google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

al'umma, duk inda naje"

"zumd'ena akeyi ana ja min Allah ya isa"" ya 'karashe yana tura kan zabo baki had'i da sakin kuka"

"""Dallah rufen baki, duk abinda ake maka yayi rabin nawa ne, ina ce..."" Hansatu shiru tayi ganin"

Abulle ta fito daga d'aki tana kallonta

"""Jar uba! Yau za'a kuma 'yar tsere a gidan nan kenan"" ta fad'a tana wage baki saboda hamma"

"""Abulle ni dai bakiji nace komai ba ko?"" Cewar Isuwalle domin ranar da akayi 'yar tsere kwanakin"

baya shiya fad'i kuma shi ya azabtu daren ranar.......

Mss Flower & Mrs Abdool

_MASOYA MUNA JIRAN A NUNA MANA SOYAYYAR DA AKE CEWA ANA MANA TA

SIYAN LITTAFIN NAN_

"*NAIRA 200 NE KACAL, ZAKI MORE KARATUNKI, KI SHA DARIYA GAMIDA"

ILMANTUWA*

"_ZAKI BIYA TA WANAN ASUSUN 0104322069, SAKINA ABDULLAHI, ACCESS. IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKI TURO KI TUNTU'BEMU TA WANAN LAYIN 08167888934_ SAI MUN JIKU "

"[8/14, 11:34 AM] Mss Flower : *ABULLE ANNOBA* "

(Sanadin neman haihuwa)

_Na_

_*Mss Flower*_

_&_

_*Mrs Abdool*_

EJ- 1D' FE-1D' 'DDG E3(

*                                                                    *

& *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* &

FCWA

*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp

*                                                                        *

*07*

""" Abulle na ro'keki da Allah ki rufan asiri, wallahi 'kashin 'kafata ya turgud'e"" cewar Hansatu tana"

'bare baki wiwiiii

"""A dakata to, bari Hansatu ta huta"" cewar Abulle tana zama"

"""Abulle 'kafata, wayyo Allah ta turbud'e 'kafata"" Hansatu ta 'kara fasa kuka"

"Isuwulle ne ya mi'ke ya nufi Hansatu da keta yarfe hannu tana matsar 'kwalla, 'kafarta ya ri'ke"

"yana 'ko'karin jaa aikuwa ta tsallara ihu tana fad'in "" Isuwulle azaba, jaa da kyau, cikata haka"" sai sumbatu take tana 'ko'karin janye 'kafarta"

"""Isuwulle ri'ke 'kafar ka ja ta da kyau, matseta sosai kada ka cika"" cewar Abulle tana ta d'irka"

dariya harda hantsilawa

"Hansatu ba 'karamin kuka tayi ba sanan Abulle tace "" yau na rushe 'yar tseren kowa ya huta"" ta fad'a tana cigaba da dariyar mugunta, Hansatu tana d'ingisawa ta samu ta d'ora ruwan zafi domin"

gasa 'kafarta

"Abulle zaune bisa tabarma ga kayan kwalliya birjik a kusada ita danginsu jar hoda, kwalli, barbad'a kumatu, ga kanta kile jambaki, ga kuma ba'kar jagira, kwalliya ta rambad'a fuskarnan taji uwar jar hoda, ga ba'kar jagira da aka sha guduma sanan aka bi aka d'iddige fuskar da ba'ki, sanan ta rambad'a jambaki a saman ido da baki, Isuwulle da Hansatu dake gefenta sai kallonta suke kamar sunga sabuwar halitta domin kwalliyar Abulle idan ta tashi yi ta kere ta kowa muni a 'kauyen, madubi ta kalla ta turo baki sanan ta she'ke da dariya tana dad'awa da shewa sanan tace"

"""kai jama'a irin kyau haka, yasin mijin Abulle ya cha'ba"" ta fad'a tana mi'kewa"

"""Abulle wane mijin hala, ko sai a dandali zaki fitar da gwanin naki"" Isuwulle ya tambaya"

"""A'a Isuwulle ni ai na fidda gwanina tun jiya, yau in aka tashi daga dandali ka sanarma zan wuce gidan mai gari, wallahi kowa ya taru da yaro da babba duk wanda bai je ba zaya sani"" Abulle ta"

fad'a tana karkad'e kayan jikinta

"""Abulle mi za'ayi a chan ne"" Isuwulle ya tambaya"

