You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta buWe sabon babi na ™alubale, sai yaushe za ta huta kenan? Meyasa Iya ta tsani ummi ne, kamar ba a cikin jikokinta take ba?"""

"Hashim ya numfasa, cike da damuwa da takaici ya ce ""Biyayyar da iyayenmu ke yi wa Iya, ta samo asali ne ga"

"wasiyyar mahaifinmu, na lallai su yi mata biyayya. Bayan haka ban san dalilin da ya sanya bayan biyayyar suke rufe idonsu a kan gaskiya ba, su kasa nuna mata hanyar da ta dace ba."

"Nayi iya yi na a kan auren nan, sai dai sun fi ™arfina, ni dama ba wani shiri muke yi ba, saboda bani da kuWi, Idris kuma sunan mahaifinta ne da shi. ˜iyayyar ummi kuma, dama ba ta son mahaifiyar ummi, saboda kawu Magaji yana matu™ar son ta, har wasu lokutan baya iya Soye son da yake yi mata, bugu da ™ari, baban ummi ba shi da komai, bai mutu ya bar komai ba, duk da haka dai, ban san dalilin da ya sanya ta tsananta ™iyayyar ummi haka ba."

"Zan cigaba da yi wa idiris nasiha, duk da ba jin shawara yake yi ba, zan kuma biya ta gidan yanzu, in ga halin da take ciki""."

"Jiki a sanyaye na'ima ta ce ""Yakamata kam, ummi na bu™atar kulawa da jaba jiki, har ga Allah ina jin tausayinta sosai"

"da sosai, dan Allah yaya magaji ka din ga zagayata""."

"""Kar ki damu, in sha Allah, ba zai gagara ba, ina godiya sosai da gudunmawar da ki ke bawa ummi""."

"""Bakomai yaya magaji, ummi ™anwata ce, ba zan manta karamcin iyayenta a gare ni ba, da yadda suke girmama"

"iyayena ba"""

"""Haka ne, ki gaida gida, da maigidan"""

"Suka yi sallama, kowa ya tafi."

"Kasa wucewa gida magaji yayi, ya wuce gidan Idris da bai taSa zuwa ba."

"Sallama yayi ya tsaya a waje, ummi ta le™o, tana ganinsa tayi murmushi ta ce ""Laa yaya magaji, shigo baka zo ba sai"

"yau"""

"Ya kalleta duk da tana da duhu, amma ga shaidar mari nan a gefen idonta."

"Ta yi gaba ta ce masa ya shigo, ya ce ""A'a bani abun zama, na zauna a nan"""

"Ta shiga ta Waukko masa tabarma, ta shimfiWa masa ta ce ""Yaya yaya na'ima ta zo fa"""

"Ya ce ""Haba?"""

"""Wallahi, duk ta sai mini kayayyaki ta bani, ita ta bani tabar nan ma"""

"""Masha Allah, Allah ya saka mata da alkhairi"""

"Ta ce ""Amin"""

"Ya Wan dube ta, ya ce ""Ummi babu wata matsala? Komai lafiya ™alau?"""

"Ta jinjina masa kai ta ce ""Eh""."

"""Na san ko baki faWa ba, akwai matsala ummi, amma dan Allah ki kwantar da hankalinki, komai zai wuce in sha"

"Allah"""

"""Yaushe zai wuce yaya? Gobe ko jibi?"" Tayi maganar idanunta na tara hawaye."

"""Lokaci ne ummi, zai zama tarihi"""

Tuni idanuwanta suka fara zubar da hawaye.

"""Ki dake ummi, ki ™arfafi zuciyarki, na san a cikin matsala ki ke, ki yi ha™uri ummi, ki share hawayenki, zai zama"

"murmushi wataran"" goge hawaye take yi, sai dai tana gogewa wasu suna zubowa."

"Idiris ne ya bankaWo babu ko sallama, yadda ummi ta zabura kawai ya isa ya baka tausayi."

"Ko kallonsu bai yi ba, ya shige ya buWe Wakin da yake kwana, ya shiga."

"Hashim ya tashi ya bi bayansa, ummi ta karkaWe tabarmar, ta Waukko tsintsiyar da na'ima ta bata, ta yi shara,"

"hayaniyar hashim ta din ga ji, da idris."

