You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bani number ka muyi magana."

"Ba zan iya ba." Ya murd'a kofar ya shiga tayi kamar zata bi bayan sa yayi saurin banging kofar yana jan tsaki. Kamal da yake zaune yana waya ya bishi da kallo.

"Kai da wa kuma?"

"Wata stupid yarinya ce, ta dauka ma kowa irin ta ne. Nonsense."

"Babe zamuyi magana."

Ya katse wayar yana kallon shi ya zauna ya dafe kansa da hannu biyu

"Da zan iya barin garin nan a yanzu da na bari wallahi."

"But ba shine solution ba, ba zai yiwu mu kyale Barr yayi amfani da ego dinsa ya cutar da ku ba, abinda mukayi magana da Sadeeq da Lamido kenan,duk abinda ma zamuyi sai munyi kawai."

"I don't think it will work, so ba zan takura masa ba, yar sa ce yana da right din yayi abinda yaga dama."

"Kai kuma fa?"

"Waye ya damu dani kuma?"

"Ni mana,Daddy ,Ya Nabee.

"Ok."

"Ok?"

"Me zance toh?"

"Shikenan kawai."

"Zan kwanta, but please karka yi min magana."

"Naji, ba zan ba, sai da safe."

***Akan hannun ta, tayi bacci rike da waya tana jiran kiran sa, da asubah ta farka da sauri tana duba wayar amma sai taga be kira ba. Tashi tayi a sanyaye ta shiga toilet ta yo alwala ta fito, ta fara raka'atanil fajr sannan tayi sallar asubah ta roki Allah ya sassautar da zuciyar Abbyn nata. Tana zaune a wajen har gari yayi haske, ta tashi ta hau saman gadon ta kwanta lamo ta dora kanta akan pillow. Wajen bakwai da rabi Hydar yayi mata knocking, ta tashi ta bud'e masa ya kalli rinannun idanun ta wanda suka jeme saboda kuka, yi yayi kamar be gani ba yace

"Kizo Muhd zai tafi."

"Na'am?"

"Eh, kizo kuyi sallama kafin ya dawo."

"Kayi hakuri Hamma Hydar, amma ba zan iya zuwa ba." Ta juya ta koma ta kwanta ta barshi a tsaye baki hangame cikin tsananin mamakin ta, tunda suke bata taba masa musu ba, ko ya sakata abu taki yi sai yau, kasa magana yayi ya juya ya ja mata kofar kawai dan idan ma yayi maganar bata da amfani. Tunda har ta furta masa ba zata ba, toh ba zata din ba kuwa.
  Muhd na tsaye yana jiran fitowar ta sai ga Hydar din ya fito shi kadai

"Muje na sauke ka, bata tashi ba."

"Oh ok, dadah ni zan wuce."

Ya juya wajen Daadah da take zaune a falon,

"Allah ya tsare, ya kiyaye hanya." Tace kawai dan a cike take dasu dukkan su, shiyasa ma taki sakar musu fuska musamman Hydar da ya zake sosai akan maganar. Fita sukayi sai ta tashi ta shiga ciki, idan sun san wata ai basu san wata ba, Muhd jikan tane kamar Raihanan, amma tunda tace bata so sai a bata zabin ta tunda dai bashi da wani aibu ya ma fi Muhd din nagarta ta kowacce fuska.

   ***Akan hanyar su ta zuwa airport Kamal sukayi waya da Lamido, Aryan dai be san me suke tattaunawa ba shi dai kawai burin sa ya ganshi a Kano,kunnen sa a toshe yake ma gaba daya yana sauraron karatun alkurani,sai da suka shiga ciki sannan ya kashe. Suna zuwa basu dade ba suka tashi, ya sake maida karatun ya kwantar da kansa a jikin kujerar har suka iso. Sauri sauri ta dinga yi tun a cikin jirgin ta ganshi amma yana dan nesa da ita, shiyasa da aka fito tayi sauri ta biyo su ta same su a wajen shiga mota. Shi Aryan be gane ta ba ma kwata-kwata suka gaisa da su ya fada motar sai Kamal ne ya tsaya ya saurare ta, ya bata abinda ta tambaya sannan shima ya shiga motar.

