gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading DOGUWAR HANYA Dajin Tsafi by Billy Galadanchi Chapter 8 | ArewaNovels google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kife littafin tae ta mik'e zuwa cikin gidan sabida tanaso tasha ruwa, zuwa yanzu tasoma sabawa da d'and'anon ruwansu me sanyaya zuciya, kai tsaye ciki tashiga bayan tayi sallama ba kowa a parlor d'in, kitchen ta wuce ta bud'a fridge ta d'akko robar ruwa d'aya ta shiga dudduba kofi, sedaga cen ta samu tana fitowa sukai karo da Hanifer cup d'in ya sub'uce mata dama na glass ne lokaci d'aya ya tarwatse, cikin tsoro taja da baya bata tab'a tsammanin abun yana tarwatsewa har haka ba

"Hanty Anny hakuri kinji?" Ta furta muryanta yana rawa, tsaki hanifer tae

"Dama mana Arniyar jeji, yaya zaki yi abu cikin nutsuwa wama ya baki damar d'akko cup na daddy kizo harki fasa? Wlhy yau keda mommy ne, zuwa zan na fad'a mata abinda kikayi idan akwai wanda kika tab'a ganin ya d'akko cup d'in daddy yana amfani dashi" ta gano masifar takeyi dukda bajin me takecewa duka take ba,jin ta ambaci momy ma ya k'ara firgitar da ita tasani kashinta ya bushe, kuka ta hauyi tana rok'onta amma da gudu ta juya saman, segata sun dawo tare da mom har lokacin kuwa Lawuri tana nan tsaye tana sharar k'walla, salati mom ta hauyi tana tafa hannu

"Hanifer d'akkomun dorinan danake zane su Nu'aiym shida Khabbab kizo ki sameni a garden tare da ita zakizo" haka Ta wuce garden Hanifer kuwa ta wuce saman ta d'akko dorina ta kuma zo taja hannun Lawuri garin tsallakawa qatoton glass ya cake ta, k'ara ta kwalla yayinda hanifer ta tizgeta zuwa garden d'in cikeda fushi, d'ingishi ta somayi tana kuka amma ko kallonta hanifer batayi ba taci gaba da janta har garden, mom zama tae akan kujera hanifer ma haka

"Hanifer tashi ki nuna mata yanda zatayi kneeldown" mik'ewa tae tayi kneel down agabanta tana nuna mata da hannu akan itama tayi, ba musu tayi harda d'age hannayenta sama yanda hanny tae, tana ganin tayi ta mike itama ta mik'e wanka mata mari hanny tae

"Danla ki koma wayace ki mik'e?" Bata gane abinda take nufi ba ga glass a qafanta se kuka take tana ambatar kalmar ki Akuri da k'yar, duka sosai mom ta mata da dorina ta kira Dawood a waya

"Ga wannan mejin yarbancin Arniyar yarinyar dakuka kawomun agida na, ka sanar mata glass cup data d'auka tasha ruwa harta fasa na daddy ne nxt time idan taga abu ta rink'a bincikawa danni ba lamuni zan mata ba" tana kaiwa nan ta kara wayar a kunnen Lawuri daga cen yayi Lawurin bayani akan shine ga abinda akace tayi ta rik'a kiyaye, tana kuka ta ansashi da ta dena zata nasu hak'uri amma a mayar da ita garin su

"Zamuyi magana idan nazo Lawuri kinji, yanzu kiyi hak'uri" godiya ta masa sannan suka karb'i wayar dukai hanyar ciki ita duka barta nan

"Allah Hanifer banajin dad'in yanda nakewa yarinyar nan, kurun dai na tsane ta ne so nake wuya tasa tabar gidan ba komai ba" jinjina kai hanifer tae

"To mom harga Allah aibaki da laifi, tunda laifi tae kika hukuntata" Jinjina kai mom tae alamar gamsu kafin tace

"Amma naga kaman Glass yashiga k'afanta kidubata da kanki" Jinjina kai Hanifer tae

"To mom zan duba ta inshaa Allah" Barbo ce ta tattare kwalban ita kuwa hanifer tunda ta shiga hidimar girkin daza'aci na dare bata k'ara tunawa da wata Lawuri ba...

