You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mace taji da batayi mata kama da ta yan matan gidan ba. Amsa sallamar tayi tana sakè matsawa daidai kofar dakin nata kamar zata shiga. Kanta ne yayi wani irin sarawa tayi azamar dafe shi tana jin jiri na neman kai ta kasa. Da sauri cikin daga murya tace

“Dan Allah karta karaso nan, dan Allah ta tafi bana son ganin ta.”

“Wacece ?” Malam yakubu yace yana nazarin yanayin da ta shiga ganin raihanan

“Ban santa ba, dan Allah ta tafi bana son ganin ta.” Ta sake maimaitawa tana yinkurin juyawa ta shige dakin nata. Kukan raihana ne ya karu, ta durkusa a bakin simintin kofar dakin tana sakè fashe wa da kukan.

“Tashi tashi, ba kuka zakiyi ba. Abinda nake son ku gani kenan dama, nasan za’a yi hakan, amma ba wai yin kanta bane ba, an riga an raba ta da kowa nata ne, an saka mata wani ciwo me Zafin gaske akan duk abinda ya danganci gida.”

“Zata warke?” Ta tambaye shi cikin muryar kuka

“Sosai ma, ai maganin ne yazo, in sha Allahu karshen abun kenan.”

“Mike muje shashen Asiya ki zauna kinji? Yaran gidan sun tafi makaranta ne amma daf suke da shigowa.”

Tashi tayi tana kallon dakin da ammyn ta shige, babu ko Motsin ta gashi tana son shiga taga Halin da take ciki amma babu dama sam, dole ta hakura ta bishi zuwa bangaren Asiya din, ta zauna a gefen dan karamin gadon dakin na kaba taje ta debo mata ruwa a randa ta kawo mata sannan suka gaisa a mutunce.

****Daga chan jikin wata bishiya Aryan ya tsaya yana magana da Kamal a waya, yana sanar dashi abinda yake faruwa, da zuwan su Adam din da duk information din da ya samu daga wajen yaron da yake tare da Adam din. Ganin Malam Yakubun ya fito yasa Aryan katse wayar ya dawo wajen domin jin yadda akayi da suka shiga

“Abinda dai na sanar daku din shine ya faru, dole sai anyi maganin sannan za’a samu waraka gaba daya.”

“Yanzu ta zamuyi? Barin ta anan yana cike da babban hatsari tunda suka gano tana nan din domin a Yanzu haka suna cikin garin nan ma already, nasan jiran fitowar mu suke kila suyi attacking dinmu, ba zai yiwu mu dauke ta mu tafi da ita va?”

Girgiza kai Malam Yakubu yayi, sannan yace

“Bana tunanin hakn zai yiwu gaskia, baka ga halin da ta shiga ba ne ganin yarinyar nan, ina tsoron ma kada ciwon nata ya tashi dan baki daya yanayin ta Ya sauya, toh ta yaya kake ganij zata yarda tayi tafiya tare daku?”

Dafe kai Hydar yayi da ya zama kamar ruwa a cinye shi a wajen saboda fargaba da tashin hankali, da kyar ya iya bude baki yace

“Ina ganin ni da kanwata ne bata so ta gani, hakan ba zai shafi Aryan ba nake gani ko?”

“Eh toh, bansan wanne irin Aiki akayi ba, amma idan gaba daya ne bana jin har shi din ma zata amince, sai dai mu gwada, bana kuma son mu kara dagula al’amarin ne.”

