You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kira ki mayi magana anjima"" ta katse wayar ta ajiye tana wani irin haki,"

ita ba mai asma ba.

***

"Dr. suna tafe a mota da shi da ummi, ya ce ""Mamana zaki ga zamu yi doguwar tafiya, ba sayar da ke zan yi ba abun alkhairi ne"""

"Ummi ta yi murmushi ta ce ""Idan sayar da ni Win ma ka yi ai na saidu kawu"""

"Yayi murmushi ya ce ""Idan na sayar da uwata ina na kama? Yakamata ace kin yi azumin farinciki kan mu yi tafiyar"

"nan"""

"""To Ubangiji ya tabattar mana da dukkanin alkhairin da yake cikinta"""

"Ya amsa mata da ""amin"""

"Ummi ta gaji da zaman motar nan sosai da sosai, sai dai tun da taga symbols da sunan borno, jikinta ya fara sanyi,"

har ta rasa tunanin me ma za ta yi ne?.

"Kawu kuma ya mayar da kai sosai a kan tu™insa, sai lokacin salla ya tsaya suka yi salla, ya saya mata abinci."

"Ta tuno lokacin da ya Waukkota daga gagarwa a wahale, ba sutura ga ciwo, ko ba komai ta samu alkhairi a dalilin ri™onta da yayi"

"A ranta ta ce ""Allah sarki kawuna, baba ya tafi amma ya bar mini Allah, Allah kuma ya bani kai, Allah ya kula da kai"

"da zuriyarka""."

"Duk da ba ga saba baccin mota ba, gajiya ta sanya wani irin nannauyan bacci yin awon gaba da ita."

"""Mamana tashi mun zo"" a hankali ummi ta motsa tare da buWe idonta, har suka fito daga cikin motar, ba ta iya cewa"

"komai ba, sai bin wurin da kallo."

"˜ofar wani gida suka tsaya, dr. Ya ciro wayarsa ya Wan daddana ya kara a kunnensa ya ce ""Gamu mun zo"""

Wani matashin saurayi ya le™o ya dur™usa ya gaida dr. Sannan ya ce su shiga.

"Suka shiga cikin gidan, ummi ta zubawa dattijon da suka tarar a tsakar ido, yana zaune a kan buzu, da Al™ur'ani"

bugun warshi a gabansa.

"Dattijon ya mi™e tsaye yana yi musu maraba, tare da bin ummi da kallo, ba ta Waga ni™abin fuskarta ba, sai dai ta"

"shagala da kallon sa ta san shi, amma a ina? Ta kasa tunawa."

"Yayi musu jagora har wani matsakaicin falo, yana ta yi musu sannu da zuwa."

"Suka gaisa da dr. Ummi ta gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa, sai dai bai tambayi wacece ba, kuma ya kasa daina"

kallonta.

"Dr. Ya ce ""Ina mutuniyar kuwa?"""

"""Wai sun fita barka a nan bayan layi, jikin ne ma ya Wan motsa, amma Alhamdilillah mun gode Allah, bari azo a Wora"

"muku girki, ai bamu san zaku zo ba"""

"Dr. Ya ce ""Ai al™awarin da na Wauka na zo cikawa, zuwan babu cikekken shiri, bari mu yi salla kafin su dawo""."

"Ya ja dr. Suka fita, bayan nuna wa ummi banWaki, tayi alwala ta yi salla, ta nemi wuri ta kashingiWa tana hutawa,"

saboda gajiyar da tayi.

"Ummi ta Wan jima a zaune, sannan dr. Ya shigo, shigowar ta sa yayi daidai da shigowar matashin da ya yi musu iso, ya"

"kawo musu nono mai sanyin gaske, da nama fal malam ya ce a kawo musu da ruwa, dan azo a Wora sanwa."

"Ummi dai ta kasa sakewa ta ci, dr. Kuma sai hira suke yi da malam."

