You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsaye ba tare da neman excuse ko knocking ba, ya murd'a kofar ya tura kansa ciki.

Wanka tayi ta fito tana zaune tana shafa lotion din jergens a fatar jikin ta da tayi wani irin sulbi da kyau. Big size pink tpwel ne daure a jikin ta wanda ya sakko sosai ya rufe bayanta zuwa saman sangalalin kafarta. Bata kawo shigowar kowa a lokacin ba dan manta bata murza key din bayan fitar Ya Nabeelan ba. Dakin a share yake tas tas sai kamshin turarukan da Ya Nabeela ta hado mata ke tashi a dakin hade da kamshin room freshener din da moping mist sai ya bada wani irin kamshi me sanyin dadi.
Farko da taji an murd'a kofar ta dauka Ya nabeela ce duk da bata shigowa kai tsaye kuma ba zata so ya ganta haka ba da kunya amma bata yi yunkurin tashi ba saboda ta riga tasan kafin tace ta tashi ta riga ta shigo dan haka gwara ta zauna a haka da ta tashi kuma ta shigo sai kunyar tafi haka. Kamshin turaren sa ne ya fara iso mata kafin shi din da kansa ya bayyana a tsakiyar dakin kasancewar dakin bashi da wani girma. Matsananciyar kunya ce ta rufe ta, ta sunkuyar da kanta ta gagara ko da kwakkwaran motsi ne. Be tanka ba, be kuma matsa daga in da yake a tsaye ba yana kallon ta yana nakaltar yanayin da ta shiga. Tun daga saman kanta zuwa yan yatsun kafafuwanta ya bi da kallo kafin ya ajiye idon sa akan gashin kanta da yake a bud'e kuma a sake ba tare da ta saka ribbon ta kama shi ba. Kusan mintuna uku ya dauka yana tsaye a wajen da yake kafin ya tattaro kansa yace

"Tashi kisa kayan ki."

Kasa tashin tayi dan tasan idan ta tashi toh kunyar sai tafi ma ta yanzu.

"Tashi kisa kayan ki ko nazo na saka miki da kai na." Ya sake fada mata cikin muryar sa da take nuna gaskiyar abinda zai iya aikatawa din. Kamar ta rushe da kuka haka ta tashi tana kara jan towel din duk da ya ma.sauka sosai ta cigaba da jan jikinta tana matse shi har ta karasa wajen da kayan nata suke, ta bud'e wardrobe din hakan ya bashi damar ganin bayan nata sosai. Taune k'asan lips dinsa yayi ya kad'a kai ya karasa wajen da ta tashi ya zauna yana daukar lotion din nata ya hau duba jikin container din. Ganin kamar hankalin sa baya kanta tayi saurin daukar kayan zata shiga toilet, ya dakatar da ita ba tare da ya kalle ta ba, ya cigaba da duba abinda yake dubawar. Fasa shiga toilet din tayi duk da ba haka taso ba, ta dauki doguwar rigar da ita kadai take jin zata iya sakawa ba tare da ta kara kunyata ba, ta doro ta a saman towel din, tana kokarin zura kan rigar taji an rik'e rigar kam. Kicin-kicin sakawa ta hau yi ya hanata duk wani yunkurin ta, ya saka hannu ya fincike rigar daga kanta ya ya rungume ta a jikinsa. Saura kiris ta saki towel din saboda yadda ta shiga shock, sai taji ya tayata rike shi saboda kar ya saukan abinda ya bata mamaki ta kalli fuskar sa ya dan harare ta kad'an sannan yace

"Idan na sake towel din nan ya fadi ai na kad'e har ganye na, dan haka ki kara rike shi gam, so kawai nake naji wani abu."
Yace yana kashe mata gira. Barin kallon sa tayi dan ta gane abinda yake nufi tayi gajeran murmushi ba tare da ta bari ya gani ba. Sai da yayi kamar minti biyu sannan ya saketa yana matsawa baya

"Kiyi sauri kisa rigar."

Da sauri ta rarumi rigar ta sake dorata akan towel din sannan ta zare shi ta kasa.

"Zonan."