**************
     Tunda ta sanya kiran wayansa agaba be d'aga ba take cikin yamutsi, ta cab'a ado iya ado sedai babu walwalar zuci, mesa ne ita Pure heart yake mata haka? Meta masa ina laifin masoyinka? Shirin zuwa gun k'awarta tafito da amma se kurun ta karkata akalar motarta zuwa Tile making company nasu ta tabbatar yana cen yanzu.

Kai tsaye office nashi ta nufa, akai mata iso ta shiga, fuskar nan babu walwala ya tarbeta

"Me kika zo kimun anan?" Kallon sa tae har idanta sun sauya sunyi ja

"Meye laifi na sufyan? Mena maka hakane wai? Na dinga kiranka kenan a waya baka d'agawa? Sannan kuma baka kirana, baka zuwa inda nake ni idan nazo seya zama laifi? Yaya kakeso nayi da rayuwata ne wai?" Hannunshi ya ssanya ya shafi sumar kansa

"Na sanar dake ai banaso kike yawaita kirana a waya ko? Nakuma sanar dake ba girmanki bane ba ace kina kawomun ziyara da kanki" cikin damuwa ta furta

"Amma idan nakira baka d'auka bafa? Kokuma idan na kira baka kirani back ba fa? Idan inaso na ganka amma bakazo bafa ya zanyi ehm Abu sufyan?" Ta k'arashe maganar cikin tausayawa kanta har tana zubar da hawaye, tausayi sosai ta bashi ya tashi daga kan kujerar da take yazo ya zauna kujerar dake fuskantar nata, cikin sanyin murya yace

"Kiyi hakuri my Ayusher kinji? Ni abunda banaso missd col ya wuce 1, idan da kin kira so d'aya ban d'aukaba idan kika jirani zan kiraki back ne, zancen ziyara kuma naji, yanzu so nawa kikeso ki ganni a sati?" Share hawayen ta tae

"Nagode sosai pure heart ni idan da wannan kalaman masu dad'i kurin ka barni zan gode maka" Murmushi yae

"Gayamun mana so nawa kikeso ki ganni a sati?"

"Niko sa d'aya ne ma kaji" murmushi yae

"Nacire kwana uku kacal a sati, zaki ganni so 4, inshaa Allah muddin ina garin nan, kira waya kuma zanna riqa kiranki kullum safe da dare wannan fa ta miki?" Ya k'arashe maganar cikin sakin fuska sosai

"Nagode pure heart" murmushi yae

"Da driver kikazo?"

"Da kaina nazo" mik'ewa yae

"Muje gidan mom nayi wanka semuje yawon yamma" murmushi tae itama ta mik'e

"Zaka sanya mom tace bana zuwar mata se idan kai ka kawoni ko" mirmushi yae

"Idan bazakiba sena tafi abuna" Rike baki tai tana murmushi

"Nina isa nace bazani ba? Aiban isaba ko pure heart?" Murmushi yae suka fita.

   Aqilu ya wurgawa key na motar Ayusher ya cafe yace

"Ka kai motar gidan Su Ayusher ka baiwa gate man na gidan kace injita ya ajiye agunsa harta dawo" cikin girmamawa yace

"To yallab'ai" Takardar dubu d'aya ya zaro ya mik'a masa

"Kayi tranport zuwa gida daga nan" nanma godiya yae ya juya.

**********
   A b'angaren Lawuri kuwa yau duk kuka ta wuni yi, ta samu Barbo ta cire mata glass d'in amma sun duba a garden d'in babu wani ganye daze iya tsayar da jinin da k'afar keyi,wajen gidan Barbo taje ta duba ko akwai ganyaye irin na garinsu....... Zaman dirshan tae a bakin gate d'in tana jiran isowar Barbo sabida yanda jinin ke zuba, ga yau banda masu gadin gidan duka sojojin sun kama gabansu,Shigowar barbo yayi daidai da dosowar motar Abu sufyan gidan, parking yae ya fito daga motar ya bita da kallon mamaki kafin ya k'ara wurinta cikin azama, durqusawa yae ya tallafi k'afar ba laifi tasha faso da kirci na rayuwar jeji