"Dr. Ya ce ""Malam ba ka ganni da ba™uwa ba ne? Baka tambayeni wacece ba"""

"Malam yayi murmushi ya ce ""Tun da baka gaya mini ba, bai kamata na yi shishshigi ba ai, na ma zata ko mai Wakinka"

"ce, shiyasa ban yi magana ba, kuma na ganta sanye da ni™abi"""

"Dr. Yayi murmushi ya ce ""Aishikenan, mama malam ne fa, baki gane shi ba?"""

"Ummi ta ce ""Na sanshi amma na manta a ina?"""

"""To ki cire ni™abin ko zai gane ki"""

"Ummi ta jinjina kai tana ™o™arin cirewa, aka yi sallama."

"Bayan matar farko ta biyun ma tayi, a nan take ummi ta daskare, ™irjinta ya buga da ™arfin gaske, ta ji tamkar"

"numfashin ta zai bar ™irjinta, wata irin tsuma ta ji ta fara yi, amma ta gaza motsawa."

"Malam ya ce ""Daga zuwa barka kun yi zamanku, gashi kun yi ba™i tafiyayyu daga kano"""

"Ta ce ""Baban ummi ne?"""

"Malam ya ce ""Eh shi ne, tun da shikaWai ki ka sani a kanon ba"""

"Shigowa suka yi tare, tana ri™e da mayafinta a hannu, hannunta kamar amarya an yi mata lalle yayi jawur."

"Ba ta kalli baban ummi ba, kai tsaye ummi ta zubawa ido, yayin da ummin ma ta zuba mata ido, tana jin yadda"

"™irjinta ke lugude. Gaba Waya suka zuba musu ido, kai tsaye ta nufi ummi ta zauna a gabanta, tana cigaba da kallon ummi ta ni™abinta."

"Ta mi™a hannu a hankali ta Waga ni™abin ummin, tayi tozali da fuskar ummin da a duniya bata ganin kyan komai,"

kamar yadda take ganin kyawun wannan fuskar.

"A gigice ummi ta yi mata wata irin runguma ta fashe da matsanancin kuka, saroro mariya tayi, ta kasa taSa ummi sai"

hawaye da ya fara zuba daga idonta.

"Mama ta mi™a hannu tana faWin ""Ki yi mata a hankali ba ta da cikakkiyar lafiya"""

"Mariya ta buge hannun maman da ™arfi, ta ru™un™ume ummi, tana wata irin ajiyar zuciya kamar za ta fita daga hayyacinta."

"Ta mi™a hannu ta warware mayafinta, ta lulluSe da ummi da shi, ta Waukko mafici kuma tana yi mata fifita tana kuka."

"Sai a yanzu suka gane wacece, malam ya sunkuyar da kai yana hawayen tausayin ´ar sa."

"Ya zura hannu a aljihunsa ya Waukko wayarsa, ya kira Maryam a waya da kuma yaya Wan lami."

"""Ummina, kina cin abinci kuwa? Naga duk kin rame, iya tana yi miki wanka? Ko dai zazzaSi ne a jikinki?"" Tayi"

maganar tana Wora hannu a goshin ummi.

"Wasu irin jijiyoyi suka WaWWaga a goshin ummi, wani irin ri™o take yi wa mariya, tana jin kamar an sanyata a wata"

ni'ima.

"Sun fi mintuna talatin a haka, sun ™i sakin juna, mariya sai kakkare ummi take yi, kar wani ya taSa mata ita."

"Dr. Yayi gyaran murya ya ce ""Yau na cika al™awari ko?"""

"Ta jinjina masa kai, tana kuka ta ce ""Wallahi ba zan taSa yafe wa iya ba, Allah ya saka mini zaluncin da ta yi mini, ta"

"™wace mini ummi bayan ba son ta take yi ba, ta ce ni na kashe mata Wa, kalli yadda duk ummi ta rame, haka zan kwanta in yi ta mafarkin ummi tana kuka, tana cewa na zo na tafi da ita"""

"Ta Wago ummi tana goge mata hawaye ta ce ""Ki daina kuka kin ji ummana, ba zan sake bari a mayar da ke wurin iya"

"ba, na san ba ta sonki ba ta ™aunarki, ban san me ki ka yi mata ba, wallahi ba zan yafe mata ba, yaya Wan lami ya™i dagewa ya karSo mini ´a ta, kullum sai na yi kuka saboda ummi, yaya maryam ma ta hantare rannan wai kamar nikaWai ce me ´a, ki daina kuka kin ji ummina, da kaina zan din ga yi miki wanka, ina baki abinci, katifata zata ishemu mu din ga kwana tare, ba zan sake bari a kai ki wurin iya ba kin ji mamana"""

"Ummi ta ™ura mata ido, yadda mama ke wannan surutan daga wannan zuwa wancan tare da kasa gane ummi ta"

"girma yanzu, ya tabbatar wa da ummi cewar mariya bata da lafiyr ™wa™walwa."

