gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading DOGUWAR HANYA Dajin Tsafi by Billy Galadanchi Chapter 15 | ArewaNovels google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

harsekin karb'i musulunci da zuciya d'aya, zan taimakeki har iyayen kima su karb'i musulunci da duka 'yan garin naku baki d'aya" shiru tayi

"Amma yanzu idan na shi kuma hurairan yace baya sona fa?" murmushi malamin yae sabida shi haukanta yake kallo, babu yanda za'ayi ya bari wannan yarinyar ta sub'uce masa

"Ai Lawuri musulunci da kike gami abune me matukar sauk'i, Allah ya had'a zukatan mu da samun sauk'i idan suka mik'a masa lamuran su, aure muk'addarine kedai idan musulunci zakiyi toki yarda dacewar akwai k'addara me kyau akwai kuma mara kyau, ki yadda da cewar kowace k'addara tazo maka daga mahaliccine, a labarin dakika bani naji cewar kinada wanda da zaki aura a garin ku to bakiga iyawar Allah ba tun a kansa? Tunda kikaga Allah ya rabaku ki d'auka cewar shid'in ba Alhkairi bane a tattare dake kingane ko?" Jinjina kanta tae cikeda gamsuwa da bayaninsa sannan suka tusa daga inda suka tsaya.

*********
"Zuwa zakiyi ki koma gidan da zama, ni babu yadda za'a nemi mayar dani uwar banza, ga zab'ina azo a wani ce wai dole se wacce lalatacciyar ta tare, shi General besan halina bane " kallon mom hanifer tayi

"Mom to akan me zance gidan amarya na tare? Kinga hakan ai shiga hakk'ine ko?" Kallon mamaki mom tanita dashi hadda su tsarabar rank'washi

"Ke wawiya ce why, Ita Cya zan turata ne gidan Abu sufyan, ke kuma zance ne kije gidan Abu hurairah kike rik'ewa matarsa ayyuka tunda yake tanada juna biyu, ai bawai zamu fito zahiran bane, a baibai zamu b'ullo musu" jinjina kai Hanifer tae

"Nagode mom" rungumeta mom tayi

"Farin cikina shine inga auren Abu Hurairah akan ki" murmushi kurinntae cikeda kunya ita adole ga surukarta.

Tunda ya dawo ya taradda Hanny agidan beji ajikinsa alkhairi bane ya kawota amma idan ma da wani k'udirin tazo shime maganin tane cikin ruwan sanyi

"Sannu yaa Hurairah ka dawo?" Ta tambayeshi cikin sakin fuska bayan fuskar nan tasha ado" kallonta yake yana mamakin Hanny sam ita bata fushi koma me aka mata

"Lapia lau, yau wuni aka kawo mana kenan" murmushi tae
."ai zama ma zanyi mom tace inzo in zauna anan, ba'a samo house help ba"

Jinjina kansa yae "To sannu da k'ok'ari ina Zuhrah?"

"Tana ciki, ni tunda nazo ma muka gaisa se kurun tabarni anan ban kara ganinta ba" Tab'e baki yae

"Batajin dad'i ne aikin sani" murmushi ta k'ak'alo

"Ea shiyasa ma na shiga kitchen ai, yayana da kaina nayi favorite d'inka semo da miyan egusi yaji kifi kuma" kallon ta yake tana bashi mamaki, yasan halin Hanny amma besanta da wannan sabon halin ba irin wannan kwarkwasan haka, k'ara tab'e bakinsa yae ya juya zuwa d'akin Zuhra yana cewa

"Thanks" a tak'aice.... D'akin da zuhra tae mata masauki ta koma ta shiga shirya wa cikin wasu kaya na d'aukar hankali....

