gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading DOGUWAR HANYA Dajin Tsafi by Billy Galadanchi Chapter 2 | ArewaNovels google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zwaga wannan b'angaren Abu huraira ya juye baki da harshen turanci yace da Abu sufyan

"Abu Takobi kaga wannan jejin kuwa, kasan wai jikina ya soma mutuwa, a gaskiya dazaran mun ajiyeta mu juyo sabida ina jiye mana yin dare a wannan muguwar hanyar" Kawar da kanshi yae gefe d'aya ya kaiwa agogon hannunshi kallo

"Dama munsan hakane aida yaseen a motan haya zamu d'urota, yanzu fa uku saura mintuna biyar kacal, dama mun juyo ne mu soma timing amma wannan masifar har ina?" Dawud ne ya karb'e zancen da cewa

"Ba masifa bane ba kadena kira mana ita, idn dai kan wannan hanyar ne ai inaga zamu juyo dare be mana ba" shiru dukkansu sukai, zuwa hud'u saura kwata sun k'arisa garin, mafiya yawancin mazauna garin fulani ne kamar Baba ladi, harkokin su suke gudanarwa cikeda aminci, sun gaggaisa da mutane kansu tsaye suka nemi yin salla azahar da la'asar kansu ce zasu koma, duk yanda akaso suci abinci sun gagara tsayawa se wuraren biyar da rabi ma sukai shirun tahowa duk saurin dasukayi...wani mutum ne me tsananin kamanni da Baba ladi yazo ya kalli Abu sufyan daya karb'i tuk'in motar ganin kamar Abu mage ya gaji yace dashi

"Yaro dazaku bi shawarata dakun hak'ura da tafiyar nan zuwa asubahi, komu damuke da garin nan bama yi masa fitar yamma, koba komai kuna baqi seku saki hanya ai" kallon Abu Sufyan yae cikeda takaici yace

"Kamana adu'a lafiya lau zamu fita mun gama haddace hanyar inshaa Allah" jinjina kanshi yae alamun gamsuwa yace

"Idan kuka miqi hanya zuwa gabashin nan, karku neki ko washe hanya sheta kudu, kunayin kudu kuka raba jejin masarau biyu seku yamma kuyi arewa se titi kuma, kushkure d'aya jal je sanya ku shaki hanya, kuma shakin hanya a wannan daren baze muku da kyau ba, ina muku fatan alheri kaji ko" jinjina kanshi yae yana sakaya murmushin yak'e kansu d'aga musu hannu subi hanyar daya dace...

**************
Shiru dukkansu sukayi kowa da abinda yake sak'awa aranshi, jin kafewar tayar motarsu ne ya sanya suka kalli juna shida Dawud dake gaba yayinda Abu Huraira ke kwance abaya yayi matashin kai da wani trow pillow daya zame masa abun yawo duk inda zashi, shi d'inma d'gowabyae yace yadai?" Cikin sanyin jiki yace

"Ga duhu ya soma sauka, ji nake fa kaman laka ne muka mak'ale aciki, amma ai d'axu bamu bi wata hanya me laka haka ba ko?" Wasu yawu Masu d'acin gaske ya had'iya kanyace

"Ko kusa bamu wani shiga laka ba gaskia, amma kaja da kyau mana" Iyakar dagewar shi yaja ya taka totor amma sam motar taqi ta motsa, kashewa yae suka fito dukkansu, babu wanda jikinshi be b'aci ba, lakar ce kuwa tsaki Abu Sufyan yaja ya koma cikin mota sukuwa suka ja baya suna me karkad'e k'afansu daya lalace da tab'o, giya ya sauya zuwa me iya fitar da motar daga wurin, dama Allah ya imakesu Hilux ce seta fito daga cikin Lakar lafiya, duhu ya soma sauka wannan ya sanya dawud ya ciro wata k'atuwar waya a aljihunsa ya kunna torchlight dake jikinta me hasken gaske, kai tsaye ta mamaye lakar da haske arziqi ma sukayi irin me zurfin gasken nan ce, cikin damuwa Abu Sufyan yace

"Dawud anya bamu sake hanya ba kuwa? Nifa sam babu wannan lakar a inda muka biyo ni gaskia na tsorata" Dafe kai sukayi dukkansu kansu d'akko ruwan faro dasukai guzurinshi su wanka k'afansu dashi sannan su koma kotar, sunyi adu'a kafin su d'auki hanyar dasuke tsammanin ita zata fitar dasu kan titin dabeda maraba da babu....

