You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ido ta ce ""MD mota Alhaji ya bani"" ta rungume raihan tana murna, ta din ga zuba masa addu'a da shi"

da Alhaji.

"Da gudu ta fita falo, tana nuna wa su mama da ba su riga sun bar gidan ba, aka din ga yi mata murna."

"Noor ta ce ""Yaya ummi baki ji zuciyata ba, na taya ki murna, amma ina son mu yi magana"""

"Suka keSe da noor, ta gaya wa ummi abun da ya faru tsakaninta da Salim."

"""Noor meyasa baki da wayo ne? To meye aibun yayan?"""

"Noor ta ce ""To ai ni yarinya ce, kuma ni bana son ayi ta yi mini surutu kamar yadda aka yi miki"""

"""To sai me? Wata™ila da ina nan a gida ban yi auren ba, ai yanzu ki samu mai sonki tsakani da Allah shi ne. Shi da ake"

"son ya yi auren ma, kin san da manyan ´an mata nawa aka haWa shi, duk ya ce ba ya so dan ya ce yana sonki zaki wula™anta mini yaya, to kin yi wa kanki"""

"Noor ta ce ""Dan Allah ki yi ha™uri"""

"""Kin fi son ki koma gida kina jerawa da kausar kuna faWa kenan? Ke ba kya son ki ganki kema a gidanki?"""

"""To ai yanzu ba a gida nake ba, gidan mama zan koma, ni ba zan koma gidanmu ba, maama haushina take ji kamar"

"ba ta son ganina ma"""

"""A'a ba sonki ne ba ta yi ba, amma dai yaya Salim dai kin yi wa kanki"""

"""Na shiga uku, yanzu ya zan yi?"""

"""Ki Wauki waya ki bashi ha™uri"""

"Noor ta tura baki ta ta ce ""Salon ajina ya zube"" ummi ta ™are mata kallo kawai tayi tsaki ta bar Wakin."

"Ummi na komawa Waki ta kira Salim, suka gaisa sannan ta ce ""Yaya ka ji Alhaji ya bani mota?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Na riga ki sani ai, ina taya ki murna ™anwata"""

"""Na gode sosai yaya salim, Allah ya saka muku da mafificin alkhairi"""

"""Amin ™anwata, Allah ya raya mana su Iman"""

"""Amin yaya. Yauwwa noor ta gaya mini shirmen da ta yi maka, abun duk ya dame ta, dan Allah ka rabu da ita, Alhaji"

"ya samu dr. Da maganar""."

"Yayi murmushi ya ce ""Kin je kin takura mata ko? Bana son takura ta, daga baya nake ganin kamar na yi wauta nayi"

"mata tsufa"""

"""Dan Allah ka bar wannan maganar, tana sonka, duk ta damu fa"""

"""Amma, kina ganin dr. Zai bani noor kuwa? Kin san ni ina da case"""

"""A'a yaya me zai hana? Kuma dan kana da case sai a ™yamace ka? Ai yanzu ka shiryu a kan yadda na sanka a da, dan"

"Allah ka ™yale shirmen noor yaya"""

"Yayi murmushi ya ce ""Auta danger, shikenan zan yi tunani, a bata lokaci"""

"""Dan Allah yaya ka ™yaleta, mun yi magana da ita fa"""

"""To shikenan, sai da safe"""

"""Yauwwa yaya, a yi wa su hajiya bangajiya"""

"Suka yi sallama, ta din ga addu'a, Allah ya tabattar da alkhairi, dan tana fatan noor ta yi aure da wuri, tun kan farida"

"ta ™wace ta, ta siffantu da miyagun halayenta."

"Har dr. Ummi ta kira, ta sanar masa da abun alkhairin da Alhaji ya yi mata."

"³an gagarawa sai da suka kwana uku a gidan ummi, da zasu tafi ta haWa kayan suna ta basu suka tafi da shi."

"Ummi ta saka noor a gaba, ta bata waya ta kira Salim."

"Sai dai da ya Waga wayar ya ji murayarta, bai kashe ba suka gaisa."

"""First born"""

"""Mmmm auta"""

"""Fushi ka ke da ni ko?"""

