gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading DOGUWAR HANYA Dajin Tsafi by Billy Galadanchi Chapter 9 | ArewaNovels google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sakin fuska abinda ya masu mamaki kenan, batako tambayi inda sukaje ba, ta mik'e tabar wurin, kallon juna sukayi kafin suma su mik'e gwiwa a sace zuwa cikin gidan a b'angaren su.

************
Tun jiya ake zuba sanarwa amma har yau babu wanda yace yasan fuskokin mutane biyu, Ayusher dukta shiga damuwa, wayan Sufyan ta kuma kira, bayan sun gaisa tace cikin sanyin jiki

"Pure heart beyi working ba wlhy, har yanzu fa shiru babu wanda yace ya sansu ma" nisawa yae ya kalli Abu huraira dayake kwance ya lumshe idansa kamar me bacci amma a zahiri ba baccin yake ba yace

"Ina kince d'ayar karaya ce kawai, a baki ake karaya ne? Tayi magana mana" Nisawa tae

"Yare takeyi kamar yarbanci kamar kuma wani abu daban" zabura yae ya kalli Abu huraira yaga bashi yake kallo ba yace

"Kina ina yanzu?"

"Ina asibitin mu" ta bashi amsa a tak'aice kashe wayar yae ya fice daga d'akin cikin hanzari, huraira yana wata duniyar dabemasan wainar da ake toyawa ba tukunna....

Kallon patient d'in yae cikin nutsuwa hankalinsa duk se ya tashi yace yana kallon Ayusher

"Ayush baki gane wannan yarinyar ba wai?" Kallon mamaki ta masa

"Ni ina zan santa bare na gane ta?" Shafar sumar kansa yae

"Yarinyar dakika tarar agidan mu ta taka glass d'innan, danakewa hanifer masifa akanta" waro ido tae

"Are you serious?"

"Wlhy itace Ayush, kwana nawa muna nemanta, ni banmasan yanda akai ban gane ba tun sanda kika gayan" nisawa tae

"Alhamdulillah yaa Allah, hankalina a tashe yake tun faruwar al'amarin, bansan madafa ba" yafita shiga farin ciki me yawa, daga bisani kuma ya shiga fargabar sanarwa Abu Huraira, ko shakka babu yanawa Lawuri Son so, duk kalaman daya fad'a dad'in baki ne kurin wa d'an uwansa bayaji ze iya sadaukar masa da soyayyar dayakewa Lawuri koda dawowa tayi arayuwar su kowa ya fanshi kansa agunta kawai, da wannan ya yanke shawarar barin hakan sirri na sanin makomarta.

"Ayusher akwai taimakon danakeso kimun" kallon sa tae cikin mamaki

"Name pure heart"

Murmushi yae

"Zanje da kaina nawa mom mgana akan yaran, muso muke su karb'i musulunci amma mom bataso ta barsu agidan mu, koda zata taimaka idan sunji sauk'i sesu xauna gunku, yaran danake gaya miki ne fa munzo dasu a hatsarin damuka shiga,kuma wannan ta taimakemu sosai, and please karta gayawa mom suna gunku" Nisawa tae

"Pure heart dan wannan sekaje gun mom, karka damu bazan mace mata su bane, kurin zan dakatar da sanarwar kuma inshaa Allah zan nuna bamu samu iyayen suba zan rik'esu zuwa time daya dace kake kuma buk'atar su" godiya yae mata sukai sallama ya yafi.

A hanya se murna yake akan ya samu Lawuri, ya k'udirta kuwa baze tab'a gayawa Abu huraira inda suke na.

************
*Bayan kwana biyar*

D'awai niya sosai yake dasu har lokacin Lawuri se adu'a amma jiyan anyi nasara ta farfad'o, Dr. jalal shine mutum na farko datayi karo dashi tun bayan data farfad'o d'in, iyakar bincikensa akanta kuwa ya gano ta samu total lost of memory!!!!! Wanda tayi matuk'ar bashi tausayi duba da yanayin shekarunta.