K'arfe takwas ta gota sanda Dawud cikin damuwa yace

"Abu sufyan ka kwatanta ka gani, uku saura mintuna biyar muka yanki jejin nan d'azu, kuma koda hud'u saura kwata tayi fa mun isa qauyen kaga tafiyar 45 mns ta kaimu, yanzu kuwa tun biyar da rabi muke zagayar jejin nan, ko shakka banayi wlhy b'atan hanya mukayi" wani dogon burki yaja ganin k'aton maciji agabansa gudun karya taka shi, bakinsa har rawa yake ganin macijin ma yaja burki ya d'ago kai yana kallon haske fitilar motar sekace yana ganinsu

"Abu Huraira maciji" Lek'owa shima yae shida Dawud, lokaci d'aya suka shiga ambaton mahalicci, basuko matsaba kuwa kaman yanda basu d'aga da motar ba konan dacen ganin yanda macijin kr kallon su kaman wani mutum.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: 🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

*Littafina na kud'ine dan Allah idan baki biyaba karki karanta, idan kinaso ki biya kudi ki riqa samu a kud'inki*


02

Adu'ar tsari dukkansu ke karantawa har suka ga macijin ya wuce abunshi batare dayayi ta kansu ba, dukda Ac dake kunne a motan hakan be hanawa dukkansu tsiyayar da zufaba

"Abu sufyan ina wannan kalan macijinne ke had'iye mutum?" Wasu yawun wahala ya had'iya kafin yace

"Ni gaba d'aya na rikice ma, jikina yae sanyi sosai da tafiyar nan, ina roqon Allah ya mana shamaki daduk wani abun k'i" cikin damuwa Abu huraira yace

"Yanada girma amma da wannan macijinne aida motar gaba d'aya xe had'iya sedai fa aganina mu juya gwara mana kwana a k'auyen nan da mu lula acikin wannan jejin, ko shakka banayi mun sake hanya sosai" Nisawa Abu sufyan yae

"Bazan iya tuk'in nan ba, mu juya kawai kaikaja" cikin damuwa Dawud yace

"Kai yanzu seka sauka ku juya, kana ganin wannan mucijin, idan kuma be tafi bafa, kaidai ka juya kurun" haka ya juya akalar motar sa sukaci gaba da tafiya........

**********
"Bana samun number yaran nan koyaya na gwada, rabon danayi wayama dasu tun da rana dasukaje ajiye Baba ladi, ga garinsu babarma ba Ntwrk inaga dan wayanta itama a rufe" Kallonta General yae cikin takaici

"Ko? Toki musu adu'a inshaa Allah suna nan lafiya lau, maybe basu juya da wuri bayan sun ajiyeta inaga basuda caji, kuma k'aninta ya sanarmun sun ajiyeta harsun juya tun yamma, Glo kurun ke aiki a k'auyen, kinga mtn take using soba lallai ki samu ba" Ajiyan zuciya ta sauke hankalinta sam baya jikinta amma batace dashi komai ba se kwantawan datayi jiki a mace.

*********
Duk yanda taso tayi bacci abun ya gagareta, bazata iya hak'ura da rashin jin yayyun nataba, shak'uwace me tsanani a tsakaninsu, Fuskar wayarta ta kalla da sunayen su a k'alla ko wanne ta kira wayanshi yafi so hamsin amma baya tafiya, duk iyakan k'ok'arinta not reachable ake cewa da ita to ina suka shiga? Wannan itace tambayar da takewa kanta amma bata samu amsaba har wannan lokacin.

