You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta bata abinci."

"Aka kawo wa Iyan kunu mai zafi, amma ta kalli ummi, ya ce ta Wauki tuwon jiya ya cinye, dan ba za a zubar ba."

"Miyar karkashin ce ba ta so, dan haka ta sake jagwalgwalawa, ta ajiye ta fito tsakar gida, tayi ta kallon ™ofar Wakin su,"

"ta ™arasa ™ofar Wakin tana ™wan™wasawa, wai ko mama zata buWe, sai da ta gaji, kawai ta fita, ta kama hanyar makaranta, lokacin kusan tara da kwata, tana tafe iska na kaWata, ga azabar sanyi jikinta babu rigar sanyi, sannan babu mai a jikinta, dan haka tayi busu-busu da ita."

"""Ke daga ina?"" Malamar da take ajin su ta tambaye ta."

"""Gida"" ta faWa a ta™aice."

"""Yanzu ne lokacin zuwa makaranta?"""

"Tuni hawaye ya cika wa ummi ido, saboda tana tsoron duka ta ce ""Mama ce bata nan, ba ta dawo ba"""

"""To kuma gidanku babu wanda zai ce ki taho makaranta da wuri? Kalli jikinki fa ko mai baki shafa ba, kamar wadda"

"zata aikatau ba makaranta ba"" ´an ajin suka kwashe da dariya."

"""Silent"" malamar ta tsawatar tana kallon ™afar ummi, da kamar an ciro ta daga ha™a rami, ummi kuwa gwanar kuka, ta kama ™asan farin hijjabinta, tana goge hawaye."

"""Wuce ki je ki zauna"""

"Ta nufi wurin zamanta, can wuri Waya, ta cigaba da sheshshe™ar kuka, tana jin muryar wani yaro, cikin murya ™asa²"

"yana cewa ""Ba™ar tukunya, yau an shafeta da toka"""

"Iya sam bata san makaranta ummi ta tafi ba, kawai sai nemanta ta yi ta rasa, hankalinta ya tashi, ta fito tana zagawa"

tana nemanta.

"Ummi kuwa da ™yar ta koma gida, saboda azabar yunwa, har wani jiri take yi, tana ta Addu'a Allah ya sa tana zuwa ga mama, sai dai kash, tsakar gidan nan fayau, ko shara bai gani ba, ta kalli wurin murhu da maman ke Wora girki, shi"

"ma babu komai a wurin, ta kalli ™ofar Wakin su, Wakin dai a rufe."

"Šakin iya ta shiga, ta nemi wuri ta kwanta, ta fara kuka tana share hawaye, tana kiran sunan mama da baba."

"Bacci ya Wauke ta, sai dai hayaniyar iya ta tashe ta, ""Dan ubanki ina ki ka je, ki ka tayar mini da hankali, nake ta"

"yawon nemanki, lungu-lungu kamar akuya."

"""Makaranta na je"""

"""Uwar makarantar, kin gaya mini zaki je?"" Ummi ta girgiza kai."

"""Kawai dan ki tayar mini da hankali, to ubanki ma bai Waga mini hankali ba, balle ke"" ummi dai tayi shiru ba ta ce"

komai ba.

"Iya ta gama zaginta tsaf, sannan ta bata abincin rana, sai dai ba dan zai isheta ba, haka ta ci."

"Da yamma yarinyar da take tafiya da ita makarantar allo, na'ima, ta zo tafiya da ita, Naima ´ar Wakin mariya ce, dan tana son ummi sosai, ita take tafiya da ita makarantar allo, kuma ta ji labarin mariya ta tafi, iya ta ™wace ummi. Ta"

"tarar da ummi a zaune tayi shiru, idonta duk hawaye."

"""Iya na zo tafiya da ummi makaranta"""

"""Gata nan, sai kun dawo"" iya tayi maganar tana nuna ummi a wula™ance."

"Naima ta tambayi iya kayan ummi, ta gaya mata in da suke, ta ga ji™a™™un kaya a ciki."

"Ta ce ""Ummi, na ji kayan ki a ji™e?"""

"""Fitsarin kwance na yi ban sani ba"""

"""To ki daina haWa su da kayanki masu kyau, idan mun dawo daga makaranta, zan wanke musu"""

"Ummi ta saka mata kuka ta ce ""Yaushe mama zata dawo?"""