"""Me ki ka yi mini zan yi fushi da ke?"""

"Ta Wan sosa kai ta ce ""Maganar da muka yi ranar suna""."

"""Ai ta wuce auta"""

"""Ba ka so na yanzu?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Ke dai ba kya so na, an bar maganar bana son takura miki"""

"""To yanzu na canza shawara ka yi ha™uri"""

"""To"" ta Sata rai saboda yadda yake bata amsa a ta™aice da izza."

"Ummi ta girgiza mata kai, alamar kar ta yi fushi."

"""Yaya Salim"""

"""Noor"""

"""Idan muka yi auren zaka bar ni in yi makaranta, ka ga yaya inteesar mijinta hanata yayi daga baya""."

"""Zan barki in sha Allah"""

"""A'a rantse da Allah, kar ka canza shawara"" yayi mata shiru, ummi ta dafe kai, saboda wautar da noor Win ke yi."

"Bayan sun gama wayar, ummi ta ce ""Eh lallai akwai jan aiki a gabana, noor babban mutum yayi magana ki ce ya"

"rantse? Ke fa baki da kai"""

"""To ba ki ji yadda yake yi mini magana da gadara ba, da fa ba haka yake yi mini ba"""

"""Ba aurenki zai yi ba yanzu? Dole yayi miki izza. Ke fa miji ba abun wasa bane ba"" ta din ga yi mata faWa."

"Ummi ta ™ara Waura aniyar, raba noor da Farida har zuwa lokacin da za a saka auren noor Win, saboda kar ta Worata a"

kan mummunar Wabi'arta na raina miji da yin asiri.

"Ummi ta kira Alhaji a waya, ta din ga yi masa godiya, tare da yi masa adduo'i masu daWi."

"Ummi ta tara kuWi da suturu, da sauran abubuwa."

"Farida kuwa tayi watsi da dr., Shi ma yayi watsi da ita ya daina shiga sabgarta kausar ma ta biye mata ba sa kula shi."

"Yau yana gidanta, tana ta cika tana batsewa, ta same shi a fall ta tsaya a kansa ta ce ""Malam yaushe za ka dawo mini"

"da ´a ta ne?"""

"Ya Waga kai ya kalleta ya ce ""Ke da noor, sai lokacin aurenta, ta bar gidan nan kenan na bawa mariya ita"""

"""Wallahi ba ka isa ba, ai ba ita ta haifa mini ita ba, da zaka bayar mini da ´a"""

"""Ni ban isa na ™wace miki ´a ba, halinki da ki ke nuna mata ne, ya sanya ta guje ki ita ma"" za ta yi magana wayarta ta fara ringing."

Ta Waga wayar ta yi sallama.

"""Farida kina ina, ki yi maza ki zo asibitin murtala emergency, Rahama mijinta ya ™onata da ruwan zafi da ita da ´ar"

"da take goyo"""

"Farida ta dafe ™irji ta ce ""Ruwan zafi me tayi masa?"""

"""Wai faWa suka yi, ta tafi tsakar gida tana girki, ya zageta ta rama, ya fito yayi balla da kurfotin gabanta da"

"tafasasshen ruwa a kai, da garwashin duk ya watse musu a jiki ita da ´ar"""

"""Innalillahi na shiga uku"" tayi jifa da wayar tayi Waki tana salati."

"Kiran sallar la'asar ake yi dama, dr. Ya fice sallar isha'i, dan bai san me aka ce mata a wayar ba."

"Daga sallar isha'i, ya tafi gidan mariya."

Ya tarar ta idar da salla tana zaune ta yi shiru.

"""Ya dai, na ganki sai a hankali, ina noor ne?"""

"""Tana gidan ummi, ai noor ta gujeni saboda sun yi jarirai"""

"Yayi murmushi ya ce ""Noor an kusa girma, Alhaji Tahir ne yayi mini magana, wai su na ri™o Salim yana so, na ce zai sha shiririta"""

"Mariya ta ce ""A'a kar ka ce haka, abu namu ´a ta wa Wa na wa, za ta yi hankali in sha Allah kan lokacin"""

"""Wane lokaci kuma, shekara Waya ne kawai fa, tana gama secondary school ne suke so"""

"Mariya ta yi dariya ta ce ""Allah ya sa zamu gani"""

"Ya Wan kalleta ya ce ""Kamar akwai magana ko?"" Ta jinjina masa kai alamar eh."