Yarinyar ta tsaya masa arai so yake ya taimaketa ta dawo daidai amma waze taimakeshi aikata hakan? Irin wannan fa dole se akwai wanda ya sanka cen baya, wacce suke tare ma tana samun sauk'i amma magana da ita ma wahala ne, shi kuwa da kanshi yakeso ya taimaketa, da kanshi yakeso ya daidaita tunanin ta zuwa duniyar ta ta baya, taji jiki ainun, da wannan yanemi Ayusher.

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

Litattafan mu ba free bane, na kud'ine dan Allah idan baki siyaba karki karanta,idan kuma kina buqatar daya daga ciki ki nemi wannan lambar 07084161619.

Kamar da wasa (ummie Aisha)
Sultan merah (fatima zarah)
Doguwar hanya (Billy galadanchi)
Zafin Rana (Ayusher muhammad)
Sanadiyya (Maman khadyy).

             18
Jinjina kai Sufyan yae bayan ya gama jin bayanin  Dr jalal

"Duk zan iya likita nidai fatana ta dawo cikin hankalinta kawai komai nata ya zama normal"

"Idan akayi hakan zamu samu sassauci kaga tana samun difficulties wurin magana so dole semun d'auki mataki wannan ciwon maya buk'atar magani sedai ayita kulawa dasu ana koyar dasu abubuwa masu yawa" Sosai sufyan yae godiya kafin su rabu.

***********
   Murna awurin sufyan ba'a magana yana fatar karma memory d'in nata ya dawo sabida yanaso tasoshi shishi kad'ai batare da wani ba, yanaso ta manta da wani Abu Hurairah tun a wancen garin ya kula cewar tanason huraira shikuma baya fatan taso waninsa.

   Zama yae da kanshi yake bata abinci abaki, se murmushi yake zuba mata yana mata magana da hannu, kallonsa kurin takeyi bata fahim tarsa sam, language data iya shibawai ya iya bane ba ruwa ya bata tasha sannan yace

"Lawuri?" Kallonsa takeyi sam bata gane ko waye bama tunaninta ya tsaya cak ta gagara tunanin komai ita kam

"Sannu" shine abinda ya furta yana murmushi, ta gane kalmar tasan ta amma bata tunano komai ba, TV ya kunna ya zauna yana kallo yana nazarin kalmomin yarbanci daya soma koya a wurin Dawood da takarda da biro a hannun sa, so yake yariqa yin magana da ita shishi kad'ai, ya iya yaren su sabida kota kwana idan ma memory d'inta ya dawo shine abu huraira shi takejin yarensa kawai.....

     "Al-Hussain ina cikin tashin hankali, yaran nanfa hakk'in su yana kanmu, mune fa mukazo dasu wannan Doguwar hanyar batare da munyi wani dogon tunaniba, yanzu kana ganin daidai ne ace mu k'yalesu? Kana ganin daidaine mu fita sha'anin su bamusan hannun wa suka fad'a ba? Bamusan inda suke ba bayan ni dakai munada tabbacin cewar yaran nan basusan hanyar garin suba, ni inaga bamuwa kanmu adalci ba bakuma mu musuba" Nisawa yae yana me kallon yayan nasa

"Twin ya kakeso muyi? Neman mutum a fad'in Nigeria nan ba abu bane daze mana sauk'i, munyi iyakar yinmu mesa newai kake k'ok'arin  jefa rayuwar ka a hallaka akan wad'annan yaran? Kaga yanda ka rame kuwa? Dan Allah bro ka dena maganar yaran nan" kallonsa kawai Hurairah yake cikeda mamaki

"Al-hussain yaushe ka dena damuwa da damuwar d'an uwanka? Yaushe ka soma sauyawa haka? Har yaushe ka soma manta wa da abinda nakeso? Ka manta soyayyar danakewa yarin yar nan kuwa?" Kallonsa shima yake cikin jin zafin jin wai yanason Lawuri har haka

"Amma Al-hassan Hannifer kuma fa? Tun yaushe take dakon sonka?  Tun yaushe take bibiyar ka, banji tausayinta ba  matsayinta na mace sekai zanji tausayin ka, idan har akasan abinda kakeji game da ita babba ne ya kamata ka dubawa wannan yarinyar itama, ka ajiye son watacen dabaka masan inda take ba kaso k'anwarka ta jini" Gabaki d'aya ya gama rikitar dashi be saba yi masa magana haka ba, rana d'aya sukazo duniya amma yana matuk'ar girmamashi kasancewar shine yazo kafinshi