"Hashim yana ce masa ""Ka ji tsoron Allah wallahi, idan ka cigaba da biye wa Iya, wallahi Allah ba zai barku ba, kuna ta"

"azabtar da marainiyar Allah ba gaira babu dalili""."

"""An azabtar da ita Win, ni na ce a aura mini ita? Ko na ce ina son ta ne, kai meya hana a aura maka ita? An bani saura"

"™azama mummuna, Wallahi ba zan zauna da ita ba, sai ta gudu da ™afarta""."

"""Amma ita ma ai ba cewa tayi tana sonka ba, haWin Iya ne, ita tayi ha™uri, kai me zai hana ka yi ha™urin?"""

"Idris ya ce ""ba zan yi ha™urin ba, ka fita daga harkata, ko kai ma na karta maka rashin mutunci"""

"Haka suka yi baran-baran, hashim ya fito, ummi tana ce masa kai gaida gida, kai kawai ya jinjina mata ya tafi."

"Yana fita, Idris ya dirar mata da duka da zagi da cin mutunci kamar yadda ya saba, yana i™rarin ™ararsa ta kai wurin magaji."

"Ma™wabciyar su da ta kasance dattijuwa, yau ta kasa jure ihun ummi, ta shigo kawo mata Wauki, ta din ga bashi"

"ha™uri, amma mursisi ya ce ta fita ta bar masa gida, ganin idiris bai yi kalar mutunci ba, ya sanya ta fita ta bar gidan tana tausaya wa ummi."

"Tun daga ranar ya ™ara tsananta azabtarwar da yake yi mata, gashi ya tula mata wankinsa, ya ce tayi masa, idan tayi"

"bai fita ba, ya kamata ya zane ta, ban da zagi da cin mutunci."

"Abinci kuwa ko tumatir bai taSa kawowa ba, sai dai ta aika wa iya, Wataran ta bata, wataran ta ce ba ta da shi."

"˜arshe sai da iya tayi ta mata faWa, wai ba zata iya rufawa Idris asiri ba, ta san dai ba wata cikakkiyar sana'a ce da shi"

"ba, ranar da ya kawo su ci, idan ba shi da shi ta din ga ha™uri."

"Dattijuwar matar nan ta fuskanci halin da ummi take ciki, ta Wauki ragamar ciyar da ita, idan ta cewa ummi ta gudu ta je gida ta kai ™arar abun da yake yi mata, sai ummi ta ce ko ta je dawo da ita za ayi."

"Da ya kalli ummi, ya tuna a yanayin da ya sameta, sai ya ™ara ™aimi wurin cutar da ita, haWi da zaluntar ta."

"Idan aka zo ana sallama da shi abokansa, sai ta jiyo suna kiransa da angon WoWWoya, ba ta kawo komai a ranta ba, sai"

"ranar da ta jiyo suna tambayarsa ina amaryarsa WoWWoya, ya ce musu kar su sake haWa shi da wannan jakar yarinyar."

"Duk da ™arancin shekarun ummi, a lokacin ta fuskanci asiri ya tona mata a wurin abokansa, hakan ya sanya ta yin"

kuka da har kanta ya yi ciwo.

"A haka a wannan ba™ar azabar, tayi wata guda cir a gidan sa, tun tana tsoronsa har ta fara dakewa da duk abun da zai yi mata yayi mata."

"Yau ta tashi da wani irin zazzaSi mai zafin gaske, wanda baya rasa nasaba da dukan ruwa da kuma azababben sauron"

da yake cizonta a wannan Wakin.

"Ga gudawa da take zugawa babu ™a™™autawa, jikinta duk yayi weak."

"BankaWa labulen yayi, ya tarar da ita a kwance, ya watsa mata kayansa ya ce ta wanke masa. Shiru tayi ba ta motsa ba, ya daka mata tsawa ta ce ""Yaya bani da lafiya"""

"""Ina ruwana, dalla fito"""

"Ta janyo jikinta ta kwaso kayan ta fito, ya fita sayen omo, ta kwanta a kan kayan, tana jin Wumin ranar dake ratsata,"

wanda hakan ya sa zazzaSi ™ara rufeta.

"Azabar zafin dukan da yayi mata da ™afarsa yasa ta tashi da sauri, tana ri™e hannunta."

