You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta, duk ma wanda yake da hannu akai wallahi ba zan kyale shi ba, idan akwai abu da ake bukata call me please.”

“Ok, best of luck Kanina, babu labarin Hajiya?”

“Babu, and I don’t care tana Ina ma yanzu, I hope ko a ina take tana cikin bakar wahala.”

“Amin, Allah yasa.”

“Bari naje, call me please.”

“Khadija fa?”

“Bata ma san ma shigo ba, zan kirata idan na natsu.”

“Ok, sai ka dawo.”

Bayan kamar minti talatin aka dawo dashi dakin nasa, lokacin ammy da Dadah sun je gida saboda kan Ammyn dake mata ciwo, Ya nabeela ce sai khadija da tazo bayan Kamal ya kirata ya fada mata, akwai matar Kanin Daddy dai da tazo duba shi ta kawo abincj bata ma jira an fito dashi ba ta tafi, su kuwa dama dangin maman su ba damuwa sukayi da sabgar su ba dan babu ruwan su dasu. Shiga dakin sukayi suka zauna tare da Raihanan duk sukayi jigum har kusan azahar sannan ya fara motsawa yana son farkawa. Kansa Ya nabeela ta tsaya tana dan kiran sunan sa a hankali wanda yake jin kiran a chan cikin kansa da karfin gaske. Yanayin yadda yake motsawar kana gani ba na dade bane ba, yasa Raihanan fita da sauri ta kira nurse din, ita kuma taje ta kira Dr ahmad suka shigo a tare, fita sukayi suka rufo musu kofar hankali a tashe dan yanayin sa ya tsorata su sosai, kusan mintuna biyar sai ga Dr Mahfouz shima yazo ya shiga ciki, sai chan kuma suka fito ya karasa wajen su Ya nabeelan

“Yana fama da severe headache ne wanda dama munyi tunanin zaa iya samun hakan, amma in sha Allah ba wata babbar matsala bace ba, amma dole sai da mukayi masa allurar baccin domin yana da bukatar ya cigaba da baccin dan tashin nasa zai iya zamar masa matsala musamman ciwon kan nasa.”

“Zai samu sauki ko Dr?”

“Kwarai kuwa, zai samu in sha Allah, Kiyi masa addua.”

“Me scan din yace Dr.”

“Babu wani abu aside ciwon kan nan gaskia, wanda yake da wahalar wa sosai musamman dama ciwon sa ne, but for better result muna tunanin yin MRI.”

“Ok, mun gode Dr.”

“Ba damuwa, madam karki damu fa, ango zai samu lafiya”

Kasa raihana tayi da kanta ya wuce yana murmushi. Baba ne yazo, Baban Kamal tare da matarsa da kannen sa su biyu daga rano, ciki aka shigar dasu suka duba Aryan din sannan suka dawo wajen.


****Daga chan Office din nasu main house din suka wuce tare da yaran sa su biyu, da normal police masu black uniform,wajen da abun ya faru suka dudduba sannan sukayi ma gateman tambayoyi ya amsa sannan suka wuce wajen gyaran wayar da suka bayar domin wayar da ta fadi ta dauke dan haka taki kunnnuwa, akwai yaron da yake musu irin wannan aikin dan haka da kansa Kamal yaje wajen ya karba sannan suka sakè komawa Office aka saka wayar a computer suka dauke komai na cikin ta har call log sannan suka bar wayar a kunne suna monitoring call din da zai shigo ko text message. Call log din Kamal ya shiga yana duba numbers din da akayi kiran da wadda sukayi magana last wadda itace number da aka fi kira a ranar gaba daya. Tura number yayj ya bada umarnin a duba masa me number, da adress da komai. Within 5min aka turo masa komai akan contact din. Tashi yayi yana kallon number da Address din cikin tsananin mamaki, tunani ko hasashen sa be taba kawo mishi ba, dan haka ne ma sai da ya sake dubawa sosai ya tabbatar da hakan ne babu mistake. Cikin shigar da suke idan zasu fita operation suka fita, zuciyar sa na faman wani irin tafasa yana jin kamar ya bude chest dinsa ta ya zare ta ya huta da tsananin bacin ran da yake ciki.



