You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
Downloaded From https://arewanovels.com *💫STAR LADY💫*
💖The Talent Troupe Writer's 💖
*DUK ƘARFIN IZZATA*
💖Story And Written💖
⬇️
*Star lady*
Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai
Book 2
*Episode 1*
Ni gaskiya Abba na sak.. bai kai ga karisa maganar ba Abba ya daka masa tsawa chikin fushi da bachin rai ya fara magana "wlh Safras ko bayan rai na kasaki hiyana ban yafe maka ba itace zaɓin da na maka itace nake son gani a matsayin matar ka, ni ko kishiya ban yar da ka mata ba.
Dafe kai Bgs yayi da karfi ya damki lips nasa na kasa da hakoran sa ya datse da karfi kan kache me jini ya fara zuba gaba ɗaya ya fasa lallausan lips nashi hannu biyu yasa ya samki kansa wani irin gigitachen kara ya saki kafi Su Abba su farga ya zube kasa wanwar ko motsi bayayi da alama ya suma, da gudu rundunar jibga jibgan sojojin sa su kayo kansa shi kanshi Abba ya tsorata da ganin halinda Bgs ɗin ya shiga na dama ya fara yi a zuchiyar sa "me yasa ma tun farko na haɗa Aure nan yanzu gashi abun yana son yafi karfi ina da tabbacin wlh hiyana zata sha wahala san nan mawuyacin abu ne Safras yaso ta, innalillahi wa inna ilaihir rajiun ba zan iya barinka ka saki hiyana ba domin idan nayi hakan na chutar da ita idan kuma na barka da ita tofa idan abu yazo da karar kwana zaka iya kasheta, ya Allah ka kawomin mafita Allah ka taimake ni ka kawomin ɗauki amma nayi nadama gaskiya kuma bayi kuskure
Sojoji uku ne suka ɗauki Bgs suka kai shi mota, san nan suka dawo suka ɗauki Aiman shima suka kai shi mota, fitowa Abba dasu Khalid sukayi kowa ya koma chikin motar da yazo da gudu motochin suka fita Masallaci a jere, kai tsaye gida suka nufa
tun daga nesa suke ta faman danna horn chikin sauri jibga jibgan sojojin masu tsaron gate ɗin suka wangale musu, kutsa motochin chikin gida sukayi kai tsaye parking space suka nufa, suna kashe motochin wasu jibga jibgan sojoji masu jini a jiki ƙo sassu masu ji da lfy, suka kariso wajen su biyu suka ɗauki Bgs zuwa babban palon Abba wasu sojoji biyu suka ɗauki Aiman shima sukayi chikin palon Abba, nan take Abba yayi kiran gaggawa akan gaba ɗaya family su hallara a Palo sai lokachin Abba ya lura da Aryan da Yusuf basa nan da mamaki Abba yace
"ina Aryan da Yusuf Chikin sanyin murya Ammi tace "Yusuf dai yana ɗaki tare da lamrat shi kuma Aryan ban san ina yake ba" chikin faɗa Abba ya fara magana "me Yusuf kuma yake wajen lamrat yanzu duk tashin hankali da muke chiki bai isa yasa ya tsaya kusa damu ba" "a'a ranka ya dade lamrat fa Allah ya mata rasuwane"chewar Ammi, a razane Abba ya ɗago tare da faɗin"what!? Me ya samu lamrat ɗin daman bata da lfy ne!? "Aa lfy ta kalau tana tsaye kawai ta yanke jiki ta faɗi "subhanallah kai Umar jeka kira Yusuf ɗin kace ya tawo da lamrat, kai kuma Khalid kiramin layin Aryan muji ai na shi kuma ya tafi" da sauri Umar ya juya ya fita shi kuma yaya Khalid ya chiro wayar sa ya fara ne man layin Aryan.