"Ta mi™a hannu ta Waukko ledar pure water, ta buWeta ta saka wa ummi a baki tana faWin ""Na san ™ishirwa ki ke ji"

"ummi, sha ruwa kin ji"""

"Babu wanda tausayin ummi da mariya bai kama a wurin ba, uwa kenan duk da ciwon ya motsa ba ta hayyacinta,"

"amma hakan bai hanata gane ´ar ta ba, duk da shekarun da suka shafe basu haWu ba."

"Dr. Yayi gyaran murya ya ce ""Alhamdilillah ala kulli halin, na gode Allah da ya sanya ummi da mahaifiyar ta suka"

"haWu, ba tare da ta Allah ta kasance ba. Ummi na yi miki laifi, kuma na yi muku duk da ina godiya da fahimta ta da ku ka yi."

"Ummi ban ™i sada ki da mahaifiyarki dan ba™anta miki ba, a lokacin da na ganota, tana cikin halin larura sosai, ba komai take ganewa ba, na yi fargabar haWuwarku ba za ta yi daWi ba, idan ku ka haWu ta kasa gane ki, abu na gaba kuma ina tsoron halin da ki ke ciki, ya sanya ki ™i zama ki dawo wurinta, alhalin kina tsaka da karatu, dan duk wanda yake ruwa, ko takobi aka mi™a masa zai kama, dan haka a matsin nan da ki ke, duk da kasancewar ki mai biyayya, zaki iya bujirewa ki zaSi dawo wa gaban mahaifiyarki, ba tare da kin yi acheiving wani abu ba."

"Wanda a lokacin babban burina da fatana, ki samu nagartaccen ilimi, da zaki iya tsayawa da ™afafuwanki, ina fatan zaki yafe mini daga ke har mahaifiyar ki"" yayi maganar a sanyaye."

"""Ai dama kai na yafe maka, baka cuceni ba, amma iya iya iya, ban san me na yi mata ba, amma za ta maimaita a"

"gaban Allah, amma wallahi ba zan yafe ba, na ji labarin azabtar mini da ummi ta yi, amma yaya Wan lami ka ™i dagewa ka karSo mini ummina"""

"Dr. Ya ce ""Haba maman ummi, ki yi ha™uri abun da ya wuce ai ya riga ya wuce, ki yi ha™uri dan Allah"" yayi maganar"

yana haWa hannayensa.

"""Ai kai na ce na yafe maka, tun da ka kawo mini ummi, kuma kana saya mini magani da abun da nake so, har yaya"

"Wan lami na yafe muku, amma ban da iya da wanda suka ci zalin ummina, bani da abun da zan gani na tuna da bashir sai ummi, amma ta ™wace mini ita dan ta wula™anta ni"""

"Dr. Ya ce ""Ba gani a gabanki kina kallona ba?"""

"""Yaya Yahaya ne fa ba Bashir ba, na gane ka yau"" yayi murmushi ya fahimci memoryn na ta yana yi yana seizing ne."

"Sun sha mamakin yadda ummi ta girma, ummi kuma kallon mamanta take yi, kamar ba ita ta haifeta ba, haryanzu"

"shar da ita, gashi gaba Waya ba sa kama, sai kaWan, kamar ya da ™anwa ba uwa da ´a ba."

"Dangin mama kamar su cinye ummi, a yamamcin nan suka din ga zaryar ganin ummi, sai dai ta Soye ummi a"

"bayanta, kowa ya zo sai dai ya hango ummi daga nesa wai kar a Wauketa a mayar da ita wurin Iya."