***********
Wayanshi ya danna gefen key haske ya bayyana, agogon wayan ya nuna k'arfe goma da rabi hadda mintuna uku na dare gumi ya sharce dan a zahirin gaskia a tsorace sosai yake, yawun bakinsa ma ya k'afe sam bayada wani abu dayae saura daze had'iya a bakin

"Abu Sufyan nashiga dana sani fa, dana sanin hanyar nan damuka d'akko cikin wannan daren damun sani damun kwana a k'auyen, gwara zazzab'in cizon sauro da wannan tashi hankalin damuke ciki, idan dai har daidai muka biyo hanyarnan tokuwa da tuni munzo wurin lakar damuka fad'a ciki d'azu, amma gashi yanzu shiru kusan sa'o'i biyu da matasan mintuna sun shud'e amma shiru kakeji, ina fatan ba wata hanyar muka k'ara cafka ba mara b'ullewa" Cikin damuwa Dawud yace

"Wannan kam tabbas wata *Doguwar hanya* ce muka d'akko me matuk'ar wahalar b'ullewa"

"Tuk'in nan danake tafiya ne kurun nakeyi amma wlhy bana gane kan hanyoyin nan, ban magana bane dankar na tsoratar daku amma hanyar seta rik'amun iri d'aya duk inda zanbi, ya dace musan abinyi gaskia" Yawun wahala Dawud ya had'iya ya tuna maganar mahaifuyarshi sanda ze fito gida

"Yanzu kai me zaka cewa kabeer? Kaine babban abokinsa amma akan ka tsaya hidimarsa kafiso kaje gantale, su sunada hujja dan ubansu ne ya aikesu kai kuma kanada wata hujjar ne, haba Dawud? Ya dace kawa kanka fad'a gaskia" Nisawa yae tunawa da ansan daya bata

"Umma ki gane tafiyan nan tunda Twins zasuyita nima dolene inje, bazan ganewa komai ba idan basa nan bikin ba wani dad'i zemu mn ba, nidai kimun kurun ita nake buk'ata" Adu'ar tamasa ya juya abunsa kuwa yabar gidan.

"Afu sufyan kasan me, Nemi wuri med'an fili kayi parkin motar nan kurun, mu kasheta mu sauke glass ko yayane, ka kunna mana karatun alqurani me girma, idan gari ya soma wayewa semu kama hanya, dan kar mui nisa inda bazamu ganeba koda akwai yalwar haske" Kallon juna sukai shida twin d'inshi ya kad'a masa kanshi akan hakan shawarace me kyau, cikin sanyin jiki yaja gefe yae parking adaidai wata bishiyar tare da janyo wayarshi ya kunna karatun alk'urani me girma a hankaki ya zuge glass na gaba duka biyu na baya d'aya kawai kwanciya yae jikin sit na kujerar ya lumshe idanshi tare da soma rero duk wata adu'ar datazo bakin sa ta tsari, haka suma sukeyi a hankali....

***********

Hasken Rana shine abinda ya farkar da Abu Sufyan dayan daga nannauyan baccin daya d'auke dukansu batare dasun shirya zuwan saba, wayarsa kuwa har cahrge ya d'auke sabida ya da take kunne, karon sa na farko kenan tun bayan daya girma da wani abu me kamada yin salla asuba ba'a cikin lokaci ba ya same shi, kallon Dawud yae dake gefenshi,baccin sa shima yake cikin nutsuwa sedai badan dad'i ba kod'an da yake a zaune yakene oho, ko shakka ba yayi sun kai nisa 5 kafin baccin ya sacesu dabadan hakan ba ba abinda ze hanawa d'ayansu farkawa adaidai lokacin daya saba tashi sallan asuba, hannu yakai yad'an bubbugi kafad'ar Dawud inda a hankali ya bud'e idanshi d'auke da salatin annabi a bakin sa, Abu Huraira ma farkawa yae suka kalli juna cikin mamakin baccin dasukayi, kan su sakko daga motar dukkansu su soma shirin d'aura alwala da d'an ruwan dasuka zo dashi na Faro.... Se bayan da suka sallaci sallolin dabasu samu sunyiba data asuba sannan suka yi addu'ar neman yafiya kan daga bisani su mik'e suna ninke carpet dake hannun su wanda dama anxo dashi, Abu Huraira ne yawa wurin kallon tsafta sosai kan daga bisani ya nisa yace

"Ko kunsan cewan kwata kwata ba alamun sawun mutane nabi nan hanyar ko zancen wata mota kaiko babur da keke banaji suna bi"  Jikin motar Abu Sufyan ya jingine cikeda damuwa yace

"Abinda ya kamacemu shine mu qarawa motar nan mai mu kama gabanmu yanzu Alhamdulillah safiyane inshaa Allah zamu gano hanyar" kallon tausayin kansu Abu huraira ya mai kanyace