"""To ya aka yi?"""

"""Dr. Tun muna waccan ™asar kamar ban kuma al'ada ba fa"""

"Yayi dariya ya ce ""To me ki ke so in ce?"""

"""Koma meye ka ce mana"""

"Dr. Yayi dariya ya ce ""Maman ummi rigima, kin fi ni sanin meyake faruwa ai"""

"""Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wai ciki ne da ni?"""

"Dr. Ya kashingiWa yana dariya, gaba Waya ta ruWe ""Haba dr. Ummi na jego nima a ganni da ciki, na shige su"""

"""To laifina ne? Ni dai ina so ina murna Allah ya raba lafiya, kowa ya kalle ki fa zai gane kin ™ara haske sosai"" gaba"

"Waya ta rikice, wai abun kunya ne, shi kuma ya din ga yi mata dariya. Gaba Waya ya manta da a gidan farida."

"Ummi na Waki tana ta yi wa noor nasiha, a kan maganar salim, ta ce mata ita tana son sa amma tsoron auren take yi,"

"ummi tana ta lallaSata, dan sun yi magana da dr. Kuma ta san zai kira noor Win ya tambaye ta."

"Anty Maryam ta shigo Wakin ta ce ""Ummi, kin yi ba™uwa, sai wani harare-harare take yi, ban san me aka yi mata ba,"

"amma da alama ´ar uwar mai gidan ce, suna kama da shi"""

"Ummi ta yi murmushi ta ce ""Anty ki ce ta shigo""."

Mintuna kaWan sai ga Maryam ta shigo.

"Ummi ta ce ""Sannu da zuwa, yanzu ki ke tafe?"""

Ta ja tsaki ta zauna.

"Noor ta ce ""To, ikon Allah"""

"""Noor kawo mata ruwa da yaran ta gansu"""

"""Ai fa, an samu abun da ake so, an samu daular da ake kwaWayi tashin farko an zubo yara biyu, yaran da aka ce babu"

"kalarsu a danginmu"""

"Ummi ta yi dariya ta ce ""Ai abun alfaharinku ne, kun samu iri a dangi. Kuma ´a´a biyu sai matar so ba kwaWayayyi"

"ba, abun alfaharinku ne, ™aninki akwai himma, ko kuma maybe daga ni ce"""

"""Ummi ni ki ke gaya wa haka?"""

"""Ke fa ki ka fara, wai kwaWayi? Ke in kwaWayi ne kawai ya kawo ni gidan nan, da ban kai haka a cikinsa ba"""

"Noor tayi sallama, ummi ta amsa, ta mi™awa maryam yaran, maimakon ta karSa ta ce ""Ba shakka, dole mami ta ce"

"akwai lauje cikin naWi a wannan yaran, ba zata taSa karSar su a matsayin jikokinta ba"""

"Ummi ta ce ""Noor mayar mini da ´a´ana wurin Anty""Noor na fita ummi ta ce ""Kar Allah ya sa ku karSe su a"

"matsayin jikokin, ku mayar da su in da suka fito, tun da ubansu ya san nasa ne shikenan."

"Dama ni ban ce ta ™aunace ni dole ba, tun da ba ku ku ka halicce ni ba. Ni yanzu a duniyar nan da a so ni da a ™i ni duk uwar ubansu Waya."

"Babu yadda ban yi ba wurin yi wa mami biyayya, da girmamata amma ba ta gani, a gaban uwata saboda rashin ta ido, take cewa wai yara ba na Wan ta bane, da yake uwata ba zuciya ce a ™irjinta ba ko? Maryam da zan baki shawara da kun daina jayayya da ikon Allah, ni da raihan ajiyar Allah ne mutu ka raba. Idan ku ka cigaba da takurawa aurena ko kun raba aurena da raihan, zan cigbaa da rayuwar aure da shi ina haihuwa ko da aure ko babu, dan a yanzu ba wani ™alubale ko abun kunya da ba zan iya fuskanta ba."

