You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya dawo ciki ya tsaya daga saitin kafafun Daddyn yace

"Yau aka fara shari'ar Hajiya Zeenat, an dage sauraron karar zuwa sati biyu, ina fatan ban yi laifi ba, ina kuma fatan zaka saka min albarka sannan kayi min fatan nasara."

"Allah ya taimaka ya baka sa'a, ina jiran bincike yazo kaina, domin nima me laifi ne Aryan, nayi muku laifi ku da mahaifiyar ku."

Kin kallon sa Aryan yayi dan yadda zuciyar sa ta karye da maganganun Daddyn zai iya fashewa da kuka, amma baya so ko kad'an yaji d'ar wajen tabbatar da gaskiya,duk da deep down baya fatan wani abu ya shafi Daddyn amma kuma ya zai yi? Idan har kotu ta kama shi da laifi dole ta hukuntashi daidai da laifin da ya aikata.

_*RQ*_
      

           Page 34

_*©®HRano*_
 
***Turo kofar akayi aka shigo, Adam ne ya karaso da sauri ganin idon Daddyn a bud'e, kujerar da Aryan ya tashi daga kai ya zauna yana kallon Daddyn cike da farin ciki. Juyawa Aryan yayi ya fice ya rufe musu kofar dan baya son ganin abinda zai bata masa rai, duk da ya yarda da soyayyar da Adam din yake wa Daddyn ganin yadda ya damu sosai akan rashin lafiyar. Be san wani a matsayin uba ba, face Daddyn kuma shine kadai gatan sa. Shi ma Daddyn yana yi masa soyayya irin ta d'a ne da mahaifi yana jin shi sosai.

"Ya ka fito?" Ya Nabeela tace tana mikewa daga wajen da take zaune

"Adam ne yazo."

"Ban ga shigewar sa ba kuma, ko lokacin muna waya da Daddyn su Amna ne."

"Eh may be, bari na wuce idan Baba Rabi'un ya dawo sai kuyi maganar, zan yi kokarin fara processing tafiyar ina hadawa da sauran aikin."

"Ok, nima tafiya zan naga dare ya fara, yace zai biyo sai mu tafi."

"Ok, Baba Rabi'un shi kadai zai kwana yau?"

"Eh ina jin tunda jikin da sauki. Kaje gida ka huta, kayi bacci sosai please."

"Baccin ne ma baya yiwuwa ai, akwai ayyuka a gabana masu yawa."

"Still dai, ka huta yau dai, kayi tafiya kana bukatar hutu."

"Zan gwada."

"Yawwa, ya labarin Kamal?"

"Muna magana a chat,yana sane ya kyale ni sanda nake matukar bukatar sa."

"Yayi min daidai ai, da ace kana da matarka ba zaka yi wani missing dinsa sosai ba, yanzu haka da yadda ka gajin nan kana komawa za'a tare ka a kula mun da kai."

"Zan gudu, sai gobe."

"Baka son gaskiya dai." Tasa dariya

"Inaso mana, kawai maganar kara min pressure zatayi, amma dai I'm planning something, hoping yayi muku yadda kuke so."

"Akan wannan maganar?"

"Eh." Ya daga mata kansa

"Good, haka muke son ji, Allah ya bada sa'a ya taimaka."

"Amin, goodnight."

"Goodnight,." Ta daga masa ya fice cikin takun sa me cike da nutsuwa.

"Allah ya tallafi rayuwar ka Aryan ya hada ka da abokiyar zama me son ka." Ta daga hannu tayi addu'a sannan ta koma ciki.

•••••••Raihana bata tashi tunawa da sakon Hamma Muhd ba sai da safe bayan tayi breakfast ma tana kitchen tana wanke kwanukan da aka bata abun ya fado mata, da sauri ta dauraye hannun ta, ta goge da kitchen towel ta dauki wayar ta bud'e whatsapp din ta shiga kan chat din nasa. Saura kasan wayar da subce daga hannun ta, ta fadi kasa saboda abinda ta karanta.

_"Ni kuma? Soyayya?"

