mata lafiya"""

"Yaya magaji ya ce ""Duk da haka, zan jarraba zuwa, duk da na san ba zamu wanyeta ™alau ba, amma zan jarraba zuwa"

"na ga yarinyar ma daga nan, Allah sarki ummi, na san yanzu ta yi wayo sosai."

"""Zata shekara goma zuwa sha Waya fa yanzu, ai ta zama budurwa"""

"Suka bar maganar a kan cewa, yaya magaji zai je ya gano ummi, idan ya ga fuska ya sako zancen tahowa da ummi."

"Ummi ta daina zuwa Wakin iya idan ba dole ba, saboda gudun kar ace ta yi wani abun, kullum cikin itace nan da"

buhhunan hatsi take kwana.

"Tsabar daka kuwa hannunta duk yayi kanta, yayi ta Wurar ruwa yana fashewa, saboda tana da taushin fata sosai."

"Tana tafe tana yada hannu, saboda gajiya ga rana, yunwa da ™ishirwa duk sun addabeta, mutumin da ta hango a"

"™ofar gidan su ne tare da kawu Ilyasu, ya sanya ta tafiya a hankali, ta ™arasa ™ofar gidan."

"Shi ma ™uri yayi da ido, yana kallonta, ta ™arasa ta dur™usa ta ce masa ""Ina wuni?"""

"Jiki a sanyaye ya amsa ya ce ""Ummi kin gane ni?"" Ta jinjina masa kai alamar eh."

"""To waye ni?"""

"Maimakon ta bashi amsa sai ta ce ""Ina mama?"""

"""Haryanzu baki manta da ita ba?"""

"Da sauri Ummi ta sake kallonsa ta ce ""Da ita ku ka zo?"""

"""A'a, na zo dai neman alfarmar na tafi da ke na kai ki wurinta, amma sun ™i yarda"""

"Kawu Ilyasu ya wani haWa rai, cikin haushi kamar tsohon kare ya ce ""Ke! Tashi ki wuce ki shiga cikin gida"""

"˜afafuwanta suka yi mata sanyi, ta ji tamkar ba zasu iya Waukarta ba"""

"""Ba zaki tashi ba?"" Ya sake yi mata tsawa. Cikin rawar jiki ta tashi, yaya magaji ya kamo hannunta ya dan™a mata"

"kuWi, yana ri™e da hannunta ya kalli Kawu Ilyasu ya ce ""Da ku da mahaifiyarku, ku shirya amsar da zaku bawa Allah, kalli wai wannan ´ar Wan uwanku ce dan abun kunya, kalli kayan makarantar da suke jikinta, kalli ™afafuwanta. Kun ce idan na tafi da ita babu ku babu ita, ku ba dangin mahaifinta bane ba, duk in da aka je aka dawo, da dangin uba ake ado, kuma ba zan cigaba da jayayya da ku ba, muna raba abun faWa, Allah zai zama gatan marainiya"""

"""Ummi ki kula da kanki kin ji ko? Ki yi ta yi wa mamanki addu'a, hankalinta yana kan ki, Allah ya yi miki albarka""."

"""Wai ba zan sake ganinta ba?"""

"""Zaki sake in sha Allah, Allah ya shiga lamarin ki"""

"Rirri™e hannunsa tayi tana kuka, tana yi masa magiyar ya tafi da ita."

"Da ™arfin tsiya kawu Ilyasu, ya fizgi hannunta, ya angizata zuwa cikin gida."

"Tana kuka suka ™arasa shashinsu, sai dai da munanan kalaman iya ta fara cin karo, tana Waga murya tana cewa ""Ni"

"dai azo a nema mini magani, a rabani da wannan dangin maitar da jaraba, sun kashe mini Wa suna bibiyata saboda ´ar su na hannuna, ba dole mariya ta haukace ba, ai kaWan ta gani, hauka bata ma fara shi ba, tun shekarun baya da na karSi ´ar ba ta yi haukan ba sai yanzu, Allah ya ™ara tuburata, yadda ta rabani da Wa na babu ita babu sukunin duniya!!""."