Wajen da yake zaune ta je, ya nuna masa gefen sa da hannu yace ta zauna, ta zauna tana sadda kanta k'asa. Gashin ta da yake har lokacin a yadda yaken ya kai hannu ya gyara mata shi yayi baya sosai, sannan ya tallafo fuskar ta da hannun sa suka kalli juna.

"Magana nazo muyi Raihana." Yace yana kara saka idon sa cikin nata ya kuma hanata dauke natan saboda ya kara samun tasiri akan ta da abinda zai fada matan,da kuma labarin da yake so ta bashi.

"Labari nake so ki bani."

"Labarin Ammy."

Yanayin ta ne ya sauya a lokaci daya, ya hangi wani irin abu me girma a cikin kwayar idon ta, wanda ya karasa kashe sauran kuzarin da yake dashi da karsashin sa, hade da wani irin matsananciyar soyayyar ta me zafin gaske dake shigaar sa tana huda shi. Lips dinta da suka yi fresh ya kalla, ya sunkuyar da kansa yayi kissing dinsu kad'an sannan ya gid'a masa kanta yana damke hannun ta a cikin nasa dukka biyun yana son tabbatar da ta ta samu nutsuwar da yake bukata daga gareta. Motsa bakin ta, tayi tana son fara magana tana kuma tunanin ta yadda zata fara.

"Come here."

Yace yana bud'e mata hannun sa, bata ki ba, ta shigo jikin nasa lamo kirjinsa ya hadu da nata ya haifar masa da wani yar. Da sauri ya dago ta ya zuba wa wajen kallo ya tabbatar da abinda yake son tabbatarwar. Murmushi ya yi me taushi ya sake rungumota yana son jin su sosai a jikin shi duk da hakan zai iya sanya shi wuce gona da iri amma zai yi takatsantsan har ya samu abinda yake son samun.

***TUNA BAYA





****Alhamdulillah.. Jamaaa sai bayan azumi ko?👏😊😁 Allah ya kawo mu wata me alfarma, Allah ya sa muyi azumi lafiya mu gama lafiya, ya sa muna cikin bayin da za'a yanta idan Allah ya kaimu. Ina barar adduoin ku dan Allah musamman akan ido, ina fatan zaku sakani cikin addu'ar ku a wannan azumin dan yana cikin abinda ya ke kawo mana tsaiko a kowanne lokaci. Ayi hakuri naso gama book din a Yan kwanakin nan amma hakan yaci tura sakamakon ido da ya matsa min sosai kuma bana so na gajarce labarin.Wanda na batawa ko zafafa suka batawa dan Allah a yafi juna, Allah ya kaimu da rai da lafiya kamar yau ne idan muna da rai da lafiya

*RQ*

    ** _53_**

_Hafsat Rano_





***TUNA BAYA

Kokarin daidai ta kanta Ammy tayi ganin bata da kowa da komai a yanzu sai Allah sai yaran ta dake biye da ita wadda gaba daya kulawarsu take karkashin ta. Idan ta nuna karaya dole suma zasu karaya har a samu matsala wadda ba zata so ba. Tashar Kano line suka nufa duk da bata da wani ishashen kudi a hannun ta dan babu wani abu da suka bar ta, ta dauka sai yan abinda ba za'a rasa ba. Motar Kaduna suka samu suka hau Lamido rike da Raihana da ta kwanta lamo a jikin sa sai Babbo Sadeeq da Hamma Hydar a gefen sa sai Ammy din. Bayan gaba daya ta siye musu dan idan aka ce za'a karo mutum daya zasu takura saboda haka nan da nan motar ta cike suka dauki hanyar barin Kano zuciyar ta a chunkushe da tayi mata wani irin nauyi. Bata neme dangin Abby ba sam dan su ma basu neme su ba tunda aka fara case din kuwa dan dama ba wani shiri suke sosai saboda babu idanun mahaifan su, tasan babu wani abu da zasu iya yi mata shiyasa ma ta yanke shawarar zuwa nata dangin kafin ta san abinda ya kamata tayi. Tunda suka dauki hanyar babu wanda yayi kwakkwaran motsi a cikin yaran har Raihana da ba wani wayo ne da ita sosai ba, sau daya tace ruwa wani bawan Allah dake gaba ya miko mata gorar ruwan dake hannun sa Lamido ya karba ya bata tasha ya maida masa yace su barshi ko zata bukata,godiya Ammi tayi daga nan basu sake magana ba har bacci ya dauke Raihanan a jikin Lamido, Hamma Hydar kuma ya kwanto jikin Ammy shima yayi baccin ya rage sai Babbo Sadeeq da Lamido kawai.

