You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba."

"Mu da muke rayuwa a wajen uban mi ya cinye mu?"

"Dan Allah ni dai, kinji kanwata dan Allah."

"Alkuran ko me zaki bani ba zan taimaka miki ba. Kuma kika sake rike ni idan zan fita sai na kira kurar nan ta shigo, zan bawa lantis tuwon dawa ta kawo miki da ruwan randa me sonyi, idan kin ci, cikinki, idan baki ci ba ma dai cikin ki."

Sai ta juya ta fita gami da barin kofar a bud'e. Da sauri Hajiya Zeenat ta mayar da kyauren ta rufe cikin tsananin tashin hankali, lallai Aryan ya shirya tozarta ta, dama tasan halin yaron shegen taurin kai da kafiya, amma bata taba tunanin zai mata wannan azabar ba. In da ta tashi ta koma ta zauna cikin tsananin tsoro hankalin ta na kan kofar tana jin gunjin kurar da take a sake tana shawagin ta kamar yadda akuya ke yawo a tsakar gida. Taba kyauren akayi ta tsorata sai ga ladidi ta shigo da wata mummunar langa da ruwa a Kofin silba ta dire mata a gabanta tana kallon ta.

"Taimako na zakiyi dan Allah, zan baki kudi da duk wani jin dadin duniya, waya kawai zaki samo min dan Allah."

"Bamu da netiwok a garin nan ai, sai an je chan hayi ake samu ayi waya, su waye ma masu wayar a kaf garin nan? Basu fi mutum hudu ba."

"Na shiga uku, Aryan!!!"

"Inna Ladi tace idan kin cinye ki taba kyauren nan zan zo na dauki langar."

"Ki zauna anan toh dan Allah karki tafi."

"Chab, so kike taci ubana Kenan."

"Toh ya sunan kauyan nan?"

"Oho nima ban sani ba."

"Shegu marasa iya magana." Hajiya Zeenat tace k'asa k'asa cikin bacin rai, juyawa Landis tayi ta fice tana kada kugu. Zame dankwalin kanta Hajiya Zeenat tayi dan wani irin tururin zafi ne ke fitowa daga cikin jikin ta. Da dan kwalin ta dinga kokarin firfita ta dan ja kwanon kad'an ta bud'e tuwon da sauri ta rufe ganin wata irin miya tsululu kamar an wanke kai, kwalla ce ta taru a idonta, lallai Aryan ya gama cutar ta, cuta me tsananin gaske, ba kuma zata kyale shi ba wallahi sai ta nuna masa ita uwar dakin sa ce a rashin mutunci. Tun da magribar fari sauro ya fara gud'a acikin kunnuwan Hajiya Zeenat, ta shiga aikin kore su amma ko gezau kamar ma kara turosu ake yi ga wani irin shegen kuka da suke kamar zasu ci babu sannan ga kukan da cikin ta yake yi dan daga prison take dole tana tare da yunwa. Bata yi tunanin yin sallah ba ko kad'an dan bata bukatar abinda zai fitar da ita waje. Ladi ce ta dawo dakin dauke da yar karamar touchlight ta haska.

"Kiritta ce ko musulma?"

"Ban..." Da ban sani ba zata ce, sai kuma ta tuna, ta ja tsaki cikin kunar Tai tace

"Ina zanyi alwalar?"

"Taso muje, ni shaf na manta ma ashe kina sallah, da naji baki magana ba na dauka kiritta ce."

"Amma ai kinsan ni mace ce ko?"

"Taso kafin K'adari ya dawo da kurar nan, sun dan fita shawagi sai kiyi da jiki."