"Bright pens fans group, da sauran masoya ummin Iya, ina ganin sharhinku, ina godiya sosai da sosai "

Ayshercool

08081012143

*CUTARWA!*

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

BRIGHT PENS

(FREE BATCH)

P9

"Gaba Waya Ummi ta ji ™afafuwan ta sun yi mata sanyi, har suna neman gaza Waukarta, tayi ta maza ta ja jikinta ta"

"shiga, kai tsaye Wakin da take ta wuce, ba ta tsaya a in da Iya ke banbaminta ba."

"Wucewar ta bai sanya Iya jan baki tayi shiru ba, sai ma ha™i™ancewa da tayi, tana cigaba da masifa ""Ni dai na gaji da"

"wannan maitar da masifar, dole in mi™e in nemi tsari da bala'i da tashin hankalin wannan mutanen su daina yi mini sintiri da bibiyata, ba dole mariya ta haukace ba, hakkin Wa na ba zai taSa barinta ba, daga haka ma in Allah ya yarda sai ta fara yawo tsirara, ni bai dame ni ba, hakkina da na Wa na ba zai bar ta ji daWin rayuwa ba, hauka ma yanzu ta fara ba ta ga komai ba tukuna""."

"Ummi ta ja ta tsaya a cikin Wakin, tana ™are masa kallo, kasancewar haddar yaro ™arami, ba abu ne da yake gogewa cikin sau™i ba, ya sanya take ummi ta shiga hasaso abubuwa da dama da suka faru a Wakin nan."

"Yanayin jeren Wakin, ™amshin turaren wuta Wan tsinke da mamanta ke yawan kunnawa, yadda take zama a kan"

"cinyar mahaifinta ta ci abinci, yadda daren da aka yi mata fyaWe ya kasance, ko ba komai ummi ke iya tunawa ba, ba ta manta yadda mamanta take iya ™o™arin ta wurin yi wa Iya biyayya, ta kalli yadda Wakin ya zame mata a yanzu ba™i ™irin, tamkar dajin da wuta ta cinye bishiyun da suke ™awata shi."

"Dur™usawa tayi ta fashe da kuka tana sheshshe™ar kuka, tana jin Iya na cigaba da ci wa mahaifiyarta mutunci, tare da yi mata fatan masifa kala-kala da aibantata da sharruka."

"Ummi ba ta samu fitowa daga Wakin nan ba, sai daf da la'asar, dan ma Allah ya taimake ta zuwa makarantar allo da"

"take yi, ana horasu a kan kula da ibada, wanda dama ta samu wannan horon daga mahaifiyarta, amma dan ta Iya, ko za ta shekara ba ta yi salla ba, babu ruwanta da ita."

"Ta yo alwala ta dawo Wakin tayi azahar da la'sar, ko tunanin zuwa makarantar allon ba ta yi."

"Tana jiyo yadda duk wanda ya shigo sai Iya ta gaya masa ai Mariya ta haukace, tana can an sakata a turu, hakkin rai"

"yana bibiyar ta, ta fara bi bola-bola tana tsince-tsince."

"Ummi ta sha kuka, sai da idanunta suka kumbura, dan duk kukan da za ta yi idonta baya ja, sai dai ya Wan sirka,"

kuma su kumbura.

"Ta kalli kuWin da yaya Wanlami ya bata, ta watsar da su a tsakar Wakin, ta ™an™ame jikinta, tana sauke numfashi hawaye na tsiyaya daga idonta."

Ba tsammani ta ga magaji a kanta.

"""Ummi"" ya kira sunanta a hankali."

"Ta Waga kai tana kallonsa. ""Kukan me ki ke yi?"""

"""Yaya magaji"""

"""Na'am ummi""."

"""Wai mamana ta haukace?"" Tayi maganar wasu hawayen na gangarowa saman kumatunta."

"""Subhanallah waye ya gaya miki haka?"""