"Ina zamu Ammy?" Lamido ya furta k'asa-kasa yana kallon sashen da Ammyn take.

"Gidan Adda Fatima zamu Ibrahim."

"Ok." Yace ya sake yin shiru yana kallon hanyar yana tuna cin kashin da akayi musu wajen fitar dasu daga gidan.

***Shigar dare sukayi wa garin na Kaduna saboda yanayin tafiyar lokacin da suka taso ma yamma ce dan haka basu isa da wuri ba gashi sai da suka tsaya a hanya sau biyu ma abinda ya kara delay din kenan. A gajiya suke tikis Raihana ta tashi Ammy ta karbe ta daga wajen Lamido suka samu motor da zata kaisu unguwar su Adda Fatiman wadda ta kasance kanwa a wajen Daadah kuma wadda suka fi shakuwa sosai da Ammyn a kaf yan uwan su. Kasancewar ta san da zuwan su Ammy ta sanar da ita yasa tuni ta saka an gyara musu dakin da zasu zauna ana jiran isowar su. Jiki a sanyaye suka shiga gidan ga gajiya da wata irin yunwa da suka kwaso Raihana sai dan kuka take saboda wahala. Da fara'a ta tarbe su suka gaisa ta dauki Raihana ta rike ta cike da tausayin Ammyn da yaran. Abinci yaran suka fara ci ita kuma Ammy ta yi alwala ta hau ramakon sallolin da suka wuce ta, bayan ta idar sun gama cin abincin tasa Lamido ya jasu sukayi alwala sukayi sallar suma sannan suka kwanta.
Abincin Adda Fatima ta ce taci, duk da bata da appetite amma haka ta dan ci kad'an saboda karfin jikinta sannan suka koma dayan dakin ta shiga bata labarin komai tana kuka sosai. Sosai Adda Fatiman ta tausaya mata dan sai data zubar mata da kwalla sai dare sosai suka kwanta duk da babu wani baccin kirki da ammin zata iya yi a lokacin. Juye juye ta dinga yi ta saka wannan da kwance cikin son samun mafita ganin ba zai yiwu ba yasa ta mike ta kara dauro alwala tazo ta hau sallah domin kai wa Allah kukan ta.