"Meya samu k'afar haka ne?" Amaimakon ta bashi ansa se kurun ta shiga rera masa kuka wiwi..... Nuni ya mata da hannu alamun ta mik'e a hankali ta tashi ta doma d'ingisawa tabi bayanshi zuwa ciki, Hanifer ya soma k'wallawa kira yama manta da wata Ayusher dasuka zo tare, da sauri ta sakko daga saman

"Zoki treating wound na yarinyar nan, bansan meya same taba" tab'e baki tae

"Yaa sufyan kofin dad ta d'akko na shan ruwa, shine kuma ta fasa shi garin gidadanci ta taka glass nisam nama manta mom tace na duba mata gun" Haukace mata yae da masifa, ita kuwa Ayusher tayi sororo tana jiyo su, haka ya dinga masifa har sanda ta shiga taitayinta, ya haura saman mom itama

"Mom yanzu daidai ne dan Allah, yarin yarnan fa mom mutum ce fa? Amma ace kun barta da miki haka tun safe kuma akan glass cup ace hadda duka, Hanny ta gayamun kin dake ta kuma nima na gani duk jikinta ya fashe" Mik'e wa tae daga zaman datake

"To ubana seka daken ai, nace seka daken, ni yanzu Sufyan ni kakewa magana irin haka acen wancen banzar, yaushe ta juyar mun da kanka har haka? Yaushe ma kai ka isa ka gayamun abinda ya dace ya wanda be dace ba?" Saukar da kanshi yae k'asa

"Mom kiyi hakuri kurun naga an qyale tane acikin jini tun safe shiyasa" tsaki taja tafice daga d'akin gaba daya.

Seda aka bata anti tetanus sannan akae dressing na gun se kuka take, lokacin ne barbo ta tallafeta zuwa d'akin su.

Sun baiwa Ayusher tausayi sosai bako na wasa ba, bataso taga ana cutar da mutane ita kam,amma haka ta gaisa da mutane gidan ta zauna a darare har ya kimtsa suka fita, fitar ba dadi sabida fuskar babu wata walwala haka suka yishi.

*********
   Ana sallan isha Lawuri da Barbo suka sakko daga saman, sa'an dasukaci ba kowa ya basu daman zarcewa har gate,  me gadin sun sansu dan haka babu wanda ya hanasu fita haka suka fice da zummar suda gidan har abada, Lawuri gida takeso taje dan haka ta nemi hanyar datafi mata sauk'i kawai, ta kula wannan mutanen kasheta zasuyi idan tayi wasa.....

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

*Littafina na siyarwane, idan kinaso ki siya, karki karanta idan baki biyaba 07084161619*

   16

Tunda suka fito duk titin dazasu tsallaka sesunji jiki, sunsha bak'ar wahala kafin subar unguwar ma, tafiya dukayi ta kusan sa'o'i uku, sun jigata sosai, ga ciwon dake k'afar Lawuri, yanxu kam so suke su tsallaka babban titi sui ta kansu amma sunfi 30mns agun suna k'ok'arin tsallakar titin sedai kuma basu iyaba, sesunkai tsakiyar titin se kuma su dawo da gudun fanfalak'i, a garin hakan ne mota ta musu d'ebar karan mahaukaciya taje ta watsar gefen titi, matashiyar budurwa ma mallakiyar motar tayi azamab fitowa da saurinta bayan tayi parking inda ya dace tayi, Takalminta me d'an uban tudu tana tafiya cikeda yanga, bazaka ita cewa ga kalar taba ka kad'e mutane har biyu kuma kana tafiyar son rai? Sedai kumafa kallo d'aya zaka mata ka tabbatar tashiga tashin hankali, a rud'e take sosai, ga alama iyakar saurin ta kenan a yanayin tafiyar ta, mutamen dabasu suka kad'e sunba har sun rigata isa gunsu, itama cikin azama ta k'arasa yanxu kam, abinda ta gani ya matuk'ar rikitar da ita sabida d'ayar gabaki d'aya fuskarta jinine ga k'afa ma haka she's unconscious ma, d'ayar ce ke ihu tana magana cikin yaren daba kowa ke ganewa ba, dafe goshi tae lokaci d'aya wani ya taimaka mata aka sanya daya a motarsa daya a motar ta duka lula asibiti mafi kusa dasu.