“Gaskiya ne.” Aryan yace yana dora hannun sa a saman kafadar hydar, wai yau shine yake kokarin kwantar ma wani hankali. Wani messege din ne ya kara shigowa wayar sa, dama abinda yake jira kenan, dan matsawa yayi kadan sannan ya bude

_”Oga suna planning shigowa ciki yanzu, muna tare da thugs ne kuma an basu umarnin daukar Madam ko Hajiyar da kuka zo gani.”_

“Adam!” Aryan ya furta a hankali yana kallon hanyar, baya son mutanen wajen su shiga Matsala saboda su, dan rayuwa suke me dadi da inganci ba irin tasu ba me cike da tashin hankali da tsantsar cin amana. Matsawa yayi wajen hydar yace ya taso suyi magana, Ya sanar dashi abinda yaron yace sannan ya dora

“Menene abun yi? Bana so mu zamar ma bayin Allah nan matsala, dan na tabbatar a yadda Adam yakeji zai iya zasu aikata komai.”

“Akwai matsala, Ammy ba zata yarda ta bimu ba, kana ganin muka barta anan zasu barta ne?”

“Ba zai yiwu mu barta ba, dole zamu sake taking risk din kawai. Zan shiga a matsayin likita da zan duba ta, idan ta amince sai mu ce zaa kaita asibiti ne, daga nan sai muyi kokarin fitar da ita daga garin.”

“Ayi hakan, Allah yasa ta amince.”

“Amin.”

“Malam dan Allah ina zamu samu mota?”

“Anan? Eh toh, akwai nan makocin mu Isah da yake haya zuwa cikin gari, dazu naga ya dawo ko hutawa yake? Sai dai idan shi zaa yiwa magana.”

“Ayi masan dan Allah. Ba zai yiwu mu bar mahaifiyar mu anan ba domin rayuwar ta na cikin hadari sosai, ina ganin zamu sakè gwada saar mu ne kawai, na gwada shiga din a matsayin likita ko zata amince.”

“Toh Bismillah, muje ciki, kai kuma ko zaka yi sallama gidan chan muji ko Isan zai sake fita.”

“Yawwa ayi hakan, bamu da time.”

Aryan yace a dan gaggauce

Ciki suka shiga zuwa dakin nata, tana kwanci kanta na jujjuya mata kamar zai fashe ga wani jiri wanda a kwancen ma yin sa take yi suka shigo.

“Innar yara jikin ne?” Malam Yakubu yace yana da jikin labile

“Eh malam, kai ne kamar zai fashe. Don Allah a samo min magani.”

“Tashi ga likita nan yazo, abokin Hamisu ne nan na makota, tashi ya duba ki idan zai yiwu sai ya rubuta maganin idan ba zai yiwu ba sai mun bishi Asibitin su chan cikin gari.”

“Toh.” Tace tana mikewa zaune, suka hada ido da Aryan din ai da sauri ta kwala kara, fita yayi shima da sauri har yana cin tuntube da kofar. Asiya ce suka fito tare da Raihana da sauri, ganin aryan yasa raihana yin wajen sa ita kuma Asiya ta shiga dakin Ammyn.

“Menene? Me ya same ta?” Ta hada tambayar waje daya tana kallon sa hankali a tashe

“Calm down kinji? Babu komai muna son ganin mun fitar da ita daga nan ne, but hakan ba zai yiwu ba sai bata ganin mu dukka, sai munyi hakuri mun bi komai a sannu, zo muje naga ko Hydar ya samu motar, idan yaso sai su, su dauke ta kawai mubi bayan su. Time yana kara kurewa.”

Hannun ta ya kama suka fito wajen suka tarar da Hydar da Isan a tsaye ana magana har ya jawo motar ma,

“Dama mota na shigowa nan?”

“Eh Amma ta chan baya ne, sai anyi zagaye idan mutum ba a garin yake ba, ba zai gane ba.”

“Haka ne, saura babura guda uku dan Allah, dan ba zai yiwu mu koma wajen motar mu ba.”

“A cikin gidan nan ma ba zaa rasa babura ba, kaga biyu nan nasu Awaisu, bari na zagaya baya na kirawo shi sai Isuhu ya dauko nasa shima.”