"Ummi ta ga ™auna da soyayya, mariya ta din ga zuba mata hira, wata tana ganewa, wata ba ta ganewa, ummi space"

"take son samu, ta kira raihan a waya ta sanar masa."

***

"Raihan yana zaune a falon hajiya Aisha yana kaWa ™afa, yana danna wayarsa cikin damuwa, ya kasa samun ummi a"

waya.

"Falon ta shigo cikin takunta na ™asaita, ta samu wuri ta zauna ta kalli raihan ta ce ""Kai, babanka ya kasa samunka a"

"waya, yana ta ´ar murya a lallaSoka ka koma fa"""

"Raihan ya gyara zamansa ya ce ""Wallahi ko dan saboda Alhaji ban so na taho ba, mami ce ta™i tsayawa ta fuskance"

"ni, na rasa yadda zan yi da ita wallahi, ta™i fahimta ta kuma anty rakiya ce take zigata"""

"""Kai dalla can, na kirata mun yi magana da ita, ba abun da za ta sake yi a kan maganar, ita ba a auren aka aureta? Mu"

"ba auren zumunci ake a danginmu ba, babanka shi ya fara karya mana wannan ta'adar, ya aurota daga nan kowa ya samu ´ancin yin hakan, sai yanzu ita kuma ta ce ba za a auro wata ba?"""

"Raihan ya ce ""Abun kuma har da gori?"""

"""Eh an yi mata gorin, da ai ba ayi ba, siyama na nemanka wai ka je ta girka maka menene oho mata"""

"Yayi murmushi ya ce ""Nifa yanzu abincin kowa ya daina yi mini daWi sai na matata"""

"""Ka ga fitsararre, amma dai da namun ka ke ci ko? Wai wani matarka ka ga idan ba ka rage rawar kan nan ba a kak"

"yarinyar nan, haka zaku yi ta faWa da babarka"""

"Raihan ya mi™e ya ce ""Ni kaina na sani, ina ™o™arin ragewa wallahi, amma hannun ummi akwai maggi ta iya girki"

"sosai"""

"Hajiya Aisha kawai ta yi murmushi ta girgiza kai, tana sake jinjina wautar mami, a irin wannan stage Win, ba a saka"

"pressure wurin cewa lallai sai an tan™wara namiji, sai nasiha da rarrashi idan ma so take ta soke auren."

"Da daddare mariya da kanta, ta gyara katifarta, ummi ta kwanta, ta kawo abun rufa ta lulluSe ummin, sannan ta"

rungumeta.

"Sai da ta tabattar da mariya tayi bacci, sannan ta tashi zaune ta kira wayar raihan."

"Aikuwa a take ya Waga ya ce ""Ina ki ka shiga ne? Tun safe nake kiran wayarki amma shiru"""

"Ummi ta ce ""Albishirinka"""

"""Goro fari ™al"""

"""Na haWu da mama"""

"Yana kwance ya tashi tsaye, ya ce ""Wace maman?"""

"""Mamana mahaifiya, ashe kawuna ya san in da take, wai dan kar in gudu in ™i zama na yi karatu ya sanya ya Soye"

"mini"""

"Adduoi na nuna godiya ga Allah ya din ga jerowa, yana hamdala can kuma ya ce ""Congratulations to both of us"

"ummi, dan wallahi da al'amarin nake kwana nake tashi, ina tunanin ta ina zamu fara nemanta, Alhamdilillah Ala mun gode wa Allah"""

"Tare suka din ga murna da raihan a waya, suka gama ta ajiye wayar, ta rungume maman tsam a jikinta, tana tuno irin"

"rabuwa da suka yi, da irin so da ™aunar da maman nata ta nuna mata."

"Bacci suka yi sosai da sosai, babban abun da ya burge ummi, ya ™ara sanyata nutsuwa, duk da rashin lafiyar da"

"maman take fama, tana yin salla, sai dai wasu lokutan akwai kura-kurai sosai a sallar ta ta, amma duk da haka tana kamantawa."

"A washegari kawu ya ce zai koma Kano, nan da sati biyu zai dawo ya tafi da ummi."