"Kayi kasuwa mutumi na." Yace yana dariya

"Kana da matsala."

"I'm serious, yarinyar nan kai ta biyo, har na bata number dinka ma, irin yaran nan ne ajeboters wanda basu san wani abu wahala ba ko kunya, idan sun ga namiji yayi musu kawai suna magana ne."

"Lallai aiki ya gansu, Allah ya sauwake."

"Amin, kaga shikenan ka samu replacement."

"She's too cheap."

"Wa din?"

"Ita yarinyar."

"Gashi nan kuwa tana kiran ka."

Kallon wayar yayi da sauri sai ya tuna a kashe take ma tun jiya, kunnawa yayi ya kira Dr Mahfouz yace zai shigo yanzu. A asibitin aka ajiye shi, Kamal yace zai shigo yace a ah ya wuce ciki shi kuma ya wuce gidan Ya Nabeela.

***Yau kwanan Daddy uku da tafiya, washegarin da suka dawo shi kuma ya tafi, basu fada masa abinda ya faru a chan din ba sun dai ce masa ya karbi sakon. Ya dan ji dadi yana kuma fatan ya duba sakon a lokacin da ya dace.
   Suna zaune a office din Aryan din Kamal na shigar da wasu ayyuka a cikin computer Aryan kuma yana signing wasu takardu Zainab ta kwankwasa ta shigo rike da takardu ta ajiye su, tun da suka dawo daga yolan aiki kawai Aryan yake yana so a lallai sai yayi keeping kansa busy saboda ya dauke hankalin sa daga abinda yake shirin faruwa. Hakan bata yiwuwa dan duk abinda yake tunanin kara kusanto shi yake ga wani irin fargaba da tsoron rasa abu me matukar muhimmaci a gare shi. Be kara tabbatar da yana son ta da gaske haka ba sai da kwanakin nan suke ta karatowa. Be kirata ba tun maganar da sukayi ranar yaki bari kuma itama ta kirashi dan baya so ya taka dokar Allah tunda akwai maganar aure a tsakanin ta da wani. Amma fa ba karamin dauriya yake yi ba, dauriyar da take neman kaishi k'asa sosai.
  Gefen kirjinsa ya dafe yana cikin aikin ya tsaya chak da komai ya yi shiru yana jin yadda gudun zuciyar ya karu sosai. Dagowa Kamal yayi ya dube shi ya ture system din da sauri yana tashi tsaye

"Are you ok?" Ya dafa shi

"Bani ruwa please."

"Ok." Ya dauko masa ruwa me dan rangwamen sanyi ya bud'e masa ya mika masa ya karba yasha kad'an sai yaji kamar an kara masa gudun bugun zuciyar. Saurin ajiye ruwan yayi yayi baya akan kujerar yana runtse idon sa

"Ya Allah, bari na kira Dr Mahfouz."

"No ba sai ka kirashi ba, zai daina haka yake min."

"Haka yake ma? Tun yaushe?"

"Zai daina fa, don't worry."

"Ba maganar zai daina bane ba, bari kaga."

Ya zaro wayar sa ya kira Dr Mahfouz, suka gaisa yake tambayar sa jikin Aryan din

"Naso bashi gado amma yaki wallahi, amma abinda yake rikewa a ransa yayi yawa, he is holding alot hakan kuma yana kara damage din, last da yazo nayi masa bp it was high, na bashi drugs nace idan yaji any slight change ya dawo ko ya kirani nazo gidan."

"Ya salam, wallahi be fada min komai ba, yanzu haka abun yana neman worst."

Yace yana kallon yadda yake numfashi da k'yar

"Subhanallahi, gani nan zanzo yanzu."

"Ko mu hadu a gida na?"

"Ok hakan yayi."

"Thank you Dr, sai kazo." Ya ajiye wayar ya zagaya wajen Aryan din

"Tashi muje please."