*
*RUMBUN QAYA🔥

*DAUDAR GORA*🔥

*IDON NERA*🔥

*A RUBUCE TAKE*🔥

*KI KULANI*🔥

*_uhmmmm_*😊😊😊😊😊😊😊😊😊😊

*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*

*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*

*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*☺️☺️

*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*

*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*

*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥

0022419171
Maryam sani
Access bank

*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+227 90 16 59 91

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*

*Thanks for choosing us*🔥

**RQ**

Page 66

***A daidai kofar gidan motar tasu ta tsaya, yaran suke sauka da sauri suka shiga gidan.

“Lafiya?” Matar tace da sauri tana kallon su.

“Ina Zainab??”

“Zainab? Bata nan ta fita wajen aiki.”

“Ok, zamuyi searching gidan.”

“Akn me? Me tayi muku?”

Id card dinsa ya zaro ya nuna mata, sannan suka shiga duba gidan suka tabbatar bata nan, suka fito suka samu Kamal yana tsaye ya bada bayan sa

“Tana Office sir.”

“Ok, muje.”

Suka shiga motar suka dauki hanyar Office din.

Tana tsaye tare dashi a compound din company suna magana kasa-kasa, a tunanin su sun samu abinda suke sun gama duk da kasan zuciyar ta na nadamar biye masa da amsar tayin sa da tayi, wanda Adam ya dade yana binta akan ta amince amma taki, sai gashi jiya ta yarda ta amsa wa wanda bata sanshi ba, bata taba sanin sa ma a rayuwar ta ba sai da abu iri daya ya hada su, suka yi taraiya wajen cimma burin su.
Shigowar motar dss din da yadda tayi parking a gaban su ya saka su niyyar fita a Dari, sai dai kafin su farga har sun d’uro sun saka su a tsakiya cikin wani yanayi. Kamal din ne karshen sakkowa ya kalle ta a matukar bacin rai yana kallon wanda suke taren da dama chan hasashen sa ya zama gaskia bayan ya samu waya daga Office din su akan an kama yaran da suka yi aika aikar har ma sun ambaci sunan mutane biyu. Zainab da Muhammad

“Arrest them !”

Kafin ya rufe baki an damke su, aka kuma tura su a motar da ta kasance baka kirin sannan suka fice daga cikin wajen da duk ma’aikatan suka firfito kallon abinda yake faruwa.

***** Ita kadai ce a dakin ta idar da sallar la’asar tana zaune akan sallaya tana azkar taga ya dan motsa kadan, mikewa tayi da sauri domin tana tsoron yayi irin abinda yayi dazu, cigaba da motsin yayi a hankali har zuwa sauran sassan jikin nasa sai dai idanun sa har lokacin a rufe suke. Tana tsaye a kansa tana tofa masa Addua ya cigaba da rage yadda yake matse fuskar zuwa kan a hankali ya dinga bude idanun sa har ya bude su tas a kanta, yadda ta rankwafo a kansa ya bashi damar ganin ta sosai ya kurawa bakin ta dake karanta adduar a hankali ido kafin ya shiga nazarin abinda yake faruwa dashi. Da sauri ya kai hannun sa Ya rike kan da yaji ya sara masa yace

“Ouch!”

“Sannu, Kan yana maka ciwo sosai? Na kira Dr?”

Ta mike yayi saurin riko ta da hannun da babu cannula

“Me nake yi anan?”

Yace muryar sa chan ciki

“Bigewa kayi, bari na kira Dr Mahfouz.”

“Um um karki tafi pleaseee.”

Yace yana yin kalar tausayi, Sai ta tsaya tana kallon sa

“Kiran sa zanyi nace ka farka.”

“Zauna.”

Ya nuna mata gefen sa, a kujerar ta zauna ya juyo da kansa a hankali yana kallon ta

“Tell me, menene ya same ni? I can’t remember anything.”