"""Zan fidda gwanina"" ta basa amsa sanan ta wuce tana tsalle, dan'kam ta tadda 'yammatan 'kauyen 'kofar gidansu kowacce ta sha kwalliya da d'amara haka suka kama hanya suna hirarrakinsu har"

suka 'karasa dandali

"Bayan samarin da suka tadda sun gaida Abulle aka fara gudanar da gad'a da wasanni, bayan"

"angama ya zamana saura lokacin hira, haka kowa ya ja budurwarsa gefe suna zance banda Abulle da Bintalo dake zaune kan wani dakali suna 'yar hira, chan Abulle ta mi'ke ta dubi Bintalo tace """

"zo mu zaga mu ga ko za'a samu 'yan iska"", Bintalo mi'kewa tayi suka fara zaga 'yammatan da"

"samarin suna ganin abinda sukeyi, idon Abulle ne ya sauka akan wajen ciyayi, gani tayi kamar mutane dan haka suka nufi wajen cikin sand'a"

"""Mati da zafi kake sha fa"" cewar wata muryarta kamar zatayi kuka, Mati kam bai kulata ba sai"

faman matseta yake

"""Jar ubancan! Dama Dije ke 'yar iska ceh, yau zaku ci ubanku, maza ku fito"" cewar Abulle"

"Mati iya rikicewa yayita, hawaye yake ya fara magiya cewa shi hira yakeyi amma Abulle sai d'ure"

d'uren ashar takeyi ta 'ki sauraronsu

"""Abulle dan girman Allah kiyi ha'kuri, na rantse da Qur'ani izihi sittin ni ba komai nakewa Dije ba,"

"ai ga tanan a tamba..."" Bai 'karashe ba yaji wani gigitaccen mari bisa fuskarsa kamar an maka masa itace mai uban nauyi"

"""Wa zaka maida 'yar iska, ca aka ce maka banganka ba, bare ka tsara, wato ka kama nonuwan yarinya kana sha ita ba shanuwa ba ko kuma kai ba jinjiri ba, salon ka ciremata su ka kasheta, to kwarankwatsa yau sai kaci 'kwal ubanka"" ta fad'a tana 'ballo tsumagiya lokacin masu hira duk sun"

yo caa hankalinsu ya dawo wajensu Abulle

"""Kai Saminu, Isiyaku ku d'aga min shi"" Abulle ta fad'a, Mati ko 'kara sautin kukansa yayi yana magiya amma haka aka d'agashi sama Abulle ta dinga zuba masa bulala, kafin tayi masa goma har ya sume, haka tasa aka bugo tu'ka tu'ka aka kwaranya masa ruwan, yana bud'e ido ta kuma cigaba"

da sambad'arsa

"Abulle ko da tagama ta buga uban tsalle tayi girgiza sanan tace "" Allah kuma ba ma wani sa'a naga yana 'ko'karin lalata da yarinya ko 'ko'karin tsinke mata nono yaga yanda zanyi dashi a garin nan"" ta fad'a tana dariya da buga 'kafa, nan kowa dai yayi tsuru tsuru, Mati kuwa jini duk ya 'bata masa"

riga gashi baya iya tafiya sai kuka kawai yake

"""Mai gari ya aikoni, yace na sanar da duk wani saurayi dake dandalin nan da yayi haramar zuwa gida ya shirya cikin ado, ya 'karaso gidansa cikin 'kan'kanin lokaci domin yau Abulle zata fidda miji, wanda bai zo ba zaya had'u da fushinsa da kuma na Abulle"" cewar d'an shela dake yawo da lasifika. Nan dukkan samarin suka fara watsewa fuskokinsu da fargaba yayinda 'yammata suka"

fara 'kus 'kus amma ba batun fiddo zance waje

Abulle ceh zaune kan kujera yayinda samari da dattawan 'kauyen sukayi dafifi a 'kofar gidan mai gari kowanne zuciyarsa cikeda zullumi da addu'ar Allah yasa kada Abulle ta za'besa musamman

samarin

"""Abulle ke ake jira ki za'ba, sanan ki saka lokacin auren"" Mai gari ya fad'a"

"Dariya Abulle ta she'ke da ita sanan ta fara kallonsu d'aya bayan d'aya chan tace "" za'bina"

shine...........