Ta furta tana sake kallon tsararren sakon wanda ya tsaro da kalaman kokarin kafa kai. Ko kad'an bata ji son sa a zuciyar ta ba, hasalima baya cikin jerin mazajen da take jin zata iya zaman aure dasu kwata-kwata, ya tsaya dai a iya yan uwantakar amma ita dai a'ah, bata shirya ba sai ta kara wayo da hankali. Rasa me zata ce masa tayi, ba zata iya ce masa a ah kai tsaye ba, babu dadi duk tsiya wanda yace yana son Ka yafi makiyinka ai, ba kuma zata iya amsa goron gayyatar soyayyar tasa ba, dan ita gaba daya ba abinda ma yake gabanta ba kenan, Kar taje tana zaman zaman ta a hada bikin ta da na su Hamman ta, tafi so ta fara rakashewa a bikin su daidai gwargwado kafin a fara maganar ta. Jin ta take har lokacin yar karamar yarinya ce ita, bata isa aure ba, dan bata san ta yadda zata fara kula da garjejen saurayi ace ita zata masa kusan komai ita din da ba'a wani dade sosai da su Hamman ta suka daina goya ta ba.
Fita tayi daga kan chat din sai tayi nazarin me zata ce sannan zatayi masa reply kar tayi a take ta kwafsa. Cikin chat din Aryan ta shiga kamar munafuka dan dama tunda ta tashi take son budewa amma ta kasa. Murmushi tayi ta tura masa hi a kasan hello din da yace mata, sannan ta dora da waye? A gaban sakon. Tana sane tayi hakan ta ajiye wayar tana murmushi ta cigaba da aikin da take yi. Sai da ta gama tas ta gyara kitchen din ta fito ta koma daki ta zauna a saman gadon ta sannan ta sake shiga whatspp din. Blue tick din da ta gani akan chat din Aryan yasa ta tabbatar ya karanta sakon ta, typing taga yanayi ta yi baya ta kwanta akan pillow tana jiran amsar sa.

"Ghost ne!" Ya yi reply ya sauka a take ya kira wayar ta. Wani irin harbawa zuciyar ta, tayi da karfi ganin shine yake kira, ta rasa dalilin da yasa take jin hakan game dashi da duk wani abu da ya shafe shi. Kamar ba zata daga ba, amma kuma bata da wannan karfin zuciyar, sakata tayi a kunnen ta bayan ta daga tace hello. Ajiyar zuciya ya sauke me dan karfi, ya tashi zaune daga kwanciyar da yayi sannan yace

"Baki da number na?"

"Na'am, mmm.. eh bani dashi."

"Oh okh, baki saving bane ba?"

"Eh."

"Ok, do it now, please."

"Why?"

"Just. Kiyi saving bana so na kira mutum ko nayi masa magana yace be gane ba."

"Ok zanyi."

"Good, how was your night?"

Gwalalo ido tayi waje, how was your night Yake tambayar ta? Lallai

"Alhamdulillah." Tace

"Masha Allah, me kike yi yanzu?"

"Ba komai, just laying down."

"Can i join you?"

Ya fada kamar me rada, kame wa tayi a wajen cike da mamakin sa. Ta jishi sarai amma sai ta nuna bata ji me yace ba.

"Na'am?"

"Baki ji ba?"

"Umm, banji ba."

"Ok, yaushe zaki dawo, we need you here,."

"Ka manta? Kaine kace na tafi,baka son sake gani na, you hate me!"

"Shhhhh!!!" Ya dakatar da ita da karfi

"Please Raihaana." Yayi lowering voice dinsa sosai sannan yace

" Duk abinda na fada ba har zuciya na bane, and I said I'm sorry, I'm sorry kiyi hakuri."

Bata ce komai ba,

"Kinji? I'm sorry, kuma nayi regretting duk abinda nace."

"Ok." Tace da k'yar

"Kin hakura? Kin yafe min?"

"Umm."

"Serious?"

"Umm..."

"Thank you so much, nagode."

"Uhum."

"Are you coming back?"