Isan yace yana barin wajen da sauri dan ya hasaso zai samu kudi sosai a wajen su, shi dama kuma mayen kudi ne kowa yasan shi. malam yakubu ne ya fito Aryan ya fada masa abinda ya tsara kawai, hakan kuwa akayi, suka hau suka bar wajen sannan aka fito da ita tare da Asiya da Matar kawu Liman na gidan sai malam yakubun a gaba.
Ba hanyar da su Aryan din suka shigo ba tanan suka bi ba, hanya ce sosai babba kuma sai dai zagaye ne. Wayar sa ya dauka ya kira Adam domin baya so ma yaje musu wajen da yan iskan da ya dauko ya sake tayar musu da hankali duk da su din ma ba baya ba, mafarauta ne a garin idan ka cire gidan su Malam Yakubun da yan tsirarin gidajen.

“Kar ka wahalar da kanka shiga cikin dan mu tuni mun wuce,kuma wallahi wallahi idan wani abu ya faru,sai na nuna maka na fika sanin duniya na rantse da Allah.”

“Kai karamin dan iska ne, idan ka isa ka tsaya a in da kake, kaga yadda zan sa karnuka su yagalgalaka na rantse da Allah, kuma Yanzu ma ba hakura nayi ba, zan biyo bayan ku idan har zaka dauke min mahaifiya babu abinda ba zan iya aikata maka ba.”

“Idan ka fasa Adam, kasan daidai nake da kai, dan haka duk abinda zakayi kayi, mahaukaci kawai. Sai nayi maganin ka.”

Ya katse wayar ya maida ta aljihun gaban rigar sa. Bayan motar suke bi har suka fita daga lungunan suka hau main titin, wani abokin sanaar Isan suka hadu dashi zai koma gida isa ya tsaida shi ya dauki su Aryan din a motar sa su kuma su Isuhu suka koma bayan Aryan din ya basu kudade masu kauri suna ta godiya.

Aryan ya riga yasan Adam sai sun biyo bayan su, ya kuma san a lokacin daf Kamal yake da shigowa tare da yaran sa, hakan ya bashi relief duk da yasan dole sai ya koma ya tabbatar da basa garin kamar yadda yace masa Amma yana da yakinin ba zai yi musu komai ba ko dan gargadin da yayi masa kuma yasan tabbas Hajiya zeenat na wajen sa dole zai bi a hankali tunda Yanzu be samu abinda yake so din ba.

A kofar shiga babban garin suka hadu da su Kamal, a waya sukayi magana dan basu tsaya ba saboda jikin Ammyn ya rikice suka ce su hadu a asibitin garin domin suna da bukatar chapke Adam da yaran nasa dan haka suka bi hanyar da su Aryan din suka baro su kuma suka shiga cikin garin. Direct babban asibitin garin suka nufa wanda yake a matsayin zone 1 saboda haka yake da duk manyan kayan aiki da manyan likitoci da suke shigowa daga chan cikin gari suna komawa kullum. Yanzu ma akwai likita saboda haka suna zuwa aka karbe ta aka duba ta sannan aka rubuta mata maganguna ciki har da na matsanancin ciwon kan. Sanda suka gama da asibitin sannan yamma tayi sosai, ba zai yiwu su dau hanyar barin garin ba duba da yanayin nisa garin, Malam Yakubu ne ya nema musu alfarma sauka a gidan bak’i, gidan da wani me kudi a garin Alhaji Ahmad ya gina saboda bakin sa idan sun zo anan yake saukar su. Mukullin ya basu dan a lokacin ma babu kowa a gidan. Chan dakunan ciki aka kai Ammy saboda ma karsu hadu aka ce mata zasu kwana anan ne zuwa gobe su wuce gida, bata kawo komai ba kuma kan nata yayi sauki musamman ga asiya a tare da ita sai ta ware. Daki biyu bayan na ammyn aka bawa su Aryan,Aikuwa ya shafawa idon sa toka yace shi da matar sa zasu zauna hydar shi kadai dan a lokacin kamal sun wuce dasu Adam da suka labe suka kama su a hanya. Lamido kuma ya tsaya kawai a kano dan yasan ko yazo zai sake complicating abun ne tunda ga halin da Ammyn take ciki. Wuce wa yayi kawai rijiyar lemo gidan wani babban malamin sunna da yake maganin ire iren wadannan matsalolin ya same shi ya sanar dashi komai, suka shirya zasu tafi gobe tare daga nan ya wuce hotel ya kwana.
Lawan ne ya maida su Malam Yakubu gida tare da matar Kawu Liman isa kuma ya zauna suka fita tare da Aryan samo musu abinda zasu ci, suka samu wani restaurant karami suka siyo abinci da gurasa sai tsire da soft drinks da ruwa. Malam Isan ne ya mikawa su Ammyn sannan shima aka bashi nasa hade da kudade masu kauri sannan yayi musu sallama ya tafi akan zai dawo da safe ya dauki Aryan din suje ya dauko motar sa.
Ledar da akayi ma hydar daban Aryan ya mika masa sannan yace