Mss Flower & Mrs Abdool

_MASOYA MUNA JIRAN A NUNA MANA SOYAYYAR DA AKE CEWA ANA MANA TA

SIYAN LITTAFIN NAN_

"*NAIRA 200 NE KACAL, ZAKI MORE KARATUNKI, KI SHA DARIYA GAMIDA"

ILMANTUWA*

"_ZAKI BIYA TA WANAN ASUSUN 0104322069, SAKINA ABDULLAHI, ACCESS. IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKI TURO KI TUNTU'BEMU TA WANAN LAYIN 08167888934_"

SAI MUN JIKU

*YAN NIGER NAKU 300F NE KU TUNTU'BI WANAN LAYI DOMIN BIYAN NAKU

+22795045822 IDAN KUN BIYA SAI KU TURO SCREENSHOT TA WANAN LAYIN

08167888934*

"[8/14, 11:34 AM] Mss Flower : *ABULLE ANNOBA* (Sanadin neman haihuwa)"

_Na_

_*Mss Flower*_

_&_

_*Mrs Abdool*_

EJ- 1D' FE-1D' 'DDG E3(

*                                                                    *

& *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* &

FCWA

*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp

*                                                                        *

"_HEY LOVELIES!! KUYI SAURI KU BIYA DOMIN SAMUN DAMAR SHIGA INDA ZAKU KARANTA ABULLE, DOMIN FREE PAGES NA GAF DA 'KAREWA, KADA KU MANTA"

"ZAKU SHA DARIYA, ZAKU ILMANTU. KU NEMI NAKU TUN KAFIN A BAKU LABARI_"

*06*

"""Kwarankwatsa sai anyi 'yar tseren nan"" cewar Abulle tana karkad'a 'kugu"

"""Abulle"" cewar Isuwalle da idanunsa suka kawo ruwa"

""" Kada kayi magana, ku jira na samo rake nadawo a fara"" Abulle ta fad'a tana ficewa"

"Tafiya take tana dirka tsalle, idan ta cilla 'kafa chan sai ta dire kamar wata 'yar rawar 'be'be, tana ta wa'ke wa'kenta tana tafa hannu. Sa'adu mai mangoro ne ya hangota, suna had'a ido ya zura"

takalma ya fara tura baron mangoro cikin sauri kafin ta taddosa dan akwai 'yar tazara tsakaninsu

"""Chalama!! Sa'adu akwai rowa kwarankwatsa, yanzu ko zanyi maganinka"" ta 'karashe tana tattare bujenta had'e da gyara murya, ta'kar'karewa tayi tana ""Sa'adu mai mangoro tsaya"", ai Sa'adu jin ta kirasa sai ya kuma daddagewa ya fara zuba gudu da baro, mangoro na fad'uwa yana d'agosu da 'kafa yana maidawa, yayi gudu mai nisan gaske sanan ya juya ganin Abulle bata bayansa yasanya ya koma 'kar'kashin wata makekiyar bishiyar kuka ya zauna yana haki had'e da maida numfashi, 'yar gorar ruwansa ya d'auko zai sha aikuwa sai yaga ruwa na tashi sama kamar ana zu'kosa ta saman bishiya, cikin kid'ima ya birkita wanda yayi sanadiyyar zubewar mangoronsa a 'kasa, d'aga"

idanunsa yayi sukayi ido biyu da Abulle tana murmushi

"Dirkowa tayi daga bishiyar ta ri'ke ha'ba sanan tace "" yanzu kai Sa'adu saboda ba'kar rowa shine kayita zabga gudu kada ka bani mangoro biyu zuwa biyar, lallai ka cika uban 'yan rowa"" ta"

'karashe tana zubewa tana dariya harda birgima

"""Kiyi ha'kuri Abulle ban lura dake ba ne"" ya fad'a idanunsa na kawo ruwa"