Da sauri Hajiya Zeenat ta mike tabi bayanta dan dama fitsari take ji, sai data fara tabbatar da babu kurar sannan ta yarda ta fito ta rakata kofar bayin da babu ko rufi sai dan zagaye shi da wanda idan kana tsaye tsaf za'a hango ka. Gefe ta samu tayi fitsarin dan babu yadda zatayi, ta fito tayi alwalar sannan ta koma ciki. Wata tsohuwar darduma ladi ta kawo mata tace ta barshi zata shinfida dankwalin ta, juyawa tayi da kayarta ta bar mata touchlight din ta yi sallar sharp sharp ta idar ta zauna jigum sai taji motsi alamun wanda aka ce ya fita da kurar ya dawo, kara nutsuwa tayi ta dauki ruwan a ba yadda zatayi tasha kad'an ta ajiye.
Kayan abincin da Aryan yasa a siyo mata Buba ya kawo dama abinda ya fitar dashi tun rana kenan, maimakon akai dakin da take sai Ladi tace akai mata dakin ta dan so take sai ta koya mata hankali sannan zata kyale ta, katifar dai da maganin sauro ta bawa ladidi ta kai mata ta shinfida mata da sabon bedsheet dan karami sai pure water leda biyar. Ta dan ji dama dama da aka kawo karamar katifar da ruwa da maganin sauro, sai dai kuma taji babu dadi dan alamu sun nuna bata da shirin tafiya yanzu kenan.

***Kamar yadda Aryan suka tsara da Hydar haka akayi daga office ya wuce airport kai tsaye yana zuwa suka taso zuwa Kano. Yana sauka ya wuce gidan Adda Maimuna bayan ya kira Muhammad ya sanar dashi zuwan sa. Sai da ya isa gidan ya huta sannan ya kira Aryan yace masa ya sauka. Gashi nan zai zo ya dauke shi yace masa sannan suka ajiye wayar. Muhammad da suke zaune tare ya kalle shi cikin son Karin bayani yace

"Kamar dan rainin hankalin nan ko?"

"Wai Aryan?"

"Eh shi, guy din nan ko? Hmm amma ba komai haka Allah ya kaddara."

"Toh ya za'a yi da abinda Allah ya kaddara?"

"Haka ne, amma ni sam be yi mun ba, bai kuma dace da Raihana ba, sai uban girman kai da nuna shi ya isa."

"Calm down bro, komai ya wuce please a daina tuna baya, Allah zai musanya maka da mafi alkhairi ."

"It's hard ai, kawai kai dai ayi sha'ani."

"Na sani, ayi hakuri dai."

"Wai ko tsoron sa kake ne?"

"Tsoro? Me yasa zanji tsoron sa?" Yace a dan hasale dan dama akwai shi da saurin tunzura kamar Aryan din

"Naga kana goyon bayan sa ne."

"Yanzu shi yake auren kanwata, ko ina so ko bana so I have to respect the fact that mijin tane."

"Ok ok, naji shikenan?"

Mikewa Hydar yayi dan har ga Allah Muhammad din ya bashi haushi sosai.

"Na fita ba lallai na dawo yau ba, zan samu hotel na zauna kawai."

"Saboda nayi magana?"

"Yes, bana so a zarge ni da abinda bashi bane ba."

Sai ya fita, ya bar Muhammad din a tsaye. Biyo shi yayi ya tarar dashi a waje yana jiran Aryan din ya tsaya gefensa yana kallon yanayin fuskar sa, zai yi magana Aryan din ya shigo layin. Fasa maganar yayi yaji duk ransa ya baci ganin Aryan din sai kawai ya juya ya koma ciki. Aryan na ankare dashi dan yana shigowa layin dashi ya fara ankarewa. Parking yayi a gaban Hydar din ya sauke glass din. Bud'e kofar side din me zaman banza Hydar yayi ya shiga ya mika masa hannu suka gaisa sannan Aryan din ya ja suka bar wajen.
Gidan ya Nabeela ya wuce dasu kai tsaye don yana so yaga Raihana dan ko da yace zai koma jiyan be koma ba sun dai yi waya da daddaren dan har sai da yaga ta fara hamma sannan yace ta kwanta suka ajiye wayar ya shiga wani aikin.
Tana falon ya Nabeelan suna hira tana tsefewa Amal kanta suka shigo da sallamar su, wani yar taji tun daga kanta zuwa kafafunta amma sai ta kasa dagowa ta kalli kofar duk da tana jin idanun sa akanta yana takowa cikin falon Hydar na biye dashi a baya. Riga ce me gajeren hannun a jikinta da dogon skirt sai Chantilly Cap da ta rufe gashin kanta. Maganar Hydar yasa ta dago da sauri dan bata yi zato ko tsammanin ganin sa ba. Fuskarta ce ta fadada da fara'ah

"Hamma na?"