"Al-hussain meke dmunka ne? Meya sameka hakane baka kallon damuwata seta wata hanifer?" Mik'ewa yae

"Hanifer fa ce wata? Nifa bro damuwata d'aya wannan damuwar daka sanya kanka aciki, ka musu adu'a kurin shine abinda suka fi buk'ata a yanzu dai daga gunka" bece masa komai ba ya d'auki towel ya shiga wanka ya fito ya kimtsa se feshe feshen turaruka yake yana gyara sumar kansa yayi kyau matuk'a, kallon sa huraira yae sanda yake k'ok'arin barin d'akin

"Twin ina cikin damuwar ne zaka fita ka barni ko kamun yanda ka saba kace nazo muje gun friends namu indan sake haka muka saba dakai?" Kallon agogon hannunsa yae

"Bro da akwai inda zan biya ne gashi kaga ko wanka bakai ba, idn ka kimtsa kamun waya zan dawo na d'aukeka kaji" Bece komai se kishingida da yae

"Twin ya canja sosai, ya fita harkarsa ya dena fita tare dashi ya dena damuwa da damuwar sa meya sameshi?" Da wannan shima ya kimtsa ya fice.

**********
   "Dawood mesa kaida sufyan bakwa tausayi nane wai? Kafi kowa sanin cewar ban tab'a samun yarinyar danace ma inaso ba idan ba Lawuri ba, amma sam ta b'ata kun wofintar da ita kun manta haqqin kulawa dasu yana rataye ne a wuyanmu" kallon nutsuwa Dawood ya masa

"Nifa Abu Hurairah inaga adu'ar neman tsari ya kamata mu nema da wad'an nan mutane, bawai kai kad'ai ba nida kaina seda na fad'a tarkon ta, da momy ta kula ta dinga mun adu'a aka saka malamai ma sunayi sannan na samu lafiya akanta, abu na gaba kuma idan ka kula da kyau zakaga cewar bamune muka koresu ba da kansu suka bar gidan kuma Allah ya gani munyiniyakar yinmu, yanzu me kakeso muyi" Nisawa yae cikeda damuwa

"Amma dukda haka baka ganin ya dace mu koma garinsu mu bincika kosun dawo, ka tabbatar fa cewar bawai sunsan hanya bane ba, bakuma wai sunajin yarukan garin bane, yarbawa kuma bawai lallai su taimaka musu ba" kallon tuhuma dawood yake masa cikeda mamaki da tunanin anya hankalinka d'aya kuwa

"Kana haukane Abu Hurairah, yanzu kai Allah ya tsamoka daga hallaka sannan kace zaka koma, kasani irin azabar damukasha da *Doguwar hanyar* damuka bi Allah ne kad'ai yasa munada sauran shan ruwa agaba, kuma banda Allah babu me iya mana wannan, bari kaji idan harkai so ya rufe maka ido ni badaniba bazan tab'a komawa wannan hanyar ba, dan inada hankali na, ko dama nifa kurun ina sha'awar mukai musulunci agarin dababushi ne amma ban shirya hallakar da kaina akan mace ba"

"Haba mana Dawood mesa bakwa tausayi nane wai? Mesa kakemun haka? Wlhy rashin ganin wannan yarinyar tamkar rasa wani b'angare ne ajikina, ka taimakeni"

"Tausayinka nakeji wlhy d'an uwana, dole zanwa mommy magana ma anema maka magani kaima dan wannan abun tashin hankali ne, ace dai duk uquba da azabar damuk sha a wannan *DOGUWAR HANYAR* har kake iqirarin zaka koma?" Ai wannan kasan bawai aikine na hankali ba" Shiru kurun ya masa harya mik'e yabar masa d'akin gaba d'aya.