"""Wanda ya tafi da ita ne yazo, shi ya bani wannan kuWin"""

"Hashim ya ce ""Kar ki sake cewa ta haukace, bata da lafiya dai, tana ganin likitan ™wa™walwa aka ce"""

"""Likitan ™wa™walwa? An ce sai mutum ya haukace fa ake kai shi wurin likitan ™wa™walwa"""

"""Ba haka bane ba"""

"""To meyasa Iya take cewa mama ce ta kashe baba, ba hatsari yayi ba?""."

"""Ki daina damuwa da maganar Iya, ki kwantar da hankalinki, ki ta yi wa mamanki addu'a Allah ya bata lafiya"""

"""Dan Allah yaya magaji ka kai ni wurinta, ina son in ganta dan Allah"" tayi maganar tana haWe hannayenta alamar magiya, tana kuka."

"Cikin matsanancin tausayinta ya ce ""Ummi Maiduguri ba nan ba ce akwai nisa, kuma ban san a ina mahaifiyarki take"

"a Maiduguri ba, lokacin da aka aureta muna yara, kuma kin ga ba taSa zuwa muka yi ba. Amma ki yi ha™uri ki daina kuka, zan bincika miki in sha Allah"""

"""Gidan uwarka zaka bincika mata, munafukin Allah ta'ala, to kar ka fasa, wallahi magaji idan ba ka kiyaye ni ba, sai"

"na hau kujerar tsiya na ci ubanka la'ada waje a kanta, kar ka fasa kai ta inda uwarta take, zaka ga cin mutuncin da zan yi maka, dai-dai nake da kai."

"Kema tsohuwar munafuka, halin uwarki haka halinki yake, duk wannan ™o™arin da nake yi a kanki ba kya gani, da ki ke hannunmu mutuwa ki ka yi? Kowa yazo sai ki Sare baki, ke a kai ki wurinta, tun da namanki nake gutsura in ci, to ki cigaba kar ki fasa, amma ki sani nayi alwashin yadda mariya ta rabani da Wa na, ke da ita har abada, sai ta WanWani abun da ta ™unsa mini, wannan kuWin na meye?"" Tayi maganar tana nuna kuWin da ummi ta watsar a wurin."

"Hashim ya ce ""Yayan babarta ne ya bata"""

"""Tattaro mini su ki mi™o mini"" ummi ta tarkata kuWin ta mi™a mata."

"Ta karSe ta kalli Hashim ta ce ""Zaka tashi ka fita ko sai na Sata maka rai, kuma daga yau na yi maka tsakani da ita, tun da kai ne ka ke zigata, shashashai kawai"""

"Hashim ya tashi zuciyarsa na yi masa zafi, muddin ya buWe bakinsa, zai iya Wurawa Iya ashar, dan haka yayi shiru ya"

bar Wakin.

"""Tashi ki fice ki auni dawa ki surfa mini, tun da baki je makarantar allon ba"""

"Haka Ummi ta ja jiki ta fito, ta fara ™o™arin aikin da Iya ta saka ta, ™asan zuciyarta tana fatan, ina ma Maiduguri babu nisa da guduwa za ta yi, ta tafi wurin mamanta."

"Kayan da yaya Wanlami ya kawowa Ummi kuwa, Iya ta tsince wanda zata tsince ta ce a fita da sauran, ba ta ™aunar duk wani abu da ya shafi Mariya."

"Duk salla sai ummi ta yi addu'ar Allah ya ji™an babanta, ya bawa mamanta lafiya, ya sa ta dawo ta Wauke ta."

"Tun wannan tafiya da yaya Wanlami yayi, wani daga danginsu, bai sake waiwayo in da Ummi take ba, suka mayar da"

"hankalinsu a kan lafiyar ´ar uwar su. Dan abun na mariya gaba ya din ga yi, babu sau™i ko sassauci, yanzu tana zaune lafiya idan aka jima, sai ta hau kuka tana burgima tare da surutai, irin na masu taSin hankali."

"Ummi kuma ta cigaba da karSar gashi a gidansu, tsangwama da kyara a cikin yara a makaranta ko kuma a gida."

"Iya ta sanya ido sosai a kan magaji, Wan taimakon da yake yi wa ummi, ta tasaya tsyin daka ta hana shi."

BAYAN SHEKARU BIYU!.