"A ah."

"Pleasee dan Allah ki dawo, Kamal ya tafi, kema kin tafi I'm so lonely, please come back."

"Hamma na ba zasu yarda ba."

"Why? Me nayi musu ne har haka?"

"Ban sani ba nima."

"Shikenan, bari nayi clearing abubuwan da suke gabana, zanzo har nan din, sai muyi magana naji, menene laifi na."

"Okh."

"Na gaji, aiki yayi min yawa kwanan nan bana samun enough sleep."

"Ayya sannu, it's not easy."

"Thank you, bari na shirya na fita, sai anjima."

"Ok sai anjima."

Suka ajiye wayar a tare. Wani fresh Aryan yaji akan sa kamar an janye masa wani abu me nauyi da ya tokare shi. Nine kuwa? Ya tambayi kansa da kansa. Be zata zai iya wannan long conversation din da ita ba, sai gashi yayi, har yana jin kamar su dawwama a haka suna magana. Murmusawa yayi ya tashi daga zaman ya tattare takardun sa sannan ya fada toilet dan yin wanka. Yana wankan yana tunanin abinda ya faru, shi kadai kawai sai yayi murmushi, ya gama ya fito daure da towel ya shirya a tsanake cikin shigar suit baka yasa bakin takalmin sau ciki sannan ya dauki abinda zai dauka ya watsa su a brief case dinsa hade da notepad dinsa ya fito. A falo ya ajiye komai ya shiga kitchen ya samar wa kansa tea ya dawo falon ya zauna yana sha yana kallon TV har zuwa lokacin da Habeeb ya karaso ya mike ya maida cup din kitchen ya dauraye shi sannan ya fito yana jin sa sakayau. Kansa da a kullum yake masa nauyi yau sai yaji kamar an cire masa ciwon an maye masa gurbi da wani irin mixed feeling me tafiya hade da farin cikin zuciya.

Tunda suka gama wayar take blushing, wani yanayi wanda bata taba jin irin sa ba take ji a yanzu. Muryar sa me cike da amo ta haddassr mata da wata irin kasala. Chusa kansa tayi a cikin filon tana murmushi k'asa k'asa, a haka Dadah ta shigo ta same ta. Tashi tayi zaune ta tankwashe kafarta tana kallon ta

"Na zata bacci kike ai da naji shiru."

"A ah, waya nake."

"Ok, yanzu mamanku Maimunatu ta kirani da wani labari."

Gaban Raihann ne ya fadi cike da tsoro tace

"Wani abun ne ya faru?"

Girgiza kai Daadah tayi

"Babu komai, sai alkhairi. Wai Muhammadu ne ya sameta da maganar ki,."

"Ni kuma Dadah?"

"Akwai wata a dakin ne da muke magana bayan ke? Kaji min shiririta."

"Toh ai Daadah maganar ce naji ta banbarakwai."

"Kinci gidan ku, ace ana sonki kice maganar ce banbarakwai."

"Ni dai gaskiya Daadah bana son shi."

Tafa hannu tayi ta hau salallami

"Menene laifin shi Raihana? Menene aibun sa? Yaro saurayi kyakkyawan gaske, me jini a jika, gashi dan dangi gashi kuma dan uwanki, me kike nema?"

"Allah ni Daadah son shi kawai ne bana yi, son yan uwantaka nake masa."

"Tirkashi, haka zaki mana Raihana? Har ina murna na sanar da yayyanki? Suma kuma murnar suke gasu chan a falo."

"Allah ni Dadah bana son shi, Allah kuwa."

"Toh wa kike so?fada min sai naji ai."

"Ni ba wanda nake so."

"Kinci gidan ku,ko aljanune dake ni jikar mutum hudu,eh?"

"Ba komai fa Daadah, na zata zaki fuskance ni, ni kawai bana son kowa ne, zaizo ne soon, amma banda Hamman gidan su Amina."

"Toh ni dai babu ruwana, kiyi tunani sosai sannan ki duba abinda zai faranta mana rai, idan kuma akwai wanda kike so ne ki fada min ni zan wuce miki gaba, amma idan har babu toh fa ba ruwana."