Dogon salati Khalid yaja lokachin da ya kammala waya da Aryan gaba ɗaya mutanen palon suka ɗago suna kallon sa "menene ya faru kuma Khalid!? Chewar Abba "Abba diyana ce aka sace yanzu haka Aryan ya tafi Maiduguri gaba ɗaya jama'ar palon suka ɗau salati har da Aunty amaryan
Wani razanannen Ihu hiyana ta saki wadda yasa Bgs farfaɗo daga sumar da yayi yanke jiki tayi ta faɗi kasa sumammi ya, da sauri su Ammi su kayi kan ta suna kiran sunan ta chikin tashin hankali "hiyana!!! Hiyana!!! Amma ina shiru ko motsi batayi
Chikin tsawa Bgs yace "kai dalla kuma mutane shiru Allah yasa ta mutuma kowa ya hu..bai karisa maganar ba green eyes nashi ya sauka chikin idon Abba dake aiko masa da sakon harara miƙewa yayi a fusache ya nufi hanyar fita, kamar daga sama yaji yo muryan Aiman yana sambatu da alama ya farfaɗo juyowa Bgs yayi chikin takun sa irin na jaruman maza ya nufi kujerar da Aiman ke kwanche sai faman sambatu yake
"Abba kada kamin haka wlh ba zan iya jure wa ba ba zan iya hakura da diyana ba zafi zuciya ta kemin pls Abba ka tausaya min mutuwa zanyi dai dai lokacin Yusuf ya shigo ɗauke da gawar lamrat idon sa yayi jawur sosai kamar wuta gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun miƙe sai wani huchi yake kallo ɗaya zaka masa kasan yana chikin matsanancin bachin rai da tashin hankali
"Kai Aiman kamin shiru wlh ko na tsine maka dan tsabar rashin zuchiya yarinyar nan zakache kana so" chewar Aunty amarya tayi magana chike da bachin rai da bakin chiki, dafe sai tin kirjin sa Aiman yayi yana juyi kamar zai mutu
Nan take Bgs yaji zuchiyar na masa zafi chike da ɓachin rai ya ɗago green eyes nashi ya sauke su kan Aunty amarya chikin tsawa da ɗaga murya ya fara magana "wlh idan kika sake magana a palon nan babu abun da zai hana ni kakkarya ki, kashe shi kike son yine yaji da wanne yaji da raɗaɗin chiwon da yakeji ne ko kuma yaji da bala'i in ki!? Shiru Aunty Amarya tayi tana zare ido dan tasan hali Bgs tsab zai iya aikata abun da yace, Ba karamin daɗin abun da Bgs yayiwa Aunty amarya Abba yaji ba duk da tashin hankali da yake chiki sai da yaɗan yi d
Murmushin jin daɗi
"Yusuf Ai lamrat bata mutuba tashin hankali ne ya hana ka kane hakan baga hannun ta na motsi ba" chewar Khalid dake tsaye ta bakin kofar shigowa, a sukwane, Yusuf ya kai kallonsa kan hannun lamrat dake ɗan motsi chikin sauri yace "haidar bani ruwa, kasa kasa Bgs yace "karka zuba mata ruwa ka kyaleta ta farka da kanta, ba karamin daɗi Abba yaji ba da alama Bgs ya fara saukowa
Da gudu Umar ya dawo chikin palon chikin ihu yake faɗin "Abba Allah yayiwa yaya Ahmad chikawa yaya Ahmad ya rasu yanzu shigana ɗaki na samesa ya rasu wani gigitachen tsawa Bgs ya dakawa Umar "akoi wanda ya tambaye kane!!? Yana maganar yana kallon Aiman dake kwache, wani irin juyi Aiman yayi ya kankame kirjinsa da sauri sauri numfashi sa ke fita sai murkusoso yake yana juyi chikin rawar murya da kyar maganar sa ke fita yace "Ahmad ya rasu wayyo Allah wani miƙa yayi nan take hannun sa suka juya
da gudu Abba ya dawo kusa da shi yasa hannu ya danne kirjinsa ya riƙesa da kyau yasa ɗayan hannun Sa ya kamo kumatun Aiman ɗin ya fara karanto masa kalmar shahada sosai Abba ya sake danne kirjin Aiman ɗin da karfi dan yana son Aiman ya karɓi kalmar shahada, duk dauriya irin na Khalid sai da yayi kwalla da kyar Aiman ya fara karɓan kalmar shahada da Abba ke ta mai mai ta masa, bai kai ga karisawa ba rai yayi halinsa, chikin karyewan zuchiya Abba ya saki kumatun Aiman tare da zame hannun sa daga kan kirjin Aiman ɗin yayi baya baya ya koma ya zauna a gefe duk kokarin da Abba yayi ya danne hawaye sa amma abun ya chi tura nan take kwalla ya fara bin kumatun sa wani na bin wani, gaba ɗaya mutanen palon kuka suke ban da Bgs wadda idon sa suka sauya sukayi jaa sosai kamar wuta ya sunkuyar da kai kasa yana kukan zuchi
Mutuwar yara biyu lokachi guda wannan azaba dayawa take wai yau me ya shiga gida na ne Alhadulillah Allah na godema chewar Abba Khalid Yusuf duk kwalla suke sun kasa magana, sunkuyar da kai kasa Fahad yayi saboda kwallan da ya chika masa idon, bakajin sautin komai a palon sai sautin kuka da shessheƙa
Abu ɗaya Bgs yake tunawa shine Aryan, yaya Aryan zai ji lokachin da ya samu labarin rasuwar ɗan biyun sa da kuma Ahmad tabbas Aryan zai shiga tashin hankali mara misaltuwa.