"""Bacci na ce ki yi?"" Shiru tayi tana sunkuyar da kai."

"Wani irin yawu ya haWiye, yana ™are wa ummi kallo, duk ba™in fatar nan ta ta fatar tana da Waukar ido."

"A wurin yayi yin™urin sake afka mata, sai dai ba ta sauya zani ba, duk da ta samu sassauci, na ciwon saboda yanzu"

"sau biyu take sauya wando a rana, kamar yadda Na'ima ta gaya mata."

"Amma duk da haka tana wannan ™arin mara daWi, duk da jikinta baya wari yanzu, saboda ta samu sabulun wanka."

"Zura masa ido kawai tayi, saboda a galabaice take da ciwo"

"Wata mummunar ashar yayi mata, yana zubar da yawu, ya Wagota ya din ga kifa mata mari."

"Kukan ma ba ya iya fita, saboda azaba da masifar idiris, da yake abu kamar dabba ba Wan adam ba."

"Ya din ga tsine mata albarka, da ita da iyayenta, dan har Iya sai da ya zaga."

˜arshe ma ya dan™ara mata saki a wurin.

"˜afarta ko takalmi babu, ta gyara suturar jikinta ta fice daga gidan a haka, ta tafi gida ga hannunta Waya kamar ba a"

"jikinta yake ba, saboda takata yayi a hannun."

"Iya da ke iza wuta ta mi™e tana faWin ""Ke lafiya?"""

"Kan ummi ta yi magana, jiri ya Webe ta ta faWi ™asa."

"Da sauri Iya ta ™arasa kanta ta ce ""Ke, menene wai?""."

"""Iya zan mutu, yaya idris zai kashe ni, dan Allah kar ki mayar da ni, ya ce ya sake ni"" tayi maganar cikin gunjin kuka."

"Ta taSa jikin ummi ta ji zafi, ga fuskarta shaidar yatsun Idris kwance a fuskar ta har idonta yayi taruwar jini."

"""LallaSa ki tashi ki shiga Waki ki zauna, daga yin aure ba a kashe shi ba, bari dai ya zo mu ji me ki ka yi masa"" Iya ta"

tashi ta fita.

"Kuka ummi ta din ga yi, tana jin dama ta mutu ta huta, idan aka mayar da ita gidan idris ta san sai ya kashe ta."

"Da ™yar Hashim ya nemo idris, aka nemo babansu, domin jin menene yake faruwa."

"Sai dai daga mugun kallon da yake yi wa ummi, ka san babu Allah a ransa."

"Babu zato babu tsammani sai ga kawu yahaya ya dira a gidan, kuma bai tsaya ko ina ba sai sashin Iya."

"Sai dai babu walwala ko fara'a a tare da shi, suka gaisa da Iya da Wan uwansa, da su Hashim. Sannan ya kalli Iya ya ce"

"""Iya dan me za a aurar da ummi, ba tare da na sani ba? Sai shekaranjiya magaji yake gaya mini?"""

"""Saboda kai ne ubanta? Uban waye ma ya ganka balle ya gaya maka, tangarWa aka samu da wadda zai aura, na saka"

"aka yi da ita dan rufuwar asirinmu""."

"Ummi da baccin wahala ya Wauka, kamar a mafarki ta ji muryar kawu yahaya, mi™a hannu ta fara yi ta ce ""Kawu"""

"Cikin azama ya nufi ummi ya ce ""Na'am mamana"""

"""Dan Allah ka kai ni wurin mama, idan na koma gidan Idris kashe ni zai yi"" ganin tana ™o™arin tashi ta kasa, ya sanya"

ya Wago ummi.

"""Innalillahi wa Innalillahi raji'un"" ya faWa a razane."

"Fuskar ummi ya gani a kumbure suntum, ga hannunta Waya ma ya kumbura ba ta iya motsa shi sosai."

"""Meyafaru haka?"""

"""Dukana yake yi kawu, dan Allah kar ka bani a nan wallahi mutuwa zan yi, idan baka san in da mama take ba, ko"

"gidan marayu ka kai ni, ko idan akwai makarantar almajirai ka kai ni, zan mutu wallahi "" tayi maganar tana wani irin gigitaccen kuka."