"Umm kanwata, sai gani."

"Sannu da zuwa." Ya Nabeela tace tana murmushi

"Yawwa sister, sannu da gida."

"Yawwa, ya hanya anzo lafiya?"

"Lafiya lou, mun same ku lafiya?"

"Alhamdulillah wallahi."

"Hamma ina wuni?" Tace a kunyace tana satar kallon Aryan da yake kokarin zama kan kujerar da take.

"Lafiya lou."

"Ya Nabeela... Ya gida?"

"Lafiya lou, Aryan."

"How are you?"

Yace muryar sa k'asa-kasa yadda ita kadai zataji. Sunna kanta kasa tayi ba tare ta amsa ba. Murmushi yayi kawai dan dama yasan ba zata amsa ba. Mai aikin Ya Nabeela ce ta kawo musu juice da ruwa Hydar na lura da yadda Raihana duk ta takura. Mikewa tayi zata bar falon ya tsaida ita.

"Raihana, banga kin gaida Aryan ba."

Diriricewa tayi, shi kuwa gogan ya coge yana kallon yadda zatayi.

"Um um... Dama."

"Ta gaishe ni, kasan gaisuwar couples sai ka kura kunne sosai zaka iya ji." Aryan ya fada yana yin baya akan kujerar. Kallon sa tayi da sauri ya kashe mata ido daya tayi saurin dauke kanta tana murmushi

"Umm lallai, abun na masoya na Kenan". Ya Nabeela tace tana dariya.

"Yunwa nake jiiii." Yace yana kallon Raihanan kamar itace me gidan.

"Kanwata kawo wa mijinki da yayanki abinci."

"Yanzu naga cin abinci a gidan Adda Maimuna wallahi."

"Ka ci dai ko babu yawa ai."

"Toh ya Nabeela." Yace yana murmushi

Kitchen din Raihana ta wuce ta hado musu abincin akan tray ta dawo falon, ta tarar Ya Nabeela ta tashi Hamma Hydar yana tsaye a jikin console yana waya sai Aryan din a zaune. A kasan rug din ta ajiye daidai saitin gaban sa. Ta yunkura zata tashi ya kamo hannun ta yana kokarin saka idanun sa cikin nata. Kin kallon sa tayi ya shiga murza hannun a hankali a hankali yana kashe mata ido daya.

"Zuba min."

"Ok." Tace ta durkusa ta shiga zuba abincin a hankali, zamowa yayi ya zauna ya rike hannun ganin tana ta cika plate din dan ba wata yunwa da yake ji kawai so yake kar ta tafi. Dawowa Hydar yayi wajen ya zauna a k'asan ta dauki wani plate din zata zuba masa Aryan yace ta barshi suci tare dan shima ba wani ci zai ba. Tashi tayi ta basu wajen suka ci abincin sannan ya Nabeela ta dawo suka cigaba da hira har kusan magriba sannan suka tafi. Direct main house suka tafi tare dan so yake ya sanar dashi komai tun daga kan binciken sa da kuma abinda suke shirin yi a goben dan yaga karar Hydar din ma sosai da be tambaye shi ba.
Bayan sun yi sallah suka zauna a dakin Aryan din ya bud'e masa komai, ba karamin mamaki da kaduwa Hydar ya shiga ba, dan sai da ya zubar da hawaye, idan abinda suke tunani ya zama gaskiya wanne irin farin ciki Abby zai? Dadah, Raihana,Lamido da Sadeeq? Ji yayi gabaki daya ya kagu yaga goben tayi, dan baya jin ma zai iya runtsawa.
Da asubah bayan sun dawo daga masjid wani tunani ya zo wa Aryan, wayar sa ya dauka ya kira Ya Nabeela yace zasu je wani waje da Raihana da Hydar idan ba damuwa. Toh tace kawai bata kuma bi baasin ina za an ba tunda dai matar sa ce. Dakin Raihanan ta wuce ta same ta tace ta shirya Aryan zaizo da Hydar zasuje unguwa. Da murnar ta, ta hau shiryawa dan yace zuwa bakwai yake so su tafi. Tana shiryawa yayi mata text message yace ta dau spare kaya two set, mamakin in da zasu yasa ta kusan makara da shiryawa a gurguje ta karasa ta sha tea da biscuits saboda yayi wuri sosai ta iya cin abinci me nauyi. Zuwa sukayi ta fita lokacin ma Ya Nabeela ta koma bacci sunyi sallama. A shirye shima Adam suka fito suka rufa musu baya, office Aryan ya fara zuwa ya fito ya dawo kujerar baya kusa da Raihanan Malam Yahya driver ya shiga mazaunin sa yaja motar suka dau hanya.