“Wasu bata gari ne suka kwala maka karfe akan ka, anan.”

Ta nuna wajen ciwon, hannu ya kai wajen da sauri yace

“Ouchhhh.”

Da sauri ta rike hannun nasa

“Da ciwo? Sannu.”

Duk ta rikice, kasa yayi da idon sa yana kallon yadda ta damu sosai, sai yaga ma kamar har ramewa tayi.

“Naje na kira shi?”

“Umm kira shi.”

Yace ganin yadda ta damu sosai, fita tayi yabi bayanta da kallo, sai kuma ya dora hannu a wajen ciwon ya sake tabawa a hankali yana tuna abinda ya faru a ranar.
Dr Mahfouz ne suka shigo tare da wani Nurse namiji, yana ganin shi ya soma dariya

“Ah lallai amarya ta iya kula, banyi expecting ganin ka haka ba.”

“Lallai kam.”

“Ya kan? Akwai wata Matsala ko wani yanayi da kake ji?”

“Akwai, kan yayi nauyi sosai sannan yana ciwo.”

“Dole ne wannan, sai a hankali.”

“Ok.”

“Bashi drugs din Abba,bari nayi ma madam magana a samu abinci a baka kaci, zaka kara samun energy zuwa dare in sha Allahu.”

“Kwana nawa nayi anan?”

“Kwana daya ne”

“Ok, zan iya rama sallolin da suka tsere min ko?”

“Yes zaka iya, ko a yadda kake ma a kwancen, idan kuma zaka iya zama ne toh, but banda a tsaye cox ba’a so ka bawa kan wahala.”

“Ok thank you.”

“You are welcome.”

Ya Nabeela ce suka shigo tare da Khadija, farin ciki fal fuskar Ya nabeela ta karaso gaban sa tana murmushi

“Alhamdulillah kanina.”

“Ya nabee kin ganki kuwa?kuka kikayi?”

“Menene ma ba zan yi ba? Na damu sosai.”

“Kin zata tafiya zan yi ko?”

“Silly boy, bana son wannan maganar, ya jikin naka?”

“Na samu sauki ai, baki ga alama ba?”

“Nasan dai karfin halin ka, da iya pretending dinka,Allah ya kara sauki.”

“Ya jikin Allah ya kara sauki.” Khadija tace

“Da sauki, thank you matar Yaya.”

“Mu shigo?”

Dr Farouk tare da su Amna yace bayan sun turo kofar

“Ashe kuna kusa ma, kace baku fito ba.”

“Tsokanar ki muke, kanina. Sannu ya jikin?”

“Alhamdulillah, da sauki.”

“Allah ya kara sauki.”

“Me Raihana take a waje ne?”

Ya nabeela tace tana kallon khadija bayan ta gaida Dr Farouk din

“Na ganta kuwa a zaune, kun zo kun cika dakin ku bar mutum da matar sa.”

“Kunya ce da ita kasan, zuwa zamuyi mu fita mu bar su, kanina muna falon sai anjima zamu wuce.”

“Ok.”

Ya juyar da kansa gefe. Fita sukayi Ya nabeela tace Raihana ta shiga ta zauna da shi ko zai bukaci wani abu. Duk a kunyace take haka ta koma ciki da sallamar ta, be juyo ba ta zauna a kujerar, kan nasa ne yake masa wani irin ciwo shiyasa yaki juyowa kar ta ga halin da yake ciki. Sai da ya dan lafa masa sannan ya juyo suka hada ido

“Zanyi sallah.”

“Tom, ko zaka fara cin abinci?”

“Um um, zan fara sallar.”

“Jikin ka yayi weak, ka fara cin abincin please sai kayi sallar.”

“Ok, bani kadan.”