"""Kar ku ce mini shi yayi mata wannan dukan?"""

"Iya ta ce ""Ka ga Yahaya, ba abu ne na tashin hankali ba, abun da muke shirin sasantawa kenan, kai me take yi maka"

"ne?"""

"Cikin fitsara da rashin kunya ya ce ""Haba Iya, kin san ni ba son ta nake yi ba, yarinya da take saura ce, ai kin san"

"komai aka li™a mini ita, ga sanyi ya kasheta ban da wari da Woyi ba abun da take yi, an li™a mini na kwashi masifa gaskiya ba zan iya ba, jikinta kamar an buWe masai, nima ba iya zama zan yi da ita ba""."

"Tsit suka yi, babu wanda ya zaci fitowar wannan maganar daga bakinsa, ba™in ciki da takaici ya rufe Hashim."

"""Madalla, ka iya rubutu ai ko?"" Ya jinjina kai."

"Kawu yahaya ya ciro takarda da biro ya ce ""Sakar mini ´a ta"""

"Iya ta fara ""A'a Yahaya, ai dauWar gora ciki ka sha ta """

"""Ba wata dauWa iya, koma menene ya samu ummi laifinki ne, kina me sanyi yayi mata wannan kamun? Da dauWar"

"gorar ciki ke shan ta, shi ya kasa rufa mata asiri ya nema mata magani, ya tona mata asiri haka, shi mai ya hana ya sha dauWar gorar?, laifin waye idan ba naki ba, ya saki ummi, da ita zan tafi, abun da yayi kansa ya yi wa, ´ar shekara sha uku aure wata Waya ya rabu, In sha Allah ba zata wula™anta ba, na yi imani da Allah balarabe ba zai bari iyalinmu su wula™anta bayan bamu ba"" yayi maganar ™asan zuciyarsa yana jinjina girman hukuncin da ya yanke, dan ya san da bada™ala idan ya je da ummi gidansa."

"(Ina godiya da tarin comments da ake yi a kan litattafan bright pens, cutarwa, munafukin miji, yi wa kai, masu ™orafi"

"a kan littafin cutarwa, ayi ha™uri da yadda labarin yazo, ina ganin sharhi da ™orafe-™orafe ina godiya sosai )"

Ayshercool

08081012143

*CUTARWA!*

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

BRIGHT PENS

(FREE BATCH)

P13

"Iya ta ce ""A'a Yahaya, kar mu yi haka da kai, wannan abu ne na cikin gida da yakamata a sasanta shi, wannan ai sai"

"asirinmu ya tonu, duniya ta zage mu"""

"""Iya zagi na nawa kuma? Kalli jikin yarinyar nan fa, baiwar ubansa ce ita? A gabanki a gaban ubansa yake aibata ta"

"yake cewa baya son ta, baya ™aunarta, wallahi dole ya saketa, zan je da ummi ta cigaba da karatunta""."

"""Gaskiya ban lamunta ba yahaya, ba zaka Sata zumunci ba da abun da na ™ulla dan ™arfafa zumunci ba""."

"Hashim da bai yi niyyar sanya baki ba, sai da ya ga abun na iya ya™i ci ya ™i cinyewa ya ce ""Iya wane zumunci kuma"

"banda wanda aka Sata?"""

"""Rufe mini baki dan ubanka, ai duk kai ne munafikin da ka kunno kowacce wuta, ban yadda a tafi da ummi ko ina ba,"

"ko auren ya mutu, muna nan a bar mini ita""."

"Yahaya ya kalli Iya ido cikin ido ya ce ""Wallahi iya idan ki ka hana ni tafiya da ummi, zan Webowa idiris hukumar kare hakkin Wan Adam, su bi mata hakkinta, kuma idan suka tashi, har ke ba zasu bari ba, da duk mutanen gidan nan, na"

"farko ga child abuse, by forced marriage, kun mata auren dole da ™anan shekaru, ga dukanta da ci mata mutunci, deformation of character Sata mata suna, ta hanyar yaWa larurar da take fama da ita a cikin mutane, wanda duk ya zo kunnena tun kan na zo nan na samu lanari, kuma mariya ma zata iya shigowa cikin lamarin nan, ™wace mata ´a babu dalili da ki ka yi, dan dai suma ba su san ´ancin su bane, da sun haWa ki da hukuma, da sai kin basu ´ar su""."