""" Bata shafan ba, kai ta shafa"" ta 'karashe da karka'be bujenta ta tsinci mangoro biyu daga 'kasa"

tayi tafiyarta tana tsallenta

"""Shegiyar yarinya mai zubin aljanu, ashe ma aljanar ce, ni naga ruwa iya sama ziiiiii ashe aljanar na bishiyar, Allah ka yayemana wanan annoba, yanzu ta jamin asarar murtala"" ya fad'a yana tsaki, sanan ya nufi mangoronsa da ya zube yana 'ko'karin kwashewa amma da ya kama sai ya koma dutse, haka yayita bin mangoron d'aya bayan d'aya suna komawa duwatsu, zaman 'yan bori yayi"

ya dinga kuka kamar zai shid'e sa'ilin nan ya mi'ke kamar an tsikaresa ya nufi gidan mai gari

yanata kumfar baki a hanya

"""Isuwulle ya kamata ayiwa Abulle aure kaga ta zama budurwa, ga kuma duk sa'aninta da tsarar"

"rakinta ansa musu rana, a nema mata miji"" cewar Hansatu"

"""Lallai Hansatu sai yau na tabbatar bakida hankali, yanzu uban wa kike tunani zaya auri Abulle,"

"wallahi ko mahaukaci aka ce za'a bawa na tabbata guduwa zaiyi, wai Abulle Annoba suke mata kirari, toh wa zaya kwashi annoba ya kai mahallinsa"" ya 'karashe da tsuka"

"""Ai idan kai son zama da ita kake kana wahala a banza sai kayita zama, amma ni nagaji da wahala,"

"azaba, da ba'kin jinin da nayi cikin mutane, bari ta dawo nace ta za'bi miji nasan dai ko yanasonta ko baiso sai ya aureta eheee"" Hansatu ta 'kare da murgud'a baki gefe"

"""Nima farincikina ne, Allah ya tabbatar da alheri"" Isuwulle ya fad'a"

"""Yanzu naji batu, da kana magana kamar son zama da ita kakeyi"" Hansatu ta fad'a"

"""Nadawo, me kuke tattaunawa"" Abulle da shigowarta kenan a guje"

"""Magana muke akan auren sa'aninki da za'ayi nan kusa, ke kuma shiru ba wanda ya turo"" cewar"

Isuwulle

"""Hehehehehe Qur'ani kun bani dariya, wayaga Abulle amarya"" ta fad'a tana kwashewa da dariya"

harda kifewa 'kasa

"""Abulle baki son auren ne"" cewar Hansatu cikeda fargaba"

"""So kai, Hansatu ni ai da sam bani maganar aure ma, ashe fa na zama budurwa"" ta 'kara kwashewa"

da dariya tana hantsilawa

"""Ai aure shine cikar mace"" Isuwulle ya fad'a"

"""Kwarankwatsa za'ayi budiri da auren Abulle, kada ku damu nan kusa za'a sha shagali, nan kusa"

"zan fidda miji"" ta fad'a tana murmushi"

"Wani farinciki ne ya 'kara kama iyayen Abulle, cikin zumud'i suka ce ""Allah ya kaimu"""

"Abulle ceh ta tattare buje, ta daka uban tsalle tace ""za'a fara 'yar tsere, yanzu za'a fara wa'ka kafin a gudanar da wasa kamar yanda aka saba"" ta fad'a tana daddagewa tana baya kamar an ri'ke"

"kafafunta sanan ta wage murya "" A bada fili fili"" "

"""Filiya!!"" Suka ta'kar'kare suka amsa fuska kamar kashin shanu"

"""A bada filin wasa "" Abulle ta kuma fad'i"

"""Filiya "" suka amsa suna matsawa domin bada filin"

"""Duk wanda bai bayar ba "" Abulle ta fad'a tana direwa"

"""Filiya "" suka amsa suna tafawa"

"""Uwarsa 'yar kamasho ceh "" Abulle ta fad'i"

"""Filiya "" suka amsa suna 'kara matsawa"

"""Ubansa d'an kamasho ne "" ta fad'i tana tafi"

"""Filiya "" suka amsa suna watsa mata harara ta 'kasan ido"

"""Daren yau ya kwan da cinnaku "" ta 'karashe tana taka rawa"

"""Filiyaaaaa!!!!!!"" Dukkansu suka ta'kar'kare iya 'karfinsu suka amsa"

"Abulle dariya ta she'ke da ita sanan tace "" kunci wanan, toh a jaaa layi"""

"Nan suka shata layi, suka tsaya 'ki'kam kamar sojoji"

"Abulle ta kallesu tayi murmushi sanan ta fara musu cewa ""Mai tsumma "", ai sai suka d'aga 'kafar"

hagu

"""Mara tsumman "" suka d'age 'kafar dama"

"""Mai tsumman, mara tsumman Hansatu ya baki d'aga ba? "" Cewar Abulle. Cikin sauri Hansatu ta d'age 'kafa sanan ta makata 'kasa da 'karfi, ai kuwa zafi ya ziyarceta ta dur'kushe tana yarfe"

hannu ...........