"Yaya maryam ta ce ""Dr. Ka tafi da ita kuma, kusan shekara goma sha takwas, ba sa tare kuma ace nan da sati biyu za"

"a zo a Wauketa a tausaya mana dan Allah"""

"Dr. Ya ce ""Eh ai ban gama maganar bane ba, abu na farko ummi tana aiki, in da take aikin kuma sun jin daWin zama"

"da ita, abu na gaba kuma an saka mata rana watanni huWu, kun ga za ta yi shirye-shirye ita da mijinta, daga kano ace ya din ga zuwa maiduguri yayi masa nisa, duk da dole zai zo ya gaisheku"""

"Anty maryam ta yashe baki tana faWin ""Masha Allah, Alhamdilillah"""

Malam ma ya din ga murmushi yana sanya albarka.

"""To amma, akwai Wan shirye-shiryenmu da muke yi wa yaranmu na aure, ai da an bar mana ita mun yi mata"""

"Dr. Ya ce ""Nan da watanni biyu zuwa uku sai ta dawo nan, ku yi duk shirye-shiryen ku a tsanake"""

"Yaya Wan lami ya ce ""Amma ba za a ™ara mana ko wata Waya ko biyu ya zama nan da wata shida ba, mu gama shirinmu mu ma"""

"""A'a kar ka damu, in sha Allah babu wani abu da zai gagara, manyan mutane ne, idan muka ce a ™ara zasu ga bamu kyauta ba, hakan ma in sha Allah babu abun da zai gagara"""

"Suka kammala tattaunawa, suna ta yi wa kawu godiya, ya kama hanya ya koma kano."

"Ummi taga gata da ™auna, babu kyara, babu hantara babu cin zarafi, duk ba a rasa wanda sukan yi maganar cewa"

"ummi ba ta kama da mariya, mariya ta fita kyau da haske, maryam ce ma a tsaye take faWan kar wanda ya sake yi musu wannan zancen."

"Ummi murmushi kawai tayi, dan da ta san abun da tayi going through, da wannan bai Waga mata hankali ba."

***

"A ka yi bikon raihan da ™yar ya koma kano, Alhaji sai tsokanarsa yake ""ni zaka yi wa yaji ko? Zamu gauraya da kai ne""."

"Hajiya ta ce ""Raihan ba a fushi da iyaye, nan gaba kar sake aikata abu makamancin haka"""

"Raihan ya ce ""Hajiya ba fushi na yi ba, na tafi ne dan na je na samu nutsuwar zuciya, amma in sha Allah hakan ba zai"

"sake faruwa ba"""

"Cikin tsananin fargaba ya tashi ya nufi sashin mami, ba addu'ar da bai karanta ba, saboda ya san dole ne zuwansa ya"

tarar da sabon Sacin rai.

"A bedroom Win ta ya tarar da ita a zaune, cikin ladabi ya dur™usa ya ce ""Mami barka da gida"""

"Maimakon ta amsa sai ta ™ure shi da ido, da har sai da ya fara tsarguwa."

"""Ai gara in ™are maka kallo, in tabattar da ni na haifeka kuwa? Ba matar ubanka ce kuwa ta haifeka ba ko har"

"ubanka? In haifi Wa a cikina ya janyo mini zagi da cin mutunci, raihan kana son gamawa da duniya lafiya kuwa? Ka sani sarai matar nan ba ™aunata take yi ba, ka je ka sameta ka kai ™ara ta ta kira ni ta ci mini mutunci"""

"""Wallahi mami ba ™ararki na kai ba"""

"""Yi mini shiru tun kan na fasa maka baki, ka kyauta ba dai wannan mummunar yarinyar ba ce ba, ka je gaka nan"

"gata, amma ka sani babu yawuna babu saka hannuna a aurenka raihan, kuma bayan ka aireta sai ka auri safiyya. Kuma ban lamunci ka yi mata kayan lefe ba, tun da bazawara ce, dubu Wari biyar Win ta isa komai da komai"""

"Cikin damuwa raihan ke ™o™arin yin magana, amma ta dakatar da shi, tare da bashi umarnin ya bar mata Waki."