"Shikenan zan fada miki shi, amma yanzu ki hana su Hamma maganar toh, yanzu sai su dauka su fadawa Abby."

"Ki dai yi kokarin bashi dama ku fahimci juna."

"Toh Dadaah,zan bashi dama."

"Yawwa haka nake son ji, Allah ya tabbatar mana da Alkhairi."

Sai ta mike

"Bari na samesu nace su bar maganar zuwa sanda kuka daidai ta kanku, amma dai zaa bashi damar zuwa wajenki, idan Allah yayi zaa yi dashi toh, idan kuma Allah be yi ba shikenan."

"Ok tam." Tace dan so take a bar maganar haka nan shiyasa ta amsa mata da yadda take so. Tana fita ta kulle kofarta ta koma ta kwanta rigingine tana kallon saman dakin. Daga chan bangaren hankalin Muhd duk ya tashi, gashi ta duba message dinsa amma babu reply gashi yayi ta kiranta dazu yana jin user busy duk sai ya kasa nutsuwa, yaje ya sanar da Adda Maimuna shine ita kuma ta kira dadah dan ba karamin farin ciki ta shiga da labarin ba, dan dama tana ta fargabar wadda Muhd din zai dauko, sai gashi ta kwana gidan sauki.

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*


*ZAFAFA BIYAR BACTH A*


1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350
*(Bilyn Abdul)*


2.. _KAI MIN HALACCI_ 350
*(Miss xoxo)*


3.. _BURI DAYA_ 350
*(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350
*(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350
*(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*


1... _DAURIN GORO_ 350
*(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350
*(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350
*(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350
*(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350
*(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350
*(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350
*(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350
*(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350
*(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350
*(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350
*(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*


_Duk biyar 1500_

*______________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (COMPLETED)_*

1... _FARHATAL QALB_
*(mss xoxo)* 400

2... _GURBIN IDO_
*(Huguma)* 400

3... _SANADIN LABARINA_
*(Hafsat Rano)* 400

4... _INAYAH_
*(Mamu gee)* 400

5... _BABU SO_
*(Bilyn Abdull)* 400

_Kuɗinsu a yanzu 2K duk biyar_




*_ZAFAFA BIYAR 2023_*🔥🔥🔥
_*Sabuwar shekara sabon salo sabon taku,*_
_*Makaranta littafan hausa kuma masoya marubutan zafafa kuzo ga sabuwar tafiya zazzafa tazo karku bari ayi babuku *_

_*Zafafan alkaluman haziqan maruban zafafa biyar kowa yasan na daban ne,wannan karon ma sunzo da sababbin salo me kama zuciya.*_
_*ZAFAFAN MARUBUTAN SUNZO DA SABABBIN LITATTAFANSU NA 2023 Kamar haka,*_