"Sauri-sauri ta kammala tulin wanke-wanken da ke tsakar gidan, ta warewa kowane sashi kwanukansu ta kai musu."

"Duk in da ta faki ido ta tsaya, sai ta yi soshe-soshe, dan itakaWai ta san me take ji."

"Guntun omon da ya ragu, da shi ta wanke kayan makarantar bokonta, duk hantsar wandon ta fatattake, sun koWe"

"sun jeme, ™afar wandon duk ta Wage ta tattare, gwiwar duk a farfashe."

"Kasancewar lokacin rani ne, rijiyoyi duk sun ™afe, ta Wau bokiti ta samo ruwan wanka, ta Wauki ledar omon da babu"

"komai a ciki, ta faWa banWaki wanka, da sosonta na buhu."

"Ta daWe a tsaye tana fargabar ta ina zata fara? Tun safe a makarantar boko take jin fitsari, ta ri™e shi bata yi ba,"

saboda azabar da take sha.

"A hankali ta cire kayan jikinta, ta ware gashin kanta, ta nannaWe shi ta tufke, ta kawo tsumma da take Waure kan da"

"shi, ta Waure yadda ba zai ji™e ba."

"Ta cire wandon da yake jikinta, subhanallah, wani irin ragargazajjen wando ne, kusan da shi gara babu, duk roba-"

"robar jiki ta zaro, har da in da aka yi Winkin zare da allura a jikin phant Win, haka ta rataye shi a jikin ™ofar banWaki, sai tsami yake mara daWi."

"Ta koma gefe Waya, ba tare da ta tsuguna ba, ta fara sakin fitsarin da ya cika mata mara fam, a tunanin ta hakan zai"

sanya ta kaucewa faruwar abun da take gudu.

"Sai dai kash! Tamkar ta zuba ruwan barkono a gabanta, wani irin raWaWi da azabar zafi, ya ratsata tun daga kanta har"

"™afafuwanta, ta toshe bakinta tana jin zafi kamar ana kekketa mata wurin, ga mararta da ta ™ulle kan fitsarin ya fita."

"Ta shafe tsawon lokaci, kan ta motsa, saboda tsananin azaba da wahalar da ta shiga."

"A hankali ta motasa, ta tsuguna wani irin ™arni mai haWe da wari ya daki hancinta, ta Webo ruwan nan da sanyinsa da"

"komai, ta zuba a wurin ta fara wankewa, wani irin ruwa mai ™arni mara daWi ya din ga fitowa daga jikinta. Zuba ruwan sanyin da tayi, ta ji tamkar ta zuba karara a wurin, wani irin ™ai™ayi kamar ta kurma ihu, duk yadda ta so ta daure, ta kasa ta din ga sosawa, ™urajen da suka feso a gabanta suka yi jawur, tun tana jin daWin susar sai da ta koma jin zafi, dan da gask take yi iya ™arfin ta, saboda azabar ™ai™ayi, sai da ta yi wa kanta rauni, har da jini."

Ta yi shiru ta jingina da jikin bangon banWakin tana tunanin haka kowa yake yi? Ko ita kaWai ce take fama da wannan

"masifar da bala'in, to idan ma haka ne wa zata tambaya?"

"Da ™yar ta samu ya lafa, ta zuba ruwa a cikin ledar omon nan, ta zuba a jikinta tayi wanka, sai dai a ™arshe ta rasa yadda za ta yi ta wanke wandonta, dan babu omo, dan haka ta wanke shi a haka, da zallar ruwa, ta yarfe shi ta"

"mayar shi jikinta a ji™en, ta fito daga wankan tana tafiya a hankali, tana Wan buWe ™afarta, saboda raWaWin da wurin yake yi mata."

"Man kaWanyarta da na'ima ta aiko mata, shi ta shafa abun ta, ta sanya uniform Win ta, ™ungun wandon saboda rashin"

"roba, da leda take kama wani sashin ta Waure, hakazalika takalminta ma, kasancewar ya mutu dan a tsinke yake, ta samu leda shi ma ta yi masa cunan leda, ta Waure shi da shi, ta saka."