"Kaima kamar mace, zai tsaya ba. Haka yake yi amma zai tsaya."

"Allah baka isa ba."

Tashi yayi kawai dan baya son su cigaba da musu, ya yi gaba Kamal din ya bishi rike da wayoyin su. Khadija na zaune suka shigo ta tashi tana kallon su, gaisawa sukayi da Aryan din ta shiga daki ta dauko mayafin ta sannan ta dawo falon. Karasowa Dr Mahfouz yayi Kamal ya shigo dashi falon yana shigowa ya kalli Aryan din ya girgiza kai

"Ok kana da matsala wallahi, akwai wanda yake wasa da lafiyar sa irin ka kuwa?"

"I'm fine fa."

"Yes gashi nan, look at you daga ranar da kazo office zuwa yau, haba mana."

Murmushi kawai yayi, Dr Mahfouz ya ciro abun auna BP ya gwada ya zaro ido da sauri yana kallon Kamal

"You see, BP dinsa ya kara high sosai, a wannan stage din mutum zai iya collapsing."

"Hmm, me ya kamata ayi yanzu kenan?"

"Abinda dai baya so din shi za'a yi, dole ya kwanta coz yana bukatar hutu."

"No Dr, dan Allah karka kwantar dani a gida."

"Wallahi sai ka kwanta, bari kaji ma."

Kamal yace kai tsaye, dariya ma ya bawa Aryan din ya murmusa kad'an be sake magana ba, an ce fadan da yafi karfin ka sai ka maida shi wasa kawai.

****Ana saura kwana biyu kamar yadda Abby ya tsara, dadah ta fito janye da akwatin ta katuwa da ta lodawa kaya, Hydar na zaune a falon yana breakfast ta fito ya mike tsaye da sauri

"Daadah wannan kayan fa?"

"Gidan ku zan bar muku."

"Kije ina?"

"In da naga dama, ina ruwan ka?"

"Wasa kike Amma ko?"

"Da yake ni sa'ar kace da zan maka wasa ko?"

"Me ya faru? Munyi laifi ne?"

"Akan me zan cigaba da zama daku? Tunda kun girma kun isa kuyi wa kanku hukunci abinda kuka ga dama. Bani da amfanin zama AI."

"Me yake faruwa?" Lamido yace suna shigowa shi da Sadeeq

"Tafiya zanyi, na bar muku gidanku tunda abun haka ne,."

"Me mukayi Daadah? Dan Allah kiyi hakuri "

"Ba zan hakura ba, gwara na tafi ai duk kun gama mallakar hankalin ku ya ci ace ma kun ajiye Yaya bibiyu ko uku ma"

"Dan Allah kiyi hakuri, ki zauna muyi magana dan Allah."

"Kasan bani da amfani a gidan nan, tunda har za'a yanke shawara ba za'a sanar dani ba,na zuba ido amma babu wanda ma yake yin maganar."

"Wai maganar Raihana ce Daadah?"

"Fisabillillah haka zaku zuba ido a cutar da yarinyar nan, marainiyar Allah, ina tausayin ku? Ina son da kuke mata? Yarinya a dan kankanin lokaci duk ta fige ta lalace."

"Wallahi Dadah Abby hana mu maganar, wallahi ko da wasa kaje masa da maganar sai kaga bacin ransa, nayi iyakar kokarin ganin ya fuskance ni amma yaki fahimta ta."

"Toh ai shikenan, sai ayi duk abinda aka ga dama, ni zama na ya kare, Allah ya bada sa'a ya taimaka."

"Dan Allah kiyi hakuri, ki zauna ayi maganar nan dan Allah."

"Kasan Allah Lamido, ba zan zauna ba, in dai ba za'a fasa auren nan ba ko a bata wanda take so ba toh zama na ya kare."

"Hydar yiwa Abby magana."

"Akwai munafuki sama da Hydar? Uwar me zaka amfana idan ka assasa abinda bata so?"

"Kai Daadah."

"Karya nayi? Ba duk kaine ka assasa ba."