"Kansa har wani sarawa yake yi, wai ita safiyyan nan dole sai ya aureta kamar wahayi? Baya son ta ba ya ™aunarta"

"amma an dage sai ya aureta, ga kuma wata magana, wai ba zai yi wa ummi kayan lefe ba, to iyayenta ne zasu saya mata sutura da kayan kwalliyar da za ta yi masa a gidansa? Kuma a wannan marrar nawa dubu Wari biyar take, da har za ta isa ayi wa ummi kayan lefe, nauyin ai sai ya yi wa iyayenta yawa, shi abun kunya ne ma a gare shi ace bai yi wa ummi kayan lefe ba. Haka yayi ta wasi-wasi yana nazarin abun a ransa."

"Farida ba ta damu da in da ummi take ba, sai dai tana tambayar dr. Tana fatan ummi ta tafi kenan, amma yayi mata"

banza ya ™yale ta.

"Noor kuwa sai bin sa take tana tambayar sa, wai yaushe ummi za ta dawo, ita fa gidan babu daWi idan ummi ba ta nan, ya ce mata zata dawo nan ba da daWewa ba."

"Ummi a gabanta aka fara haWa kayan turarukan wutanta, wai akwai turarukan da sun fi shekara a binne a ™asa ana"

tsuma su.

"Yaya maryam ta kasa zama, kullum tana yawon kasuwa ita da mama, matar malam wurin yi wa ummi sayayyar kayan aure."

"Ita babban abun da yafi faranta mata, bai wuce kasancewar ta da babarta ba."

"Mami ta ™ara matsanta wa raihan, ga gefe guda kuma, Safiyya sai ta wani kira shi wai za ta gaishe shi, duk rashin son"

"wula™anta Wan Adam irin na raihan, ™arshe sai da yayi blocking Win ta, dan ta daina damunsa da kira."

"Ya cewa ummi zai zo Maiduguri ya ganta, ya kuma gaida mama, amma gudun matsala ya sanya ta ce masa ya bari ta"

kusa dawowa.

***

"Sai da ummi tayi sati uku cif, sannan dr. Ya koma Waukar ta, kamar ta ce masa dan Allah ya barta a nan, amma sai ta ji nauyin hakan ta kasa, kayanta ™waya biyu da ta je da su, sai da aka Winka mata kusan kala goma a can, kuma tuni suka haWa kayan gyaran jiki masu haWe da turarrruka, ummi ta fara amfani da shi."

"Yaya maryam sai jaddada mata take yi, kar ta yi wasa da kayan gyaran da aka ba ta ta yi, da sabulan da aka haWa"

mata.

"Mariya ta kalli dr. Ta ce ""Ka yi mini al™awarin ba wurin Iya zaka mayar da ita ba?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Ai aronta na ce ki bani, ba zan kai miki ita wurin Iya ba"""

"""To ai zaka dawo da ita ko?"""

"""In sha Allah"""

"""To dan Allah ka kula mini da ita sosai da sosai, kar ka bari ta yi kuka"""

"""In sha Allah zan kula da ita sosai da sosai"""

"Ta kalli ummi ta ce ""Kar ki yi musu kuka kin ji ummi, ban da ™yuya da kuka, ba ruwanki da yara, kar ki je su din ga"

"dukanki kin ji ko?"""

"Ummi ta ri™e hannunta ta ce ""To mamana, me ki ke so na taho miki da shi idan zan dawo?"""

"Ta Wan yi jimm sannan ta ce ""Bakomai, ni dai kawai ki dawo, ba dan ina jin kunyar kawu yahaya ba, ba zan bashi ke"

"ba"""

Ummi ta cigaba da kallon mariya tana jin daWi.

Da ™yar suka rabu suka nufo hanyar Kano.

"Duk rashin surutun ummi, haka ta sake ta din ga yi wa kawu hira tana bawa kawun labarin mamanta."

"Bayan azahar suka sauka a kano, noor kamar ta mayar da ummi cikin ta, dan murnar ta dawo."

"Ummi ta shiga har falo, ta ce wa farida sun dawo, ta amsa mata a yatsune, sai dai fuskar inteesar kawai ta kalla ta"

san matsala ce ta kawota gida.