"Zaman gidan raihan, da zazzago ´a´a yanzu na fara, idan kin ga dama daga nan ki je wurin mami ki yi mini wani sharrin ke ta shafa da ke da ita"""

"Maryam ta mi™e ta ce ""Ummi, mamin ki ke gaya wa haka?"""

"""Idan tsoho bai ji kunyar hawa jaki ba, jaki ba zai ji kunyar kayar da shi ba. Na yi iya yi na, na gaji, ba zan cigaba da"

"cusa kaina in da ba a ganin kima ta ba. Kuma wallahi idan kuka cigaba da uzzura mini, hakkina zai fara bibiyarku ai ke ma mace ce, kuma a gidan wani ki ke aure, a sannu kema zaki haWu da dai-dai ke""."

Ta fice ta bar ta a Wakin a tsaye.

"Farida kuwa hankalinta ya tashi, saboda yadda ta je ta tarar da rahama, a asibiti, jikin yarinyar duk ya saSule, haka"

"na rahama cikinta, fuskarta da ™afafuwan ta duk sun ™one ´an sanda sun kama mijin nata."

Ta din ga kuka tamkar za ta zare.

"Ummi kuwa duk da furucin da Maryam tayi mata, ko a jikinta ta mi™e ™afa ta cigaba da sabgoginta a gidanta."

"Hausawa suka ci idan kana da kyau, ka ™ara da wanka, ummi ta san in dai Sangaren kula da mijinta ne, to tana da"

kyau ba a magana a Sangaren kula da raihan.

"Amma duk da haka, maganar hausawa gaskiya ce, dan haka ba ta yi ™asa a gwiwa ba, wurin lalubo lambar Amina Gachi, CEO beenad herbal center, mussaman ita da taSa fama da ciwon sanyi, kuma galibi ciki ya kan tayar da ciwon, dan haka nemi Amina gachi, domin shiryawa koma wa Wakin mijinta."

"(Bari na baku bayani, beenad herbal center, ba iya maganin sanyi suka ™ware ba, suna bayar da magunguna daban-"

"daban dai-dai da matsalolin ku, damun kawo daidaito a gidajen auren ku. Suna da kaya kamar haka;"

Shedaniyar gumba Gumba mai saying Garin mai kabbara Mai dalalan miyau

Wayyo dadi

Zumar kwakwa Zumar ridi Zumar dabino

Zuma mai ma'ul ijaba Farin jini

Gumba kalla kalla da dai sauran su

A BEENAD HERBAL suna da turarukan wuta da humrah kalla daban daban sai Wanda kuka zaba Ga kuma maganin slimming

Gyaran nono Maganin hips Maganin Kara kiba Da dai sauran su.

Kayan mu tested and trusted ne

Suna maraba da masu siyan Daya ko sari Suna Nan cikin garin kaduna

Kuma suna tura Kaya duk inda kike da yardar Allah

AMINA GACHI

07034404975

CEO BEENAD HERBAL MEDICINE &INCENCE KADUNA

Phone no 07034404975.

"Da labarin abun da ya faru da rahama ya zo kunnen ummi, hankalinta ya yi mummunar tashi, dan sai da ta yi kuka,"

"dan yadda Abdul ya gaya mata abun babu daWin ji, ummi ta ce raihan ya bar ta je ta dubata, ya ce ba zata fita ba sai tayi arba'in."

"Yaran raihan kamar ana hura su, dan baya wasa wurin kula da su, ummi na cin abinci mai gina jiki, da zai samar mata"

"da ruwan nono, kunu masu kyau da kayan marmari, su kuma yaran ga isashshiyar madara yana saya, kan su yi arba'in suka cika Sul-Sul gwanin sha'awa."

"Can gagarawa, aka samu wani irin maimakon ruwan sama, kamar da bakin ™warya, ga ™arfi ga kuma iska hakan ya"

sanya rufin Wakin iya kwashewa.

"Dama dr. Ne ya bayar da kuWi, a gyara mata Wakin ta saka aka yi rufi ta karSe sauran kuWinta ta cinye, sai ledar Waki da ta saka."