Kadan ta zubo masa bayan ta zuba masa fav tea dinsa ta kawo masa ya fara shan shayin saboda cikin sa ya dan warware sannan yaci abincin kadan yace ya koshi. Toilet din ta shiga ta dauko wani dan karamin bawo ta zubo ruwan a bucket ta kawo dakin dan ko da ya yunkura zai tashi jiri ne ya kwashe sh, taimaka masa tayi yayi alwalar daga zaunen yayi dukka sallolin dake kansa sannan ya koma ya kwanta ta gyara masa pillow. Gefen sa ya nuna mata, ta zauna ba musu ta zauna ya dawo da kansa saman cinyar ta sannan ya hade hannun su waje daya ya rufe idon sa yana jin kamar ana tsira masa allura akan nasa.

***Bayan isha su Ya nabeela suka musu sallama suka tafi, suka biya suka ajiye khadija dan kamal yace zai yi dare. Bacci Aryan din yake raihanan na kusa dashi dan hanata tashi yayi ko da su Ya nabeelan suka shigo sallama tana kusa dashi knsa na kan kafarta kuma ko motsawa be yi ba bare ya bata damar tashi.
Kayayyakin da ke ajiye a dakin ta gama gyarawa ta dan tattare wajen duk da babu datti an zo anyi sharar yamma amma kuma tana bukatar taga wajen neat, Hamma Hydar ya dawo da yamma yayi musu sallama shi da Babbo sadeeq saboda zasu koma wajen aiki Abby dai yana nan da Dadah da Ammy saboda zuwa wajen malam sannan sun fara neman gidan da zasu zauna zuwa a gama maganin saboda ba zai yiwu suyi ta zaman gidan adda maimuna ba, gidan Aryan kuwa dama tun a ranar suka kwashe kayan su.
Tana zaune jigum ita kadai tana dan duba wayar ta akayi knocking a kofar ta zata ma Dr ne ta dan gyara mayafin ta da ya dan yi baya sannan tace a shigo. Kamal ne, waya yake amsawa ,shigowar ya saka shi katse wayar yayi sallama ta amsa ya yi mata murmushi

“Sannu da zuwa.”

“Yawwa, sannu ya mai jikin?”

Yace yana karasawa wajen gadon yaja kujerar ya zauna

“Da sauki.”

“Sai Yanzu zaka zo ka ganni?”

Aryan yace yana bude idon sa

“Ashe kana jin mu.”

“Maganar kace ta tashi ni.”

“Nazo dazu kana bacci, sai na wuce Office.”

“Agogo sarkin Aiki.”

“Aikin dole ne, ya jikin naka?”

“Da sauki, as you can see.”

“Allah ya kara sauki.”

“Me kayi a Office din?”

“Arresting suspects din da suka yi maka wannan illar?”

“Are you for real!?”

“Ka zata wasa nake? I’m serious Yanzu haka suna hannu, dan ma yanzu ba anan nake ba, but nayi handing over case din wajen wanda nasan bazai musu ta dadi ba.”

“Lallai, kayi kokari.”

“Ba zaka tambayi su waye ba?”

“Mts! Na gaji ne kawai, ko ma waye dai ba shikenan ba? I’m alive wannan kadai Ya isa.”

“Be isa ba, ran ka suka nema, idan kuma da abun yazo da tsautsayi fa?”

“Be ma zo ba.”

“Still dai, you have to be very careful, Yanzu ba kai kadai bane ba, bamu sani ba ma ko akwai unborn nan tafe.”

Da sauri ya kalli raihana, tayi maza ta kauda kanta, murmushi yayi kawai

“Nayi mamaki matuka da na ga wadanda suka saka yaran,

“Su waye?”

“Muhammad da zainab.”

“Muhammad? Zainab?”

Ya maimaita sunan yana son tuno su waye ma haka?

“Zainab ta Office suka hada kai da Muhammad, cousin din Raihana.” Yayi kasa da murya da zai fadi cousin din, da sauri raihana ta dago dan taji, suka hada ido da Aryan din da Shima ita ya kalla don be so taji ba, amma yanayin ta ya nuna ta jin.



.