**RQ**

57

***Dan satar kallon sa tayi ganin ya dawo bayan, gaba daya attention din sa yana kan wayar dake hannun sa. Kauda kanta tayi zuwa windown ta zurawa tagar ido cikin tunanin in da zasu haka kuma har da hamma hydar. Kamar ba shi ba ma dan tunda suka shigo motar be yi magana ba, bare kuma Aryan din da dama shi ba gwanin magana bane ba. Ya dau kusan mintuna sha biyar akan wayar tasa kafin ya kashe ta ya ajiye ta a gefe sannan yace

“Kunyi magana da Lamido ne?”

“Eh munyi, yace be samu flight din safe ba sai dai na 12pm.”

“Ok, Kamal ma yace yana hanya duk da nace masa noo, Ya dage sai yazo. tafiya ce me dan tsawo, inaga sai dai ma su same mu a gida kawai idan abinda muke so ya tabbata muna zuwa in sha Allah zamu juyo ai.”

“I hope so, amma dai inaga so dai suke ayi komai suna nan, ban zata Lamido zai samu time haka ba.”

“Dole ne ai, idan ka duba muhimmancin abinda za’a yi din.”

“Haka ne, Sadeeq dai ban sanar dashi ba, kasan Shima he’s always busy a hospital plus nasan yana da wani surgery da zai yi yau a private hospital dinsu bana so na raba masa hankali.”

“Yeah it’s good da ka kyale shi, mu ma mun isa ai.”

Sai ya juyo da kallon sa kan raihana da tayi tsam tana son fuskantar abinda suke cewa din amma ta gaza gane komai.

“My wife.” Yace yana dan jan jikin sa kadan zuwa bangaren ta sannan ya kwanto da kansa gefenta.

“Umm.” Tace a hankali ya sa hannu ya dauki wayarta dake saman cinyarta ya kunna, hoton ta ne akan wallpaper din sanye da khakhi na Nysc tayi murmushi me kyau da ya kara fito da ainahin kyawunta sosai.

“Corper.” Yayi dariya da ya tuna sunan da yake fada mata. Murmushi tayi itama ya ajiye wayar a inda ya dauka Maimakon ya tashi zaune sosai sai ya dora kansa a saman cinyar tata ya kulle idon sa.

“Jiya banyi bacci sosai ba. Bacci nake ji sosai.”

“Me yasa?”

“Ina ta tunani, kaina kamar zai fashe na saka wannan na warware.”

“Ok, ayya.”

Shiru yayi idon sa a kullen amma ba bacci yake ba, kasa nutsuwa tayi har sai da ta furta

“Ina zamu?”

Bude idon yayi ya zuba mata su akan fuskar ta, tayi saurin janye idonta ganin yadda kallon nasa yayi tasiri akanta.

“Siyar dake za muyi,Hydar nawa ma akayi cinikin kan ta?”