***Kwanan su uku a gidan Adda Fatima suka hau shirye shiryen tafiya Adamawa domin Dadah tace ta taho gida zaman anan ba zai yiwu ba ga yara, dama itama tana da niyyar tafiyar a kwana daya ma dan dai addan ta hanata ne shiyasa ta hakura ta zauna din amma yanzu da Dadah tayi magana dole ta hakura ta barsu su tafin itama zata fi sakewa a gidan su kafin ta san abinda ya kamata tayi. Da asussubah suka dauki hanyar Adamawa saboda su samu su isa da wuri dan babu dadi tafiyar dare ga yara.
Zuwan su Adamawa ya dan rage wa Ammy abubuwa da yawa musamman na daga nauyin da take ji a kirjin ta da ya zo ya tokare ta ko ruwa ta hadiya sai taji zafi, Dadah ta tsaya mata sosai da ban baki da shawarwari sannan ta dauke mata duk dawainiyar yaran sai dai kawai ta zauna shiru tana tunanin yadda rayuwa ta sauya musu lokaci daya tayi tafiyar yaji da farin cikin su ya tarwatse ya barsu da tarin bakin ciki irin wanda yake da nauyi da wahalarwa. Ta ina zata fara ne? Haka zata hakura ta zuba ido ta bar Mijinta a irin wannan halin? Gashi bata da komai bare tace zatayi wani hubbasa wanda take ganin ko zatayi din ma ba zata iya karawa da Alhaji Ibrahim Mukaddas ba. Bata da zabi illa ta koma Kano ta je ta same shi, ta nemarwa mijinta gafara ta hanyar tunasar dashi dah da rayuwar su ta baya, wala Allah ya iya sauraron ta ya farfado daga ramin da ya shiga. Ire-iren wadannan tunanin take yi a ko da yaushe har tafiya ta soma mikawa. Basu da wani arziki dan ita kanta Dadah ma fama take da kanta dan ma mace ce me neman na kanta da kokari sosai. Dalilin da ya hanata waiwayen Kanon kenan ta maida rayuwar ta kachokam wajen kula da yaran ta da suke bukatar ta, babu batun maganar makaranta a yanzu saboda bata da kudin da zata iya sakasu a irin makarantar da suke yi a chan sai aka saka su islamiyya suka fara zuwa kafin komai ya daidaita.
Watan abby hudu da rufewa aka bada damar zuwa a ganshi dan ko barin ganin shi ba’a yi ba tun lokacin nan. Cikin tsananin farin ciki ammy ta hau shirye shiryen tafiya ganinsa sannan ta samu ta je taga Alhaji Mukaddas ta roke shi. Lamido yaso zuwa amma tace su yi zaman su ita kadai zata je wanda ba haka yaso ba dan yana so yaje yaga Abbyn amma kuma dole ya hakura dan raihana ma rigima zatayi idan suka tafi. Ita kadai ta shirya ta dauki hanya bayan ta dan masa siyayyar abubuwan da zata kai masa ta isa kanon ta sauka gidan wata yar uwar abbyn da suke shiri ta kwana sannan ta nufi prison din da safiyar asabar din domin ta samu ganin sa. Ta dade sosai a layi tana jira har layi yazo kanta aka bude mata ta shiga ciki aka bata tag ta saka a wuyanta sannan suka shiga ciki sosai har zuwa wani dan madaidacin daki me dauke da dogon benci. Zama tayi tana kallon wajen a hankali jikin ta a sanyaye tana cike da zulumin ganin sa. Tare da wani ganduroba suka shigo yana sanye da dark blue uniform na yan prison yayi wata irin rama da baki tamkar bashi ba. Da sauri ta mike tsaye hawaye na zubowa a idon ta, ya dan yi murmushi kadan cike da farin cikin ganin ta ya girgiza mata kai alamar kar tayi kuka sannan ya zauna itama ya ce ta zauna ta zauna tana cigaba da kallon sa.

“Ya yarana?” Yace tana zama dama kuma tasan su zai fara tambaya

“Suna Adamawa.”

“Adamawa?”

“Umm, chan muka koma ai.”

“Me yasa!?”

“Ba komai, kana lafiya?”

“Toh, kamar yadda kika gani dai, Alhamdulillah ala kulli halin.”

“Baka cin abinci ne?”

“Abinci Aisha?” Yace sai yayi wani irin murmushi kawai da yasan maanar sa shi kadai

“Kuna lafiya? Babu wata matsala dai? Me yasa kuka koma adamawa?”

“Lafiya lou.” Ta share wasu hawayen da suka sake sakko masa, bata son sanar dashi an kore su ne ta sake tashar masa da hankali amma ta ga alamar ba zai kyale tambayar ba

“IBRAHIM ne ya tashe ku?”

“Mu ne kawai muka tafi.”

“Karya ne, ban yarda ba.”

“Me yasa?” tace tana kokarin boye damuwar da take ciki. Girgiza kansa yayi sannan yace

“Nasan babi dalilin da zai saku tafiya, me yasa zai min haka? Me yasa?” Ya furta cike da bacin rai

“Ban sani ba nima.”

Shiru yayi be ce komai ba, sai wani irin harbawa da zuciyar sa take yi cikin tsananin bacin rai ya hadiya wani abu be ce komai ba, dan bashi da abinda zai ce din dama kuma dan a halin da yake ciki babu abinda zai iya yi.

“Karka damu dan Allah, muna nan lafiya suma yaran saboda nisan da kuma bana so suzo su tashi hankalin su shiyasa ban zo dasu ba, amma suna lafiya dukka.”

“Shikenan, ba komai. Akwai wata bakar jakata ina fatan kun dauke ta, akwai debit cards dina a jikin wata wallet dina sannan akwai dayar wayar nan tawa a ciki itama, zai muku amfani.”