"Saminu ya ce ""A'a yaya yahaya, ba za ayi haka ba"""

"Cikin rikicewa Iya ta ce ""Yahaya ni zaka kai ™ara hukuma ka saka a rufe ni?"""

"""Ba ™ararki zan kai ba, ™arar wannan sakaran zan kai, idan kuma na kai ™ararsa su hukuma zurfafa bincike zasu yi, ina gaya miki abun da hakan ka iya haifarwa ne, kai kuma Wauki takarda da biro, ka sakar mini ´a, ko da™i™ancin naka bai"

"bari, ka iya rubutun ba?"""

"Cikin kumbura baki ya Wauki takarda da biron, ya rubutawa ummi saki biyu."

"Kawu yahaya ya karSa, ya kalli ummi ya ce ""Tashi in tayaki ki haWo kayanki mu tafi"""

"Magaji ya ce ""Bari na tayata"" a hankali ta ce ""Ai kayan suna can gidan, sai kuma kayana da ke Wakin itace"""

"Kawu Yahaya da kansa ya tashi, ya je Wakin itacen, ya Waukko vivar kayan ummi, sai dai ya ga tsummokara ne kawai,"

dan haka ya ce ba za su tafi da su ba.

"Iya ta din ga harar ummi, amma ummi tayi kamar bata gani ba, magaji ya kawo kayan ummi."

"Jama'ar gida suka taru, suna kallon ummi za ga tafi birnin kanon dabo gidan kawu yahaya, wasu na tausaya mata,"

wasu kuma na yi mata murna.

"""Yahaya"" Iya ta kira sunansa."

"Ya amsa mata, ta ce ""Ka yi mini al™awarin ba za ka kai ummi wurin mariya ba, dan idan haka ta faru, abun da zai biyo"

"baya ba zai yi mana daWi ba""."

"""Abu Waya na sani, na Wauki ummi tsakani da Allah dan inganta rayuwarta, ni ban san a in da mahaifiyar ta take ba,"

"amma akwai lokacin da lallai dole a nemi dangin mahaifiyar ummi, ta gansu, dan babu in da shari'a ta ce a yanke ala™a tsakanin uwa da Wan ta, ko da kuwa kafura ce, abun da yake tsakanin ki da mahaifiyar ta daban, kuma bai kamata ya shafi ummi ba"" Iya tayi mu™us, dan ba ta son yi wa kanta sagegeduwar Wan abun duniyar da yake bata."

"Sosai kawu yahaya ya yi wa ´an uwansa ta tas, a kan abubuwan da suka faru a kan ummi, kasancewar shi ne babba"

"suna girmama shi, duk da kaf Win su sun riga shi yin aure, dam su ba karatun boko suka yi ba, wasun su ma shakara sha tara suka yi aure, amma suna girmama shi sosai mussaman da yana da abun duniya."

"Magaji ne ya ri™o ummi, sai layi take saboda yunwa da kuma rashin lafiya."

"Magaji ya ce ""Ummi shikenan sai tafiya, in Allah ya yarda wahala ta ™are, sai jin daWi da kwanciyar hankali, ki kula da"

"kanki, ki yi karatu da kyau""."

"Ummi ta ce ""To yaya, kai ne ka gaya wa kawu halin da nake ciki?"""

"""Eh ummi, aron waya na samu, na kira shi, idan ba haka ba, bani da wata mafita da zan taimake ki""."

"Ummi ta yi ajiyar zuciya ta ce ""Allah ya sa kar iya tayi ta yi maka faWa, dan Allah idan ka ga yaya na'ima ta zo ka gaya"

"mata bana nan, ba zan iya zuwa yi wa mama sallama ba, jikina ba ™wari ba zan so ta ganni a haka ba"""

"Ya ce ""To shikenan, in sha Allah"""

"""To zaka din ga zuwa kanon muna gaisawa?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Zan din ga zuwa, ai kema zaki din ga zuwa muna gaisawa ko?"""