A kwance ya taddata, kai tsaye kuwa wurinta yaje

"Zuhrah menene?" Kallon sa tae idanta ya d'anyi ja

"Jiri nake yawan ji, ga ciwon kai kuma inajin yunwa amma bana iya cin komai"

"Subhanallah sannu, tashi muje asibiti" kallon sa tae

"Ai inaga damun hak'ura ze sauka ne da kanshi" b'ata fuska yae

"Zaki fara mun wasa da lafiyan yara nane ko?" Batace komai ba adaidai lokacin wayanta ya soma bulayin neman d'oki, tanaso ta d'akko amma tana tsoron abinda zeje yazo, ringtone d'in kawai ya isa sanar mata da cewar yaa Faruk ne me kiran nata, kallon allon wayar yae wani zafi yaji ya taso masa amma seya kawar da kanshi ta hanyar barin d'akin

"Ki tashi ki sanyo hijab ki sameni waje" bata d'auki wayar ba harya tsinke a karo na biyu, da k'yar ta iya tashi ta wanke fuskarta ta sanyo hijab, a mota ma se kiranta faruk keyi tunda tace masa batada lafiya yake danna mata call har seda ta tsargu shi kuwa gogan se wayancewa yae tamkar be gani ba.........

*********
"Dama na barta ta tafi ne sabida in kashe su,tace sunan yaran Abu Sufyan da Abu hurairah , ka aika musu dodon tsafi su mutu ita kuwa a karkato da hankalinta ta dawo gida aure zan mata" kallon sa bokan yae

"Haba K'uru kafin ta tafi kyau in sani, kafin komai insan me zanyi, seda kanaso ta dawo zaka ce wani inmata aiki" Kawar da kanshi yae

"Kayi Hakuri Lantai, bani k'arawa amma dai yanzu kamata maganin suma a kashe su" wasu surutai ya somayi na hauka kusan mintuna ashirin kafin daga bisani ya kalli sarki k'uru

"Kafin wayewar garin gobe 'yan biyu sun zama tarihi, ita kuwa koda k'afane seta dawo gida na aika musu mutuwarsu yanzu" Tashi yae tsaye ya soma dirzar rawa sekace wani hauka sabon kamu......

*wannan littafin na kud'ine, idan kinsan baki biyaba karki karantamun dan Allah, mesonta siya seta tuntub'i wannan lambar 07084161619*

Tunda Abu Sufyan ya farka yau be k'ara samun nutsuwar zuciyar saba, wani irin fad'uwar gaba yake fama dashi mara misaltuwa, tun yana iya daurewa har ya soma jin ciwon kai da jiri, dolensa ya tattare komatsan sa yabar office cikin tsananin tashin hankali....

Kallon zuhra yae yau shima zuciyarsa a wani cunkushe yake jinta

"Ki yawaita adu'a zuhrah, shed'an yana tattali sosai wurin ganin yayi rinjaye a kaso 75 na al'amuran rayuwar ki, bakya sonyin azkhar, bakya sonyin nafila bakuma kyason tsawaita adu'a, bana miki fatan koma se Alheri zuhrah banida niyyan cutar dake, gaki da ciki irin wannan lokacin kyau ace kin fauwalawa Allah lamuranki, ki kuma sani martaba da darajar aurenki yana hannunki idan kin rik'e knki idan baki rik'e bama kanki, ki sani babu namijin daze aminta dake bayan kinci amanar auren wani tare dashi koda nan gaba k'addarar aure ta had'aki dashi kowaye shi anwurin ki kuwa, anan zan iya cewa dake Fatima kukan kurciya ma jawabine me hankali kad'ai kan iya ganewa, doguwar hanyar damuka d'akko nidake ya dace ki sani had'in bana mutum bane na Allah ne" jikinta ne yae mugun sanyi tama rasa me zatace, kaddai ya gano kiran da yaa faruk ke mata? Batace dashi komai ba kurin dai tayi murmushin yak'ene wanda akace yafi kuka ciwo.......... Ganin yanda Abu sufyan yazo ya shallake ta gabansa da wani mahaukacin gudu ya firgitar dashi, yasan yanda tuk'i wannan yayi yawa kam, wayarshi ya zaro yakira sufyan d'in, adaidai lokacin kuma shi ya kaiwa allon wayarsa kallo, beyi auneba yaji ammasa eban karan mahaukaciya, wata motar tazo ta ebeshi sunyi gaba, Abu Hurairah dake kallon komai hankalin sa ya tashi, ya k'arisa wurin yae parking yanata faman sharce uban gumi, yana kallon yanda ake kokarin ciro d'an uwanshi, jini ta hanci data baki ga wani uban yanka a saman cinyar sa daya ratso har kana hango naman jikin sa, gaba ki d'aya Abu Hurairah rikicewa yama rasa abinyi.....
Zuhrace ta kira mahaifinta atake yazo wurin aka kwashi sufyan da Hurairah da shima ga alama kanshi ya tab'u, se surutai yake suka nufi asibiti..