"""Ki yi ha™uri, nima ban sani ba, amma za ta dawo"" ta shirya ummi ta sakata a gaba suka tafi makaranta, tausayin ummi ya kama ta."

"Kwana Waya kawai, mariya ji take yi tamkar ta taka da ™afa, ta koma gagarawa, ta Waukko ´ar ta, duk sallar da tayi,"

"bata iya addu'ar komai, sai ro™on Allah ya kula mata da ummi, Allah ya dawo mata da umminta."

"A kwana a tashi mariya ta gama takaba, sai da tun bai fi watanni biyu da daowarta gida ba, ta fuskanci tana Wauke da"

"juna biyu, kuma ta ja bakinta ta yi shiru, ta din ga rashin lafiya, ba cin abinci, duk ta rame ta fita daga hayyacinta, maryam ta rakata asibiti, sai a lokacin da likita yake yi mata tambayoyi ta tabbatar musu da tana da ciki."

"Da suka koma gida, aka din ga yi mata faWa, saboda ya zama dole a sanar da dangin su bashir maganar juna biyun"

nan.

"Watanni huWu da barin ummi a hannun iya, Ummi ta gane shayi ruwa ne, dan duk da ba girma ne da ita ba, amma"

"tafi samun sau™i da sassauci, a lokacin da mariya tana nan."

"Gashi son makaranta ya shiga ranta sosai da sosai, idan ta yi wa iya laifi, sai iya ta hanata abinci, da ™yar take iya zuwa makaranta, sai dai da ka ganta a cikin uniform Win nan, ka san babu kulawa, da babu wanda ya kai ummi tsafta a makarantar, amma wataran idan ka ganta, kamar ta shekara babu wanka, a wannan shekarun, ita take wanka da kanta, idan gari babu sanyi sosai tayi wanka da ruwan buta, idan da sanyi ta™i yi, dan wataran ruwan kawai take zubawa a jikinta."

"Man shafawa sai iya ta ga dama zata bata ta shafa, shi ma ba iya shafawar tayi ba, iya ta daina bata, wai tana yi mata"

Sarnar mai.

"Wanki kuwa, sai idan na'ima za ta yi nata, sannan ya ta haWa da na ummin, tayi ta goge mata, idan ba haka ba kuwa,"

sai dai tayi ta yawo cikin dauWa.

"A wata ukun nan, ummi ta koma kamar rainon mahaukaciya, wannan uban gashin babu mai kula mata da shi, ga cin"

"zali da yara suka cigaba da yi mata, tun ummi na saka ran dawowar mama, har ta ha™ura."

"Saboda sabo, da sassafe idan ta tashi, sai ta Wauki tsintsiya ta share sashin, ko da kuwa ba zai fita ba, saboda haka"

"mama take yi, ta wanke bakinta da gawayi, ta ji™a jikinta da ruwa buta Waya."

"Idan ba makaranta ta tafi ba, mutanen gidan wannan ya ja ya aika, wancan ya ja ya aika, kamar baiwa, masu aiken"

"nata, wani lokacin idan sun yi abinci su bata, domin kuwa bata ™oshi da wanda iya take bata."

"Duk ranar da tayi kuskuren yi wa iya fitsarin kwance kuwa, ko wani laifin, sai ta kira idris, ta bashi bulala, ta tuSe"

"ummi, ta ce ya zane mata ita."

"Ga shi ya cigaba da kawo mata farmaki, gashi ta yi girman da ba zai yiwu ya Wauke ta ba, sai ya tsiro da salon aike, ya"

ce idan ta sayo ta kai masa Wakin su.

"Yau idris ya kasa jurewa, ya aiketa sayen omo, ta dawo ta tsaya tana raSe-raSe, cikin ikon Allah sai ga naima, suka yi kiciSis da ummi a soro ta ce ""Ummi, tun Wazu nake jiranki, ina kallon yadda malam babba ya zane ki, saboda makara,"

"amma shi ne baki taho ba""."

"""Yaya idris ne ya aike ni sayen omo, ya ce na kai masa Wakin su""."