“Sai da safe Yaya.”

Da sauri Hydar ya riko shi suka saka dariya a tare, yanayin shekarun baya ya dawo musu a lokacin

“Dan wulakanci bari na zakayi?”

“Me zanyi? Zan kwana da kai ne?”

“Kafi karfi na, sai da safe.” Hydar yace yana sakin shi. Murmushi kaawai Aryan din yayi yana jin wani closeness da hydar din kamar a shekarun baya, ya wuce dakin da Raihanan take ciki. A chan gefen katifar dake malale a kasan dakin Ya hango ta, ta kwanta l’amo kana gani kasan ta gaji sosai. Ajiye ledar yayi a kan carpet din dakin ya karasa gareta gami da dagota ya jawota jikin sa yana kallon kumburarrun idanun ta da suka daga saboda kuka. Da yasan abinda zasu tarar kenan da be zo da ita ba, shi a tunanin sa suna zuwa komai lafiya tafiya kawai zasuyi, amma sai aka kuma samu akasi.

“Ina ammyn?”

“Tana dakin ta, ta samu sauki ma ta ware fa, aikin sihiri ne amma in sha Allah komai yazo karshe kinji?”

Gida masa kai tayi, ya share mata fuskar da gefen hannun sa sannan yace ta wanko hannunta tazo suci abinci. Toilet din dake cikin dakin ta shiga ta wanke hannun ta dawo suka zauna Ya bude musu abincin suka fara ci a hankali. Gurasar suka fi ci da naman sannan suka sha juice din ta matsar da ragowar gefe ta koma gefen katifar bayan ta kara wanke hannun ta. Rigar jikinsa ya zare ya makale ta jikin kujera ya bar singlet yazo ya zauna a kusa da ita.