“Wa fa?” Hydar yace yana waigowa bayan dan ba jin hirar su yake ba. Da hannu Aryan ya nuna masa raihana sai hydar yasa dariya

“Kan kanwata ai me daraja ne, ba zai siyu ba.”

Tashi zaune Aryan yayi jin wayar sa tayi vibrating, dubawa yayi sannan yace

“Malam Yahya duba side mirror akwai masu bin mu ko?”

Kallon side mirror Malam Yahya yayi sannan ya kalli rear mirror ya gida kansa.

“Na lura kamar ana bin mu tun dazu, ganin yadda suke kokarin bin bayan mu sai da kafa ba tare da sun zo sun wuce mu ba duk kuwa da yanayin tafiyar da muke a hankali.”

Murmushi Aryan yayi, hydar ya waigo yana bukatar karin bayani

“Nasan suna bin mu, Adam ne tare da yaran Hajiya Zeenat.”

“Ka sani?”

Gida kai Aryan yayi,

“Yaji convo dinmu da Kamal, na ganshi ta jikin window din kitchen sanda yake eavesdropping ma conversation dinmu, shisa na bashi damar yaji komai dan nasan dama abinda zai yi kenan, zai biyo mu not knowing zai fadama trap ne.”

“Woaw! I’m impressed.” Hydar yace yana murmushi, be san Aryan din yana da basira haka ba, dan wani kallo yake masa duk da yaga kokarin sa sosai ko akan case din Abby Amma be dauka haka yake ba. He act calmly kamar ba wani abu bane ba ma. Menene trap din? Menene kuma plan din da Ya shirya?

“Malam Yahya muje kawai, ka lura sosai da moves din su, hydar watch from your side,”

“Ok.” Hydar yace yana kallon mirror side din shi ya kara tabbatar da, da gaske bin sun suke.
A nutse suke tafiyar duk kuwa da doguwar tafiya ce, yana cikin plan din Aryan din dan ya riga yayi calculating hour nawa zasuyi covering akan speed din da suke kai. Wani messege din ne ya sake shigo masa, ya kalli wayar sannan yace

“Taka motar nan malam yahya.”

Take motar malam yahya yayi suma sai suka taka tasu, abinda ya bawa raihana matukar tsoro, tayi saurin riko shi tana matsowa jikin sa sosai. Riko ta yayi ya sakata a jikinsa ta makalkale shi. Hannun ta ya kama ya saka cikin nasa ya damke yana mata dariya.
Idan kana neman kwararre a tuki ka samu malam yahya ka gama, dalilin da yasa Aryan ya zabi tafiyar tare dashi kenan dan yasan dama hakan zata faru. Kokarin bace ma su Adam din suke amma suma sun rike wuta gashi dama hanyar ba kowa sai yan motoci jefi jefi.
Daf da zasu shiga garin ne wajen wani karkacewa da titin yayi Aryan yace malam yahya ya dauke hanya, abinda ya jawo suka bace wa su Adam, wani irin ihu Adam yayi kamar zai damki kan sitiyarin ya buga jikin dashboard cikin bacin rai yace driver ya sauka daga titin ya gangara kasa. Gangarawa suka yi ya hau duddubawa dan basu ga alamun hanya a wajen ba, sai wannan dai titin guda daya tal da suke kai.
Tafiya suka soma yi a cikin garin har suka iso garshen dan titin da babu kwalta akansa, parking sukayi daga chan gefe sannan suka fito, a kaida machine ake hawa daga nan sai a shigar da kai garin amma sai Aryan yace su taka a kafa har su karasa dan baya so raihana ta hau bayan machine din,

“Idan da nisa nake ganin gwara mu hau Aryan. “

“Daga nan zuwa gidan malam yakubu akwai nisa?”

“Malam Yakubu wanne?”

“Wani farin bafulatini, ya zauna a cikin gari kafin ya tattaro ya dawo gida.”

“Oh na gane, gidan Baffan Kudu yake nufi, da yar tafiya gaskia musamman Yanzu da tsuka tayi yabanya hanyoyin sun zama masu wahala dan idan ba kwakwaran sanin wajen kayi ba sai ka bata.”