"""Šakin su kuma? Ina laifin ya ce ki kai wa babarsa, kuma ina sauran yaran gidan? To wallahi ko da wasa, kar ki"

"kuskura wani a mazan gidan nan, ya aike ki ya ce ki kai masa Wakinsa, ko wani wuri da mutane ko da kuwa zasu dake ki"" ta waiwaya ta ga awwalu zai shiga sashin mazan ta karSi omon ta ce ""Kai auwwalu, ka kai wa idiris aiken da ya yi wa ummi, wuce muje ke kuma"""

"Suka tafi makaranta, ta saya wa ummi awara a hanya, da suka je ta zaunar da ita a makaranta ta bata ta ci."

"Suna tafe a hanya naima na sake jaddadawa ummi, kar ta kuskura wani ya aiketa, ya ce ta kai masa Wakinsa a"

samarin gidan.

"Ta raka ummi har cikin gidan, tana shirin tafiya, Idris ya shigo yana yi wa naima bala'i."

"""Wacece ke a wurinta, da har zan aiketa ki hana ta kai mini aike?"""

"Naima ta ce ""kamar yaya, makaranta zamu tafi mun makara"""

"""Dole tare zaku tafi makarantar? Har in aike ta ki hanata kawo mini sa™ona?"""

"""Amma dai da alama baka da gaskiya, ba dai an kai maka aiken ba, ya zaka din ga aiken yarinya ka ce ta kai maka"

"Wakin ka"" nan da nan bala'i ya kaure abunka da gidan gandu, nan da nan aka taru, ya din ga kurarin zai yi mata dukan tsiya."

"Iya ta hau naima da masifa, har da cewa kar ta sake shigowa, tun da sharri za ta yi wa idris."

"Ita duk wannan abun ba shi ne damuwar ta ba, tausayin ummi take ji, ta kalli yadda ummin ta rakuSe tana kuka."

"Naima ta ce ""Ba abun da zai sake shigo da ni in sha Allah, amma dai wallahi idris ka canza hali, mutumin banza"

"kawai"" iya ce ta hana shi, da cewa yayi sai ya zane naima."

"Iya ta ce kowa ya watse, har ya nufi hanyar fita, ya dawo ya sha™o ummi tare da lu™a mata wata irin ashar. ˜ara tayi"

tana kakari.

"""Dan ubanki, daga yau idan na sake aikenki, ki ka biya wani wurin, ko kuma na sake ganinki da wannan yarinyar, sai"

"na kashe ki"" ya jefar da ita a wurin, ta ri™e wuya tana tari, wani irin yawu mai kauri na wahala, na zubowa daga bakinta, ta cire hijjabin makarantar ta tana gogewa, gashin kanta kuwa, kalba biyu ce tafi wata, ita ma naima ce tayi mata."

"Mariya kuwa sallar magariba ake yi, kawai suka ga ta fito daga Waki, tana ™o™arin fita, mama wadda take matar"

"babansu, ta ri™e ta, ta ce ""Mariya lafiya ina zaki?"""

"""Mama kukan ummi nake ji, kamar tana ™ofar gida fa"""

"""Mariya ummi na jigawa, kina Maiduguri ta ina ki ka ji kukan nata?"""

"""Iya wai ba kya ji ne? Ni kukan ummi nake ji"""

"Mama ta ce ""Iya kuma, nice fa mariya"""

"Mariya ta yi ™uri da ido, tana kallon mama, sai yanzu ma ta dawo hayyacinta, gaba Waya ta kasa gane menene yake faruwa, bacci take ko idonta biyu, ita dai kamar kukan ummi kunnunwata suke jiye mata."

Ayshercool

08081012143

*CUTARWA*

BRIGHT PENS

(FREE BATCH)

"Shiru mariya ta yi, tana bin mama da kallo, jiki a sanyaye ta ce ""Ki yi ha™uri, na zata gaske ne, magungunan da na sha ne, bacci ya Wauke ni na ga ummi"""

"Mama ta ce ""Mariya ki sassauta wa kanki a kan yarinyar nan, kar ki je ki haukace a banza fa"""

"Mariya ta amsa da ""To"""

"""Ki din ga yi mata addu'a, Allah zai tsare miki ita"" gyaWa mata kai kawai ta yi, ta koma Waki."

"Ummi kuwa ta ci kuka kamar babu gobe, saboda zafin sha™ar da ta sha."

"Iya ta ritsuta a Waki tana tambayarta, ko wani abun take gayawa na'ima, ummi cikin kuka ta din ga girgiza mata kai,"

tana tsoron kar ta dake ta.