"Abu Sufyan kasan Allah, wlhy a madifar tsorace nake, dabadan da Hilux mukazo ba da ba abinda ze hanamu shan bak'ar wahala tun daren jiya, yanzu kuma tsorona Allah banga inda zamu biba, ko ina yakoma mun iri d'aya" Mamaki ne sosainya bayyana a idon Dawud

"Kaima ka kula kenan? Na zata d'emuwane ya kamani ai" Hannunsa ya zura a lajihunsa d'aya jal

"Nikaina ban fahimci komai ba, kasan me dana farka senaga kaman jiya banan na ajiye kan motar ba" shiru ne ya ratsa wurin na wuccin gadi kafin daga bisani Abu sufyan yace

"Allah ya gani iyayen mu mukewa biyayya mukazo wanan jejin, da yardar Allah da qarfin adu'ar su bazamu tab'e ba, kuzo mui lalube inshaa Allah zamu b'ulle" cikin damuwa suka d'akko man fetur suka zube ajikin motar sannan suka koma ciki suna tashe  tax wannan karon Dawud ne ya karb'i Tuk'in, Abu sufyan yana baya ya kwanta yana me lumshe idansa, yunwa yakeji ma sosai dan haka ya janyo musu cake da drinks ya baiwa kowa yanka suna tafi sunaci badan dad'i ba, gabaki d'ayansu hankulansu a tashe suke kasancewar basu tab'a tsintar kansu a jeji ba se wannan karon........

********

  Yajima tsaye a kanta yana nazarin yanayinta, samsamsam ya kasa gane kan Haj Adama,tunda aka gagara samun lambobin wayoyin yaran nan jiya ko abinci tak'i taci, zama yae kusa da ita ya rik'o hannun ta

"Haba hajiyar general mesa kike hakane?  Ai duk yayinda kikaji shiru tokuwa da yardar lillahi lafiya ce take kawo hakan, nifa inaga yarannan dan kurin sunyi tafiyar nan ne basaso suka kama suka rufe wayoyinsu, suna kan fushi har yanzu, amma zasu bud'e ne" d'ago idanta tae dasu kae ja ta kalleshi, cikin takaici tace

"Bana tunanin na d'aura kyautar Allah akan wata turba masiffanciyar wannan, da kansu bazasuyi fushi da iyayen suba akan abinda yafi wanan ma bare wannan abin dabe taka kara ya karya ba, girman nak'uda yawane dashi koda bazaka yarda dani ba kasani koyaya matsala take kad'an tokuwa tabbas itace ta hanasu bud'e wayoyinsu kokuma a samesu" Sauke nannauyar ajiyan zuciya yae

"Bamuda wani zab'i daya wuce mu musu adu'a arayuwa, da damuwar nan tana maganin wani abu data miki Haj, ina baki shawara kurun ki musu adu'a zatafi saurin isa garesu akan wannan damuwar dakika sanyawa kanki, kici abinci ki miqawa Allah lamuranki inshaa Allah zakiga haske" Batace masa komai ba harya mik'e yabar mata d'akin.

*********
Duk yanda sukaso su gano kan hanyar abun yaci tura, sunyi zagaye sunyi kwana har sun gaji amma sam basu gano komai ba, zuwa yanzu man motar tasuma yayi qasa sosai ga yamma tayi cake kurin sukeci se sallah dasuke idan time yayi, alwala ma se sun riqe sabida ruwan su saura roba bakwai kurin, kansu ya kunce ainun.

Tunda magrib tae musu a wannan jejin suka sare da fita aciki a wannan ranar, to save there remaining fuel kurin sukae parking sukai sallah skaci cake se dabino suka sha lemo sa ruwa suka hau karatun alqur'ani me girma, sun jima sunayi har suka kintaci lokacin sallan isha suka tashi sukayi sannan suka shinfid'a qatuwar dadduma ajikin bayan motar su, suka koma suka kwanta acen cikin budadd'en booth d'in dasuka shinfid'a dandumar, sama dukkansu ke kallo bayan sunyi pillow da trow pillows dake cikin motar farin wata ya haske sararin samaniya bakajin sautin komai se bugawar zuciyoyin su dakuma sautin kukan tsuntsayen dake tashi lokaci zuwa lokaci, Abu sufyan ne ya kai hannunshi ya rik'o hannun Abu Huraira cikin muryan damuwa ya furta