Kutashi kuje ku shirya asamu a musu sutura mu kaisu gidan su na gaskiya, chewar Abba yayi maganar yana goge kwalla tun Abba bai gama rufe baki ba Bgs ya miƙe chikin sauri ya fice daga palon ya nufi part nashi
chikin rawar murya Khalid yace "Abba bazan iya zuwa ba bazan iya ganin yadda za'a saka Ahmad da Aiman a chikin kabari ba, bani da wan nan jaruntar ɗago green eyes na shi Yusuf yayi zai yi magana kenan sukaji sallama daga bakin kofar shigowa palon
Nan take kowa ya daka ta da kukan da yake
aruɗe suka kai kallon su bakin kofar shigowa kasan chewar sunji irin voice na Ahmad ne, zubur Abba ya miƙe chikin zafin nama Yusuf ya kwantar ta lamrat a kasan kapet ɗin shima ya miƙe, muryan sa har kerma take wajen furta Ahmad daman baka mutu ba!?
Murmushi yaya Ahmad yayi tare da ƙarisowa chikin palon yace "ban mutuba Yaya Yusuf ina raye Allah ya raya ni kuma ya tai makeni sana diyyar hiyana, gaba ɗaya jama'ar palon suka zubawa Ahmad ido suna juran karin bayani, nan ya fara basu lbr yadda hiyana ta taimaka masa har izuwa yau da ta bashi ruwan addu'a ya sha bayan na sha ruwan adduar da ta bani ɗazun ne sai naji gaba ɗaya jijiyoyina sun rike basa motsi nan take naji numfashi na ya ɗauke daga nan kuma ban sake sanin komai ba sai yanzu nan dana farka naji ni garau kamar ban taɓa chiwoba.
Alhamdulliah Alhamdulliah kawai mutanen dake chikin palon ke furtawa chikin sanyin murya Abba ya fara magana "yanzu mace mai irin wan nan halinne Safras zai che baya so lallai kuwa da ɗazun ka saki hiyana da ka tapka babban kuskure arayuwar ka" "Abba me kake shirin faɗane wache hiyanar kuma ba dai hiyana da tamin addua ba Abba nifa yanzu ma da kaga nazo palon nan, nazo sanar da kai chewar ina son hiyana ne ina son ta kuma zan Aure ta,
tirkashi chike da tashin hankali Khalid ya fara magana "Ahmad sai dai kayi hakuri domin hiyana dai matar Bgs che yanzu, kai in ta kai che maka gaba ɗayan mu yau Aka ɗaura auren mu, chikin tashin hankali Ahmad yace "yanzu shike nan hiyana tayi Aure innalillahi wa inna ilaihir rajiun hasbunalluhu wani mal wakil, shikenan ba komai nasan haka Allah yaso wai ina Aiman da Aryan da Bgs ne? A sukwane Abba ya ɗago yayi saurin chewa Aiman baya nan yana Maiduguri wajen Aunty farida, juyawa Ahmad yayi yanufi hanyar fita yana faɗin zuwa Maiduguri ya kamani a yanzu nan kenan dan ina matikar son naga ɗan uwana kuma shima nasan yayi kewana sosai zai ji daɗi sosai idan ya ganni yana kai karshen maganar ya fice daga palon ba tare da ya lura da yanayin fuskokin su Ammi ba Allah ma yasa Aiman na kwanche a kujerar bayan ne shiyasa Ahmad ɗin bai ganshiba, dafe kai kawai Abba yayi yana addu'ar Allah ya kawo masu mafita dago ido yayi chikin bada umar ya fara
"Kar wanda ya kuskura ya sanar da Ahmad rasuwar Aiman yanzu ku kyalesa ya tafi Maiduguri dan musamu muyi jana izar Aiman ɗin, idan ɗaya daga cikin ku yayi kuskuren sanar dashi yanzu tofa za'ayi gawa biyu kunga yanzu ya tashi daga chiwo dan haka ku kyalesa, Abba ya karisa maganar dai dai lokacin da hiyana ta farfaɗo
Sambatu ta fara yi tana faɗin "wayyo Allah na lamrat ta mutu diyana ta ɓata na shiga uku na dan Allah wadda ya sace diyana ya dawo da ita ya ɗauke ni ko kashe ni ma yake son yi ya kasheni ni dai ya dawomin da yar uwa, wayyo Bappa na Inna ta" gaba ɗaya palon ba wanda bai tau sayawa hiyana ba harta Aunty Amarya wadda yanzu mutuwar Aiman yasa tafara na damar rayuwar ta da abun da tayi