**RQ**_

**59**


A hankali yake shafa gashin kanta har ya samu bacci ya dauke ta. Sosai closeness dinsu ya haifar masa da wani irin yanayi me wahalar fassarawa. Zame jikinsa yayi a hankali ya wuce toilet din ya sakar ma kansa ruwa me sanyi ya dinga ratsa sumar kansa zuwa saman kafadarsa. Kansa a chunkushe yake matukar a yan kwanakin nan, sosai ya tsorata da al'amarin Hajiya zeenatu ganin halin da Ammyn take ciki, be taba tunanin akwai irin wannan kullin ba sai a yanzu, rashin imani ne tsantsa a rabaka da kowa naka domin samun biyan bukatar duniya. Da ruwan a jikinsa ya fito ya zauna akan kujerar dake gefe yana kallon fuskarta, yanayin yadda take fidda numfashi kadai ya tabbatar masa da bata wani jin dadin baccin. Tsaki yaja ya mike bayan ya dan share jikinsa da dankwalin ta sannan ya baza ji a saman kujerar ya zura boxer dinsa ya karasa wajen da take kwance. Rigar jikinta doguwa ce ta atamfa, ya tabbatar ba zata iya cin dadin kwanciya da rigar ba ganin yadda yanayin garin yake da dan zafi duk kuwa da akwai solar da fan tanayi amma garin a chunkushe yake babu iska tana kadawa sosai. A hankali ya juyar da ita ya kama zip din rigar ta baya ya shiga zare mata shi ya kawo mata zuwa kasan cibiyar ta sannan ya juyo da ita. Saurin janye idonsa yayi daga kallon saman kirjinta da yake a bayyane bayan ya janye rigar. Numfashi yaja da dan karfi sannan ya fezar da iska me zafi yana sakin ajiyar zuciya. Ya kai kololuwa a hakuri yana kuma tunanin hakurin nasa gaf yake da karewa, ba dan baya so ya takura mata ba, duba da yadda ta galabaita yau da babu abinda zai hanashi karban hakkin sa a yanzu, sai dai yana da tausayi sosai, ba zai iya kara mata wata damuwar ba, ya kara wahalar da ita ga damuwar Ammy da take ciki kuma.
Juyi tayi ba tare da tasan wainar da ake toyawa ba, taji sanda yake zare mata rigar amma bata kawo wani abu ba, duk a tunanin ta ma mafarki take yi shiyasa ta cigaba da baccin ta hankali a kwance. Gefen ta ya kwanta sannan a hankali ya jawo ta zuwa jikinsa ya manna kirjinta a jikin sa, abinda ya janyo wani irin shock ya furta

"Subhanallah!"

Da dan karfi sai kuma ya samu kansa da yiwa kansa dariya, ya murmusa kad'an sannan ya sake matseta yana jaddada kansa ita din halilin sa ce. Yanayin yadda ya rik'e tan da kuma dan zafin da jikin tan yayi yasa taji ta takura har ta dan sake yinkurin juyawa amma sai ta jita a jikin mutum. Da farki ta manta a inda take kwata kwata, tunanin ta tana gidan Ya Nabeela kwance a gadonta tana bacci, jin ta jikin mutum yasa ta yin saurin yinkurin mikewa amma sai ya hanata, ya sake matse ta kam kam yana chusa kansa a jikin kirjin nata ya shiga sakar mata numfashin sa me zafi. Numfashin tane ya kusan daukewa take kuma sai kwakwalwarta ta shiga hasaso mata a yanayin da yake ciki. Hannun ta, ta kai ta taba kasan rigar ta, taji ta a zame sai tayi saurin kai hannu sama, daga ita sai bra daga sama.

"Na shiga uku."

Tace a ciki ciki kirjinta na bugawa da sauri. Yi yayi tamkar be ji ta ba, ya cigaba da chusa kan nasa hade da sakar mata zazzafan kiss a tsakanin wajen ga numfashin sa da yake hura mata.

"Bacci nakeyi fa."