"Iska ta yaye kwanon, ruwa ya din ga zuba a kanta, ruwa ya ji™a tsohuwar ™asar da aka yi ginin Wakin da ita, ita ma ta zube wani ya danneta, ban da katakon rufi da ya din ga ™walo mata a ka."

"Gashi itakaWai take kwana babu kowa a wurinta, dan haka babu wanda ya san abun da ya faru sai washegari."

"Babu wanda yayi zaton za a ciro iya da rai, haka aka kwashe ta aka yi asibiti da ita, tamkar an ji™a kaza a ruwa, ga"

"jikinta duk ™azantar zawon wahala da tayi, kan nan kamar an suWe ™wallon giginya, duk ta zama abun tsoro."

"Su farida kuwa an kai ruwa rana, da su da mijin rahama a wurin ´an sanda, dan kuwa ´ar kwananta goma sha Waya ta mutu, kasancewar uwarsa tana da kuWi, sai kaiwa ta ke tana komowa a kan lallai sai an sake shi."

"Ana wannan ™adamin, su Alhaji Tahir suka kai kuWin auren noor, aka saka watanni tara watan da za ta kammala karatun sakandare, za a yi bikinta da Salim."

"Tun da aka saka auren nan, ummi ta dage wa noor da addu'a, tare da yi mata nasiha sosai a kan zamantakewa."

"""Noor, bani da burin rabaki da anty farida mahaifiyarki ce, kuma komai ta yi miki, mahaifiyar ki ce. Abun da nake so"

"ki sani shi ne, kar ki yadda wani ya Wauki wani abu na tsafi ya ce miki ki yi wa mijinki. Daga zarar abun ya karye, za ki ji kunya, kuma sai mushen kare ya fi ki daraja a wurinsa."

"Noor Allah bai halicci namiji dan ya bi mace ba, mace ita ce a ™ar™ashin namiji, gwargwadon biyayyarki, gwargwadon mallakarki. Idan ki ka kwantar da kai, ki ka yi addu'a ki ka mi™a lamarinki ga Allah ki nemi aljannar ki da gaske, zaki juya namiji yadda ki ke so. Wasu abubuwan sai lokacin auren yayi zan gaya miki, babu ruwanki da Waukar shirmen ™awaye su gaya miki abun da ba zai amfane ki ba."

"Babu ke babu yi wa miji asiri noor, asiri ba ya tasiri, ko yayi na lokaci kaWan ne."

"Namiji kullum shi ne a gaba, dan haka ban da Waga masa murya, kuma ki fara yi muku addu'a samun zaman lafiya tun yanzu""."

Noor ta jinjinawa ummi kai.

"Hajiya kamar ta taka rawa, ganin a wannan karon Salim ya yadda zai yi aure. Kuma ta ji daWin zaSar noor da yayi, ko"

"ba komai ta ga misali a kan ummi, ahalin gidan dr. Suna da tarbiyya."

"Dr. Ya je gagarawa, ya duba Iya, sai dai aka tabattar masa da spinal code Win ta ya taSu, ba zata ™ara takawa ba, komai sai dai ayi mata."

Dr. Ya tsorata da yanayin da ya ga Iya a ciki sosai da sosai.

Gashi babu wata cikakkiyar kulawa ta a zo a gani.

"Bayan ya koma gida, ya tarar an dawo da rahama gidansa, a nan za ta yi jinya, da kamar ya ce bai yadda ba, kawai ya"

™yale su.

"Ummi ta na ta Alla-Alla tayi arba'in, tana son ta je ta duba rahama, kuma ta duba jikin iya."

"Sai dai shi YallaSai MD, lissafinsa kawai tayi ta koma turaka."

"Da dr. Ya gaya wa Farida batun karSar kuWin noor, bala'i ta hau bala'i ta™i nutsuwa yayi mata bayani balle ta ji waye."

"Hankalin kausar yayi mummunan tashi, jin an karSi kuWin auren noor, ita kuma ba ta ga tsuntsu ba ta ga tarko."