"Har gari ya waye, tana jin wuyanta babu daWi, ta yi wanka, ta sanya cukurkuWaWWun uniform Win ta, dan ma an yi sa'a a wanke suke, dama na'ima da yamma ta ce zata yi musu guga, aka yi uwar watsi."

"Iya bata kulata ba, dan haka ta yi sharar tsakar gida, ta Wau kofinta, ta je sashin sa'adatu, da niyyar a bata kunu, sai dai ta tarar ta gama rabawa yaranta, suna sha zasu tafi makaranta."

"Ta juyo da kofin a hannunta, tayi karo da magaji."

"""Baki tafi makarantar ba ne?"" Ta jinjina masa kai."

"Ya kalli kofin hannunta, babu komai a ciki."

"""Kunun ma baki samu ba? Iya bata baki ba?"" Ta jinjina masa kai."

"Ya karSi kofin, ya shiga sashin su na maza, ya fito ya mi™a mata kunun cikin kofi."

"Har ™asa ta tsuguna ta karSa, ta zauna a kan wani kututture, ta kafa kai ta din ga sha, saboda uwar yunwar da take ji."

"Ta shanye ya karSi kofin, ya bata naira ashirin, ta karSa ta ce ""An gode"""

"""Kiyi sauri ki tafi makaranta, kar su dake ki"" ta ce ""To"""

"Ta kamar hanya ta tafi, jin ta a ™oshe da kunu ya sanya ta tafiya cikin nishaWi."

"Sai dai yau ma ta makara, a bakin gate discipline mistress ta fara zane ta, tare da ci mata mutunci saboda ™azanta, jikinta bususu fuskarta duk busasshshen koko, ga sauran kwantsa a idonta."

"Ta tafi aji tana kuka, saboda zafin bulala."

"Ta je ta tarar ana yi musu darasi, ta buWe jakarta da yanzu a ba™ar leda take zuba su, duk sun zama shara da tarkace,"

"fensirinta kuwa dama tsintar sa tayi, ya zama Wan mitsitsi da ™yar take iya ri™e shi ta yi rubutu."

"Head master ya shigo ajin, duk suka tashi suka gaishe shi, yayi musu umarnin su zauna."

"Ya dubi malamarsu ya ce ""Malama, yara biyar zaki zaSo mini masu ™o™ari, zamu tafi da su gidan talabijin, za ayi wani"

"shiri da su, a haska su"""

"Malamar ta ce ""Ok sir, yanzu kuwa"""

"Ta tashi ta kira yara uku, ta huWu ta kira sunan Salma Muhammad Bashir."

"Wani irin farinciki ya kama ummi, saboda malamarsu ta zaSeta a cikin wanda za a tafi da su gidan talabijin na"

"jigawa, tana ta murna za ta ganta a talabijin, dan duk da rashin kulawar nan, ummi tana da matu™ar ™o™ari, in dai aka yi darasi a gabanta, to ta Wauke."

"""Ke!ke tsaya"" headmaster ya dakatar da ita a tsakiyar aji."

"""Wannan kuma ina zata?"""

"Malama ta ce ""Sir, yarinyar na da ™o™ari fa, ita ce take first position"""

"""A hakan, wannan yarinyar da ya take karatun,? Ba ita ake kora ba ba ta biyan kuWin PTA, da yaya take iya karatun"""

"Ta ce ""A haka, ita take ta Waya?"""

"""Kai canza wata dan Allah, haba wannan tayi muni da yawa, wannan ko an saka mata camera ai ba za a ganeta ba,"

"ba™i ™irin da ita haka, ji uniform Win ta fa, tubarkallah ni wannan tayi ba™i samo wata mai Wan kyan gani, ke koma ki zauna ba za a tafi da ke ba, ji kayan jikinta kamar ´ar ci rani"""

"Tuntsirewa da dariya da yaran suka yi,hakan ya bawa hawayen idonta ™warin gwiwar zubowa, ta tafi lungun aji ta zauna, tana share hawayen."

"Tana gani aka zaSi wata daban, bayan malamar ta fita, suka Wora da yi mata dariya da tsokanar ta, har da masu ja mata hijjabi, suna ™azama ba ta wanka ba ta wanki, wa™ar da aka saba yi mata a assembly idan an zo duban tsabta,"

"har misali ake yi da ita, na ™azamai."