miƙewa Abba yayi ya koma kusa da ita hannun ta ya kamo chikin nashi murya kasa kasa ya fara magana "hiyana kiyi hakuri kinji jarabawa che Allah ya jarabce mu gaba ɗayan mu kiyi kokarin muchi jaraban nan kinji? Kuma ita lamrat bata rasuba doguwar suma tayi zata farfaɗo nan ba da jimawa ba, diyana kuma zamu gano ta kinji ko? Jin abun da Abba yace yasa hiyana miƙewa zaune da sauri tana faɗin "yanzu lamrat na raye wayyo Allah Alhadulillah Alhamdulliah Allah na godemaka, shiru Abba yayi yana kallon ta tunani yake
ya wan nan marainiyar Allah zataji idan ta samu lbr yanzu matar Safra che ita mutumin da ya nuna mata tsantsar tsana da kiyayya agaban idon ta, gakiya nayi na damar haɗa wan nan Aure dan nasan mawuyachin Abune Safras yaso yarinyar nan tun da ya furta da bakin sa ya tsaneta gaskiya nayi ganganchin sauri haɗa Auren nan.
To masu karatu bari mu leko yaya Aryan kuma muga wani wai nar yake toyawa tun da munji yadda Aunty amarya tafara karɓan hukunchi abubuwar da ta aikata hakkin mutane ya fara bibiyan ta
Maiduguri
Gaba ɗaya chikin birni da kauye Aryan ya baza sojojin sa ta ko ina an rufe hanyar shige da fice duk in da yake tsammanin zai ga diyana awajen an duba babu ita babu lbr, yashiga tashin hankali mara misaltuwa yama rasa ina zai sanya kanshi bayaji baya gani haka ya baza sojoji ta ko ina anyi sanarwar a gidan redio jaridu gidan Tv amma shiru babu diyana ba lbr Aryan kamar zai zauche wani azaba da raɗaɗi yakeji a zuchiyar sa sai jin faɗuwar gaba yake time to time kuma yana yawan jin voice na Aiman a kunnen sa yana faɗin "ɗan uwana ina kaunar ka ina matikar son ganin farinchi kin ka gaba ɗaya Aryan ya rasa meke damun kwakwalwa sa da take ta tariyo masa voice ɗin Aiman
To masu karatu dan Allah kumin afuwa wlh ina hanyane shiyasa kuma bani da charji amma idan na isa gida na samu charji to gobe zaku sammu sakon zafafan page har 2 yanzu dai ayi kuskuren baki da wan nan ina ganin addu'oe ku ina godiya
NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'💖
*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
👇👇👇👇
*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
by(Star Lady)
*2,GIDAN AUNTY*
by(mss lee)
*3,SARKI SAMEER*
by(xeemat....love)
*4, JINI DAYA*
by(mrs bbk)
*5,YA FITA ZAKKA*
by(mum Sayyid)
*Baby*
By (Mhiz innocent)
*💫STAR LADY💫*2
💖The Talent Troupe Writer's 💖
*DUK ƘARFIN IZZATA*
💖Story And Written💖
⬇️
*Star lady*
Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai
Book 2
*Episode 2*
......sosai Aunty amarya take kuka kamar ran ta zai fita sai rarrashin ta Ammi da Ummi suke chikin nitsuwa Abba ya fara magana "ku tashi muyi musamu mu kai Aiman ma kon chinsa, ku kuma Aisha ku tashi ku tafi kowa tayi part nata, kukan ya isa yanzu ba abun da Aiman ke bukata face Addu'a, kuma ina son sanar daku chewa ban yar ku sanar dasu farida yanzu ba ku bari sai bayan kwana biyu domin idan kuka sanar dasu yanzu tofa dole Aryan da Ahmad zasu samu lbr kuma kunsan me zai biyo baya idan suka sani a yanzu, yana kai karshen maganar ya miƙe ya fiche daga ɗakin miƙewa su Ammi ma sukayi gaba ɗaya suka fice sai kuka Aunty amarya take kamar ranta zai fita.