Lawuri tafi Barbo shan azaban dan ita batako san wake kanta ba, Barbo kuwa ta k'arye a k'afa, ita Lawuri ba'a san iyakan ciwukan datajiba har yanzu, matashiyar budurwar data kad'esu se kuka take tana mamakin sanda sukazo gabanta batai auneba, kamar aljanu? Gidansu ta kira waya lokaci d'aya asibitin ta cika fam da mutanen gidansu.

***********
   Hanifer ta kula yaran basa d'akin su da dare amma tana mamakin ina sukaje? Taso ta ankarar da mutan gidan amma setayi tunanin suna garden, tunda k'auyawane ko tsakiyar dare saje garden ai, wannan ya sanya tana kammala ayyukanta tae shirin kwanciya, tana sakaran ta koma gidansu ma nanda 2days.......Cyama ma tayi mamakin rashin ganinsu amma hakan be sanya ta wani damuba dan itama tunani d'aya tae suna garden suna hira cox haka sukeyi dukda basu saba kai dare ba, da wannan ta watsar da tunaninsu tae shirin kwanciya abunta kamar yadda Hanny tae.

***********
   Duk mutan gidan sun hallara dining kasancewar General ya dawo, k'a'idane idan yana gari ko bakaso se dole ka fito cin abincin safe a dining dake babban parlor na gidan, sun shirya sosai abinci kala kala, ita kamma mom bata ko damu da rashin suba tama manta dasu, seda aka nutsu ana cin abincin kowa yayi tsit sannan General ya kalli Adama

"Ina bak'in gidan ne ko kunya suke?" D'ago idanta tae ta kalleshi had'e da tab'e baki

"Oho, ni yau duk ban gansu ba" Cyama ce tace

"Dad jiya da dare ma basu zo d'aki da wuri ba, nazata ko suna garden sabida cenne gun zamansu shisa banyi magana ba har bacci ya kwasheni, yanzu mun wayi gari basa d'akin na tambayi hanifer ma tace bata gansu ba" Duka ya kaiwa table d'in da k'arfi

"What?!!!! Kuna haukane shine bazaku sanar da wuri ba? Bama wannan ba da ban tambaya da bazaku sanar ba kenan" tsoro ya kama su Hanny tace

"Dad na gayawa mom tinda na idar da sallan asuba, setace badai inda zasu waiko a garden suka kwana tunda sun saba kwanan jeji" Wani kallo ya wurgawa adama daya sanya ta sadda kanta k'asa ba shiri sannan ya kalli twins

"Kai Huraira jeka ka duba mun lungu da sak'o na gidan ina yaran mutane suka shiga" A tare suka mik'e da sufyan dukkaninsu cikin tashin hankali mara misaltuwa, neman duniya sunyi agidan basu gansu ba, sedaga baya suka tambayi securities na gidan anan sukejin wai tun jiya da kusan isha suka fita babu kuma wanda yaga dawowar su gidan, hankalinsu ya tashi suka koma ciki suka sanar, mom dai ko gezau su hanny ma ganin dad a wani yanayin duk se ya rikitar dasu suka shiga taitayin su

"Mesa nida gidana bazan kawo ajiyar abinda nake so a kular dashi ba? Shisa Captain yace zeje dasu gun matarsa bayarbiya na hana, yanzu a matsayin ki na uwa me kenan kikai? Kin burge kenan? Kin cinye kike gani? Yaran mutane dasuka fice dalilin masifar wlhy tlahi na baki awa ashirin da hud'u duk inda sukaje ki nemosu inba hakaba kinsan sauran" Mik'ewa tae cikin b'acin rai

"Haba Muhammad, se yaushe zan girma ne a wurinka wai? Nina koresu? Koni nace su bar gidan? Banko san sun tafi tayaya zan nemosu? Idan har kace akan yaran nan zaka mun haka wlhy sena bar maka gidan, kaida ka kawosu sekaje cen ka nemesu danni babu ruwana" Kallonta yae cikin b'acin rai

"Yanzu dama kafin na fita nakeso na duba CCTV nawa, an sanar mun har dukanta kikae a dining, suma securities sesunsha wuya a hannuna, yanda zasu bari su fita ba tare da sanin kowa ba, dan sunga shamsu baya nan" Juyawa tae rai a b'ace ta haura sama tana mejin zafin abinda ya mata agaban yara.