********
Lawuri tana zaune tana yanke farce kamar yanda malam ya umarceta aka kuma koya mata, sabida bawai yankewa suke be sukam, se kurun taji tamkar an tsikare ta, mik'ewa tae cikin gid'ima tasoma yin hanyar waje, da malam taci karo yasha gabanta akan ina zataje, amma qememe tace gun mahaifanta zata, yae yae se bori take seda ya had'a da gardawa aka kaita d'aki.


Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:02 PM] Maamah twins💕❤: 34***** Abu Hurairah tunda aka shiga da d'an uwansa emergency yake adu'a, ya saisaita nutsuwar sa danya tabbatar wa kansa wannan kad'ai itace itace mafita agareshi, bashida zab'in daya wuce yin hakan shima, zuwa dare an mayar da sufyan ward wannan ya baiwa Abu Huraira damar zama kusa dashi ya dinga tofa masa adu'an samun sauk'i dan wannan ita kad'ai ce gudummawar daze bayar ga rayuwar d'an uwansa a wannan lokacin...


***********
Bacci b'arawo shine yae awon gaba da Huraira a wannan daren, bashi ya farkaba se asuba cikin tsanani firgici da rud'un mafarkin da yae, da ambaton Allah ya farka yae saurin kai dubansa zuwaga d'an uwansa da har lokacin yake unconcious, da sauri ya kunna fitilar d'akin ya nufi gadon, ga mamakinsa mafarkin dai dayayi shine, gashi yana kallo jini yana malala daga bakin d'an uwan sa wai wani bak'in halittane yazo ya kwashe masa 'ya'yan hanji shine yaketa zubar da jini, rungumarsa yae cikin tausayi

"Nashiga uku sufyan meya sameka haka?" Bazeko iya magana ba, haka ya dinga kwarara aman jini, ba shiri Abu hurairah yaje kiran likita bayan ya tashi Dawood daga kwanciyar da yake ta bacci......

Iya bincike anyi amma babu komai a tattare dashi daya shafi dalilin aman jinin, hankula sun tashi ainun har yanzu be farfad'o ba amma jinin yanzu abun ma ya k'ara yawa ta hanci data baki, ga yanka a cinya ga buguwa da yae kai komai ma damun sufyan yake gwanin tausayi.......

"Yaya Huraira ni dama nacene ko zaku gwada yin masa adu'a ne asanya malamai daku kanku kukeyi, al'amarin nan yafi k'arfin accident gaskia, ya dace kusan me ake ciki" kallonta yae cikin damuwa

"Zan gayawa Dad inji mezece, Zuhrah nimafa banida lafiya wlhy tsaye kurin nake" kallon sa tae kafin tae magana ya soma tari, da gudu ya wuce toilet jikinsa har b'ari yake haka ya dinga kwarara aman jini bako k'akk'autawa, hankalinta ya mugun tashi ganin hakan

"Nashiga uku Al-hassan kaima irin na d'an uwanka kakeyi, mekenan yake shirin faruwa da rayuwar ku haka? Innalillahi wa inna ilahiraji'un" se kuka take wiwi ganin aman yak'i tsayawa ta juya da gudu tana k'wallahwa hanifer kira, tare suka dawo d'akin zuwa ban d'akin, yafi 10mns kafin abun ya tsagaita, kallon sa sukeyi dukkansu cikin tausayi se kuka sukeyi

"Yaa Hurairah muje asibiti dan Allah" hanifer tace bayan sun tayashi gyaran jikinsa ya dawo d'akin kan gado

"Base munje ko inaba hanny, karki damu kusan kwanaki 5 inayi ai, idan kuma ya dena shikena ai" waro idanta tae waje

"Kwanaki 5 yaa Hurairah ban saniba, mekenan kake shirin aikatawa rayuwar ka, menene matsalar ka wai?" zuhra ta furta tana ta kuka, sunyi sunyi ya kafe akan bazashi asibiti ba, ganin haka ya sanya hanifer ta kira Dad a waya take sanar masa.