************
Tunda yake maganar general kallonsa kurin yakeyi, mamaki yake yanda yaron ya k'wallafa ransa akan yarinyar ya sani uwarsa koze mutu bazata yardaba, kuma yasani tabbas idan be masa abinda yake soba akwai matsala

"Amma kai Huraira dolene sekaje da kanka? Idan neman yaran kakeso ayi kabari da kaina zan tura manyan soji suje garin amma bazan bari kai kaje ba" langwab'ar da kanshi yae ya marairaice fuska

"Dad ka taimakeni aje dani, dan Allah na roqeka, kuma ni base ka gayawa mom ba kurun dai nika barni i promise u zan tsaya bayan sir shamsu akoma meye" Shiru yae yana nazarin maganar sa secen yace

"Idan kun tashi kubi ta wannan ruwan, ta garin wannan fulanin wannan jejin yanada matuk'ar hatsri, zan maka adu'a kakuma tabbatar hadda yad'uwar musulunci ya sanya kakeso kaje da wannan Allah ze dafa maka" haka yae godiya ya tashi murna fal aranshi.

**********
Tunda yaje gunta suke magana da 'yan kalmomin daya iya na yarbanci, komai shine yake shige mata gaba tanayi, sunyi shak'uwa me yawa, a hakan kuma yake mata hausa, lokuta da dama tare suke kulawa da ita shida Ayusher ko yanzu atare suke suna hausa suna yarbancin dasuma tsinta gwanin dariya, danma tanada kan kamawa sabida acikin 3 weeks harta soma iya mayarwa da hausar, ita kuwa Ayusher baiwar Allah har ita ake koyon yarbancin sabida tanaso taga Abu sufyan acikin farin ciki, kuma zaman yarinyar agidansu ya k'ara janyo kusanci a tsakanin su sabida kusan kullum yana gidan..

Mik'ewa yae ze tafi ya soma sallama dasu, kurun se Lawuri ta soma kuka akan zata bishi, hannunta ya rik'o duka biyu

"Má binó Lawuri (kiyi hak'uri Lawuri)" Langwab'ar da kanta tayi cikin shagwab'a tace

Igbawo lóma dé ? (Yaushe zaka dawo)


Murmushi yae yaji me tace amma besan meze ce mataba da
yarbancin se cewa

"Da sassafe gobe" sarai ta fahimce shi setayi murmushi tace tana zare hannayenta

"Odaró (seda safe)

Ta furta tana me juyar da kanta alamun btaso ya tafi, takaici duk se ya kama Ayusher amma seta had'iye kurin itama ta soma rarrsahinta da hausa.

Abu sufyan yabar wurin cikeda begen Lawuri yanaji aduniya baze tab'a iya yafewa waninsa itaba har abada.

**********
Shirin tafiya sukayi akan shi Huraira zashi tafiyar aikine sokoto, adu'a sosai mahaifiyar sa ta masa sannan yabar gidan, inda akayi zasu had'u da sojojin anan suka had'u general ma yayi adu'a sannan suka kama *Doguwar hanyar* dasuke fatan binta a wannan karon ya zamar musu alkhairi.

Niko nace Allah ya fitar ga A'i ga cinikin rogon ta kodai ta fad'i ko taci riba.

*********

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

 

*Littafina  na kud'i ne, dan Allah idan baki siyaba karki karantamun, kokimun ki tura wani gurin, bana Allah ya isa bane amma dai haqqina yana wuyan wanda ya aikata d'aya daga ciki, kuma koda ban fad'a ba duniya shaidace akan Allah isashene. Idan har kina buqatar karantawa ki nemeni ta wannan lambar 07084161619*

       19
Zaro wayrsa yae daga aljihunsa cikin takaici dan sosai ta dameshi da ringing, ganin Al hussain da yae yana kiranshi yasa ya d'aga cikin mamaki

"Mekenan haka kayi bro? Mesa zakamun haka?" Kishingida yae ajikin kujerar  motar yana lumshe ido

"Me kuma nayi maka?" Ya furta cikin mamakin kalaman d'an uwan sa

"Dad ya gayamun komai, Amma na sanar dakai yaran nan basa garinsu fa mesa zaka nace akan sekaje?" Sumar kansa ya shafo zuwa sajensa har zuwa gemunsa yad'anja a hankali

"Wane yaqini ne dakai nacewar basa garin su? Hakan yana nuni ne da cewar kasan inda suke kenan?" Se a sannan ya gano wowtar da yae na furta hakan

"Da nasan inda suke yaya zan barka ka tafi a banza? Kurin dai ni nasan basu san hanyar bane ba ko alama, kuma naga k'afarka har yanzu kana d'ingisawa ai"