“Ai ban ma san wajen ba, zuwan mu na farko kenan.”

“Ina ganin mu hau kawai su kaimu Aryan.” Hydar yace

“Ok, baba kai sai ka dauketa.” Yace yana nuna wani dattijo a cikin masu baburan. Girgiza kai hydar yayi, ya d’ane bayan machine dinsa. Taimaka mata yayi ta hau ya karbi jakarta ya saka a tsakiyar machine din tsakanin ta da baban sannan yace su yi gaba sai wanda zai hau yabi bayan su maana tana gaba yana bayanta kenan. Shi dai hydar be ce komai ba, burin sa kawai su isa, jikinsa yayi masifar sanyi ga wani irin tsoro, tsoron kar su tarar da labari mara dadi ko ace ba nan bane, duk da Aryan ya tabbatar masa da mutumin shine ya dauki ammyn kuma shine Hajiya zeenat take zuwa gani a lokacin.

***Babban gida ne da ya amsa sunan babban gidA, baki daya kauyen babu gida me girma da tarin mutane irin sa ba. Malam Yakubu shine Yanzu a matsayin babba a ahalin gidan kuma shine ya tatttara yanuwansa dukka ya hade kansu bayan ya tattaro ya dawo a lokacin da ake harin rayuwar sa. A duk safiyar duniya bayan sun dawo daga dubo gonar su su kan zauna a kofar gidan a shinfida babbar tabarma su zauna su sha fara ko kunu da gaya ko koko duk dai abinda ya sauwaka kafin kananan ciki su wuce zuwa aikin gonar na ranar zuwa dagawar rana su sake tattaro wa su dawo gida suci abinci tare. Babban abinda mutane da yawa basu gane ba shine cin abinci tare yana matukar kawo shakuwa tsakanin yan uwa, miji da mata da sauran su. Babban Dalilin da yasa suke da matukar hadin kai kenan suna kuma girmama Malam Yakubu a matsayin sa na babba suna kuma mutunta duk wani abu da ya jibance shi. Karar shigowar mashinan ya sa suka maida hankali wajen ganin su waye suka zo? Ganin baki ne yasa suka ajiye abinda suke a gefe. Gaban malam Yakubu ne ya fadi, daidai lokacin da raihana take sauka daga machine din, bata da maraba da Ammy sam, nan take ya gane su waye da kuma abinda ya kawo su.

“Sani matsar da kayan nan gefe, sannun ku da hanya.”

“Yawwa.” Suka amsa a tare sannan suka zauna a gefen tabarmar bayan sauran duk sun tashi, gefe Raihana ta samu ta tsuguna ya cigaba da satar kallon ta ganin tsananin kamar tasu. Gaishe shi sukayi sannan aka gaisa da sauran yan uwan sai malam Yakubu yace duk su koma bakin aikin su, su basu waje. Ba musu kowa yayi nasa waje ya rage sai su kadai.

“Yan samari ban gane daga ina ba.”

“Daga kano muke.”

“Toh toh Masha Allah, me ke tafe daku.”

“Munzo akan maganar mahaifiyar mu ne dama.” Aryan yace

“Madallah, jini na karya ba, tun da kuka nufo mu nake kallon fuskar innar yara da wannan Baiwar Allar, kamar ta baci matuka. Ya gida ya hanya?”

“Alhamdulillah.”

“Anzo lafiya dai ko?”

“Alhmadulillah.”

“Toh Madallah, me kuke son sani game da mahaifiyar taku?” Ya tambaya

“Munzo ne muji idan tana raye, muna so mu ganta.”

“Menene sunan mahaifiyar taku?”

“Aisha Nasir.”

“Madallah, tana nan da ranta kuma a yanzu haka ma tana cikin gidan nan.” Ya nuna gidan nasu da hannu.

“Alhamdulillah! Suka hada baki wajen fada. Kallon rashin sani da fahimtar abinda yake wakana raihana take musu dan Itafa bata fuskanci komai ba.