Mss Flower & Mrs Abdool

_MASOYA MUNA JIRAN A NUNA MANA SOYAYYAR DA AKE CEWA ANA MANA TA

SIYAN LITTAFIN NAN_

"*NAIRA 200 NE KACAL, ZAKI MORE KARATUNKI, KI SHA DARIYA GAMIDA"

ILMANTUWA*

"_ZAKI BIYA TA WANAN ASUSUN 0104322069, SAKINA ABDULLAHI, ACCESS. IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKI TURO KI TUNTU'BEMU TA WANAN LAYIN 08167888934_ SAI MUN JIKU "

"[8/14, 11:40 AM] Mss Flower : *ABULLE ANNOBA* "

(Sanadin neman haihuwa)

_Na_

_*Mss Flower*_

_&_

_*Mrs Abdool*_

EJ- 1D' FE-1D' 'DDG E3(

*                                                                    *

& *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* &

FCWA

*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp

*                                                                        *

"_HEY LOVELIES!! KUYI SAURI KU BIYA DOMIN SAMUN DAMAR SHIGA INDA ZAKU KARANTA ABULLE, DOMIN FREE PAGES NA GAF DA 'KAREWA, KADA KU MANTA"

"ZAKU SHA DARIYA, ZAKU ILMANTU."

08

"Kyakkyawan saurayine dogo mai kimanin shekaru 32 a duniya, sanye yake cikin suit Dark blue"

"mai mugun kyau, hannunsa na dama daukeda brief case sai dayan hannun kuma daukeda suit din saman, yarage dagashi shi sai long sleeve light blue da butterfly neck tie,"

"Tafe yake cikin sassarfa yana duba time a hannunsa dake makale da kyayyawan agogo, kofar exit din katafariyar asibitin yake tunkara,harya fito yaji ringing din wayarsa, da sauri ya dauka ganin"

"""first love"" dauka yayi tareda karawa a kunne,"

"""Hello Mom on my way, wallahi aikine yad'an min yawa shiyasa but in the next 20mins Ina gida"""

"Banji me taceba, kawai yakashe wayar, da sauri yashiga motarsa ya tada yabar harabar asibitin."

"Mintina ashirin ya iso bakin wani kantamemen gate, horn ya danna da 'karfi daga inda mai gadin yake zaune ya danna remote nan da nan kuwa gate ya zuge, kutsawa yayi, kaitsaye ya perker"

"mortar a inda aka tanada ya bud'e ya fito d'auke da jakarsa,"

"Direct apartment d'in mahaifiyarsa ya tunkara, handle d'in ya murza tareda yin sallama, budurwar"

"dake zaune a falon ta wani amsa masa a da'kile, shi da baima lura da ita ba direct hanyar stairs ya nufa don shiga d'akin mahaifiyarsa,"

"Ahankali cike da yanga ta kirsa tace ""Doctor barka da dawowa"", tsayawa yayi tareda juyowa sai a lokacin ya lura da akwai mutum a palon, bai ko amsata ba, sai kallon ta yayi sama da 'kasa tana sanye cikin riga da wando damman mu sai wani juya ido take irin na 'yan duniya, tsaki kawai yaja"

"tareda hayewa kan stairs d'in,"

"'Dakin mahaifiyarsa ya bud'e tareda zama akan cushion d'in d'akin, kana ganin sa kasan a gajiye"

"yake,"

"Kallonsa tayi cike da 'kauna tace ""son yau ka dad'e dayawa, tinda dazun Meema tazo tana jiranka"""

"'Bata ransa yayi yace"" Mom is that why u have been calling?, plss mom wai meyasa matan nan suke damuna ne plss su 'kyaleni na huta mana, when it's time zanga wacce nake so da kaina, duk bana son su kar nasake ganin 'kafar kowace shegiya a gidan nan inba haka ba zan mata rashin mutunci, I can't marry such type of gals ba class bare kamun kai, God forbid ma"" ya 'karashe"

maganar ransa a d'an 'bace.