Lawuri dai malam ya ciwo kanta ta hanyar mata adu'a da kuma sanya karatun alk'urani agaba, koma menene yasan mugun abu ake turo mata tunda ta musulunta, yanzu sunan ta Naja'atu sunan da ita da kanta ta zab'a abunta dan kanta, sedai har yau takanyi borin nan tamkar wata zautacciya.
********
*Bayan sati uku*

Dukda Abu sufyan ya farfad'o hakan baze hanashi yin aman ba, likitoci da kansu sun tabbatar wa mahaifinsu basuda wata matsala b'angaren lafiyar su daze sanya su dinga wannan uban aman jinin, sabida ko pcv nasu duk sanda za'ayi toko ze nuna kusan 40% ne koma fi, dukkkaninsu sunyi fari run rame sunyi wani fayau, yanzu abinda yafi komai ban tsoro shine yanda sumar kansu da girar idansu dana saman kai harma da gashin gabansu ke komawa fari kamar na tsofaffi kuma ayau an tashi da tashin hankakin gashin yana cirewa da kanshi...... Matsalar datafi kowacce tashin hankalin iyayen su itace wacce basa magana sam, sedai yake bak'i ya tafi, mom kam ta dakatar da ciwon ta ta dawo gunsu susu biyu tana jinya.

Zuhrah tana zaune ta k'urawa Abu Huraira ido banda kuka babu abinda takeyi, lokaci zuwa lokaci takan share k'wallan dake malalo mata cikin bak'in cikin ganin yanda mijinta ya koma, hannunta taji ya rik'o ta mayar da dubanta zuwaga hannunsu dake tsark'e kafin ta kuma kallon sa, murmushi ya sakar mata yana girgiza mata kansa alamar ta dena kuka hakanan, wani yawu me d'acin gaske ta had'iya kafin cikin tausayi tace

"Yaa Huraira yanzu naga baka magana, abincin nan baka iya ci, baka iya tashi fa, bansan meya same kaba, na sanar dasu abin nan iskane, amma basu kulani ba" Sauke k'wayar idanshi yae a k'asa shiya tabbatar cewar mutuwa zeyi bashida sauran shan ruwa agaba, yana so ya rayu da yaranshi, yanaso ya rayu da matarshi yana son zuhra, dukda a k'ark'ashin zuciyar sa yana son Lawuri har gobe amma shikam bayaso ya rayu babu zuhran sa, so yakeyi ya bata hak'uri ya rarrasheta soma yakeyi ya rungumeta ya bata baki amma besan meke hanashi yunk'urawa ba, gashi kuma babu abinda yake masa ciwo yarasa gane kan shi shi kanshi..... Ganin haka ya sanya kukanta ya tsananta shi kuwa se matse hannunta yake yana nodding kanshi alamun ta dena dan Allah amma ina kukan yaci k'arfinta sosai....

***********
Abu sufyan ma hakan take a gunshi domin kullum Ayusher sedai ta tasashi agaba tana kuka, dad yaukam abubuwan sunfin komai rikice masa musamman da akace tun daren jiya Abu Sufyan yake faman aman ba k'akk'autawa... Abu sufyan yana matuk'ar mamakin yanda sam baya iya adu'a ga abun aranshi amma baya iyayi, sedai ya dinga zuba gurnani yana ihu aduk sanda yake bacci domin kuwa har bayason wani abu me kamada bacci a yaud'eshi ya dinga mugayen mafarkai kenan kaman babu gobe....