"Ku bani waje na tafi dan Allah, kuna bata min lokaci."

Rike jakar Sadeeq yayi, Hydar kuma ya tafi bangaren Abbyn ya kirawo shi.

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*


*ZAFAFA BIYAR BACTH A*


1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350
*(Bilyn Abdul)*


2.. _KAI MIN HALACCI_ 350
*(Miss xoxo)*


3.. _BURI DAYA_ 350
*(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350
*(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350
*(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*


1... _DAURIN GORO_ 350
*(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350
*(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350
*(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350
*(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350
*(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350
*(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350
*(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350
*(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350
*(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350
*(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350
*(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*


_Duk biyar 1500_

*______________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (COMPLETED)_*

1... _FARHATAL QALB_
*(mss xoxo)* 400

2... _GURBIN IDO_
*(Huguma)* 400

3... _SANADIN LABARINA_
*(Hafsat Rano)* 400

4... _INAYAH_
*(Mamu gee)* 400

5... _BABU SO_
*(Bilyn Abdull)* 400

_Kuɗinsu a yanzu 2K duk biyar_




*_ZAFAFA BIYAR 2023_*🔥🔥🔥
_*Sabuwar shekara sabon salo sabon taku,*_
_*Makaranta littafan hausa kuma masoya marubutan zafafa kuzo ga sabuwar tafiya zazzafa tazo karku bari ayi babuku *_

_*Zafafan alkaluman haziqan maruban zafafa biyar kowa yasan na daban ne,wannan karon ma sunzo da sababbin salo me kama zuciya.*_
_*ZAFAFAN MARUBUTAN SUNZO DA SABABBIN LITATTAFANSU NA 2023 Kamar haka,*_

1 _*IDON NERA*_
Mamuhgee

2 _*DAUDAR GORA*_ ciki ka shata
Billyn Abdul

3 _*RUMBUN QAYA*_
Hafsat Rano

4 _*KI KULANI*_ mallakin zuciyata
Hafsat Miss Xoxo

5 _*A RUBUCE TAKE*_ qaddarata
Safiya Huguma


_DUKA GUDA BIYAR DIN ZAKA SAMESU A FARASHIN 1200_

Guda 5 1200
Guda 4 1000
Guda 3 800
Guda 2 600
Guda 1 400

_*zaku saka kudin a wannan account din👇*_

_*0022419171 Access Bank Maryam sani*_

Saiku tura shedar ta👇

_*09033181070*_

Idan kuma katin Waya ne zaku tura katin MTN ta wannan layin👇

09166221261



TEAM ZAFAFA BIYAR🔥🔥
MUNGODE🙏🙏❤️

_*RQ*_

    Page 43

***Tare suka dawo da Abbyn ya shigo falon ya durkusa har ya gaishe ta, ta amsa babu yabo babu fallasa sannan yace

"Dan Allah Hajiya kiyi hakuri."

"Ni ai ba laifi akayi min ba sam, abinda kake ganin daidai ne ka zartar akan yar ka, bani da wani iko akai na hana balle a nemi shawara ta."

"Subhanallah, kiyi hakuri Hajiya wallahi ba haka bane ba, abubuwan ne suka zo a baibai, amma ba anyi hakan bane domin a bata miki rai, yaran nan gaba daya dani kaina a karkashin ikon ki muke, kece mahaifiyar su kuma kece mahaifin su, dan Allah kiyi hakuri Hajiya."

"A ah, babu komai fa, tunda har an riga an yanke hukunci magana ta kare, zan tafi zamana ya kare a gidan nan, Allah ya bada zaman lafiya"

"A ah Hajiya, ba za'a yi haka ba, dan Allah kiyi hakuri."

"Toh..."

"Yanzu me kike so ayi Hajiya?"