"Wannan ba damuwa bane kaidai bakaso ka joining hand dani mu taimaki musulunci, baka kuma so in smu abinda nakeso so kayi abinda ya shafela plss ni zanyi nawa"  mamaki sosai kalaman sa suka baiwa sufyan

"Bro abin yakaimu haka mesa zakamun wannan maganar" tsaki Huraira yae

"Sufyan plss pray for me if u can, babu abinda zaka gayamun yanzu, banaso mui wata doguwar magana yanzu plss" yasan halin huraira tunda yace fushin yake da gasken kuwa shiyake mutunci d'aya zewa kanshi ya barshi for now, da wannan yamai adu'a kurin yana mejin zafin zuciyarsa duk yanda yaso ya sanarwa d'an uwansa gaskia zuciyar sa ta hana.

***********
    Yau duk sukuku Sufyan yake har Lawuri ma ta fahimci haka seya kasance basu wani hira, tunanin d'an uwansa duk ya dameshi, shibesan meke damun saba, zama kusa dashi tae ta shagwab'e fuskar ta amma ta rasa ma me zatace masa, da k'yar ta tattaro kalmar

"Kiló shiyé lèni "Meke damunka yau" be fahimta duka ba amma tabbas ya gane abnda take nufi, murmushi ya qaqaro

"Ba komai fa Laure" Langwab'ar da kanta tae adaidai sanda Ayusher ta shigo d'akin da sallamar ta hankalin ta yana kan yanayin sa dakuma yanayin zamansu, zama tae ad'an nesa dasu idanta yana cikin nasa

"Sannu" shine abinda tace dashi kurun ta kawar da kanta gefe d'aya cikin takaici

"Menene damuwar kuma? Naga duk kin canja" ya tambayeta cikin nuna kulawa

"Ba komai idan ka gama abinda kake zan jiraka a babban parlor akwai maganar danakeso muyi" jinjina kansa kurun yae

"Muje a shirye nake, kallon Lawuri yae ya shafi sumar kanta

"Zan dawo yanzu kinji?" Ya furta cikin harshen hausa, gyad'a masa kanta tae danta fahimci me yake nufi.

"Dama akan abinda kakeyi da yarinyar cenne, kaga ka zire mata da yawa fa pure heart, bama wannan ba kaifa ka hanani hugging naka, shaking hand dakai amma yanzu se inga kana rik'ewa yarinyar cen hannu, kana matse wurin zama da ita anya hakan daidai kuwa?" Wani yamutsatsen kallo yabita dashi cikin hargitsi

"Me kenan kike nufi da wannan maganar? Zargi na kike da yarinyar kome?

"Wannan wace irin magana ce Yaa Sufyan? Ni yaushe nace wani zargi anan? Kurun ina gaya maka gaskia ne, mom ma tayi magana akan zaman yarinyar agidan nan, tunda an sallameta daga asibiti ka kaita gidanku kurin" cikin takaici ya kalleta

"Sabida na nemi alfarma agunki shine zaki zomun da hauka? Mesa zakimun haka ne wai? Ni yanzu kin rainani idan da inason ta zauna gidan mu daban kawo ta nan ba ai sabida kanki ne cewar munada muhallin ajiyetan" Yanzu kam itama ta fusata

"Sabida ina bautawa sonka seka mayar dani baiwarka? Sabida ina jarabtar sonka seka laftamun wata jarabawar, mayar dani wawiya kakeso kayi ko wacce batasan metake ba, idan hakane na dena damunka da zancnm soyayyata koda hakan ze zamo ajalina, ada roqonka nake kazo gidanmu amma sekayi wata kanamun yawo da hankali tunda kazo da wannan dangin mayun kake ziyartar gidannan wani zubin agunta kake wuni, an gayamaka banida zuciya ne? Daga rana me kamar ta yau na yafe duk wani abu daya dangance ka koya shafeka aiba kai kad'ai bane autan maza amma ka kwashemun dangin maguzawan cen daga nan gidan kaje dasu koma inane" yaukam mamaki Ayusher ke bashi iya mamaki, har wanda be tab'a tsammani ba, kwantar da murya yae

"Karkimun haka mana Ayusher, ki tallafeni ki k'aramun lokaci wlhy dik abubuwan da kika lissafa bawai haka bane ba, tausayi kurin suke bani" k'ura masa ido tayi

"Zan barsu su zauna, zan kuma yiwa mom magana akansu amma daga rana irin tayau karkai tunanin zan kula maka dasu, ka neki me aiki zasu koma b'angaren ma'aikata, karkuma ka k'ara zuwa inda take ka nemeni, ni bana mason ziyarar nabar mata" rarrashin duniya yayi amma haka ta kafe akan idan be yarda da hakan ba ya kwashe su agidan, badan yasoba yace ze duba me kulawa dasu d'in.