“Zamu iya ganin ta ?”

“Sosai, me zai hana? Sai dai wani hanzari ba gudu ba…”

Duk sai suka tsaya suna kallon sa cikin tarradin abinda zai fada

“Mahaifiyar ku na raya kuma cikin koshin lafiya, sai dai ta gamu da wani iftilai a shekarun baya in da mota ta kade ta har ta kai kan ta yayi mugun buguwar da ta manta komai da kowa da ita karan kanta. Bata san wacece ita ba bare tasan komai akan rayuwar ta. Anyi mata magani a lokacin daidai gwargwado sai dai duk lokacin da mukayi mata maganar gida da dangin ta takan birkice mana tamkar ana saka guduma ko karfe ana buga mata kanta. Haka zatayi kwana da kwanaki tana ciwo na fitar hayyaci, da muka gano haka sai muka daina yi mata maganar, tun daga lokacin shikenan ta samu sauki, muka cigaba da rayuwar mu tamkar babu abinda ya faru.”

Shiru sukayi kamar ruwa ya cinye su, sai raihana da ta saka kuka a durkushen da take.

“Yanzu menene abun yi?” Aryan yayi ta maza ya tambaya

“Sati biyu da suka wuce na samu wani babban malami munyi maganar, domin tabbas ba kalou ba, anan ne yake tabbatar min ko dai anyi mata sihirin da aka raba ta da gida da danginta ne aka kuma saka mata tsanar su da tsanar waiwayar gida tunda bata shiga yanayin sai idan an mata maganar, dole sai anyi mata maganin sihiri idan har akwai shi toh sai an cire shi sannan zata iya dawowa daidai ta iya waiwayar danginta.”

“Ya Allahu!”

“Minti daya bari na daga waya.”

Aryan yace yana tashi ya matsa gefe shi kuma malam yakubu Ya cigaba da yiwa su hydar bayani. Kamal ne ya kirashi sukayi magana sama-sama sannan ya kashe, sakon ne ya sake shigo masa ya duba sai yaga yace sun samu shigowar garin gasu a inda ma sukayi parking din motar su. Komawa yayi ya zauna kusa da hydar sannnan yace masa

“Sun shigo suna wajen motarmu.”

Kallon sa Hydar yayi da idanun sa da suka dan chanja kala, gida masa kai Aryan yayi sannan ya kalli malam yakubu

“Baba dan Allah toh ko zaa shiga da ita ciki? Idan yaso ko maganar ce kar ayi mata tunda nasan ba gane ta zatayi ba.”



“Abinda zan ce kenan, taso yan mata muje ciki, ya sunan ki.”

“Raihana.”

Jerawa sukayi tare da Aryan din har kofar gidan

“Please karki yi kuka, komai zai wuce zamu san yadda za’a yi,just be strong kinji? For me.”

Gida masa kai tayi, ya tsaya daga kofar ita kuma tabi bayan Baba Yakubu zuwa cikin gidan kirjinta na dukan uku uku.
_*_*RQ_**

58


*****A tsaye take a gefen dakin ta, ba kasafai ta fiye fitowa a irin wannan lokacin ba, ta kan zauna a daki a mafiya yawan lokutan musamman idan gidan ya zama babu yaran duk sun fice. Yau tunda ta tashi gabanta ke faduwa kamar wani babban al’amari yana shirin faruwa da ita. Randar dake gefen dakin nata ta bude ta zuba ruwa a buta ta zagaya bayi domin kama ruwa sannan ta dan wasa kafarta ta dauke hankalin ta kuma daga tunanin dake bijiro mata. Fitowar ta kenan tana tattakowa a hankali zuwa kofar dakin nata tana kallon yanayin yadda rana ta bude kwal kamar irin azahar din nan sosai. Sallama taji ta Malam Yakubu yana shigowa cikin gidan, lullubin dake kanta ta ja ta gyara zuwa saman kafadarta sannan ta amsa masa jin kulin ta Ya shigo kai tsaye, a bayansa muryar

Please Login or Register in order to submit comment