"Ummi tana jikin raihan, tana ta zuba shagwaSa, ta kalli fuskar sa tana ™o™arin tashi ta ce ""Malam cikani na tashi,"

"yarana jarirai ne, ba zaka haWa ni da ™ajaga ba ban gama warkewa ba, ka sakani konika"""

"Yayi dariya ya ce ""Ke matar so ita ce ke konika, ki yi wa duniya proving Win ke Win matar so ce ga raihan"""

"""Ni zaka yi wa wayo? Ai na riga na gama yi wa duniya proving ni Win Waya ce a zuciyar mijina"""

"""Wallahi faWi ki ™ara faWa, ni kyautar da Alhaji yayi miki ni na so yi miki ita, wata gigitacciyar kyauta nake son yi miki""."

"""Ni ba na son kowace kyauta, wuri nake son ka ™ara gyara mini a zuciyarka na mi™e ™afata"""

"Raihan ya ce ""Kin samu, ba kowa a ciki sai ke Salmana, Allah ya ™ara miki lafiya da nisan kwana, ya ™aro miki lafiya,"

"ki yi ta haifo mini ´a´a"""

"Ri™e hannunsa tayi tana dariya ta ce ""Ni zaka yi wa wayo, wai ba zuwa ka yi kana cewa ba ka da lafiya ba?"""

"Ya kwashe da dariya ya ce ""Duk cikin neman hanyar tsira ne, bani da lafiya idan har ba tare da ke nake tare ba, ni a"

"idona duk wata mace idan ba Salmana ba ba zata taSa zama Waya da ke ba. Ke daban ce a kowane fanni""."

"Kalaman jinjina da girmamawae da yake yi mata, ya sanyata jin kamar ta fi kowace mace sa'a a rayuwarta."

***

"Idris da sasassafe yana ta shirin fita zuwa karSar wani kuWi, sai faWa suke yi da hindu suna zage-zage kamar ´an tasha a kan kuWin cefane."

"Sallama aka yi a waje ya fita, ya tarar da ´ansanda a tsaye, ba su yi wata-wata ba suka cafke shi suka tafi da shi. Babu wanda ya san in da yake, dan babu wanda ya san kama shi."

"Sai da aka je wurin ´an sanda, wai ana tuhumarsa da yi wa wata yarinya fyaWe, an tsinci yarinyar a hanyar"

"makarantar islamiyyar su, an yi mata fyaWe an kasheta, wai shi ake zargi saboda hanyar wucewarsa ce, kuma an san halinsa na biye-biye yaran mutane."

"Farida na tsaka da jinyar rahama, Wakin da take ™onuwa sai wari take yi, duk da yadda ake kula da ita sosai."

"Inteesar ta shigo falon gidan, fuska duk a kumbure, idanunta sun yi jawur."

"""Ke inteesar lafiya meyafaru?"" Ta mi™a wa farida takarda, tana kuka ta ce ""Hajiyar sa ta saka ya sakeni, wai sun gaji da ciyar da ni sai dai na yi kashi babu haihuwa, alhalin Wanta ne silar komai!"""

"*Ina baku ha™uri, na san ina laifi rashin posting, ayyuka da bukukuwa ne suka yi yawa, ayi ha™uri dan Allah ina"

godiya da kulawa jama'ata ko in ce na ummi *

Ayshercool

08081012143

CUTARWA!

AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

(BRIGHT PENS)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION

https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

50

"Jikin farida na tsuma, ta karSi takardar ta duba, ga saki nan rangaWa-rangaWa guda biyu."

"""Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wai meyasa duk maza halinsu Waya ne? Butulci kawai suka sani? Ita ma uwar ta sa shegiya mummuna mai ba™in hali. Šaukko mini wayata maza na kira babanku, na shiga uku ni farida wannan masifa"

"hawa-hawa"" ta kira wayar dr. Amma bai Waga ba."

"Ta dungurar da wayar ta ce ""Ai na sani, ba zai Waga ba yana tare da wannan mahaukaciyar, na shiga uku ni farida""."