"Haka ta tafi makaranta tana kaffa-kaffa da jikinta, ko yaya ta saki jiki za a iya ganin tsiraicinta, saboda yadda kayanta suka mutu. Ga wannan bala'in da take ciki, na sanyi da yayi mata mugun kamu."

"Iya kuwa hankalinsu yana kan bikin Idiris da za ayi, ana ta shirin biki a gidan, shi ya™i karatun boko ya™i na islamiyya, ya ce shi aure yake so, Hashim ya kaWa ya raya, ya ce shi ba zai iya wannan wahalar banzar ba."

"Kawu Yahaya ma sai da yayi mitar idiris Win nawa yake, da har zai ce zai yi aure me yake da shi? Iya ta goya masa baya, ta ce su haWu su yi masa aure."

"Aka kama masa hayar wani gida mai Waki biyu da kitchen da banWaki, ginin ™asa ne dai, amma an yi floor, da plastar"

™asa an shafa farar ™asa.

"Wata yarinya ya nema a can gaban unguwarsu, yake ta yi musu sintiri yana son ta, babanta ya ce idan da gaske yake"

"ya fito, shi ne ya zo ya saka Iya a gaba, lallai shi aure yake so, aka je aka nema masa auren ´ar mai suna Hindu."

"Kawu yahaya ya ce lokacin auren, yayi dai-dai da lokacin zuwansa umara, ba zai samu zuwa ba sai dai matarsa za ta"

"zo, ya kuma aika musu da gudunmawa mai tsoka."

"Albarkacin bikin Idiris, Iya ta sayawa ummi atamfa, da takalmi na kayan fitar biki, ummi duk da ba shiri suke yi da"

"idiris ba, ta ji dadin zai yi aure ya bar gidan ko ta samu ta sarara."

"Ana ta shirye shiryen biki, gida ya Wau harama, ´an uwa na nesa tuni sun fara zuwa, ummi na ta aiki kamar jaka, Wan"

"wannan idan yayi kuka a bata rarrashi, Wan wancan yayi kashi ta wanke, haka dai ba ta da sukuni."

"Yau kusan tun bayan azahar, yanayi ya nuna akwai matsala, duba da yadda Iya ke ta shiga tana fita ita da mahaifin su"

"magaji, kasancewar ba abun da ya shafi ummi bane, ya sanya ko a jikinta, ta cigaba da sabgoginta."

"Shi kansa yanayin Idirs ya nuna hankalinsa a matu™ar tashe yake, alamu suka tabattar da akwai matsala."

"Ba a tsaya da shirye-shiryen biki ba, dan magana ake ta bai fi saura kwana huWu a shiga hidimar biki ba."

"Da yamma hashim ya shigo, ya tarar ummi na cikin mutane ana ta aiki, yayi mata nuni da ta zo."

"Ta wanke hannunta ta bi shi, ya kalleta ya ce ""Ke ina naki shirin bukin, ki ke ta fama da aiki haka, ko gajiya ba kya yi?"""

"Murmushi ta yi masa, sai da fararen ha™oranta suka haska fuskarta, fi™arta da ta karye tana nan a yadda take, sai"

"´ar siriryar wushiryarta ta ce ""To yaya magaji wani shiri zan yi? Ina da atamfata sabuwa da takalmin da zan saka"""

"""Ke ba zaki yi Wan lallen da ake yi na zamani ba?"""

"Ta kalli hannunta, ta Wan rausayar da kai ta ce ""Bana so, ba zai yi mini kyau ba"""

"Ya kamo hannunta ya ce ""Jan nan da ake yi tafin hannunki fari ne masha Allah, ko kitson ma ba ayi miki ba, kin"

"cukurkuWe gashi kin Waure"""

"Yayi maganar yana kallon yadda Wankwalin kanta yake cike fam, ko ba a gaya maka ba, ka san wannan uban gashin nata ta Waure."

"""Ai ka san ni ba a iya yi mini kitso, duk sanda na cewa yayi mini kitso, sai ya ce wai bs zai iya ba kaina ba zai yi ba,"

"lalle kuma ai sai an biya Wari biyu huwaila take yi hannu da ™afa"" tayi maganar cikin yanayinta na shagwaSa da Iya take cewa sangarta."