Tace muryar ta a karye amma sam yaki dagowa bare ya nuna yaji me take cewa bare har ya iya amsa mata, maimakon haka ma sai ya sa hannun sa ta bayan ta ya shiga kokarin balle maballin bra din yadda zai samu full access da wajen. Kicin-kicin ballewa yake tana kokarin hanashi amma sai da ya samu ya balle su, sannan ya zare ta da dan karfi ya ajiye ta a gefe, da sauri tayi ruf da ciki tana manne jikinta da katifar dukka, dariya ta bashi sosai yadda tayi, amma sai ya kanne dan yanzu ba wai abinda yake gabansa ba kenan, so yake ya rage zafi ko yaya ne. Hargitso ta yayi gaba daya da hannu daya, ya dora gaba daya jikinsa akanta yayi mata rumfa ta yadda babu yadda zata iya hanashi abinda yayi niyya. Daidai saitin fuskar ta, ya kai tashi fuskar har numfashin su na sarkewa waje daya, ya shiga bin fuskar tata a hankali yana zagaye ta har ya kawo kan lips dinta. Kulle idonta tayi da sauri ya kai bakinsa kan nata ya shiga kissing dinta a hankali, duk da idon ta a rufe yake kokarin kare chest dinta take da hannun ta yana jin ta, ya kyale ta sai da ya gama kissing din bakin nata ta sakankance sai jin hannun sa tayi a saman kirjinta yana zagaya su ko ina, jikinta ne ya hau rawa ta shiga kokarin ture hannu tana masa magiya, amma yaki ya cigaba da abinda yake kansa tsaye, sai da ya ga dama dan kansa sannan ya kyale ta, zuwa lokacin gaba daya jikinta rawa yake yi, shi kuwa dama be ma san abinda yake ji ba, da be yi karfin halin kyale ta ba, da babu abinda zai hanashi aikata aika aikar, shiyasa ya hakura ba dan yana so ba. Toilet ya shige ita kuma ta yi saurin maida rigar ta, cike da mamakin Aryan din tamkar bashi ba. Tana kwance ta kulle idon ta, ta kudundune ya fito daga toilet din ya karaso gabanta idonsa ya dan tashi kad'an yayi ja, yace taje tayi wanka, yi tayi kamar bacci take ya sake maimaitawa sannan yace

"Zan ciccibe ki na kaiki fa."

Da sauri ta tashi, sai dai bata jin zata iya sakawa jikin ta ruwa a lokacin dan zazzabi zazzabi take ji, sai kawai taje ta kama ruwa ta dawo ta tarar har ya kwanta ta rakube a gefen shi ta kwanta kamar zata fada k'asa dan tayi masifar tsorata dashi. Mirginowa yayi ya jawota jikinsa a hankali muryar sa a ciki sosai yace

"Ba zaki koma gidan Ya Nabeela ba, nayi kara ai, bana so a samu matsala."

Bata ce komai ba, dan bata da amsar da zata bashi saboda maganar tafi karfin ta. Sai ta kulle idonta tana jin shi yana gyara mata kwanciyar sosai a jikinsa bata ce komai ma. A haka suka karasa daren bata san lokacin da yayi bacci ba.

Ita ta fara tashi ta wuce tayi alwala tana fitowa ta ganshi a zaune yana kallon wayar sa, mikewa yayi ya isa toilet din ita kuma ta gyara tasa Hijab dinta zata tada sallar ya fito yaje ta jirashi. Kayansa ya mayar yazo ya jasu sallar sannan ya fita ya barta a dakin zuwa wajen Hydar. Hankalin ta gaba daya yana wajen Ammy ji take kamar taje ta ganta amma babu hali haka ta hakura ta zauna lamo sai ga kiran Lamido ta daga da sauri tana dagawa ta saka mishi kuka, dama neman wanda zatayi ma take yi sai gashi ya kira, kwantar mata da hankali yayi ya ce yana hanya zaizo tare da me maganin sannan ta dan samu relief.

***Wajen Hydar ya je ya kwankwasa masa sannan ya shiga, suka gaisa ya zauna.

"Ina kanwar tawa?" Hydar ya tambaya yana kallon sa

"Na cinye ta!"

"Haba ka isa? Ai kanwata ba zata cinyu ba sam."

"Wait and see, Lamidon sun tashi?"

"Eh wayar sa ce ma ta tashe ni, sun dauko hanya."

"Good, Allah yasa Isa ya kawo mana motar yanzu, Kamal ma nasan zai dawo in sha Allah yau zamu juya."

"In sha Allah!"

Kwankwasa kofar akayi, Aryan ya tashi ya bud'e, me gadin dake kula da gidan ne, hannu ya bashi sukayi musabiha sannan yace

"Wai Isa ya karaso, suna waje tare da Malam Yahya."

"Yawwa Masha Allah, dama yanzu muke maganar."