*
*RUMBUN QAYA🔥

*DAUDAR GORA*🔥

*IDON NERA*🔥

*A RUBUCE TAKE*🔥

*KI KULANI*🔥

*_uhmmmm_*😊😊😊😊😊😊😊😊😊😊

*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*

*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*

*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*☺️☺️

*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*

*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*

*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥

0022419171
Maryam sani
Access bank

*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+227 90 16 59 91

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*

*Thanks for choosing us*🔥

**RQ**


*67*


“Hamma Muhammad?” Tace tana zaro ido

“Yes Raihana, shi da Zainab. Ba shi kadai ba.”

“Innalillah.” Tace a kidime, dan bata taba kawo Hamma Muhammad da irin wannan halin ba.

“It’s ok, ba komai.” Aryan yace ganin yadda raihanan ta rude

“It’s not,dole sai an musu hukunci daidai dasu, kuma ba wai a hannuna ma case din yake ba, dan haka kar ma kace komai.” Kamal yace yana mikewa daga zaunen. Dr Mahfouz ne ya shigo aryan din na shirin yin magana

“Ashe ka shigo.”

“Na shigo Dr, Barka da dare.”

Ya mika masa hannu.

“Barka dai, Aiki?”

“Alhamdulillah, ya akaji da patient?”

“Baka ga patient din nawa bane ba? Kamar bashi ba da yake madam tana kusa.”

“Na gani fa, Shiyasa Nima zan yi nawa waje tawa madam din nima tana jirana.”

“Ah ya kamata.” Ya fada suka saka dariya, murmushi kawai Aryan yayi hankalin sa na kan raihana da ta nuna kamar ma bata jin abin da suke cewa.

“Akwai security sosai a asibitin nan ko?”

“Ba laifi gaskia, wani abun ne?”

“No ba komai.”

“Ya jikin naka?”

“Alhamdulillah, please ka cire min drip din nan ya ishe ni wallhi.”

“Yayi half ai, bari mu cire ka huta zuwa safiya sai a maidashi.”

“Ba za’a hakura ba?”

“Ai kana bukatar shi.”

“Ok, zan iya wanka?”

“Yes of course, zaka iya sosai, in dai kana jin karfin jikij naka zaka iya tashi, but sai ka kula wajen kan kar ka jika shi...”

“Ko da yake, ga amarya ma she can help you.” Ya karashe yana dariya. Taji wannan dai, amma sai ta fuske tayi kamar bata ji ba, ta hau dudduba abubuwan cikin ledar gabanta.

“Shikenan, idan akwai wani abu just call the nurses, sai da safe.”

“Ok, sai da safe.” Aryan yace

“Let me walk you to the door.” Kamal yace suka jera tare, dan dama akwai maganar da yake son tambayar sa amma baya so yayi a gaban aryan din. Suna fita yace

“Come here.”

Ta kowa tayi zuwa gabansa, nauyi da kunyar abinda Muhd yayi ya hanata kallon sa. Ya sani sarai abun sai ya dameta, shi kuma ko kadan be ji komai ba, domin a yanzu baya jin akwai wani abu da zai faru dashi da zai bashi mamaki, komai aka ce mutum zai aikata toh fa zai aikata shi ne.
Yunkurawa yayi ya zauna ta gyara masa pillow ya jingina sosai, sannan yace ta zauna a kusa dashi akan gadon, zama tayi ya dora kanta a saman kafadarshi yace

“Kar kiji komai akan abinda Kamal yace, babu wani new abu a wajena akan halin mutanen duniyar nan, kowa zai iya komai akan selfish interest dinsa, so ki manta komai kinji? So nake mu manta da komai da kowa mu fara sabuwar rayuwar mu, away from everything.”

“Duniyar nan kamar rumbu ne da kayan abinci, sai dai an cika shi da kayoyi wanda zaka sha wuya kafin ka kai kasan har ka mori wannan kayan, duk in da kasa kafarka k’aya ce zata soke ka..”

“Haka ne.” Tace a sanyaye tana jan kukan da yake ta neman cin karfinta

“So ki daina damuwa, na daina nima from the moment da nasan ina dake, I have someone in my life that needs me, tun daga lokacin na watsar da komai.”