"Ta yi saurin girgiza masa kai ta ce ""In Allah ya yarda ni da gagarwa har abada, ba zan sake zuwa ba, dan Allah idan ka"

"samu labarin in da mama take, ka gaya mini"""

"Sak yayi jikinsa yayi sanyi yana kallon ummi, jin abun da ta faWa, sai dai bai kamata ya ga laifinta ba, an azabtar da ita"

"azabtarwa mai munin da dan ta faWi hakan, ba ta yi laifi ba."

"Kawu yahaya ya tsaya suna magana da kawu Ilyasu da sagir, wanda yanzu suka zo riski zasu tafi."

"Kawai Idris ya tsinci kansa da dawowa, dan ya tabbattar da gaske tafiya za ayi da ummin? Ko kuwa ba gaske bane"

ba?.

"Hannun hashim ya gani a cikin na ummi, ya ri™ota sun tsaya suna magana, wani zazzafan abu mai raWaWin gaske,"

"tamkar sukar kibiya, ya soki ™irjinsa."

"TaSe baki yayi tare da jan tsaki, hashim suka ™arasa gaban motar, ummi ta shiga ta zauna tana kallon hashim da"

"™ofar gidan da nan ne tushenta, amma azabar cikinsa ko zamanin bayi sai haka."

"Yaran gidan har da mata, da ma™wabta sun yi dandazo suna kallon tafiyar ummi."

"Kawu yahaya suka gama magana, ya shiga ya kunna motar Ummi ta sauke idanuwanta masu kama da na mage a"

"cikin na Idris, idanun da suka kumbura saboda duka Waya yayi taruwar jini a cikin sa, wani irin kallo take yi masa mai kama da na ka saurari dawowata, zaka girbe abun da ka shuka."

"Hanyar kano suka kama, suna tafe kawu yahaya yana yi wa ummi nasiha tare da rarrashin ta."

"Ya kalli ummi ya ce ""Idan mun je, kar ki kuskura ki gaya wa wani kin taSa aure, kin ji ko?"""

Ummi ta jinjina masa kai alamar to.

"Suna tafe tana amai, kasancewar baya son su yi dare a hanya, ya sanya ya tsaya ya saya mata ruwan gishiri da suga,"

"da kuma maganin zazzaSi, suka cigaba da tafiya, ya tanbayeta ko za ta ci wani abun ne? Duk da yunwar da take ji, cikinta babu daWi, dan haka ta ce masa ba ta bu™atar cin komai."

"Tsayawa yayi ya saya mata kankana, ya ce ta sha, kaWan ta ci ta kashingiWa, tana tuna wula™anci da cin zarafin da"

"idiris yayi mata, da yadda ya tona mata asiri a gaban mutane."

"Ko da suka isa kano, wani asibiti ya fara wuce wa da ummi, aka yi mata teses, sannan aka rubuta mata magunguna,"

"har za su tafi, kawu yahaya ya cewa ummi, ta yi wa likitan bayanin Waya matsalar ta ta."

"Sai dai ummi ta sunkuyar da kai, ta kasa magana saboda tsananin kunya da ganin kamar tozarci ne bayanin wannan"

matsalar ta ta ga wani.

"Ganin ta™i magana, ya sanya likitan tura su wurin wata nurse, tun da mace ce, za ta fi iya sakin jiki tayi mata bayani."

"Sai dai ba ta sauya zani ba, nan ma ummi kasa magana ta yi."

"Nurse Win ta kalli kawu yahaya ta ce ""YallaSai me yake damunta ne? Ta ™i magana""."

"Ya ce ""Kina ji ´a ta ce wannan, a ™auye take hannun mahaifiyarmu, aka yi mata aure na je na tarar da matsala mijin ya ce ba ta da lafiya, sanyi yayi mata yawa, auren ma dai ya mutu"""

"Nurse Win ta kalli ummi sannan ta kalle shi ta ce ""Bawan Allah kai gaka wayayye, ya zaka bari a yi wa wannan"

"yarinyar ™arama aure a yanzu, kalli fuskarta ma kamar shaidar duka, ni wannan yarinyar ai ba ta fi in saka zani in goye ta ba""."

"Ganin za ta fara yi masa faWa, saboda yadda ta Wau zafi, ya sanya ya yi mata bayanin komai."

"Jikinta duk yayi sanyi, tana jinjina lamarin, gaba Waya tausayin ummi ya kamata, wannan ´ar ™aramar yarinyar ita ce"

"aka yi wa aure, har ya mutu."