"Ai naga mutumin ba baya ba, he's very hard working."

"Yeah sosai, bari na je wajen sa."

"Ok zan fito yanzu nima."

Tare suka fito da maigadin suka tarar da Isan a waje tare da Malam Yakubu da Awaisu, key din motar ya karba bayan sun gaisa sannan yace su shigo ciki, ya kaisu dakin Hydar sannan Malam Yakubu ya kira Asiya yace zai shigo ta fadawa Innar Yara. Wajen Maalm Yahya Aryan ya karasa suka zauna ya tambaye shi yadda akayi jiyan bayan su Adam din sun zo wajen motar, guduwa yayi ashe ya buya be fito ba sai bayan magriba bayan ya tabbatar sun tafi. Shiru kawai Aryan yayi yana tunanin abinda ya kamata yayi next for now yasan ya gama da babin Adam da duk iskancin sa

Wajen sha biyun rana Lamido suka karaso tare da malamin, lokacin duk sun shirya sun yi wanka suna jiran zuwan nasa, Kamal yace ba zai samu zuwa ba saboda a jiyan suka bar Kano tare da su Adam dan haka duk yadda ake ciki suyi waya kawai. Raihana na jin malamin yazo ta hau murna, zata fita ma Aryan ya riketa yana mata wani irin kallo, sunkuyar da kanta tayi k'asa cike kunyar sa, yana sane yake mata hakan dan ya lura gaba daya taki yarda ta hada ido dashi tun abinda ya faru jiyan

"Ina zaki fita haka babu ko mayafi?"

"Hamma Lamido zanje na gani."

"Ba shi kadai bane ba, ko so kike a kalle min mata?"

Komawa tayi ta zauna yayi murmushi ya fice. Gaisawa sukayi da Lamido da malamin me cike da kamala. Malam Yakubu ne ya jagorance shi zuwa in da Ammyn take, sukayi sallama bayan sun gyara jikinsu sun rufe sannan suka shiga, hannun sa dauke da Babbar jarka cike da ruwan addu'a, yana shiga Ammy ta mike zata gudu yayi saurin tura kofar yana murmushi

"Bakaken shaidanu ne wallahi Malam, kaga sun ganni zasu gudu, suna matukar tsoron ayar Allah, domin kona su take kurmus, wannan ruwan da kake gani, ruwan addu'a ne da aka karance masa ayoyin alkurani me girma, idan ana zuba musu tamkar ana sheka musu tafasashen mai ne, amma in sha Allahu an zo in da za'a samu waraka, da yardar Allah zata samu sauki."

"Allahu yasa."

"A kujerar Malamin ya zauna sannan ya umarci Ammyn ta zauna, Asiya da duk ta tsorata tayi tsuru tsuru kamar za'a ce kyet ta gudu, amma haka ta daure ta zauna daga gefen amma sai Ammyn taki, cikin daga murya ya daka mata tsawa.

"Zauna!!!"

Da sauri ta zauna tana kin yarda su had'a idanu kwata kwata saboda tsabar tsoron sa da take nan take.

Fita waje Malam Yahya yayi, ya matso yace ta mike kafa, ta mike a tsorace, sannan yace Asiya ta gyara mata Hijabin ta baya goshin ta ya bayyana, gyara mata tayi,yayi bismillah ya dibi ruwan ya zuba mata a saman kanta zuwa saman fuskar ta. Wani irin razanannen kara da ta saki sai da gaba daya gidan ya dauka, da sauri Aryan ya koma dakin da Raihana take, domin tana bukatar shi a lokacin. Cigaba da zuba mata ruwan yayi tana ihu da kururuwa kafin su fara magana daya bayan daya, tun yana irga su nawa ne a kanta har ya fara sarewa, ba karamin wahala tasha ba, domin duk abinda aka hada da bakaken shaidanu akwai matukar

Please Login or Register in order to submit comment