"Dr. Kuwa sallama yayi ya dawo daga salla, mariya ta shirya masa abinci, ya lumshe ido ya ce ""™amshin abincin kawai"

"ya sa na ji na ™oshi"" tayi murmushi ta ce ""Ka dai fara ci tukuna"""

"Ta zuba masa faten wake doya, yana ci ya ce ""Yauwwa, noor ta dawo ta zo ki fara koya mata irin abincin nan, kar tayi"

"aure ba ta iya girki ba"""

"""Waye ya ce maka ba ta iya girki ba? Idan ta zo gidan nan tana yi ai, noor Wina ta iya girki sosai ta ce a wurin ummi ta"

"koya"""

"Dr. Ya ce ""Ai tun da ummi tayi aure, na yi kewar abinci mai daWi"""

"""Son kai, saboda ´ar ka ce ko?"" Yayi dariya yana kashe mata ido Waya."

"""Yauwwa ga wayarka, an kira ban Waga ba"""

"Ba tare da ya karSa ba ya ce ""Ki na tsoron kar ki Waga ki ji budurwa ta ce ko?"""

"Tayi dariya ta ce ""Haba dai, ko ma budurwar ce na san ba za ta wuce maman ummi ba, maybe ko tana bu™atar wani"

"abun ne, idan ka gama kar ka manta ka kira ta"" ya Wan ™ura mata ido. Ita har cikin zuciyarta tsakani da Allah take son su zauna lafiya da farida, wai ko ba komai ta ri™e mata ummi, daga baya ta ha™ura ganin faridan ba haka ne abun a wurinta."

"Ya gama cin abincin, ta kawar da kwanukan, ta zauna tana matsa masa ™afa ya lumshe idonsa."

"Ta ce ""Baban ummi, ba ka ce mini komai ba a kan zuwa maiduguri"""

"""A'a"" ya faWa a ta™aice."

Ta sunkuyar da kai ta cigaba da abun da take yi masa.

"Ya Wago haSarta ya ce ""Kin yi fushi ne?"""

"""A'a, amma in anjima ma zan kuma tambayar ka, dan Allah baban ummi, ka san menene?"""

"Ya ce ""A'a sai kin faWa"""

"""Taron family aka shirya mana, wai an binciko tun farkon asalinmu, an gayyato mutane da dama da muke da ala™a,"

"ba tare da mun san mu ´an uwa ba ne, dan Allah baban ummi"""

"Ya Wan yi murmushi ya ce ""Na ji, amma ni kin ga bani da lokacin kai ki, bana son kuma ki hau motar haya, kin ga kina"

"da juna biyu kar ki wahala"""

"""Ai zan gaya wa ummi, idan ya barta sai mu tafi da Abdul da noor, dan Allah kar ka ce a'a"" yanayin yadda ta kwantar"

"da kai take lallaSa shi ya sanya shi jin daWi a ransa tare da jin kansa eh shi ne maigida. SaSanin yadda farida ke yi masa magana gatse-gatse, wani lokacin ma sai ta yi abun da take so yake sani."

"""Shikenan, Allah ya kaimu lokacin, za ki je in sha Allah"""

FaWaWa murmushinta ta yi tana yi masa godiya.

"Sai magariba ya je gidan farida, dan duba su."

"Sai dai ta fara da yi masa ™orafi, da zazzaga masa masifa, sannan ta mi™a masa takardar da inteesar ta zo da ita."

"Ya karSa ya karanta, sannan ya kalleta ya ce ""Na gani, me zan ce?"""

"""Kamar yaya me zaka ce? Ba zaka kira shi ba a kan abun da ya aikata, ya wulakanta ´ar ka"""

"Dr. Ya ce ""³ar ki dai, ki nema mata wani uban da zai tsaya mata, ni da ban isheku kallo ba ke da su, ai na yi zaton"

"wani uban ki ka canza musu, kuma ba wani abu da zan kira mijinta na ce masa, tun da ya riga ya saketa, in dai irin halin da ki ke yi, ta je tana yi dole a korota, yayi ha™uri ma. Idan baki ri™e tawa ´ar bazawara karo biyu ba, ga zaurawa biyu nan har da ™arin budurwa Allah ya haWa miki, kuma dolenki ki ri™e"" ya fice ya bar mata gidan."

"Inteesar ta Wora hannu a ka ta din ga rusa kuka, can gefe ma rahama kuka take yi, dan an saki mijinta, ya ™wace mata"

"sauran yaran, bayan aiko mata da tata takardar sakinta."

"Farida ta koma

Please Login or Register in order to submit comment