"Ana tashi ta fita daga aji, ta nufi gida har da gudunta, dan kar ma ´an ajinsu su taso, su tireta a hanya, ta ™arasa tana ta numfarfashi."

"Sai da ta Wan huta sannan ta shiga sashin su da sallama, muryar iya ta fara jiyo wa tana hayaniya, da muryar baba saminu, ba ta san dai faWan me suke yi ba, ta kutsa kai ta shiga."

"Wan mahaifiyarta ta gani, a zaune suna ta jayayya da su iya."

"Hayaniyar da suke yi, ba ita ce ta dame ta ba, murnar ta Allah ya sa da mama suka dawo."

"Bai lura da ummi ba, sai da ta ri™e hannunsa, ya waiwayo ya kalleta ta ce ""Ina maman take?"" Yayi ™uri da ido yana kallon ummi, sai ka ce ba ´ar mutane ba."

"Yadda mariya ke ™al™aleta, take kula da ita, amma ya ganta kamar an janyota daga ramin ™asa."

"Ya ce ""Baki gaishe ni ba"" ta tsuguna ™asa ta ce ""Ina kwana"""

"""Lafiya ™alau, ya makarantar?"""

"Ta ce ""Lafiya lau, to ina maman take?"""

"""Mama tana lafiya, ta ce; a gaishe ki"""

"Ummi ta sake kallonsa ta ce ""To zaka kai ni wurinta?"""

"""Ke wuce ki je ki cire uniform, ki yi salla"" Iya tayi mata tsawa. Yayi shiru ransa a matu™ar Sace, bai taSa tunanin ganin ummi a cikin wannan mummunan yanayin ba."

"Ta fito kanta babu Wan kwali, gashin nan a cukurkuWe, sai soshe-soshe take yi, saboda yadda ya addaba mata da"

™ai™ayi.

"Ya dubi iya ya ce ""Shikenan, tun da kun ce cikin ba naku bane ba, baku san da shi ba, ni ba dan wani abun hannunku"

"ya sanya muka zo muka sanar da akwai cikin ba, saboda a cika umarnin Ubangiji, amma tun da abun haka ne, Allah ya kyauta, mu mun ji mun gani, mun karSa. Amma dan Allah ku bani ´ar ta in kai mata, mariya ta kasa zaune ta kasa tsaye, hankalinta ya™i kwanciya, ku bata ´ar ta dan Allah"""

"""Ba rashin ummi ne ya hanata nutsuwa ba, mugun abun ta ne yake koma mata kanta, hakkina da na Wa na ba zai taSa barinta ba, ya din ga bibiyar ta kenan"""

"Ganin idan ya cigaba da zama, wannan jayayyar zata kai su ga maganar banza, ya sanya ya tashi tsam, ya ce"

"""Shikenan babu laifi, Allah ya kyauta"""

"Jin ya ce zai tafi, ya sanya ummi fitowa da gudu daga Waki, ta ce ""Ba zaka tafi da ni, ka kai ni wurin maman ba?"""

"Ya dur™usa ya shafa kanta ya ce ""Ki yi ha™uri, in sha Allah nan gaba kaWan, zaki koma wurin mamanki, Allah ya yi miki albarka"" ya ciro kuWi dubu biyar, ya bawa iya ya ce ""Dan Allah a canza mata uniform, a saya mata wasu ´an"

"kayan bu™ata"""

"Ba kunya iya ta amshe, tana harare-harare."

Ummi ta tsaya tabi bayansa da kallo har ya fice.

"Dukan da aka yi mata a kanta ne, ya sanya ta dawowa hayyacinta, ta firgita ta kalli Iya."

"""Duk wanda ya sake zuwa gidan nan, ki ka ce ya kai ki wurin uwarki, sai na saka idris ya zane miki jikinki, wato salon"

"ace ba a kula da ke, saboda ™warewa a munafunci kin tsotsa a nono ko?"" Tayi shiru ta sunkuyar da kanta ™asa."

"""Munafuka, ga muni ga kinibibi, tashi ki wanke kwanukan nan na safe"" sumi-sumi ta nufi wurin tara kwanukan"

"wanke wanke, ta haWa ta fara wankewa."