***********
   Lawuri unconcious take har washe garin, anma rasa gane meke damunta, dole yanzu ct scan za'a mata tunda yake ta samu rauni aka.... Yarinyar data kad'esu duk a rikice take tarasa nutsuwarta dukda kasancewar ta likita hakan be hanata shiga tsananin rud'u ba, musamman ganin wannan kamar zata mutu ma.

    Neman duniya anyiwa su Lawuri ba labarin su, Abu sufyan daren ranar bekoyi baccin kirki ba, yayinda Abu Huraira ya gagarayin baccin ma kwata kwata, hankalinsa ya tashi sabida yasani tabbas hanyar gidansu zata nema kuma bawai tasan hanyar bane ba, sedai ya kula tanada basira tabbas inda suka biyo tanan zata nemi komawa, sedai ta yaya? Tunda yake jirgi suka hau daga babban garin dasuka sauka zuwa nan garin Abuja, yashiga rud'ani sosai ya rasa tudun dafawa hankalinsa in yayi dubu to tabbas a tashe yake kuwa.

************
   
Banida zab'in daya fi in koma garin su Lawuri, banida zab'in dayafi inje garin nasu in binciketa inji kota gane hanya tazo, ai taji ana anbatar sunan garin dasuka hau jirgi sukazo wato OGUN state in hakane mota zata hau, taje cen sekuma ta nemi hawa wannan motar dasuka hau suka tafi wannan k'auyen na fulani, duk yanda akayi gida zataje amma bari ya bada sati d'aya idan ba'a samu labarin suba dole yaje garin koyaya ne kuwa!!!.


*****Bayan sati d'aya*

Har akayi sati d'aya babu neman dabasu musuba amma shiru kakeji, bame hotonsu bare su saka a media, general yayi bk'in cikin wannan abun, yanaso yarinyar ta karb'i musulunci yana so ya nuna mata cikar musulunci abun arziqi amma anzo an tilastata guduwa tabar gida sabida wani ra'ayin banza, damuwar sa d'aya ma besan hannun dazasu fad'a ba, nagari ko mugu?, yama rasa tudun dafawa!

*********
Hankalin Twins baya jikinsu, Abu Hurairah be fahimci tsananin so da illar dason ya masa ba se yanzu, hankalinsa ya matuk'ar tashi ainun, har 'yar rama, wannan wace irin masifa ce wai? Yana cikin dubun tashin hankali akan wannan abun, sabida ya shirya sosai akan yanda ze shawo kan iyayensa ya musuluntar da ita ya aureta, amma shine za'a wani ce ta gudu? Lallai wajibine ya koma wannan *Doguwar hanyar* yasan abunyi akan Lawuri idan ma batacen duk inda tashiga aduniya seya nemota yaga cewar sun sake had'uwa itace farin cikin sa, itace komai na rayuwar sa yakeji dai........

A b'angaren Abu sufyan kuwa shisam bama shida lafiya, wani ciwo ne ya sameshi me wuyar magani, ya tabbatar rashin ganin Lawuri a rayuwarsa abu ne me shirin kasheshi har abada ba shiri, mesa yarinyar nan ta masa katutu a zuci ne wai? Meke damunsa game da ita? Ne kodai haukacewa yake shirin yine be shirya hakan ba? Duk iyakar tunaninsa ya rasa abinyi.

Dawood yaji zafin wannan abin sosai
Sedai shi bekaisu damuwa ba kasancewar ba wani d'ad'ashi da k'asa tayi ba, shidai kawai yana mata kwad'ayin musulunci ne, bayaga haka kuma yaso ya aureta ya sanyata a rigar musuluncin gaba daya, abu mafi damunsa shine besan hannun dazasu fad'a ba, sun shigo garine kurin batare dasun san waye mutanen birnin ba? Yana musu fatan alheri.

*********
Duk wani shiri daya kamata huraira yae yayi abunshi na zuwa garin su Lawuri, babu wanda ya gayawa, se Sufyan daya kula tamkar da abinda yake b'oye masa yamasa shiru ne kurin yaga iya gudun ruwan sa.