"Ta kalli ummi ta ce ""Gaya mini menene yake damunki a wurin?"" Ummi ta sunkuyar da kai tare da jin ta a takure."

"Ta kalli kawu yahaya ta ce ""Šan bamu wuri"" ba musu ya fita waje."

"Ta haWe rai ta kalli ummi ta ce ""Ke dan gidanku ki gaya mini nan asibiti ne, idan baki warke ba haka zaki yi ta aure"

"yana mutuwa, saboda wannan matsalar""."

"Ummi murya ™asa-™asa ta ce ""˜ai™ayi yake yi mini""."

"""Tun yaushe?"""

"""An daWe"""

"""Ya aka yi aka daWe, wasa ki ke da wurin?"""

Ummi ta girgiza kai alamar a'a.

"""To ya aka yi yake ™ai™ayi, kafin ayi miki auren ya fara ko bayan an yi mikk auren?"""

"""Kafin ayi mini ne?"""

"Nurse Win ta numfasa ta ce ""Sau nawa ki ke canza wando a rana?"""

"Ummi ta kalleta ta ce ""Kan ayi mini?"""

"Auren ne ba zata iya faWa ba, tana jin nauyin haka."

"Ta ce ""Eh, kan ayi auren"""

"""Wandona Waya ne, idan na wanke sai na saka"""

"Tayi ™uri da ido tana kallon ummi, da ta ji ta ce wando Waya."

"""Yaya ki ke tsarki?"""

"Amsar da ta bawa nurse Win ta girgiza ta, dan ciwon sanyin ummi, yana da ala™a da rashin iya tsarki, da tsugunawa a banWaki barkatai, da kuma rashin kyakywar kulawa na uwa da wurin bai samu ba."

"Ta dubi ummi ta ce ""Daga yanzu, wando sau uku zaki din ga canzawa a rana, kuma idan ki ka yi bayan gida, sai kin"

"fara wanke wurin fitsarinki, sannan ki wanke wurin bayan gida, ba haWe tsarkinsu."

"Kar ki kuskura ki yi fitsari kina Wigar da ruwan tsarkin, ki mayar da wando jikin ki, ko ki saka ji™a™™en wando, ki samu Wan tsumma mai kyau, ki din ga wankewa kina ajiyewa a banWakin da ki ke, idan kin yi tsarki, ko kin yi wanka, ki din ga tsane wurin kan ki saka wando."

"Idan fitsari ya kama ki a wani wuri daban ba gida ba, ki yi fitsarin a tsaye, idan kin gama sai ki wanke ™afarki, da jikinki, ki daina shiga banWaki barkatai"" ta din ga yi wa ummi bayanin yadda za ta din ga kula da tsabtar wurin, dan babu wanda ya taSa zaunar da ita yayi mata wannan bayanin."

"""Kin fara al'ada ne?"""

"Ummi ta ce ""A'a"""

"Nurse Win ta a aika ummi ta kira kawu yahaya, ta ce masa ""YallaSai gaskiya sanyi ya yi mata yawa, kuma na lura"

"rashin tsabta da kula ne ya haddasa mata hakan, dan haka dole ku kula, tun da yanzu ka ce ta dawo hannunka. Ku dawo ranar lahadi akwai gynea doctor Win da yake zama, sai ka kawota ta ganshi."

"Na so ace da mace ku ka zo, sai ta fi fahimtar bayanina, amma kai Win ba ta Saci ba, ai uba ne kai. A yanzu, abu na farko a sama mata isasshen wanduna, a ™alla shida zuwa dozen. Sai kuma a sama mata flask mussaman na ruwan zafi, na ta ne ta din ga kama ruwa da ruwan Wumi."

"Banda tsarki da sabulu, a samo mata ganyen magarya, a tafasa shi ta din ga kama ruwa da shi."

"Kuma ka san shi ciwo ne mai naci, dan haka a kula sosai, sai kuma ku nemi kanumfari, tafarnuwa ba mai yawa ba, da namijin goro, a ji™a su a robar ruwa mai murfi, ta din ga tsiyaya tana sha, ta yawaita amfani da kanumfarin nan."

"Sai kuma a samo saiwar zogale a din ga tafasa mata da jar kanwa,

Please Login or Register in order to submit comment