"Brother am really scared please pray for us" Matse hannun nashi danashi cikin tausayi yace

"Keep reciting Ayatul kursiy brother, everything will be alright ok?" Yafad'a yana me duban face d'inshi acikin d'an hasken na farin wata, dawud ma a hankali ya soma adu'a ba k'akk'autawa........ Kuka suka soma jiyo tamkar na zaki, a tare suka miqe a zaune dukansu, se zare ido sukeyi yayinda kukan ke qara kusan tar inda suke, da gudu suka sakko suka bud'e motar, amma ina kafin sukai ga shigewa har abun ya qarado inda suke.....

Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: *🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*

       04

Sojojin basu isa garin nasu Baba ladi ba se bayan 2 days,haka suka wuni a garin bayan an tabbatar musu sun juya, amma wannan karon tare da Baba ladi suka juyo, sabida ta kaisu wannan Hotel dasuka sauka aji kosun koma, ga mamakin su basu koma ba tun ranar, ga kayansu ma dasuka bari anan kuma kud'in sati suka biya gashi yanzu kusan 6days babusu babu labarin su sam, sojojin hankalinsu ya tashi, anan sukawa kansu masauki washe gari suka juya k'auyen nasu Baba ladi da guzurin man fetur me yawa kaman yanda sukeyi idan zasuje jeji aiki.

K'anin Baba Ladi yae gyaran murya yace da Oga Shamsu

"Ranka ya dad'e kamar dai yanda ka sani wannan yankin namu muna boader da k'ashashe kusan uku, kuma idan ka lura da kyau zakaga cewar bama kusa da mutane sam, mun yanko jeji sosai munbar gari da nisa, itama sanadi ne ya fitar da ita daga garin nan dabadan haka ba bana tunanin akwai wamda ya taso ba'a nan ba, Hanyoyine muke dasu masu rikitarwa sosai anan jejin, dagazaran ka saki hanya da kuskure d'aya tokuwa tabbas zaka yanki wata uwar *Doguwar Hanya* ne dabakasan sanda zaku rabu da itaba, acewar kakan ninmu, hanyoyin kana isa zasu koma maka iri d'aya kuma da gabas da yamma da kudu da arewa duk zasu zame maka alqibla d'aya ne, sa'n nan kuma bazaka gane inda ka dosa ba, duk inda ka duba zaka ga kamar nan kafito, seka bi seta dulmiyar dakai, acewar su ko namun jeji basa zama a jejin duk wani naman daji daka gani agun tokuwa tabbas aljanine dansu kad'aine ke iyawa da gun" Wani tashin hankaline ya ziyarci Oga shamsu ya kalleshi cikin takaici yace

"Yanzu kenan bamuda ikon shiga jejin neman su?"

"To nidai bazance bakuda ikon shiga ba, ikon shiga kam aikowabyanada shi, ikon fitowa ne babu kaga anan zab'i nakune,tunda mutane suke shiga jejin ana zuwa nemansu, Barde ne ke zuwa kafin a haifeshi kakanshi keyi, yazo Baban shi nayi yanzu shiya gada jikan sarkin malamai ne anan garin, babu wanda aka tab'a samu da ranshi ajejin, kowanne zaka tarar gawa aka tsinta kokuma alamun yaje jejin, baka tab'a samun tarihin wanda yaje ya fito, idan ma ansamo mutum tokuwa zakaga dawani ciwon ze dawo, to idan ma mutum yakai gab'ar kogin ko Barde baya shiga wannan ruwan zaka hau su bakada tabbacin sauka kuma idanma ka saukan baza'a k'ara samun labarin kaba, mahaifin Barde ma daya tsallaka haryau shiru kaga akwai matsala kenan?" Hular kansa ya zare cikin mutuwar jiki yace

"Lallai wannan doguwar hanya ce, to amma shi barden baya zuwa tare da wasu ne? Kaman yanzu yajagoran cemu?"  Murmushi yae

"Yakanje tare da mutane matsalan shine ko kabishi ba amfanin ka bishi dan ba'a kagana a jejin, kana yi kana dulmiyewa, bafa k'aramin mugun abu bane a wannan wurin, koda kuna tare kanshi kurun yake iya baiwa kariya sabida haka gwara karkuje, ku koma ku bashi aiki ya muku acikin kwana uku yake dawowa da bayanin wanda yaje nema, ko rai ko babu idan ma mutum beje ba ze gane, idan yaje kuma ze gane meya sameshi koda ya tsallaka kogi ne kuwa, matsalan d'aya ne baya wa kowa aiki seya bashi damin hatsi 20, na dawa 20 na masara ma haka, sannan ga tsaban kud'i jaka talatin" Kallon shi oga yae

"Nawane jaka talatin?" 