“Basu barmu mun gama daukar komai ba, amma yanzu zanje gidan zan duba na gani.”

“Lokacin ki ya cika hajiya.” Ganduroban dake zaune a dakin yace yana mikewa tsaye. Kallon Abbyn tayi idonta na sake ciccikowa ta kalli kayan da tazo dashi tace masa gashi, gid'a kansa yayi ta mika masa kudin dake hannun ta da nufin bashi ganduroban yayi saurin fizgewa yana kalle kalle.

"Ba'a ce miki banda kudi ba? Idan ma zaki bayar dole mu zaki bawa." Yace yana muzurai gami da chusa kudin cikin aljihun sa, sannan ya nuna mata kofar fita da hannu

"Sai anjima."

Da wani irin sauri ta fice saboda kukan da ya taso mata gaba daya bata kuma son yi a gaban Abbyn.

***Abun hawa ta tsayar bayan ta fito daga prison din ya dauke ta zuwa unguwar tasu, duk da bata da tabbacin samun abinda taje nema din amma kuma dole zata gwada sa'ar ta dan suna bukatar kudin sosai. A gaban gate din gidan nasu ya ajiye ta, ta bashi kudin sa ta sauka tana kallon katoton padlock din da aka makala a jikin kofar. Matsawa tayi gaban dayan gidan ta saka hannu ta kwankwasa gate din tana daidaita kanta saboda gaba daya zuciyar ta tayi masifar yin weak kamar zata zube a wajen haka take ji. Gateman din ne ya leko ta dan opening din wajen kafin ya saki abun ya juya zuwa wajen su Hajiya zeenat da Daddy dake shirin fita ya duka cikin girmawa yace

“Hajiyan gidan chan ce tazo.”

“Hajiya? Ban gane ba?”

“Makotan dake dayan gidan da suka tashi kwanaki.”

“Aisha?” Daddy yace yana kallon Hajiya Zeenat

“Shigo da ita Moses.”

“Ok.” Yace ya juya da sauri.

“Me ya kawo ta?”

“Bari tazo muji.” Tace tana murmushi

Yana gaba ammy na biye dashi a baya suka nufo su, idon su a kanta da yadda tayi wata irin rama da baki, murmushi hajiya zeenat tayi tana da yakinin zuwa yanzu Ammyn ta gama tantance wacece ita.

“Kawata kece da tsakar rana haka?”

Motsa bakin ta, tayi ba tare da tayi magana ba dan ji tayi bakin yayi mata nauyi sosai.

“Muje ciki ko?” Daddy yace yana yin gaba.

“Muje Kawata.” Tace tana mata murmushi. Bin bayan ta ammy tayi cike da zulumi da tsoro dan ta gama tabbatar da rashin imanin Zeenatu ya wuce duk yadda take tunani

*_ZAFAFA BIYAR COMPLETE DOCUMENTS_*


*ZAFAFA BIYAR BACTH A*


1.. _WUTSIYAR RAƘUMI_ 350
*(Bilyn Abdul)*


2.. _KAI MIN HALACCI_ 350
*(Miss xoxo)*


3.. _BURI DAYA_ 350
*(Mamu gee)*

4... _DAURIN BOYE_ 350
*(Huguma)*

5... _SAUYIN KADDARA_ 350
*(Hafsat Rano)*

_Duka biyar 1500_

*___________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BATCH B_*


1... _DAURIN GORO_ 350
*(Hafsat Rano)*

2... _ALKAWARIN ALLAH_ 350
*(Huguma)*

3... _QAUNAR MU_ 350
*(Mamu gee)*

4... _IGIYAR ZATO_ 350
*(Miss xoxo)*

5... _GUDU DA WAIWAYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH C_*

1... _MIN QALB_ 350
*(Mamu gee)*

2... _SARAN ƁOYE_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _KIBIYAR AJALI_. 350
*(Miss xoxo)*

4... _ABINDA KE CIKIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _SIRADIN RAYUWAR BILKISU_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*____________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH D_*