*********
Seda suka zo k'auyen fulanin dazasu hau ruwa sannan sukai shiri suka ajiye motocinsu suka kama hanyar wacen garin fulanin na biyu, basu kwana ba suka kara tsalaka ruwa suka shige d'ayan garin inda aka musu karamci, sosai sukayiwa dattijon hakimin k'auyen bayanin dalilin dawowar su, jinjina kansa yae cikin jimami

"Bana tunanin yaran nan sun dawo ta wannan hanyar gaskiya, kuma kunce basusan waccen hanyar ba, akwai gari idan an tsallaka ruwa anan yamma damu da suke cin naman mutane, abinda ya hanawa garin yawa ma kenan, sabida naman junan su ma ci sukeyi, yazamana aka shard'anta atsakanin su duk gidan dasukayi magana da juna so biyar arana agidan za'a d'auki mutum a yanka, idan baku manta ba na sanar daku kuma arziqi kukayi sabida zamansu matsafa, zakaga ko kallonka ma ba wanda zeyi a k'auyen ya kamata suma ku kula dasu sosai, rayuwarku da lafiyar ku itace tafi komai muhimmanci agareku, zancen musulunci dakukeso ku yad'a bazan hanaku zuwa isar da sak'on Allah ba, amma idan ba haka ba ku hak'ura wad'an nan matan dai basu dawo ta wannan hanyar ba sam" Abu sufyan ne ya tare da cewar

"Babu damuwa Ranka ya dade, dukda hakan zamuje mu duba su, hankalina baze kwantaba sena tabbatar basuje d'inba, kuma na isar da sakon Allah" jinjina kai dattijon yae

"Bari na baku aron mutane dasuka san kan jejin sabida tsaro" haka ya had'asu da fulani su hud'u suka shirya tsaf bayan sun basu ajiyar muhimman kayansu ciki jarda wyoyin salula suka lula doguwar hanyar....

*********
Cyama yauma kamar kullum se rarrashin mom take amma abun yanaso yafi k'arfin ta, general ya sanar mata inda Abu Hurairah yaje se kuka take akan ya cutar da ita, yaya zebar yaronta yaje wannan mugun wurin akan wad'an cen yaran

"Cyama tun shigowar yaran nan arayuwata nake ganin jarabawa iri iri, wlhy halinsu ya isheni, nagaji da mugun abun dake bibiyata, daddynku kamar bashi ya haifi yaran nan ba, duk wata musiba ita yake jansu ya kaisu aciki, shi mesa bejeba in hakane?" Rufe mata baki Cya tae

"Hana mom, mesa kike hakane wai? Ya dace kisan me kike fad'a gaskia, dad daya dage wurin ganin ya inganta rayuwar mu da taki ma, shine kuma yanzu kike zancen yayi kaza yayi kaza, sam be dace ace hakan daga bakinki yake fitowa ba gaskia, ki masa adu'a Allah yasa ya ganta kuma su dawo lafiya" wani hargitsatsen kallo mom tayiwa Cyama

"Su dawo dawa? Idan ma mafarki kuke kedasu toku farka indai ina numfashi a doron duniyar nan wlhy kinmaji na rantse d'aya daga cikin yaran nan baze aure wannan shaid'aniyar 'yar maguzawar ba, koda bazasu auri matan dake sonsuba toko tabbas wannan shegiyar ma bazasu aureta ba" kame baki siyama tae sabida sanin halin mom tasani indai ta kafe akan abu ta kafe kenan, haka dai ta ringa rarfashi harta sakko.