Ranar da ya fita aiki kuwa bekoma waiwayen gida ba ya Lula *Doguwar Hanya* wacce besan wane tanadi tae masa ba yanzu..........

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

*Assalamu Alaikum masoya, litattafai namu masu suna kamar haka na kud'ine.*
*Sultan merah*
*Kamar da wasa*
*Doguwar Hanya*
*Zafin rana*
*Sanadiyya*
*muna roqon duk wani me tsoron Allah da idan be biyaba karya karanta mana book koda marasa tsoron Allah sun fitar kuwa, yin hakan ganganci dan gashi munyi bayanin kanmu, idan kayi hakan kaida Allah mahalicci, munyi garab'asa gaduk meson duka biyar ya biya N500 kacal,meson 1 N200 kacal, me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


******** 17

Abu Hurairah bebi ta k'auyen su Baba ladi ba, ya kula hanyace me rikitar wa mara b'ullewa, jejin tamkar aljanaine aciki, da wannan ya samu isa OGUN STATE da yamma sakaliya, yayiwa wayoyinsa kisan gilla dan karma wani ya sameshi, shidai burinsa d'ayane shine ya samu Lawuri, rashin ganin babban tashin hankali ne agaresa, koda yake b'angarora da dama na zuciyar sa suna sanar masa tsabagen wowtar da yae na tunanin komawa wannan masifar, har wata zuciyar sa tana sanar masa tunda harshi ya kawo kansa tokuwa tabbas babu abinda ze sanya idan yae adu'a Allah ya amsa masa, sedai kuma a wani b'angarn yanaji ajikinsa cewar tabbas Allah ze nuna masa hanyar b'ullewa, dan kuwa bayaga soyayyar data janyoshi akwai kwad'ayin ya janyo musulunci a garin, abu d'ayane yamai tsaye arayuwar shi shine yarensu da bayaji? Yaya zeyi huld'a dasu, yaya zeyi communicating dasu? Ta ina ma ze fara? Daga wane b'angaren ze soma ? .......

**********
Ayusher yarinyace me matuk'ar tausayi tunda abin nan ya faru da yarinyar nan kullum setayi kuka ga yarinya a ICU dukta fita hayyacinta gashi batasan ina zataga iyayenta ba batasan inda ya dace ta dosa ba gun nemansu, kodai zasu d'auki hoton tane sukai sanarwa gidan tv da kuma sauran media flatform taga ko za'a dace? Da wannan shawarar yau ta kira Sufyan, yana d'agawa suka gaisa yace

"Ayusher tunda kikai accident d'in nan ko nemana bakyayi duk kin nemi d'aga hankalinki a banza" murmushi tayi sannan tace

"Kayi bak'uri nutsuwarce tamun k'aranci wlhy ina cikin tsananin damuwar rashin sanin iyayen wanda na kad'e" Nisawa yae

"Haba Ayusher kema dai kunyi sakaci mezai hana kanki tsaye mana ki kai agidan tv na dad d'inku, a duk fad'in abuja wane gidan TV ne yafishi suna? Zakiga an dace ai" Nisawa tae

"Shawara dana yanke kenan amma nace sena kira pure heart, barin gayawa mom kawai, yanxu kana ina" Nisawa yae

"Ina OGUN STATE fa" wara ido tayi

"Yinme pure heart?" Murmushi yae

"Zan gaya miki daga baya kinji yanzu dai kiyi yanda nace d'in" sallama sukai sannan yaci gaba da tuk'insa.

**********
Tsoro ya baiwa Abu hurairah sanda ya ganshi akan kwanar da ake d'aukewa aje wannan k'auyen na fulani, bashida dabarar dayafi ya gangara ya tsaya danya tabbatar yanda ya ganshi shima ya ganshi ido cikin ido, fitowa yae dama shi a tsaye suka kalli juna ido cikin ido, a hankali ya tako yazo ha rik'e hannun d'an uwansa cikin sanyin jiki yace

"Al-hussain" amma seya gagara furta komai bayaga wannan kalmar, har wannan lokacin idonsu yana cikin na juna, Abu Hurairah yau duk dauriyarsa seda yae kuka besan sanda ya rungume d'an uwan saba yace cikin muryan kuka