1... _ALKIBLA_ 350
*(Huguma)*

2... _DALAAL_ 350
*(Miss xoxo)*

3... _UBAYD MALEEK_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MABUDIN ZUCIYA_ 350
*(Hafsat Rano)*

5... _MAKAUNIYAR KADDARA_ 350
*(Bilyn Abdull)*


_Duk biyar 1500_

*____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH E_*

1... _SO DA ZUCIYA_ 350
*(Mss xoxo)*

2... _TAKUN SAAKA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

3... _HALIN GIRMA_ 350
*(Hafsat Rano)*

4... _DAB'IZAR ZUCIYA_ 350
*(Huguma)*

5... _DEEN MARSHALL_ 350
*(Mamu gee)*


_Duk biyar 1500_

*______________________________*


*_ZAFAFA BIYAR BACTH F_*

1... _BAKAR INUWA_ 350
*(Bilyn Abdull)*

2... _RAYUWAR MACE_ 350
*(Hafsat Rano)*

3... _NOOR ALB_ 350
*(Mamu gee)*

4... _MASARAUTA_ 350
*(Mss xoxo)*

5... _KUFAN WUTA_ 350
*(Huguma)*

_Duk biyar 1500_

*_____________________________*

*_ZAFAFA BIYAR BATCH G (COMPLETED)_*

1... _FARHATAL QALB_
*(mss xoxo)* 400

2... _GURBIN IDO_
*(Huguma)* 400

3... _SANADIN LABARINA_
*(Hafsat Rano)* 400

4... _INAYAH_
*(Mamu gee)* 400

5... _BABU SO_
*(Bilyn Abdull)* 400

_Kuɗinsu a yanzu 2K duk biyar_




*_ZAFAFA BIYAR 2023_*🔥🔥🔥
_*Sabuwar shekara sabon salo sabon taku,*_
_*Makaranta littafan hausa kuma masoya marubutan zafafa kuzo ga sabuwar tafiya zazzafa tazo karku bari ayi babuku *_

_*Zafafan alkaluman haziqan maruban zafafa biyar kowa yasan na daban ne,wannan karon ma sunzo da sababbin salo me kama zuciya.*_
_*ZAFAFAN MARUBUTAN SUNZO DA SABABBIN LITATTAFANSU NA 2023 Kamar haka,*_

1 _*IDON NERA*_
Mamuhgee

2 _*DAUDAR GORA*_ ciki ka shata
Billyn Abdul

3 _*RUMBUN QAYA*_
Hafsat Rano

4 _*KI KULANI*_ mallakin zuciyata
Hafsat Miss Xoxo

5 _*A RUBUCE TAKE*_ qaddarata
Safiya Huguma


_DUKA GUDA BIYAR DIN ZAKA SAMESU A FARASHIN 1200_

Guda 5 1200
Guda 4 1000
Guda 3 800
Guda 2 600
Guda 1 400

_*zaku saka kudin a wannan account din👇*_

_*0022419171 Access Bank Maryam sani*_

Saiku tura shedar ta👇

_*09033181070*_

Idan kuma katin Waya ne zaku tura katin MTN ta wannan layin👇

09166221261



TEAM ZAFAFA BIYAR🔥🔥
MUNGODE🙏🙏❤️


RQ

54


****Bata zauna ba ko da suka shiga dan hankalin ta be gama kwanciya da yanayin da Zeenatun ta nuna ba.

“Ki zauna mana kawata, kamar wata baku wa.”

“Ba zama nazo yi ba, abu nazo dauka a gidan mu da kuka kwace saboda tsantsar zalunci.”

“Da yaushe ya zama gidan ku Aisha?”

Daddy yace yana dariya

“Kafi kowa sani ai, saboda tsabar zalunci da rashin tsoron Allah kuka kwace.”

“Be sanar dake daidai ba, babu biyar dinsa a gidan nan saboda haka ba mallakin sa bane ba, sai dai ba zan hana ki daukar ahinda zaki dauka ba, kuje tare madam ta dauki abinda zata dauka kizo mu tafi kar mu makara.”