"Ummi ta koma Wakinta, suka din ga hira ita da noor tana bawa noor labarin mamanta."

"Noor ta ce ""Kuma ki ka yadda ki ka dawo, wallaahi idan ni ce ba zan dawo ba, amma na san saboda yaya raihan ki ka"

"dawo ko?"""

"Ummi ta ce ""Ban sani ba"""

"Suka din ga dariya, noor ta ce ""In gaya miki, Inteesar mijinta ya Wauki amaryarsa sun tafi umara, shi ne take kuka wai ba a tafi da ita ba"""

"""To waye ya tambaye ki?"""

Noor tayi shiru tana ™ifta idanu.

"Haka nan take murna, ta san yau za ta ga raihan, ta rasa dalilin da ya sanya take murna."

Haka nan ta samu kanta da yin shirin haWuwa da shi.

"Ta Wauki kayan tsaraba da ta zo da su, har da su kayan turaren wuta ta kai wa farida, ta karSe ba tare da godiya ba."

"Bayan sallar magariba ummi ta saka rigar atamfa bubu, tana ta fama ta Waura Wankwali, abu ya gagara saboda ba ta"

"saba ba, ™arshe noor ce ta Waura mata da ™yar, shima gashin ya ™i rufuwa, sai da ta saka hula sannan aka Waura Wan kwalin."

"Ta yafa mayafi, tana ta rufe-rufe tana tunanin anya za ta iya fita a haka? Kiran wayarsa ta gani, ta tashi ta kalli noor ta"

"ce ""Anya in fita a haka kuwa?"""

"""Wallahi kin yi kyau, kin rufe ko ina kuma"""

"Da ™yar ummi ta iya fita, tana ta kare jikinta, ta ™arasa in da yake."

"""Oyoyo sweetheart, long time"""

"Tayi murmushi ta zauna, tana kawar da kanta gefe."

"""Congratulations once again, ya ki ka baro mini maman?"""

"Ummi ta yi murmushi ta ce ""Tana lafiya ™alau"""

"""Kin bata labarina kuwa?"""

"Ummi ta ce ""Idan na yi mata babu lallai ta gane ma"""

"Ya ce ""Ba ki yi niyya ba dai, zan je da kaina mu gaisa ai"""

"""Ka gama yajin?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Ke ma haka zaki ce?"""

"Ummi ta ce ""To ba yajin ka yi ba, ko kunya ba ka ji ba?"" Yayi dariya ya ce ""Na samu mafita ai, kin yi kyau sosai da"

"sosai wallahi, Allah ya nuna mana ranar nan lafiya babyna"" ummi ta yi shiru tana sunkuyar da kanta."

"Kausar ce ta nufo in da suke zaune, dan haka yayi shiru yana kallon ta."

"Cikin mamaki take kallon raihan, yanzu wannan ne zai auri ummi? Wannan yaron, amma kuwa tayi asara, ko kuma"

shi yayi asarar kyakykyawan matashi kamar wannan ya auri ummi. Ta yi maganar a zuciyarta

"Cikin gadara ta ce ""Ke ki zo maama tana kiranki, wa ki ka barwa yin abincin daren da haryanzu baki Wora ba,"" tayi"

maganar cike da son wula™anta ummi a gaban raihan.

"Raihan ya ce ""Tana magana da mijinta ne, idan kun matsu ku ci, ku dafa, tana bu™atar hutu, tun da yau ta dawo daga"

"tafiya, kuma ina bu™atar yin magana da ita"""

"Zare ido ummi tayi ta ce ""Na shiga uku, raihan"""

"""Shhh"" ya Wora yatsansa a kan lips Win sa yana zare mata ido."

"Ya sake kallon kausar ya ce ""Ki koma ki ce ba za ta yi ba"""

Ayshercool

8081012143.

*CUTARWA*

*BRIGHT PENS*

(FREE BATCH)

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

34

"MASU BU˜ATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ŠINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO"

IN SHA ALLAH.

Follow the COOL HAUSA

Please Login or Register in order to submit comment