"Mom itama da abun saddiq yafara damun ta tace ""son yaushe ne zaka cikamin burina naganin matarka, its high time fa shekarunka 32 a duniya fa idan ba yanzu ba sai yaushe, I am sick and tired of ur attitude plss enough, kowa baka so then wa zaka aura?!!"" itama ta 'karashe maganar"

"ranta na 'kuna,"

"Mi'kewa yayi ya koma kusa da ita yakama mata hannun ta ""plss Mom just pray for me kinji koh, so nake na samu yarinya mai tarbiya da hankali wacce zata kula dake, Mom u won't understand it's only u I have am doing this all because of u, meyasa bazaki gane ba kinsan insonki banson na auro wacce zata baki problem kingane koh Mom to plss calm down just pray for me, cos ur prays matters a lot, bazan ta'ba yin abu don na 'bata miki rai ba, kinson banson 'bacin ranki ko yaya ne"

"kiyi ha'kuri ki yafe min kinji Mommy na"" ya 'karashe maganar kamar zeyi kuka."

"Murmushin jin dadi tayi "" I know my son kullum Ina maka addua Allah y baka tagari Allah kuma yayi maka albarka"" tafad'a tana murmushi tareda saka hannu cikin curly hair d'inshi tana murzawa"

kamar wani yaro.

"""Yanzu tashi muje kaci abinci yau favorite d'inka na dafa ma"" tafada tana kallonshi tareda 'kara"

fad'ad'a murmushin fuskar ta

"Ware idanuwansa yayi ""wow really, u are the best Mom ever, I love u so much"" ya fad'a cikeda"

"farin ciki yana hugging d'inta,"

"Zamewa tayi, tayi gaba yana biye da ita har suka sauko stairs d'in, kallon falon yayi yaga Meema"

"bata nan it means ta gaji tawuce abunta,"

"Dining yawuce ya zauna, serving d'insa tayi lafiyayyar fried rice da coslow tareda liver souce, ci yayi sosai har ya 'koshi suna fira, kallon ta yayi yace ""Mom u are the best cook ever wallahi"

"banta'ba cin abinci mai dad'in naki ba"" ya karashe zancen yana kai lomar shinkafa baki,"

"Fashewa tayi da dariya tareda cewa ""kaide ci bance kamin santi ba"""

"""Allah Mom Idan zanyi aure sai tazo ta koya kalar girkinki don shi zata rin'ka min"""

"""To naji, maza cinye ka tashi kaje ka dibo 'kanwarka batada lafiya inaga ciwonta ya tashi"""

"""Mom kinsan dai bana zuwa can sasshen saboda Umma banson abubuwan da takeyi"""

"""kayi hakuri kaje saboda Allah ai taimako zakayi"""

"""To shikenan"" yafada tareda mi'kewa ya wuce part d'insa, kayan sa yacire ya shiga wanka tareda"

"d'auro alwala don an rigada anyi sallar zuhr a masallatai, agida yayi nashi yasaka jallabiya mara nauyi ya nufi hanyar apartment d'in Umma,"

"Da sallama yashiga falon, amman ba kowa wuce wa sama yayi d'akin Sultana, kwance yaganta ta"

"du'kun'kune da duvet tana rawar sanyi,"

"Da sauri ya yakice duvet d'in yana ""Sultana meke damunki?"""

"Ahankali ta bud'e idonta tareda d'an mi'kewa ta jingina da gado cike da 'karfin hali tace ""Ya"

"Saddiq ina ta neman lambarka baya zuwa"""

"""Am sorry sis nashiga thearter shiyasa, how are u feeling now?"""

'Dan gyada masa kai tayi kawai numfashinta na fita sama sama

"""Sultana bakijin magana kinsan lalurarki but kina wasa da lafiyar ki gashi baki shan drugs, Ina"

"umma take?"""