Yace yana kallon Hajiya Zeenat da tayi kamar bata falon tunda suka fara magana, tana kuma sane tana so ammyn ta gane babu wani abu da yayi saura tsakanin su da Daddyn idan ba tazo da niyyar rokon sa ne. Dama kuma abinda tazo da niyyar kenan sai dai furucin Daddy ya wargaza duk shirin ta na neman wa mai gidan nata sassauci a wajen sa. Aryan ne ya sakko daga sama, ganin ammyn yasa shi yin saurin tahowa wajenta, itama shi take kallo sai taga ya rame ya lalace yaron gaba daya, da sauri ta bude masa hannun ta ya shige jikin ta sai ya fashe da kuka. Tsananin tausayin sa ya kamata fiye da tausayin nata yaran da aka raba da mahaifin su, su a kalla suna da ita amma shi kuwa fa? Babu tabaccin Zeenat zata barshi ya samu kusanci da mahaifin nasa sannan kuma ga rashin uwa wadda ta kasance jigo a rayuwar yayanta. Ran Hajiya zeenat ne ya baci, ta kalli fuskar Daddy taga kamar ta sauya mata, sai tayi saurin matsawa ta kama hannun Aryan din tana fadada murmushin fuskar ta

“Menene my boy? Me kake so eh?”

Kwace hannun sa yayi da karfi yana matsawa sosai daga jikin ta

“Karki sakè taba ni, bana son ki ni mom dina nake so, ammy dan Allah ki tafi dani.”

“Baka da hankali ne Aryan?” Daddy yace

“Calm down alhaji na, he’s just a kid, kuma kasan sai a hankali aisha ce kawai take son wasa da hankalin sa, idan ba haka ba ai Ya hakura ko?”

“Kiji tsoron Allah Zeenatu, ki sani zaki mutu sannan zaki koma ga Allah a lokacin zaki girbi duk abinda kika shuka.”

“Da nayi me?”

“Ya isa haka please, kuje please ta dauki abinda zata dauka ta wuce, Aryan wuce sama kafin na saba maka.”

“Zakayi nadama sosai IBRAHIM, nadamar da bata da amfani kuma.”

Shiru yayi be ce komai ba, ta juya tayi hanyar fita daga falon kwalla na sake taruwa a idanun ta. Tana jin ihun kukan Aryan din Amma babu yadda zata iya. A compound din ta tsaya zeenat din ta fito, bata kalle ta ba, kawai tabi bayanta suka fita daga gidan zuwa tsohon gidan nasu, ta bude kofar ta matsa mata hanya ta shiga, yadda suka fita suka bar gidan haka suka tarar dashi sai uwar kurar da yayi, bedroom din Abby ta nufa kai tsaye tana danne abinda yake taso mata na rauni sosai. Wajen da tasan ya ajiye jakar ta bude ta dauko ta bude ta, ta tabbatar da komai yana ciki sannan ta dauki duk abinda take tunanin zasuyi amfani dashi sai ta koma bedroom dinta nan ma ta dauki abinda zata dauka din ta gama ta fito ta nufi hanyar barin gidan.

“Baki ji ba, sai na fara bincika me kika dauka sannan zaki tafi.”

“A wanne dalili kenan?” Ta ja ta tsaya cike da mamakin ta

“Wai kina nufin har yanzu bakiyi laushi ba aisha? Na fa ciku wasa ya kamata ace kin saduda , kin gane ni din ba ta wasa bace ba, idan kuma kina so kibi khadija in da ta tafi sai ki sanar dani, abu me mafi sauki a gareni na sa a kaddamar miki, duk wani abu da zai bani matsala kawar dashi nake ya kamata ki sani, dan haka idan kina son kanki da arziki kar na sakè ganin kafarki anan, ki koma chan kiyi rayuwar ki da yaranki.”

“Idan raina a hannun ki yake Zeenat karki barni na bar nan wajen ba tare da kin kashe ni ba, har wani tinkaho kike da abinda kika aikata kenan.”

“Hmm, kar dai ki cika baki wallahi, shawara na baki saboda har yanzu ke din kawata ce, amma idan kika ce zaki shiga gonata, toh tabbas zakiyi dana sani mara amfani.”

“Idan kuma na samu hujjar da zan rusa miki duk shirin ki, ina fatan zaki iya wanke kanki

Please Login or Register in order to submit comment