"Ka saurari yarka, kaji damuwar ta, kaji abinda take so sannan idan be sabawa shari'ar musulunci ba kayi mata, Raihana yarinya ce karama wadda ba zata dorar da rayuwa tare da soyayyar uwa ba, ta girma a karkashin kulawa ta data yan uwanta gasu nan, bata taba bijire musu ko yi raina su ba, bata taba batawa kowa rai ba, yarinya ce me cike da walwala da farin ciki, akan me za'a dakushe ta? Akan me za'a bata mata rayuwa ta hanyar yi mata auren dole, kunsan illar sa kuwa? Kunsan abinda zai jawo? Me yasa ba zaku yarda da kaddara ba, KU zama masu hakuri? Allah ma muna masa laifi amma ya yafe mana, me yasa abinda ya faru ba zai wuce ba? Rayuwar gaba daya nawa ce? Sannan duk abinda ya faru ya faru ne tsakanin ku, ku iyayen yaran nan, menene nasu su? Me yasa abun zai shafe su? Me yasa ba zakuyi kokarin gina sabuwar rayuwa ba? Bansan dalilin ka na zafafa wa har haka ba, nasan an bata maka, an zalunce mu ciki har dani, wanda har yanzu bansan shin da gaske Aisha ta rasu ba, ko tana wacce duniyar? Bamu ga gawarta ba duk da mun samu tabbacin tana cikin motar da tayi hatsari, me yasa ni ba zan rike abun ba? Me yasa ba zamu fawwwalawa Allah komai ba? Mu zama masu karbar kaddara a duk yadda tazo mana, sai mu hau fushi muce mu sam ba zamu zama masu yafiya ba? Rayuwa zata yiwu a haka? Muna so kuma muma Allah ya yafe mana zunuban da muke aikatawa, bayan mun kasa zama masu yafiya da jin kai ga sauran mutanen da kaddara ta hada mu dasu. Ni dai nasan ban isa nasa dole ayi ba, ko na hana ayi ba, shawara ce dai a matsayi na na babba, ga Raihana nan, zabi ya rage naku, ku zaba mata rayuwa me inganci ko ku dakushe ta, ta hanyar tursasata tabi abinda bata so."

"Ayi hakuri Hajiya, ayi hakuri." Abby yace maganganun sun yi mugun shigar sa. Juyawa tayi kawai ta bar musu falon ta koma ciki. Abby ne ya fara fita ya koma part dinsa, ya bar su a zaune cikin wani irin yanayi.
   Direct wajen da ya ajiye envelope din da Daddyn ya aiko masa yaje, ya bud'e ya dauko dan tun ranar be bude ba, ya zauna a gefen gadon sa ya bud'e a hankali bayan ya zura medicated glass dinsa. Takardun filaye ne da gidajen da ya mallaka tun a wanchan lokacin, sai kuma takardar share din da yake dashi a company Mukaddas oil and gas. Duk bayanan da ya kamata ya samu suna ciki. Ajiye su yayi a gefe ya sake fito da wasu takardun wanda suke dauke da bayanin health condition din Aryan, wanda suka kasance na shekarun baya a lokacin da ya shiga matsalar PTSD at a very young age. Ajiye su yayi suma a gefe bayan ya gama dubawa cike da tausayawa. Wani dan karamin flash ya fado daga ciki. Ya dauka ya jawo system dinsa ya jona a ciki. Maganar Daddyn ce cikin muryar dake nuna jikin sa babu dadi yake rokon Abbyn ya yafe masa sannan ya taimaka ya bawa Aryan Raihana, yasan be kamata ya tambayi alfarma a wajen sa ba, kuma shi kansa Aryan din be san ya nemar masa alfarmar ba, amma idan yaga da takura shikenan babu komai. Ajiye flash din yayi bayan yayi copying maganar akan system dinsa sannan ya dauko takardar karshen. Wadda take kunshe da bayanan dalilin fitar Abbyn daga prison wacce ke dauke da sa hannun Daddyn. Jikinsa ne yayi wani irin sanyi sosai, hankalin sa ya tashi, yanzu idan wani abu ya samu Daddyn ya zaiyi? Me yasa be danne zuciyar sa ya saurare shi ba? Me yasa shi be rama sharri da alkhairi ba, ya nuna masa ya fishi ko a wajen Allah. Amma sai ya biye wa dokin zuciya ya aikata abinda sam ba halin sa bane, gashi har yana neman ya gurbata rayuwar yarsa kwaya daya tilo saboda wani dalili nasa na daban. Tashi yayi ya hau zagaye a tsakiyar dakin yana tuna maganar da sukayi da Alhaji Kabir akan maganar auren. Be goyi baya ba sam dan dai Abbyn ya matsa ne ya amince saboda kar yaga kamar ya ki yarsa. Amma daga shi har Adda Maimunan basu zama masu son kai ba, sun kuma nusar da Muhd yayi hakuri amma ya nuna musu shi dai ya amince. Tausayin Raihanan suke ji dan su ba zasu iya aikatawa Amina hakan ba. Zagayen ya cigaba da yi cikin son neman mafita, gashi saura kwana biyu kachal ta ina zai fara? Ya dade yana sakawa da warwarewa kafin ya tsaida shawara guda wadda yake ganin itace zata zama maslaha ga kowa da kowa. Alhaji Kabir ya fara kira, ya sanar dashi komai ya kuma basu hakuri, be damu ba, duk da yasan Muhd zai ji babu dadi amma yasan zai hakura a karshe tunda shi namiji ne. Ganin ya sauke wannan ya sa ya kira Lamido a waya yace suzo dukkan su part dinsa yana son ganin su, dama suna tare basu riga sun tashi ma daga falon ba dan ko aiki babu wanda cikin su yayi yunkurin tafiya saboda daga Daadah har Raihanan sun rufe kofar dakunan su sun shige ciki suna kuma tsoron wani abu ya same su. Part din Abbyn suka nufa suka same shi a falo yana zaune yana jiran isowar su, zama sukayi ya kalle su daya bayan daya sannan yace