"""Tafita tin d'azu"","

"""Kinci abinci?"" ya tambayeta, girgiza masa kai tayi,"

"""Toh meyasa?"", yasake tambayarta"

"""Yaya banason abincin da aka dafa ne"" ta fad'a tana d'an yatsina"

"""Zaki ci fried rice?"", gyad'a masa kai tayi yace"

"""toh Ina zuwa"" yafita"

"Babu dad'ewa sai gashi tareda plate d'in abinci, taimaka mata yayi taci sosai sannan ya d'auko box"

"d'in magugunnan ta yabata,"

"""Ki huta yanzu Idan kinji wani abu call me kin. """

"Bai gama magana ba yaji hayaniya daga bakin kofa wanda ko bai juya ba yasan Umma ce, ""muryar wani kwarton namiji nake ji a dakin 'yata"" juyawa yayi zai fita ta tare shi ""wai kai wani irin mara zuciya ne wato harkafara shigomin d'akin 'yata bana nan ko, to ahirr dinka, kar na sake"

"ganin 'kafarka cikin gidannan banzaye masu asiri"""

"Fashewa Sultana tayi da kuka ""haba Umma Yaya taimakona yayi fa banda lafiya, wallahi Umma"

"karki kara zagin Yaya meya miki saboda kawai baki son Mom shine zaki had'a dashi?"""

"Rushewa Umma tayi da kuka tana ""shikenan Allah y isa tsakanina da Amina wato banda mutanen"

"gidannan dana gari yanzu har 'ya'ya na ma ta asirce su nashiga ukku na lalace wallahi da sake"" ta 'karashe da kururuwa"

"Sunkuyar da kai saddiq yayi yana ""Allah y baki hakuri Umma"""

"Cikin masifa tace "" fice min d'aki tsohon munafiki kawai kamar mutumin kirki sai wani sun sun"

"da kai yakeyi"""

"A hankali ya ra'ba ta gefenta yafita yana girgiza kai,"

"'Kara fashewa Sultana tayi da kuka, wani mugun kallon Umma ta watsa mata ""munafuka kema"

"daya sai kitayi tinda na kori ubanki"" tafitana tana banko kofa."

"""Ai Umma Yayana ne kuma baki isa ki raba mu ba duk duniya banda kamarshi, kuma inasonshi."

*ABULLE POV*

"""Abulle to kinyi shiru munata sauraronki, ai kwarankwatsa ki fidda duk wanda kikeso a nan,"

"wallahi sai an aura maki, in bayada gida ma ni zan bashi"" cewar Mai gari"

"Dariya Abulle ta she'ke da ita sanan ta girgiza kai irin abun na mata dad'i, chan ta mi'ke ta fara tattakawa tayi gaba tayi baya tana 'karewa jama'ar wajen kallo, murmushi ta saki sanan tace "" duk"

"'kauyen nan wa yafi kud'i?"""

"Aikuwa jama'a suka d'aga murya har suna rigegeniyar furta "" Mai gari"""

"""Gonakin wa suka fi yawa"" Abulle ta kuma wage murya ta tambaya"

"""Mai gari"" Jama'a suka dad'a amsawa. Mai gari kam zufa duk ta ji'kashi bai san lokacin daya zamo"

daga kujera ba

"""Abulle ai gonar taki ce, ki za'bi miji sai na barmasa"" cewar Mai gari"

"Wani kallon zakaci ubanka Abulle tayi masa, sanan ta kuma tambaya "" wane ne ya ta'ba zuwa"

"binni?"""

Ai ko suka kuma d'auka sunan Mai gari

"""Jama'a to ni Abulle na tsaida Mai gari matsayin mijina, domin shi yafi cancanta ya zama mijin"

"Abulle"" ta fad'a tana washe baki"

"Mai gari wasu zufa da hawaye ne suka kuma zubomasa, rarrafawa yayi gabanta, gwiwoyi 'kasa"

"yace "" mi zaki yi da tsoho?"""

"""Shine za'bina"" Abulle ta fad'a..........."

"_Few pages to last page, ku garzayo ku biya naku, kada ayi babu ku_"

Mss Flower & Mrs Abdool

_MASOYA MUNA JIRAN A NUNA MANA SOYAYYAR DA AKE CEWA ANA MANA TA

SIYAN LITTAFIN NAN_

"*NAIRA 200 NE KACAL, ZAKI MORE KARATUNKI, KI SHA DARIYA GAMIDA"

ILMANTUWA*

"_ZAKI BIYA TA WANAN ASUSUN 0104322069, SAKINA ABDULLAHI, ACCESS.

Please Login or Register in order to submit comment