Gado kusa da juna aka ajiye dukkansu sedai su kalli juna babu bakin magana maganar wannan matsalar tasu kuwa tagama zaga duniya kaf!!! Kowa da abinda yake cewa yana damunsu, mom ganin surukanta mata sunata kuka ya sanya itama tashiga yin nata, sabida yau jikin yafi ko yaushe rikicewa

"Seda na rok'i mahaifin yaran nan akan ya barmun yarana ya dage ya turasu wannan *Doguwar hanyar* yanzu gashi sanadin ratsa wannan jejin komai ya dagule mana, sanadin bin Doguwar hanya be amfanemu da komai ba yanzu ma kafiya irin nashi nace abin nan na addini ne akomawa malamai islama yaqi ya yarda jifa ne, ina kallo kenan yarana zasu mutu kalli yanda duk suka dawo, susu kad'ai suka san me sukeji,surukan nata duka rungumeta sukai sunata zuba uban gunjin kuka babu k'ak'autawa........gurnani sukajiyo daya sanyasu nausar dukkansu da sauri, tarar wa sukai dukansu ciwon ya tashi sun had'e hannayensu gu d'aya sunata gurnani da aman jinin yau hadda sare jinin me uban yawa, iyakar tashin hankalin sun shigeshi ko wannen su yanaso yae adu'a amma babu baki a zuci ma sunaso suyi amma sun gagara tunano komai acikin adu'a....

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:02 PM] Maamah twins💕❤: 35*** "Duk abinda kace ayi shi akayi, sedai ga hoto nan bata juyo ba, wani abu suke fad'a da bakinsu dan baji nake ba amma gasunan kallesu a ruwa, narasa menene a hannunta kullum shine yake hana mata zuwa kwata kwata....yanzu haka abunda muka mata na duk wanda ya kalli cikin idanta ya soma santa ya karye nayi nayi yak'i yaje, daso nayi wannan dasukaxo suka saceta su kashe juna ma akan soyayyarta, d'ayan har janyoshi nayi ya kamo hanya bansan meya hanashi k'arasowa ba, wani abu suke ambata dayake yawan k'onamun tsafi na" kallon sa K'uru da k'uruwa keyi kaman zasuyi kuka suce wayyo Allah

"Amma ai ya kamata kasan menene suke cewa, yanzu ace anan nahiyar akwai abinda ze gagari tsafin ka?" Shu'umun murmushi yae
"Ada babu amma yanzu akwai!!!! An samu a wata duniyar da damu bamusan dashiba me burgewa kalli yanzu suke rayuwa ma, dolene sena hallak'ar da yaran nan biyu saura musu kwana uku duk aljanan jikinsu su gama cinye musu hanji su gama tsiyayar musu da jini inyaso duk su mutu!!" Murnushin mugunta k'uru yae

"To Lawuri fa zata dawo?"

"Zata dawo dole ma, tunda farko kaine ka turata baka gayamun ba ai" cikin takaici ya kalleshi

"Ainasan kanada k'arfin ikon dawo da ita koda ta mutune, sabida haka nace taje danaga ta damu yanzu kuma suka dawo da ita, kuma ka kafeta anan bata sha'awar k'ara zuwa wani wurin su kuma a kashesu dukansu uku har wannan dasuke cewa Dawood" Wak'a da hauka ya somayi take hoton dawood ya bayyana yana zaune yana shan tea a hannun shi, wata k'ara ya k'walla ya nunashi da bindin dokin dake hannunshi yae wasu hauka sekuma ya kalli k'uru

"Su mutu a rana d'aya?" Da sauri k'uru ya d'aga kanshi alamar e, wani shirme ya somayi take agun Dawood ya soma tari tamkar tea d'in ya sark'eshi daga haka se aman jini bako k'akk'autawa, momyn sa dake zaune kusa dashi tana shan tea a take ta rik'eshi ta soma tambayar sa menene, ganin abun ya wuce wuri ya sanya ta soma kiran k'anwar sa, da gudu tazo, alk'ur'ani me girma ta d'akko ta soma karatun sa da k'arfij sauti, bata gushe agunba seda ta tabbatar ya dena, duk wannan abun dasukeyi Boka dasu k'uru suna kallonsu acikin k'warya, ihu suka k'walla ganin k'waryar ta boka ta koma koriya shar, wannan abu shine na farko daya faru a garin tun bayan samuwar mafarin al'ummar su, haka ya dinga gunji cikin k'araji da surutai bako k'akk'autawa bashiba hatta su k'uru sun rud'e da wannan al'ajabin.

*******
Babu shakka su twins suna cikin tashin hankali, abun ya soma wuce tunanin general ido ya k'ura musu yana tunanin mafita yanzu kam, sabida ba shakka akwai damuwa a wannan hatkar duba da yanayin su a wannan lokacin idanuwan su sun kad'a sunyi jajir tamkar an zuba musu jini ajiki ga fatar jikinsu ta soma tamurewa tanayin fari sekace wanda ya shekara be sgafa mai ba a lokacin da ake kwarara uban sanyi!!!!