"Na yi tunani na kuma yanke shawarar bawa Raihana zabin zuciyar ta, zan kuma cika alkawari kamar yadda na dauka sai dai na dawo da daurin auren gobe ba sai jibi ba, inaso Lamido ka kira Kamal ka sanar masa, idan mutum daya ne ma ya samu zuwa ya wadatar, idan ba'a samu me zuwa ba, ni nan zan zamar masa wakili sai kawun ku ya yi waliccin uwata. Idan yaso ku dauke ta ku kai ma mijinta ita, ni kuma sai ku fara nemar min visa domin zan bi bayan aboki na."

Wanan karon har Hydar maganar tayiwa dadi, suka yi murmushi dukkan su sannan suka ce alhamdulillah. A take Lamido ya fita daga falon ya kira number Kamal a lokacin yana tare da Aryan din da ake kara masa drip jikin nasa ya sake rikicewa sosai fiye da dah dan ma yana da masifar karfin hali da dauriya. Ba dan sun nuna masa dole dole ba da babu abinda zai sa ya yarda ya kwanta wanda kuma yake da matukar bukatar hutun.

"Lamido ne yake kira."

Yace yana nunawa Aryan din wayar, juyar da kansa yayi Kamal ya d'aga suka gaisa sannan ya tambaye shi idan suna tare da Aryan ne, ya amsa da eh sanann yace ya dan fita waje zasuyi magana. Chan compound din gidan ya fita sannan sukayi maganar, wani irin dadi ne ya lullube Kamal din, ya dawo dakin da Aryan din yake ya tarar dashi kamar me bacci, be fada masa ba dan dama plan dinsu kenan shi da Lamido. Zama yayi a gefen gadon ya hau duba available flight da zasu yolan gobe, yaci sa'a ya samu na safe amma da yar tsada, haka ya siya musu sannan ya dauki key din motar sa ya fita. Yana driving din suna waya da Baba (Malam Hassan) ya sanar dashi abinda yake faruwa sannan ya kira Ya Nabeela ya sanar da ita itama, lokacin tana hanyar zuwa gidan Kamal din saura kiris ta saki steering motar saboda murna. Rokon ta yayi kar ta fadawa Aryan din surprise zasuyi masa kawai.