"Ya ce ""To shikenan, da safe zan baki kuWin lallen, kitson kuma sai na yi miki"""

"Tayi dariya ta ce ""To mata ne kawai suke yi wa mata kitso ban da maza"""

"Ya ce ""Shikenan, je ki sai goben in Allah ya kaimu"""

"Cikin murna ta tafi ta cigaba da aikin, tana matu™ar son lalle, amma rabon da ayi mata, tun kan na'ima tayi aure, da"

"take yi musu, yanzu yaran na'ima biyu a gidan miji."

"Da magariba Saminu baban su Idris ya shigo hankali a tashe ya ja hannun Iya suka fita, wata duhuwa ya ja ta ya ce"

"""Iya muna cikin tashin hankali da masifa, Idris ya zubar mana da mutunci"""

"Cikin kaWuwa ta ce ""Menene? Meyafaru?"""

"""Ban da masifa da bala'i, saura ´an kwanaki a Waura maka aure, a ganka kana watsewa da wata, saboda rashin"

"mutunci"""

"Iya ta ce ""To ba mun gama wannan maganar ba? Har wurin maude mai babban carbi na je, ya yi mini aiki ya ce"

"maganar an bar ta har abada, ba zata fasu ba, ko ta fasun ne?"""

"""To yanzun nan ™anin baban yarinyar da zai aura Win, ya dawo da kuWin auren, sun ce aje a karSi kayan auren gobe"

"da safe, ba za su bawa mutumin banza ´a ba"" yayi maganar yana nuna mata kuWin."

"Iya ta dafe ™irji ta ce ""Mun shiga uku, amma mutanen nan basu da mutunci, basu san tsautsayi ba?"""

"""Koma menene ai shi ya janyo wa kansa, da bai yi ba wa zai ce yayi, ni wannan mutanen da muka tara ne, ban san ya"

"zamu yi da su ba"""

"Iya ta ce ""Ni kuma tashin hankalina, garin Allah ya waye a dawo da kayan nan, kowa ya ji abun da ya faru, da sassafe"

"ka je da kanka ka karSo kayan, ka kai mini gidan kuluwa""."

"""Ni kuma Iya? Ni zan je Waukko kayan?"""

"""To kar ka je tsaya asirinmu ya tonu, sai ka ji daWi, santolo kawai""."

"""To Shikenan zan je in sha Allah """

"""Kai ka ga idan da hali, ka tafi yanzu cikin daren nan, ka tafi da babur ba wanda ya ji balle ya gani"""

"""To bari sahu ya ™ara Waukewa, amma Iya yaya zamu yi da wannan mutanen, ta yaya zamu ce musu an fasa auren nan?"""

"Iya ta ce ""Nima shi nake tunani, dama ga akuyarsa tayi kuka a dangi, dan ma ana tsoro na ne, ya sanya ba a magana,"

"amma jeka na san abun yi """

"""Meye abun yin to?"""

"""Ka tafi na ce, idan ka dawo sai ka ji"" ya jinjina mata kai ya tafi."

"Šakin samarin ta shiga, neman Idris, amma ba ta tarar da shi ba, dan haka ta juya ta tafi."

"A daren saminu yayi yadda Iya ta ce, ya je ya karSo kayan a daren."

"Sosai Saminu, ya din ga yi wa idiris faWa, a kan tashin hankalin da ya sanya su a ciki."

"Washegari kamar yadda Hashim ya yi wa ummi al™awari, ya bata kuWi ta je aka yi mata lalle."

"A ™ofar gida ta gan shi ya karSo kayan guga, tun daga nesa take Waga masa hannu ta ce ""Yaya ka ga lalle na?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Inyee an sha kyau, lalle yayi kyau, ki yi sauri ki shiga gida, Iya ta fara faWa ana nemanki"""

"Cikin faWuwar gaba ummi, ta ce ""Bari na yi sauri"" ta yi cikin gida da gudu."

"Cikin damuwa Saminu ya

Please Login or Register in order to submit comment