***

"Bayan sallar magariba, yaya garba ya je ya samu mahaifinsu ya sanar da shi cewa iya ta ce ba su san da ciki ba, dan haka a nemi ubansa."

"Malam yayi shiru, lamarin ya girmame shi ya ce ""Haka suka ce?"""

"""Wallahi, matar nan ba ta da mutunci ba ta da imani ko kaWan, ba ka ga Yarinyar nan a halin da na baro bata ba,"

"kamar ´ar jari bola saboda azabar datti da ™azanta"""

"""˜yalesu, yarinya kullum muna yi mata addu'a, in sha Allah babu wanda zai sake bi ta kansu, ita kuma Allah ya raba"

"ta da ciki lafiya"""

"Ya amsa masa da ""Amin"""

***

"Na'ima kuwa ummi na ranta, amma babarta ta ce mata ba ita ba ummi, dan kakarta ba mutunci ne da ita ba, kar ta yi mata wani sharrin."

"Sai dai ta kan ™ulle abinci wasu lokutan, ta tafi da shi makaranta ta bawa ummi."

"Yanzu babu mai yi wa ummi wanki balle guga, dan haka dauWa kamar ka kankarota a jikinta."

"Ummi na iya ™o™arin ta wurin kaucewa haWuwa da idiris, ga bala'in tsoronsa da take ji, saboda dukan da yake yi"

mata idan tayi laifi babu tausayi babu imani.

"Allah ya taimake ta, wasu lokutan magaji na taka masa burki a kan wasu abubuwan."

"Tsabar rashin gyara, ya sanya kwarkwata cika wa ummi gashi, kayan ta duk suka cukurkuWe suka yi mata kaWan, tana zaune har sakkowa kwarkwata suke yi daga kanta, suna bin ta, sai dai ta Suya tayi ta kashewa, ba ta son a gani."

"Ga wasu irin manyan ™uraje da suka din ga fitowa a cikin gashin kan nata, suna Wurar ruwa, suka ™ara bawa kwarkwatar nan damar hayayyafa babu ji babu gani."

"Banda zarnin fitsari da warin datti, babu abun da take yi, dan kuwa da kanta take yi wa kanta wankin kayanta,"

"wando sai ya fi kwana uku a jikinta, ba ruwan iya balle ta ce cire ki wanke."

"Sa'adatu ce babar auwwalu, ta fara lura da wannan ™urajen na kan ummi, ta kamata ta buWe kan, ta ga ™azantar da"

take cikin gashin.

"Ta nuna wa iya, Iya ta yamutse fuska ta ce ""TaS gaskiya ba zan iya taSa wannan kan ba, to gashi ne ba kaWan ba, gaba"

"Waya ba irin namu ba, kalar na mutanen ™etare, shiyasa nake cewa anya ma kuwa tamun ce, duk zuriyar mu, babu irin wannan gashin, yanzu meye abun yi kar kan ya ruSe ace ni ce ina kallonta, na bari ya ruSe ji yadda wani mugun ruwa yake tsatstsafowa da ™wayayen kwarkwata a ciki""."

"""Aikuwa sai dai a aske kan nan, dan ban ga yadda za ayi maganin abun nan ba"""

"Cikin ™yan™yami, sa'adatu ta sauke wa ummi gashin nan tsaf, ta koma sai ka ce namiji, ga hudar kunnenta ma, tana"

"ruwa saboda tsufan Wan kunne a kunnenta, ba a taSa cirewa ba."

"Iya ta saka aka haWa kanwa da gishiri, da omo aka wanke kan nan, ummi ta din ga wani irin masifaffen kuka, saboda azabar raWaWi, da bal'in zafi haka nan da ruwan sanyi aka tuSe ta, aka wanketa a tsakar gidan, iya har tana cewa"

"wannan ba™ar fatar ba da dutsen goge faso za a wanketa ba kuwa?. Wata irin annakiyar dauWa ta din ga zuba daga jikin yarinyar. Yara suka cika sashin dan™am suna kallon ummi, da tana ta ™o™arin rufe jikinta, amma azabar wahala da zafi ya sanya ta manta da tsiraicinta."

"Ummi na ji na gani, aka Waure gashinta a leda kaya guda da shi aka zubar, iya ta ce a sakawa kan ummi fiya-fiya, idan"

"ba haka ba, sauran ™wan zai ™yan™yashe kansa."