   Su uku suka shirya, Malam Hassan, Dr Farouk mijin Ya Nabeela sai wani cousin din Daddy. Da sassafe driver ya kaisu airport ko tashi Aryan din ma be yi ba suka lula sai Adamawar yola. Duk abin nan dake faruwa Daadah bata sani ba haka ma Raihana, suna dai tare Daadan na bata baki dan ta lura kaamar abinda tace be shige su ba, ganin yadda suka cigaba da sabgar gabansu a ranar. Dangin Ammyn ne suka zo gidan bayan Daadah ta sanar dasu, duk sun dauka ma Raihana sun daidaita kansu da Muhd din ne ashe ba haka bane ba, sai da suka zo sai duk jikin su yayi sanyi haka dai aka cigaba da zama a gidan kamar ba aure za'a yi ba.
   Hydar ne yaje ya taho dasu daga airport din suna sauka, ya kawo su gidan suka hadu da Daddy a falon sa suka zauna har lokacin ya kusan karasawa sannan suka dunguma zuwa masallacin. Asabar ce sai kuma tazo da daurin aure da yawa, sai da aka fara na wadanda suka riga su sannan aka shiga daura auren Raihana Nasir Matawalle da angon ta Muhammad Ibrahim Mukaddas bisa sadakin dubu dari da Kamal ya bayar. Kasancewar anyi daurin aure da yawa ya saka ma ba zaka gane wannan mutanen wannan bane haka ma wannan, haka aka gama aka watse suka dawo gidan cikin farin ciki da annashuwa. Matan gidan na zaune aka shigo musu da alawa da goro.

"Kar dai zargi na ya tabbata auren nan aka daura yau?"

"Eh Dadah, an daura auren Raihana da angon ta Muhammadu."

Lamido yace yana murmushi.

"Yanzu har da kai Lamido?"

"Muje ciki zan miki bayani Daadah."

"Me zaka fada min?"

"Muje dai, sirri ne."

Da k'yar ta bishi cikin ya sanar da ita abinda ya faru, sai kuma ta hau murna tana saka musu albarka, ta juya zata je ta sanar da Raihana ya hanata

"Angon yana chan kwance babu lafiya, karki fada mata dan Allah suprise za'a mata."

"Akan me? Yarinya na chan na ciwon so Allah ya share mata hawayen ta za'a ce ba za'a fada Mata ba."

"Dan Allah Dadah, dan Allah."

"Gobe da safe zasu wuce da Kamal, sauran da suka zo dai yau zasu koma."

"Haka da wuri? Me yasa ba za'a bari muyi biki ba."

"Kai Dadah, da fa bakuyi niyyar bikin ba dama."

"Wannan ai auren soyayya ne, wanchan kuma na dole, kai Allah ma yaso na jima ina gyara Raihana, da irin wannan auren bagatatan haka za'a kaita dakin miji ba wani gyara."

"Wannan maganar ku ce Dadah, bari na koma waje."

"Allah dai yayi maka albarka kaji, bari naje na sata tayi wanka ta ci abinci dan wannan ramar da tayi ma Allah yasa kar kasusuwan su ciji mijin."

Dariya ya kwashe da ita, ya barta a ciki yayi waje, ta fito ta nufi dakin Raihanan ta same ta tare da wata kanwar Ammy da tazo ta fada mata an daura auren. Tsabar kukan tayi ta gaji ya ma ki zuwa, ta hakura kawai duk yadda sukayi da ita. Sata taje tayi wanka Dadah tayi babu musu taje tayi ta saka kaya ta zauna da kudaddiyar fuskar ta da ko mai bata saka mata ba bare ta samu arzikin powder. Abinci aka kawo mata taaci kad'an ta koma ta kwanta tana tunanin rayuwar da zata shiga da yadda abubuwan suka faru a dan kankanin lokaci. Tabbas Muhd ba zai taba jin dadin zama dashi ba, tayi biyayya ta aure shi amma ba zata taba son sa

Please Login or Register in order to submit comment