“Yanzu ya kake ji? Kan ya daina ciwo.”

“Alhamdulillah. But it feels so heavy, kamar an dora wani babban dutse akan”

“Sannu, Allah ya kara sauki.”

“Amin. Zaki taimaka min? Nayi wankan?”

“Um.” Ta gid’a kanta.

“Thank you.” Yace yana murmushi

Tashi tayi ta sauka daga gadon ta nufi toilet din. Wayar sa ce tayi yar kara kdan saboda baya son karar.

“Na wuce sai da safe.” Kamal yace yana dagawa

“Ok, night.” Ya kashe ya ajiye, sai ma ya kashe ta gaba daya ya sakata kasan pillow.

Ruwan ta hada me dan dumi sannan ta fito

“Saka key a kofar kamal ba zai dawo ba.”

“Ok.” Tace ta je ta saka key din sannan ta dawo. Da hannu ya nuna mata botir din rigar, ta matso ta taimaka masa ta bude su sannan ta zare masa rigar.

“Thank you.”

“Zaki ya sauka.”

“Um um ba zan iya ba.”

Yace mata a shagwabe ta kalle shi da sauri ya sake marairace fuska, hannun sa ta rike ta taimaka masa ya sakko a hankali, suka nufi toilet din yana dan cijewa saboda kan nasa da yayi masa kamar zai fado. A toilet din ma kin yi komai yayi, komai tace sai yace ba zai iya ba, haka da daure ta cije tana gogocewa daga kallon sa yana kokarin sakata dole sai ta kalle shin, haka aka gama suke fito yace ta kashe ac dakin saboda ji yayi yana jin sanyi, da sauri ta kashe ta bashi duvet ya rufa, ya dan dauki some minutes sannan ya dawo daidai, ya saka wasu kayan sannan ya zauna akan carpet din yayi sallah a zaune. Yana sallar ta koma toilet din ta gyara shi sannan tayo alwalar tazo ta dauki doguwar rigarta ta saka ta cire na jikinta da suke jike ta kai toilet din, duk in da tayi yana kallon ta har tazo tayi sallar a gefen sa ta idar. Matsowa yayi ya dora knsa a saman cinyar ta, ya rufe idon sa yana jin babu dadi jikin sa.
Sun dade a haka shiru babu wanda yayi magana, kowa da abinda yake tunani, ta kasa cire abinda ya farun a ranta, ya adda maimuna zata ji idan taji abun da ya faru? Kowa yasan Dss basu dagawa kowa kafa dan haka tasan dole zasu sha wahala sosai, bata tausaya masa ba ko kadan, saboda abinda yayi ma Aryan din ya chanchanci hukunci me tsauri.

“Tunanin me kike?”

Yace yana kallon fuskar ta yana daga kwancen, ya dan dade da bude idon sa yaga tana tunani.

“Emm, ba komai.”

“Menene date din yau?”

“30th.”

“Yaushe zaki je clearance?”

“On 2nd.”

“Ok Allah ya kaimu.”

“Amin ya Allah.”

“Abinci?”

“Umm, zanci kadan.”

“Ok.” Kallon kansa tayi, yaji dadin kwanciyar bata so tace ya tashi,

“Na tashi ko?”

“Un.” Tace tana murmushi

“Dan kara ko 5min ne sai ki bani abinci.”

“Toh.” Tace ta zauna suka sakè yin shiru, yana rike da hannun ta daya yana wasa dashi, sai da aka kusan mintuna biyar din sannan ya tashi a hankali ya jingina da kujarar ta tashi ta je ta zuba masa abincin tazo ta zauna a gabansa ta tankwashe kafarta ta shiga bashi abincin a hankali. Yaci sosai har tayi mamaki, sannan ta kwashe plate din ta je ta ajiye ta dawo tace ya koma gadon.

“Um um, nan ya ishe mu. Bani pillow kiga.”

“A kasa?”