"Wlhy ina santa Al-hussain, rashin ta baze barni acikin sukuni ba, soyayyar ta tagama zagaye ilahirin jikina, dan Allah karkace zaka hanani zuwa nemanta kaji" murmushin takaici yae ya kula da wannan tunba yanzu ba shisa ya k'udirta a ransa koda soyayyar yarinyar zata hallakar dashi toze sadaukar da rayuwarshi akan d'an uwansa yaji dad'i, dukda shima yana shan wahala amma yasani beyi sabo da ita yansa za'ace baze iya barwa d'an uwansa ita ba

"Nasani Al-hassan amma wannan baze barni in barka kabar wannan duniyar tamu zuwa wata duniyar ba me cikeda abun tsoro kala kala gakuma doguwar hanya me rikitarwa, iya kar wacce mukasha ta wadatar Al-hassan, sabida haka zuwa zakayi mu koma Abuja, idan nemanta kakeso aje semuje da soja yanda Dad amma kafito bakako nemi adu'ar iyaye ba ka ganta yaya? Ka gane ta aya? Shin kanada tabbacin taje garin nasu ne, karka manta Lawuri fa ko nan garin bata san sunan saba, kai koda ta sani ma tayaya zata zo nan? Ya zata iso har nan garin? Kay8 tunani mana, kokai aka bari kazonan da k'afa ta ina zaka fara? Karfa ka bari soyayya ta rufe maka ido, tasha makance ka daga ganin gaskia me amfaninka, ka nutsu kayi adu'a ka kuma nemeta a garin abuja da kewaye amma sam bata wannan Doguwar hanyar ba, nasan kalar tunaninka wannan ne ya sanya na biyoka tanan hanyar, agarin na kwana senawa nan hanyar sakkon asubahi, ina me fatar ganin ka dikda na kula sam ka manta da tracker dake jikin motarka dakuma agogon hannunka daka iya sanya nasan location naka aduk inda kake, hotel d'inma ban nem bane dana iso sabida gajiya" Nisawa Abu huraira yae

"To yanzu Al-Hussain kana ganin zamu sameta a gari?" Murmushi yae

"Nama alk'arin zanyi amfani da ilimina da basirata dakuma k'arfin ikon danake dashi wurin ganin na nemota, idan har kaga ban nemotaba Allah ya yanke had'uwa tsakaninmu da ita ne na har abada" Sauke nannauyan ajiyan zuciya yae

"Yanzu gida zamu koma?" Murmushi Sufyan yae

"Da jirgi ba,dama na mana booking akwai wani inyamuri abokina ne, ana garin yake zamu bar masa motocin nan, zanje inji nawa zamu bashi ya kawo mana su abuja"

"Baka gudun ya gudu dasu?" Murmushi yae

"Daze gudu dasu da bazan bashiba ai, yanada motocin jigila ne yana jarkar mota kuma ya siya ya aikama duk garin da kake, yanada qwararrun direbobi zasu kai mana ne mu biyasu" murmushi shima yae

"Kasanni da mota subi a hankali ko gogewa tae bazan k'ara hawanta ba ka sani" Girgiza kai Abu sufyan yae

Zaka rantse da Allah huraira me sauk'in kai ne amma komai nashi na gayu ne se high taste yafi kula da mota akan jikin sama, Abu huraira ze iya maka komai amma banda aron mota sam shi ko wankin mota yakai seya kasa ya tsare, tsaftar sa kuwa har takaici take baiwa sufyan wani zubin dukda shima ba baya bane gun tsaftar.

*********
Abun sam bewa mahaifiyar su dad'i ba tun faruwar abun take cikin fushi da general, shikuwa yayi biris da ita har gashi yau kwana 8,abin mamaki Kyautar Allah duk basu kwana a gidaba, to ina sukaje? Hakan ba sabon su bane ba, me sukayi hakan kenan? Ina sukaje? Yanzu k'arfe d'aya na rana? .....sallamar sune ya katse mata tunaninta gaba d'aya ta d'ago a hargitse tana kallonsu, dukkaninsu tashin hankali suka shiga sunsan halin mom, zuwa sukai kusa da ita suka gayar da ita ta ansa cikin

Please Login or Register in order to submit comment