Wayar sa ya zaro ya kira malam, bayan sun gaisa yake snar masa yazo asibiti, shisam yama manta da wata Lawuri ya kula kamr wannan damuwar da yae da ita soyayyace yanzu kuwa ya dena ji mezai damesa?.

Koda malam yazo yashiga rud'u sosai, umarni ya bayar akan a mayar dasu gidansa, wannan abun koba menene iskane kuma a haka yakeso ya kashe su, da wannan shi kanshi malamin seda ya kira mahaifin sa sabida yana ganin abun yafi k'arfin sa.......

Dawood kuwa sedaga baya abun ya k'ara tashi masa, inda atake mommynsa ta tuna da zancen su Twins,kai tsaye mom twins ta kira suka tabbtr mata ga inda aka wuce dasu, ita kanta alfarma ta nema na wucewa da Dawood shima a tallafeta a dubashi san gaskia baida lafiya.

******
Lawuri kuwa tana zauna aka kawosu, sam ko alama bata gane suba sedai ta gane daddy ta kuma gane Oga shamsu wanda idansa ke kanta, yana mamakin yanda hasken musulunci ya gama karb'ar fatar jikinta!!! Tayi sumul abunta dukse yaji ta burgeshi haka aka kwana ana abu d'aya karatun alk'urani ake yi da adu'a ana tofesu dashi amma se a hankali sauk'i d'ayane daya zamana yau duk basuyi aman ba, amma bnda haka babu abinda ya sauya na dangane da halittar da suka dawo su dukansu, haka haka dai aka bar su kwana anan, Lawuri jin cewar sune tasha kuka dan Dawood kurun ta gane ita kanta duk wata soyayyar datake ma Abu Hurairah jin take a irin yanayin datakeji yanzu badai soyayyar aure take masa ba, gaba d'aya hankalinta da nutsuwarta sun karkarta akan ciwon su itama adu'a tashiga yin musu babu k'akk'autawa.

Boka ya fusata dan haka yau yace aje lallai a kashesu, dan aljanan tsafin sa sun sanar dashi lallai suna samun barazanar wannan littafin dasuke karantawa ko yanzu ma da k'yar suka sha, umarni ya basu akan su kshe su yau har Dawood yaga tsiyar shi d'an sarkin tsafin k'asar ne kuma ya jima yana gagarar kowa yaya za'ace mutanen wata k'aramar al'umma su fishi iya tsafi!!!

An je sallan azahar an barsu se lawuri dake salla a d'akin tare dasu, gunjin kukansu da gurnanin da suke shine ya sanyata zanzarin son ta kammala salla taji menene? Da gudu gudu ta idar da sallar, abinda tagani ajikinsu susus uku yafi komai bata tsoro, tunawa tae da azaban da mahaifinta ya saba baiwa mutane idan sun masa laif agarin, tabbas duk sukai haka daganan zasu shek'a lahira da gudun fanfalak'i, waje tae tana ihun kiran malam su kuwa har lokacin sallah sukeyi, gashi ta tabbatar cewar daga garin sune wannan mugun abun!! Ilahirin jikinta tsuma yake ganin basu idar da slla ba ya sanya ta koma d'akin da gudu abinda ya saura su gangara shine jini a baki!!!! Ko shakka batayi wannan mugun abun ne ze kashe su, ga jikinsu yanata tsagawa jini na fita duk sun dawo sekace wasu fatalwa! Tana nan tsaye har su malam suka shigo da daddy malam ma ya rikice haka a saki radio sa sautin karatun alk'urani me girma, sukuwa adu'a kowa keyi yana faman tofa musu ana nan har suka soma tari a tare jini ya soma fita daga bakinsu susu ukun...Lawuri kam k'ofar waje ta nausa da gudu tana ihu lallai k'uru mugune me suk masa? Haka nan tana ganin jinin ta tabbatar sunma mutu shine abu na k'arahe dazatayi arayuwarta indai ya kashesu seta koma gida ta kashe har ubanta har bokan!