1 _*IDON NERA*_
Mamuhgee

2 _*DAUDAR GORA*_ ciki ka shata
Billyn Abdul

3 _*RUMBUN QAYA*_
Hafsat Rano

4 _*KI KULANI*_ mallakin zuciyata
Hafsat Miss Xoxo

5 _*A RUBUCE TAKE*_ qaddarata
Safiya Huguma


_DUKA GUDA BIYAR DIN ZAKA SAMESU A FARASHIN 1200_

Guda 5 1200
Guda 4 1000
Guda 3 800
Guda 2 600
Guda 1 400

_*zaku saka kudin a wannan account din👇*_

_*0022419171 Access Bank Maryam sani*_

Saiku tura shedar ta👇

_*09033181070*_

Idan kuma katin Waya ne zaku tura katin MTN ta wannan layin👇

09166221261



TEAM ZAFAFA BIYAR🔥🔥
MUNGODE🙏🙏❤️

__**RQ**__

       
       Page 35

®️®️ Rano

***Tsawon sati biyun nan Aryan be zauna ba, shine daga nan yayi chan har ya samu ya kammala processing tafiyar Daddyn sannan ya tabbatar duk evidence din da zasu gabatar a kotu yana hannu. Sau daya sukayi waya da Malam Hassan ya kara rokar sa ya kuma amsa masa da zasu zo in sha Allah.
    Yana tsaye a gaban table dinsa bayan ya gama tattare hannun rigar sa zuwa sama yana jiran shigowar Zainab kafin ya shiga ya dauro alwala ganin lokacin sallah yayi. Knocking ta fara yi ya bata izinin shigowa ta shigo ta gaishe shi sannan ta ajiye takardun a saman table din ta saci kallon sa ta gefe tana jin wani shaukin soyayyar sa na sake kamata.

"Komai ya cika? Babu wata matsala?"

"Eh sir, babu."

"Ok good, sannu da kokari."

"Thank you sir, akwai abinda kake bukata ne sir."

"No babu, sallah zan na fita akwai in da zanje, zaki iya tafiya thank you."

"Ok, Allah ya bada sa'a."

"Amin." Yace ya shige toilet din bayan ya tabbatar ta fita ta rufe masa kofar. Alwala yayi ya fito ya samu dan karamin towel ya goge ruwan hannun sa da fuskar sa, sannan ya maida hannun ya saka links din ya kashe komai ya fito rike da wayar sa. A reception din ya tsaya ya dan duba abinda zai duba sannan ya leka office din su Abdulhakeem ya tarar dasu suna aiki ya kalli empty desk dinta ya kad'a kansa ya fito ya fice gaba daya daga cikin building din.

****Adam na zaune a office din shima ya hango fitowar Aryan din, waya ya dauka ya yi kira ya sanar dasu ya fito yanzu sannan ya kashe, tunda ya daure damarar ganin bayan sa toh shima zai yi nasa kokarin wajen ganin bayan Aryan din ya kuma taimaki mahaifiyar sa, a da ya kasa tunanin abinda ya kamata yayi ya taimaka mata sai da ya samu kira jiya akan maganar sannan ya zaburo,ya kuma kuduri aniyar sai ya hana shi aiwatar da komai.
  Driving yake hankalin sa na kan titin gaba daya zuciyar sa ta lula zuwa kundin tunani har be san ana bin sa ba. Wayar sa dake a silent sanda yana aiki ya maida ita shaf ya manta be cire ba tana ta faman ringing a gefen sa amma be ji ba, he was so focused akan abinda yake yi har ya kusa karasawa asibitin, sai ya tuna wata allura da ya kamata ya siya ya manta gashi an ce masa sai yaje wellcare sannan zai samu. Yana daidai wani U-turn ya tuna sai kawai ya juya motar ya koma. Juyawar sukayi suka cigaba da bin sa cikin dabara. Sai da ya isa wellcare din sannan ya dauki wayar ganin tarin missed calls din Habeeb yasa shi shan jinin jikin sa, ya waiga bayan sa da sauri amma be ga kowa ba. Da sauri ya shige cikin wellcare din sannan ya danna kiran Habeeb din.

"Kana jina? Ka jira mu a cikin wellcare din karka fito please, suna following dinka tun daga company luckily baka shiga wata hanya da babu mutane ba."

"Su waye su?"

"Idan nazo zamuyi magana, oga Kamal yace please karka fita, zai mana wuya mu iya tracing naka yanzu ma dan ka dauki wayar ne har muka ga location dinka."

"Ok, sai kinzo." Ya katse wayar ya shiga ciki ya nufi bangaren magunguna yana dubawa. Biyo shi ciki sukayi, biyu suka zauna a mota. Kamar masu siyan abu haka sukayi pretending suna dubawa har suka kawo saitin da yake suna kallon sa suna monitoring din sa. Sarai ya lura da yadda suke bibiyar sa a cikin wajen. Glass din da ya ciro a aljihun sa ya saka me dauke da camera da Kamal ya bashi yayi amfani wajen capturing abinda yake faruwa duk da ba komai ba amma yayi sa'ar samun hoton fuskar daya daga ciki.
   Cikin casual dress Habeeb suka shigo su ma wajen su uku, kunnen sa dake makale da Bluetooth ya taba yace

"Kana ina?"