"Ba tare da tunanin wane hali zata shiga ba, suka shafe ™wallon kan da suka saukewa sumarta da fiya-fiya, hakan ya"

"sa ta din ga tari da atishawa, gaba Waya kanta ya juye, ta din ga jiri, kan dare zazzaSi ya rufe ta da ciwon kai."

"Ba wanda ya kula ya saya mata magani, haka ta kwana tana rawar sanyi, da ta yin™ura ta tashi, sai ta tafi luuu zata"

faWi.

"Da safe gwaggo ta bata, koko da ™osai, sai dai ta kasa ci, ta cigaba da kwanciya tana burgima a ™asa, kanta yana"

"ciwo, ga tari da take ta faman yi."

"Cikin barccin wahala, ummi ta ji wani ™amshin turare mai daWi, ta ji magana sama-sama kamar muryar babanta."

"Da sauri ta buWe ido, ta yi ™uri da ido tana kallonsa, ga iya a gefe suna magana da shi."

"Yayi murmushi ya ce ""Uwata ta kaina, kin tashi? ˜araso mu gaisa"" sai yanzu ta lura ba baba bane ba, mutumin nan"

ne mai kama da shi.

"Tasowa ta yi da sauri, sai dai ta faWi, saboda jirin da take ji."

"Da sauri ya tashi, ya ce ""Iya ba ta da lafiya ne?"" Iya ta taSe baki, mussaman jin ya kirata da uwassa ta kansa ta ce ""Eh"

"zazzaSi take""."

"""Subhanallah, kuma ba a kaita asibiti ba?"""

"Ya zaunar da ummi, ya sinsuna kanta ya ce ""Ya na ji kamar kina warin fiya-fiya? Ya cire hular kanta, sai ga kai sol ba"

"gashi, ga dagwalon gyambo a kan, ciwon duk yayi ba™i saboda fiya-fiya."

"A razane ya ce ""Meye wannan? Iya meya sameta a kanta?"""

"""Kwarkwata ce, da wasu ™uraje, shi ne aka aske kan aka shafa mata fiya-fiya"""

"""Innalillahi wa Innalillahi raji'un, iya wannan ai ganganci ne, ina laifin a kaita asibiti, wannan ™aramar yarinyar a saka mata fiya-fiya a ka, ai shi ya sanya mata zazzaSi""."

"""To ban da kai yahaya, ana ta abun da za a ci, waye yake ta wani asibiti, wa zai bayar da kuWin kai ta wani asibiti?"""

"Mi™ewa yayi ya ce ""Wannan abun kunya da yawa yake"""

"Cak ya saSa ummi a kafaWarsa, yayi waje da ita, iya ta biyo shi tana tambayar ina zai kai ta?."

"""Asibiti zan kai ta, idan ta mutu ba makawa ku ne ku ka kasheta"" yayi waje da ita."

"A mota ya kwantar da ita, ya ja suka tafi."

"Sosai likitoci suka din ga faWa, dan ma asibitin kuWi ne, aka sake wanke kan ummi, da magunguna, aka saka mata"

"ruwa saboda zazzaSin da ya rufeta, take ta rawar sanyi."

"Ya fita ya sayo kayan marmari, da ta farfaWo zazzaSin ya sauka, ya din ga bata da kansa."

"""Kana kama da baba"" ta faWa a lokacin da za™in kankana ya ratsa kwanyarta, wanda rabon da ta sha har ta manta."

"Yayi mata murmushi ya ce ""Ai nima baba ne"""

"""Ai an ce baba ba zai dawo ba, ya mutu yana cikin kabari""."

"""Haka ne mamana, kina yi masa addu'a ko?"" Ta gyaWa kai alamar eh."

"""Yanzu me ki ke son na saya miki?"""

"""Littafi"" ta bashi amsa."

"""Littafin makaranta?"" Ta jinjina masa kai alamar eh."

"Ya ce ""To shikenan, zan sai miki in sayo miki kifi ko nama, wanne zaki ci?"""

"""Nama"" ta faWa tana murmushi."

"Yayi mata murmushi shi ma, ya ce ""To bari su sallame mu, sai na saya miki mu tafi gida"""

"Har ummi ta Wan murmuro, ya saya mata

Please Login or Register in order to submit comment