“Um, carpet din ai yana da girma, kuma yana da laushi.”

“A ah ni dai, please ka koma saman, ba zaka ji dadin kwanciya anan ba.”

“Kiyi hakuri ki barni anan,pleasee.”

Tsayawa tayi shiru, bashi da alamar tasowar

“Miko min pillow din kizo mu kwanta.”

Zuwa tayi ta dauko ta kawo masa, ya kwanta a hankali sannan ya mika mata hannu, ta tako ta zauna a gefen sa tana jin kamar be kamata ya kwanta a kasan ba.

“Oya kwanta.” Yace yana kulle idon sa. Hijab din jikinta da tayi sallah ta zare ta dora a saman kujerar sannan ta kwanta a gefensa, hannu ya saka ya matso da ita sosai jikinsa ya maida idon sa ya rufe saboda baya son buden idon sosai.
Cikin bacci taji alamun yana ta jujjuya wa, bude idon ta, tayi da yayi mata nauyi saboda baccin dake kanta ta kalle shi sai taga ya hada zufa sosai ya rike kan yana jujjuya shi.

“Subhanallahi, ciwo yake yi? Sannu.”

Ta tashi da sauri tana rike shi.

“Kai na zai cire Raihanaa.”

“Ba zai cire ba, bari na kira su, sannu, ba zai cire ba.”

Ta ce tana mikewa da sauri har ta soma kuka.

“No Karki kirasu, bani maganin a cikin drawer din chan, nasha.” Ya fada da kyar. Wajen su drawer ta yi da sauri ta dauko maganin, ta dauko ruwa ta kawo masa ta ballo ta bashi yasha, still yana rike da kan nasa. Tana durkushe a gaban sa har ya soma lafawa a hankali yana fitar da gumi sosai.

“Kana jin zafi ne?”

Da ido ya amsa mata ta karo ac ta dawo gabansa ta durkusa tana jera masa sannu. Bayan ya lafa gaba daya ta taimaka masa ya koma gadon ta dan rufa masa duvet a kafarsa zuwa cinyar sa, bacci ya dauke shi nan take. Haka suka karasa daren wajen shida na safe nurse din da zata tafi ta shigo ta duba shi ta mayar masa da drip din sannan tace idan ya tashi ga maganin da zai sha sannan ta fita. Sallah tayi dan ta dan makara sannan ta gyara dakin dan kafin masu sharar su zo ta share idan suka zo moping kawai suke su wanke toilet.

***Gaba daya hankalin Adda Maimuna da na abban su Aminan Ya tashi matuka, musamman da suka samu labarin tafiya da Muhd din a bakin wani abokin sa da suke a tare a lokacin yana daga gefe sai dai shi, duk kiran da zasuyi sunyi amma shiru baa san su waye suka tafi dasu ba. Yanke shawarar sanar da Ammy sukayi da Dadah a kalla idan aka sanar da Lamido zai iya yin wani kokarin tunda an ce SS ne suka dauke shi.
Tun jiyan jikin ammyn ba wani dadi sosai shiyasa ko fitowa batayi daga dakin ba, tana kwance kawai dama karfin hali ne kawai amma tana jin jiki ba laifi. Dakin da suke kwana Adda Maimunan ta shigo jiki a mace ta zauna ta gaida Dadah sannan ta duba jikin ammyn.

“Ya akayi Maimunatu? Na ganki haka jiki a mace.”

“Wallahi Dadah, wai muhd ne jiya Wasu da ake zargin yan sanda ne na farin kaya suka zo suka tafi dashi, toh tun jiyan muke saurare amma shiru gashi har an kwana.”

“Innalillah, yaushe? Me yayi musu?”

“Wallhi Dadah muma bamu sani ba.”

“Kai Subhanallahi, toh! Allah yasa ba wani babban abun bane ba.”

Ammy tace tana mikewa daga kwanciyar da tayi

“Toh Allah yasa, amma su DSS ai basa kwansu sai da zakara, dole akwai dalili, amma

Please Login or Register in order to submit comment