"Wajen pharmacy, ina tunanin sun shigo ciki,

"Ok, ka shiga wani dan corridor haka muga"

"Okh." Yace ya juya ya hangi wani dogon corridor ya nufi wajen ya shiga, suna ganin ya shiga wajen suka rufa masa baya a daidai lokacin su Habeeb suma sun shigo. Su biyu suka yi wajen da Aryan din yake daya kuma ya tafi wajen receptionist din ya nemi office din manager ya nuna masa. Suna shiga lungun su Habeeb suka dirar musu, suka yi arresting dinsu a take.
  Tare wanda ya shiga wajen manager suka fito bayan yayi masa bayanin abinda ya kawo su wajen, godiya manager yayi musu suka fito har wajen da motar su take, suka tura su a ciki sannan Habeeb ya mikawa Aryan wata yar karamar na'ura ya shige motar.
  Tsaye kawai Aryan yayi cike da mamakin abinda ya faru just now, wato akwai mutanen da zasu iya goyan bayan duk zaluncin da hajiya Zeenat tayi kenan, har suyi kokarin taimaka mata da karfi da aljihun su. mutum daya ya rage DSS su kama shine SAN Mandawari shi kuma tun kama Hajiya Zeenat ya bi dare ya fice daga k'asar amma suna dakon dawowar sa wanda tabbas akwai saka hannun sa a harin nan da aka kaiwa Aryan din kuma shine mutumin da yake taimakawa Hajiya Zeenat din wanda suke da alaka me karfi tun da. Shine yayi shari'ar Abby kuma shine ya tabbatar da an tura shi prison.


***Kotun ta cika makil fiye da zaman farko, Adam na gaba dan da wuri ya iso kotun dan tun kafin a bud'e ma ya iso ya zauna a mota duk abin duniya yayi masa zafi. Tun da aka kama yaran nan da suka tura su tare Aryan yake cikin zulumi duk da kamasu ba bashi da direct alaka dashi sai na wanda suka tura shi, amma kuma idan har suka shiga hannu toh fa shima bincike zai iya zuwa ta kansa. Duk da ba lallai nasa yayi wani tasiri ba saboda su din manyan masu aikata laifi ne a k'asar kuma suna da daurin kafa shiyasa a sau da yawan lokuta Hajiya Zeenat din take having way din ta, wannan karon ne dai aka mamaye ta bayan ta gama sakankancewa itace da nasara domin ta samu duk wata hujja tasu a hannu not knowing that sunyi outsmarting dinta a matsayin su na yara matasa masu ji da zarra.
  Shigowar judge din ya saka wurin ya dau shiru daidai lokacin aka shigo da Hajiya zeenat ta saka gefen mayafin ta, ta rufe fiye da rabin fuskar ta. Aryan na zaune tsakankanin manyan lawyers tare da Barrister Awais da yake leading din su.
  Shi ya fara mikewa ya gabatar da kansa ga kotu sannan lawyer da yake kare Hajiya Zeenat din ya mike shima yayi introducing kansa sannan su Aryan da Barrister Hakim da Barrister Fatima suma suka gabatar da kansu. Cikin shari'ar aka shiga kai tsaye ba tare da bata lokaci ba, Judge din ta sake karanto tarin laifukan da ake tuhumar Hajiya Zeenat din dasu wanda suka hada da zargin salwantar da rayuwar Hajiya Khadija Mukaddas, Hajiya Aysha Matawalle, satar yaro jinjiri Ahmad tun yana zanin goyo sannan tayi yinkurin kashe mijinta Alhaji Mukaddas wanda yake kwance a asibiti yanzu haka da kuma sauran laifukan. Barrister Awais ne ya sake mikewa a isa gaban wajen da take tsaye saboda yana da bukatar ta amsa masa wasu tambayoyi.

"Sannu Hajiya Zeenatu, akwai wasu yan tambayoyi ba masu yawa ba, da nake so ki amsa min."