*Nazata munbar labarin doguwar hanya tuni, ashe k'afafuwan mu da gangar jiki kurin ta baro hanyar amma ruhin mu yana cen har yauu be baro doguwar hanya ba!!! Ko zasu kub'uta?****

*wannan book nawa na kud'ine me buk'atar siya seya biya 200 kacal a sakashi a group..nemi wannan lambar 07084161619*

Mom Nu'aiym.
[11/21, 8:21 AM] Maamah twins💕❤: 36**** lokaci d'aya jikinsu ya soma tashi daga farin da yae zuwa kore shar!!! Hankalin malam ya tashi ga malam babba ya d'aga, dad ma haka ya kira mahaifin zuhrah take yazo shima ya taradda wannan mummunan tashin hankalin,mahaifin Ayusher shine yazo da wani malamin na daban inda yasoma nashi adu'o'in acikin ruwa yana tofawa haka ya dinga watsa ruwan ajikin su na tsawon lokaci, a hankali abubuwa suka soma sauyawa zuwa samuwar lafiya daga barin aman jinin da kuma sauyawar fatar jikinsu zuwa asalin fatar su ta halitta, basu gusheba daga yi musu adu'a dakuma karanto ayoyi daga alk'ur'ani me girma har sanda suka fahimci nutsuwa ta saukarwa dukkansu!! Har suka soma bacci cikeda nutsuwa.

Ihu boka keyi yana guje guje daka ganshi kaga hauka sabon kamu tuburan!!! Gabaki d'aya gidan sa seda ya qone da duk wani abu daya shafi tsafinsa da mugun bokancin sa, haka ya dawo tsirara ya ruga da gudu se waje, haka mutanenngarim suka d'auka cewan boka ya haukace gidansa ya qone k'urmus ana haka k'uru yazo ana rirrik'e da Bokan, ya shiga tashin hankali shi kanshi sabida jin me ya faru, acewar en garin duk sanda wani abu ya samu boka toko tabbas masiface zata afka musu dukkansu, haka suna kallo jikin bokan ya soma ci da wuta dole suka sakeshi ya dinga gudu yana ci da wuta har inda ya dena motasi ya mutu a sandare!! K'uru se kuka yake ga 'yan gari hankalin su duka a tashe yake.

*************
*Bayan sati uku*

Yanzunkam alhamdulillah dukkansu sun samu waraka daga ayayoyin Alk'urani me girma da kyawawan adu'o'in da ake musu dukkansu, da wannan suka bar gidan malam zuwa kowa gidan sa se dawood daya koma gidansu inda mahaifiyarsa, Dad kanshi yayi mugun d'aurewa da wannan abun, gashi Lawuri ma tayi bayanin haka boka keyi idan akawa K'uru babban laifi har amutu tsafi ne, ita kanta ta k'arayin imani da Allah da manzan Rahma (S.A.W).....ganin a garin su sedai ka shek'a lahira amma anan dazaran aka soma ambaton Allah se waraka ta samu lallai tayi imani da Allah kuma ta yarda annabi muhammadu bawan sand kuma manzan sane.....

Nisawa yae bayan dogon tunani kafin, kafin ya tattare nutsuwar sa sosai zuwaga Oga shamsu ya soma magana

"Shamsudden kasani koba maganar aiki na d'aukeka ne matsayin d'a wanda na haifa da cikina, nakuma yaba sosai da yanda kake girmamani bako kad'an ba, kaima ka d'aukeni matsayin uba bawai wani bare ba, to anan wata alfarma nake nema a gunka har qwaya biyu, wanda babu takura ciki alfarma nake nema idan kuma kaga akwai takura aciki don Allah ka gayamun gaskia, ayau ina magana dakaine ba a matsayin Babba dake sama dakai agun aiki ba ina magana dakaine a matsayin mahaifi"

D'agowa Oga shamsu yae ya kalli General kafin ya mayar da kanshi k'asa, yana matuk'ar so da k'aunar general be tab'a ganin babba me karamci kamar oga shamsu ba, yana matuka'r tallafawa maraicin sa shi kuwa menene a duniya oga shamsu ze nema

Please Login or Register in order to submit comment