After 8 days da rasuwar Aiman, gaba ɗaya family sun haɗu a palo Abba, harda su Aunty mardiya Su Aunty farida gaba ɗaya family Abba sun haɗu A nitse Abba ya fara magana
"Duk kan ku ina mai baku hakuri da rashin da mu kayi san nan ina rokon Allah da ya baku hakuri da juria rashin ɗan uwan ku, a tare suka haɗa baki wajen chewa Amin, sun kuyan da kai kasa Aryan yayi sai furzar da iska mai zafi yake daga bakinsa chigaba da magana Abba yayi
"Safras Khalid Fahad Yusuf Aryan duk da chewa kai Aryan matar taka bata nan Amma In Sha Allah zamu gano ta, to ga amanar ƴaƴana nan na baku ku kulamin dasu idan ni bana ganin ku to kusani Allah na ganin ku musamma Safras Aryan Yusuf Fahad kusani marayu kuka Aura idan kuka chutar dasu wlh Allah ba zai kyale kuba.
Chikin rashin fahimtar Aunty amarya tace ranka ya dade ban gane me kake son kace ba wai wasu ya'yan naka kake maga kuma amanar wasu ƴaƴan ka basu? Dawo da kallon Abba yayi kansu ya chigaba da magana
"Kamar yadda kuka ji na faɗa hakane gaba ɗaya yaran nan na musu Aure nan dai Abba ya basu labarin yadda ya haɗa Auren nasu da kowa da matar sa, chike da tashin hankali da ruɗu hiyana ta ɓoye fuskantar a chikin chinyoyin ta saboda wani kukan bakinchiki da yazo mata shike nan na shiga uku na yaya prince ne mijina wayyo Allah ni nasan rayuwata tazo karshe kenan.
Chikin ɓachin rai Aunty amarya ta fara magana "wlh ban yar da ba tayaya za'ayi a haɗa ɗana da wanchan kazamar yar kauyen, dawo da kallon ta tayi kan Aryan dake zaune ya sunkuyar da kansa kasa yana kukan zuchi dan tun lokacin da ya samu labarin rasuwar Aiman kullun chikin kukan zuchi yake ya koma shiru baya magana bayama fitowa waje kullun yana kwanche a ɗaki
"Kai Aryan idan har na isa da kai to ka saki yarinyar nan yanzu dan ni bazan haɗa zuri'a da masu kiwon shanu ba, chikin jin haushi Aunty Maryam tace "haba Aunty amarya dan Allah ki kyale yaya Aryan yaji da abun da yake ji mana" "zaki min shiru ne ko sai na zabga miki mari wlh yau idan kunga Aryan bai saki diyana ba tofa mutuwa nayi tana magana tana huchi kamar wata zakanya
"Ba yau ba yanzu zan rubuta wasiya idan kika kuskura koda mutuwa nayi ki ka sanya Aryan ya rabu da matar sa tofa sai kin fuskanchi hukunchi mai tsanani gaske" chewar Abba
Chike da izza Aunty amarya tace "wlh babu wan da ya isa yasa na bar ɗana ya zauna da wan chan kazamar yarinyar, rai a matukar ɓache Bgs ya miƙe tare da miƙar da Aryan ya riko kafaɗar sa suka nufi waje tun lokachin da Aryan yasan Aiman ya rasu kullun yake chikin rashin lfy bai da wani kuzari sai yawan tunani
Miƙewa Aunty farida tayi tare da faɗin "ku tashi mutafi tayi magana tana kallon su hiyana, a tare suka miƙe gaba ɗayan su har da su Aunty Maryam suka nufi waje.
Palon ya rage daga Abba Ammi Ummi sai Aunty Amarya, shiru sukayi suna jin yadda Aunty amarya ke surfa ruwan bala'i dole sai Aryan ya saki diyana,Abba batare da yayi Magana ba yasa hannu a aljihun sa ya chiro wayar sa, ya shiga contact ya fara kiran wata number wadda akayi saving da My Brother.