"Dubu shida fa, shiyasa wasu idan d'an uwansu sun tafi basa iya biyan barde wlhy" murmushi yae

"Ba kud'in bane abinji mu zamu ma qara masa ninkin ba ninkin, mu cetosu mukeso yayi, gashi kuma kace baya iya baiwa wani kariya, yazeyi to idan ya gansu?" Murmushi yae

"Yasan yanda zeyi ai, masu rabon fitowar sukan fito tare dashi, wannan aikin sane, ku bari muje gunsa inyaso kunga semui magana dashi idan ze iya jagoran tarku ko?" Hakan kuwa akayi sedai ya sanar dasu shi sam se laraba yake zuwa jejin dan haka tunda yake yau alhamis sedai su jira nanda kwanaki shida, yakuma musu alqawarin inshaa Allah zeje tare dasu indai zasu biyashi kud'in aikin nasu... Ba b'ata lokaci sukai na'am da wannan sabida basuda yanda suka iya haka dole suka juya zuwa gida domin sanarwa da mahaifiyar yaron bisa jagorancin wani d'an k'auyen gudun kar hanya ta k'ara saka subi doguwar hanya mara b'ullewa.

***********
Ruwan yanda ya taso da k'arfi sekace had'iyesu zeyi, idan ana zancen tsorata sam baza'a kawota anan dan abinda sukeji azukatansu a wannan lokacin yafi k'arfin tsoro, dukkaninsu sun sare da rayuwa se Abu sufyan ne kurun ya soma adu'a cikin muryar sa me dad'i, ilahirinsu d'auka sukayi babu wanda abakinshi ba adu'a yake ba, jirgin se tangal tangal yakeyi dasu kaman ze kife, suda sukeda niyyan tsallakawa seya juyar da akalan jirgin zuwa mik'ewa ata tsakiyan ruwan tsaye, duk yanda sukaso su juyo abin ya faskara, da k'arfin adu'a cikin iyawar Allah suka samu suka daidaita kan jirgin zuwa tsallakawa, hakan ce ta basu damar samun yar nutsuwa a hankali suka ci gaba da tuk'a jirgin har zuwa sanda sukazo gab'ar Tekun suka gangara suka ajiye shi suka sakko daga kai suna me zaunawa, ilahirin jikinsu ruwa ta gama jiqashi gashi kala d'aid'aya dama suka zaro daga kayansu gudun kota kwana, wannan najikinsun tun ranar dasuka zo yake, gyara jikinsu sukayi suka shirya dukkansu cikin qananun kayan sannan suka ninke wancen suka mayar a qatuwar jakar bayan dasuke juyawa daga wannan zuwa wancen.

Tafiya suka somayi suna mamakin ikon Allah azukatansu, wannan shine Allah d'aya amma gari banban, ka kalli nisan dabe wuce sa'o'i uku ba daga shigarsu jirgin su tsallako wannan wurin har sunga sauyin yanayi, babu wani gari dasuka hanga amma tabbas wurin ya k'ayatar, sabida ga 'ya'yan itatuwa nan burjik se kalan wanda bakaso dogayen itatuwa sunwa wurin k'awanya wurin ya burgesu sosai dukda zukatansu ba dad'i hakan be hanasu yada zango anwurin ba suyi sallah azahar harma da la'asar kasancewar su matafiya an halatta musu aikata hakan, bayan sun idar sukaci dabino da lemo harma da korawa da ruwan robar dabe wuce musu saura roba uku ba yanzu suka kama hanya bayan sunji cikinsu ya musu nauyi suka naushi hanyar suna tafe suna bin karatun alqur'ani me girma dake tashi daga k'aramar wayar Abu Huraira, yayinda suke tsintar lemon zak'i dakuma Tufa da suka taradda itaciyar kowannen burjin agun suna wurgawa a jakarsu wasu kuma a hannayensu.....