**********
Daren da yae musu ne a hanya ya basu damar kafa tent irin na soja suka kwanta aciki, Abu Huraira seya rasa meyake yawan fad'ar masa da gaban sa a wannan lokacin, da k'yar da sid'in goshi bacci b'arwo ya sace sa badan yaso bama, baccin sam bawai yana masa dad'i bane wannan ya sanya gari yana soma haske alamun sanyin asuba ya farka, shiya soma fita fitsari domin yasamu damar yae alwala yae sallah ya tashi sauran musulman dam tafiyar akwai arnan soji acikinta susu biyu, seda ya lula duniyar wasu itatuwa sannan ya tsaya ya soma fitsarin, kaman daga sama yaji an k'wala mar abu akai seda yae wata uwar k'ara daga nan ya some besan me ake ciki ba, Oga sufyan dayaji ihu ya duba tent baya nan seya fargar da sauran suka lula jejin nemansa.

*************
Abu Sufyan tunda yabar gidan su Ayusher se wani zazzafan zazzab'i ya rufe shi, tunanin sa ya tsaya cak akan yanzu idan kuma garin wannan tafiyar Abu Huraira ya rasa rayuwar sa fa? Yace masa me? Mesa sanda sukai waya be sanar masa Lawuri tana nan ba yasan inda take? Tunanin d'an uwan sa sosai ya addabesa harya saukar masa da zazzab'i shi yasan yana son Lawuri amma ganin yanayin d'an uwansa kurin ya isa ya nuna maka cewan beko kama k'afarsa ba a soyayyar ta Lawuri, amma bayaji ze iya bar masa ita kam, sedai yanaso ya ganshi tare da d'an uwan sa, duk sanda ya tuna yanayin tsoro daya shiga a wancen lokacin dakuma wahalr dayasha se taimakonsa da Abu Huraira keyi seyaji zuciyar sa tana masa zafi akan abinda ya masa, ya tabbatar da Huraira yasan yana son Lawuri baze ma nuna masa yana santa ba sedai ya mutu dan nashi farin cikin kawai, abubuwa sun taru sunwa Sufyan yawa duk inda hankalin sa yake atashe yake...

**********
Yanayin mutanen dake kan Abu Hurairah abun ya tsoratar dashi, duk jikinsu fenti ne, ja da fari, idanuwansu ma abun tsoro ne ja jajir anja musu layin bak'i a k'asansu, gasu suma k'arti bak'i k'irin dasu, yama rasa shi tunanin me zeyi, an tub'e masa kayan jikinsa gashi tsirara, besan wannan wace kalar al'umma bace kuma? Shidai yaga rayuwa se wasu surutai suke da sam baya gane komai akansu, hankalinsu yakai k'ololuwa gun tashi.

***********
Wani daga cikin fulanin ne ke magana akan b'atan Hurairah

"Al'ummar songai ne suka d'aukeshi, matsalar su kuma basa zama gu d'aya, yanzu Allah kad'ai yasan me zasu masa" shiru OGA shamsu yae yana tunanin komawa gida dazaran sun ganshi,musiba daga wannan se wancen gaskia shi bega amfanin haka ba, oga beyi tunani me kyau ba, wanban ba aikin qasa bane na ra'ayin sane.



Mom Nu'aiym.

[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

*Littafina na kud'i ne, idan kinaso ki karanta kine mi wannan lambar 07084161619, koki tura 200 ta wannan acc number 0026971316 Balkisu musa galadanchi gtbnk. Seki wa waccen number magana, idan katin wayane kuma ki tuntub'i wannan number 08030811300*

20

Nutsuwar sa ya tattare yana nazarin me mutanen suke nufi dashi, bega alama suna cin mutane ba, bare yace namansa jikinsa suke hari, began su da wata alama ba ta nuna cewar zasu cutar dashi ko suna shirin cutar dasu bare yace, kurun dai ya kula suna zagayeshi suna wani yare sa ihu wasu daga cikin suma harda kukan su idan suna yi, be gane kan komai ba shikam duk iyakar zurfin tunanin sa, dukkanin wani abu dasuka ci suna bashi ruwama besan ina suke nemowa ba amma sukan bashi yasha, ya kula da sanduna suke fad'a kuma kullum cikin training suke kome suke nufi

Please Login or Register in order to submit comment