Kira ɗaya a ka ɗaga sanya wayan a hand-free Abba yayi chikin girmamawa ya fara magana "Assalamu alaikum, daga ɗayan ɓangaren aka amsa da wa'alaikumus salam jin muryan wadda ya amsa Sallamar yasa Aunty amarya tayi sauri kwache wayar a hannun Abba ta katse kiran tana faɗin "dan girman Allah kayi hakuri karka sanar wa yaya wlh in dai Aryan ne na barshi yaje ya chigaba da zama da matar sa har abada Allah ya basu zaman lfy Allah yasa a gane ta" tana kai karshen maganar ta miƙe tare da ajiyewa Abba wayar sa a gefen sa ta nufi waje da sauri tana faɗin Allah na tuba kayafi min, duk bachin rai da raɗaɗin rasuwar Aiman dake damun Abba hakan bai hanashi yin ɗan murmushi ba dawo da kallon sa yayi kan Ammi da Ummi ya fara magana
"Aisha kije ki sanar wa farida nache ta shirya hiyana ta mata duk abun da ya dache ta kai ta part ɗin mijinta, ita kuma salma ta shirya Zahra itama ta kai ta part na mijinta, ke kuma hauwa'u ki sanar da mardiya akan ta shirya lamrat da amrat suma ta kai su part na mazajen su, suyi sauri yana kai karshen maganar ya miƙe ya nufi betroom nashi.
Kallon Ummi Ammi tayi chikin fargaba da tsoro abun da zai biyo baya tace "ki tashi muje mu isar da sakon ko? "To kawai Ummi tache a tare suka miƙe suka bar palon
After some hours
Aunty farida da Hiyana ne zaune a bakin gadon a ɗakin su hiyana Aunty farida ta tsara mata make up sosai
hiyana tayi kyau sosai kamar ka sache ta ka gudu da ita, sanye take chikin wata danƙareriyar lace pink colour ta yafa mayafi fari a kanta, chikin nitsuwa Aunty farida ta fata magana
"My Hiyana na san baki son Yaya prince Amma kiyi hakuri wan nan itache kaddarar ki kuma kisani hakan kamar jarabawa che Allah ya jarab cheki to kiyi kokari ki chinye jarabawar ki, kuma awan nan karon mu zaki tai makawa kinji ko? ina mai rokonki da ki daure nasan kina da hakuri sosai kuma nasan zaki iya to ki kara hakuri nasan zaki sha wahala zama da yaya prince amma ki daure In Sha Allah zamuyi nasara a kanshi kinji ko? kuma In Sha Allah kema zaki fara son shi yanzu zan faɗa miki ta yadda zamu fara yakar sa
abu na farko duk da nasan baya san ganin mace a kusa da shi amma ya zama dole kirin ƙa kasanche kusa dashi koda kuwa baya so
Abu na biyu ki dai na saka hijabin da kike sawa ki koma saka kananan kaya idan kin san yana gida, na uku zan roki maki alfarma a wajensa ko da yake ma koban roke saba nasan Abba zai che ke zaki rinƙa kai masa abinchi, kinga a nan ma zamu iya yin nasara, san nan idan ya dawo daga wajen aiki kiyi kokari ki saba masa da chire masa takalmi da socks da kan ki, nasan zaki sha wahalan hakan Kuma nasan zai iya chewa baya so to amma ko yache hakan karki dai na kirin ka yimasa kinji koh?
Kuka Hiyana take sosai kamar ranta zai fita rungumota Aunty farida tayi sosai tana bubbuga bayan ta tana bata hakuri awan nan yanayi Ammi ta shigo ta samesu "feeda Abban ku fa yace kiyi sauri ki kai Hiyana part na mijinta tun ɗazun fa su salma suka kai su Zahra" "to kawai Aunty farida tace tare da miƙewa ta kamo hannun Hiyana suka sufi wajen
Wani hawayen farinchiki Ammi taji ya zo mata burinta ya chika hiyana ta zama matar ɗan ta, sai dai awani ɓangare na zuchiyar ta kuma tana tausayawa hiyana sosai dan tasan Hiyana ba karamin wahala zata sha a wajen Bgs ba amma ta ɗauki kudirin taya hiyana yaki ta kowani hali
Maiduguri
ɗankareriyar mota kirar marcedes Benz che ta shararo a guje gudu mai motar yake sosai kamar zai tashi sama,ji kake kiiiiiii mai motar ya kwashe wata mahaukaciyar yarinya da ta zo tsallaka titi, wata mahaukachiyar birki yaja chikin sauri ya buɗe kofar motar ya fito kyakkyawa ne sosai fari tas dashi, chike da tashin hankali ya nufi inda yarinyar ke kwanche a saman titi ko motsi batayi kamar ta mutu ga jikin ta duk jini kanta ya fashe sosai, wani dogon salati yayi kafin ya karisa in da take juyawa yayi gabas
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31