Idon ta akan Aryan da yake zaune daidai saitin ta yana facing dinta dan shi kadai kawai take gani a wajen.

"Kina jina? Da farko dai kotu zata so sanin alakar ki da wadannan mutanen, Aisha da kuma Hajiya Khadija."

"Kawaye na ne da muke tare tun makaranta."

"Wani abu na rashin jituwa ya taba faruwa tsakaninku? Ko sun yi miki wani abu da ya bata miki rai har kika ji bari ki salwantar da rayuwar su?"

"Objection My lord." Barrister Sule yace yana mikewa

"Me kamata Barrister Awais ya dinga jinginawa mata kalmar kisa kai tsaye ba, tunda har yanzu zargi ne ba'a tabbatar da gaskiyar ba."

"Barrister Awais ya kiyaye."

"Ok, my lord."

Komawa Barrister Sule yayi ya zauna ya yi folding hannun sa.

"Muna son sanin me ya faru ranar bakwai ga watan October, da daddare wajen asubah, a lokacin da aka samu gawar Hajiya Khadija a kwance cikin jini."

"Bansan komai akai ba, kamar yadda aka samu gawar ta haka nima na ganta,."

"Hmm."

"Abinda ya faru a ranar 7 ga watan October da misalin karfe biyar na asubah an samu gawar Hajiya Khadija a kwance a cikin jini, wanda barrister nasir Matawalle ya samu gawar tata bayan ta tura masa wani sako da misalin karfe biyun dare, in da be tashi samun sakon ba sai da asubah saboda ko a lokacin da ta tura masa sakon dare yayi, ga abinda sakon ya kunsa ya mai girma me shari'a."

  Ya mikawa daya daga cikin na zaune gaban wajen sannan shi kuma ya mika mata, ta karba ta gani sannan ta ajiye a gefe

"Kotu na sauraran ka Barrister Awais."

"Bayan Hajiya Khadija ta kama Hajiya Zeenat da abokin aikin nata sai tayi yinkurin daukar hoto a lokacin ne suka lura da ita, sannan suka biyo ta har cikin daki suka kashe ta."

"Objection My lord, ya za'a yi barrister Awais ya dinga jingina mata laifin kisa kai tsaye? Hakan yayi muni sosai, ina rokon da ya janye kalaman sa ya kuma tausasa lafuzan sa."

"Ko kana da shaidar abinda ka fada barrister?" Tace tana kallon sa

"Kwarai da gaske, ina da shaidu guda biyu, na farko shine d'an marigayiya Hajiya Khadija wanda duk da karancin shekarun sa a lokacin yana iya tuna abinda ya faru akansa, na biyu shine shaidar da aka samu a cikin CCTV camera din dake hanyar shiga dakin marigayiyar wanda ya dauki hoton hajiya Zeenat da abokin harkar ta wanda bamu iya ganin fuskar sa ba a lokacin da suke shiga cikin dakin."

"Kotu tana bukatar ganin shaidun a gabanta."

Aryan ne ya mike ya isa gaban wajen ya sake yin gaisuwa sannan ya gabatar da kansa a matsayin shaida duk kuwa da ba lallai shaidar tasa tayi tasiri ba sosai duba da karancin shekarun da yake dashi a lokacin da kuma kasancewar sa cikin lawyers masu kara. Yana maganar kirjin sa yana harbawa sosai saboda yadda a duk lokacin da ya tuna memory din yake shiga matukar tashin hankali, da kyar ya karasa maganar ya koma wajen zaman sa ya zauna dafe da kirjin sa. Ruwa Barrister Hakim ya bashi Yasha sannan ya dan samu daidatuwa. Shiru ne na dan sakannni ya bayan komawa wajen zaman Aryan din, sannan aka cigaba da sauraron karar. Sosai barrister Awais yayi kokari wajen bada hujjoji kwarara kafin ya gangaro laifi na biyu wanda yake akan batan ahmad ne. Hankalin Aryan gaba daya yana ga kofar yana lokaci zuwa lokaci yana kallon agogon dake daure a

Please Login or Register in order to submit comment