Ganin su da yarinyar tae ne yabata damar k'ara fitowa daga jikin itacen data bu'ya ta k'ura musu ido, shigar jikinsu kurun take kallo tana mamakin wad'an nan wane irin muta nene haka? Tun tashinta tana k'arama duk shekara se k'addara ta kad'o wani garin nasu amma wannan ne karanta na farko dataga masu irin wannan shigar kuma ga alama mazane ma, Dawud ne ya fara ganinta seda yaja baya ya rik'o hannun Abu Huraira

" Abu Huraira kalli wata aba!" Ya furta cikeda tsoro dan harga Allah shi kallon aljana yake mata, Atare suka d'aga suka kalleta kowa yae turus yana kallon ta ita d'inma su take kallo bata ko k'iftawa amma tafi nacewa kallon Abu Huraira da tawayensa kasancewar tana musu kallon aljanai gasu iri d'aya komai nasu iri d'aya tosu waye? Ta tambayi kanta

"Dawud mugodewa Allah mun had'u da mutum, wannan mutanene masu rayuwa jeji bakaga yanayin shigartaba?" Sauke ajiyar zuciya yae

"Toni naganta kaman daga sama kuma ta wani tsaya ta kafemu da ido ko k'iftawa batayi" Murmushi Abu sufyan yae yace

"Muda muke tare da tsarewar Allah, kai banda ikon Allah ka isa kazo nan wurin da ranka, koma aljanar ce magana zam mata niba ruwa na" takawa yae har zuwa inda take seda ya k'are mata kallo sannan yace

"Baiwar Allah dan Allah nand'in inane? B'ata mukayi wlhy muba en nan nahiyar bane" kallon sheqeqe ta masa sarautar da mulkin suka motsa dan dama ita ba'a kallonta a garin kwata kwata, baka isa ka kalli 'yar sarki ba, k'wak'ulemaka ido d'aya akeyi musamman mazan garin, cikin yaransu dabayaji ta sanya hannu ta tankad'a shi yae baya yaje taga taga ze fad'i seda Abu Huraira ya rik'eshi sannan tace

"Kai waye dazaka kalleni ido cikin ido? Zan saka a kashe ka fa" kallon juna sukai da tawayen nashi, shi Abu huraira ya fahimci sam batajin yaransu suma kuma bawai gane komai sukayi dangane da yaran nasu ba, hard'e hannaye Dawud yae ya langwab'ar da kanshi gefe d'aya ba tsinta dukaba, amma tabbas magana takeyi akan kisa dakuma fad'an yana kallonta, ko shakka bayayi yarbanci takeyi sedai banbancin kalamai da wurin furtasu daya kula akwai da yaren shida yakeyi, matsawa yae kusa da ita ya juye yaran bakinsa, cikin harshen na yarbanci ya soma bata amsa

"Kiyi Hakuri baze k'araba kinji" kallonsa su Twins suka tsaya yi sun gano yarbanci tae sedai suma natan ya musu wani iri, dukda yake sunsan abokin nasu Mahaifanshi duka yarbawa ne zama acikin hausawa yasa suka riqa, gasu musulmai ne kuma sosai tun kakaninsu shisa har komai nasu ya juye zuwa al'adun hausawa sedai kam sukanyi yarbanci sosai agidan nasu.
Kallanshi tae ya sauke k'wayar idanshi k'asa da sauri yanaso ya gane idan ya fahimceta sosai kallon natane ba'ayi, murmushi tae

"Wane magana yake haka? Bana ganewa?" Ta tambayi Dawud kanshi a k'asa yace

"Yaren sa kenan" Murmushi ta k'arayi

"Bayan yamura yarenmu sekuwa yamura kawal susu kad'aine yaruka biyu aduniya kuma duk na iya, ya akayi nashi bako d'aya aciki" D'an kallonta kad'an yae ya fahimci sosai bata san annabi ya faku ba, ko yanayin shigar tama ya nuna rayuwar dabbobi suke a jeji

"Akwai yaru kan dabaki saniba ne ai, duniyan yanada fad'i sosai yaruka sunfi a irga" Wata dariya ta kwashe dashi, sannan tace

"Ni babu inda ban saniba aduk fad'in duniyar nan, ko ina nasani kuma

Please Login or Register in order to submit comment