You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da mahaukaciya sbd yanayin shigarta da rashin lafiyarta.

Saida aka fara tambayarsa ya tabbatar musu da itace mahaifiyar babyn kafin aka sake tambayarta itama tace babynsa ce.

Ganin yanayinta na tabin hankali yasa aka sallameta ta tafiyarta dayake yan sandan sunga gurin samun kudi sai suka Kama MAJEED din akan yayiwa mahaukaciya fyade ta Haihu.

Take Yan sanda suka sauya zancen Kuma suka tabbatarda Hadiza ta tafiyarta sbd karma aci gaba da tambayarta tadawo daidai tafada wani zancen Bayan wannan.

Babban tashin hankali yashiga Yana son mahaifiyarsa kadai ta yarda dashi ta fahimcesa Amma tuni taji tana danasanin fifita sonsa akan sauran 'yayanta.

Kasa danne abinda takeji tayi zuciyarta take tafara Neman bugawa aka kwasheta zuwa asibiti.

Acan station kuwa ba Imani yan sandan suka rufesa tareda cike Masa laifin dabai aikataba.

Zafi zuciyarsa da kansa sukeyi kaman zasu fashe,
Wace irin masifaffiyar qaddara ce wannan?
Tayaya mahaifiyarsa da 'yan uwansa zasu yarda da zai iya Koda kallon wannan matar so ukuma bare iya wani abun da ita sbd tsananin qyanqyamin dayake dashi.

Bai taba kukaba tun girmansa Amma ayau baisan lokacinda wasu hawayen baqin ciki da qunci suka gangaro masaba.

A rufe ya kwana Saida yakuma wuni a rufen kafin alhj jamilu qanin Haj umma yazo yayi belinsa shima ransa amatuqar bace da abinda MAJEED din yayi.

Ko sauraronsa baiyiba yayi Masa diban albarka da maganganun dasuke kaman Yana Masa Baki.

A gidan ma saida ya zubda hawaye ga maganganu marasa Dadi da 'yan uwansa suka ringa jifansa dasu
Mahaifiyar tasa kuwa ko qaunar ganin batayi hakan ta ringa hawaye tana jujjuyar dakai batason ganinsa yatafi yabarta kawai.

Nauyi zuciyarsa tayi ta yanda baisan mezaiyiba,

Mahaifiyarsa ta tsanesa Bata son ko ganin inuwarsa,
Yan uwansa ma sun tsanesa,

Yan uwan mahaifinsa Dana mahaifiyarsa sai Allah wadai sukeyi dashi.

Kiransa akai daga asibiti akan yazo ya tafi da babysa.

Baida wani zabi bayan zuwa ya karbota sbd bazai iya barinta acanba ayanzu da kowa yagama alaqanta shine mahaifinta.

Koda ya karbota ya dade Yana tunanin Inda zai kaita sbd dagashi har ita bazasu taba karbuwa ba a gidansu.

Hakanan ya daure ya iso gidan da ita saidai tun kafin ya shiga ainihin gidan su Anty safiyyah suka tabbatar Masa bazai zauna da 'yar ba a gidan.

Zabi zaka dauka ko ka kaita gidan marayu kokuma kasan Inda zakaje ka raineta Dan bazai taba yiyuba ayi renon 'yar qaddaraba a gaban hajiya sbd baka damu da damuwa ko baqin cikinka ya kasheta.

Bai tsaya ya sauraresuba ya wuce ciki da 'yar a hannunsa rungume ya nufi dakinsa.

Cikin fada sosai da tsawa anty juwairiyyah tace"

Bakaji abinda safiyyah ta fada bane?
Ina zaka wuce ana magana?
Ka fice kakoma tun dare baimaba kakaita gidan marayu idanma bazasu karbaba ka maidawa mahaukaciyar uwarta idan taga dama ta Yar da ita...

Tsananin zafi da quncin da zuciyarsa me Masa yasa tafara bushewa a fusace yace"

Duk abinda zanyi da ita da Inda Zan kaita ba ruwan kowa bane matsalata ne tunda nine nakawota..

Idan sbd wannan 'yar alhakin aketa tada hankali to naji nine ubanta zai raineta daga Nan har girmanta Kuma Babu Wanda ya Isa ya hana hakan.....

Nima ban isaba Amma Kuma na Isa danace kabar gidan Nan da ita tunda gidan bana uban nata bane.

Kai yanzu MAJEED har kayi nisan da yannanka suna magana kana mayar masu Kai me 'ya?
To wlh wallhi wannan 'yar dai bazata zauna a gidan banba,

Banason ganinku daga Kai har ita ka tattara ku koma gidan marayun har Kai sbd kaima kazama marayan daga yau...

A Rikice ya kalli hajiyar idanuwansa na sauyawa
Muryarsa na rawa yace"

umma nabar gida?????

Ban Isa bane?
Ai kakai tunda kazama uba yanzu.

Innalillahi wainna ilaihrrjiun""
Umma........

Daga Masa hannuwa tayi tareda fashewa da kuka Mai ciwo da qunan zuciya tace"

Idan Ina ganinka zuciyata bugawa zatayi MAJEED Dan Allah ka tafi na daina ganinka da 'yar nan.

Kaci amanar tarbiya da tsananin kaunar dana fifitaka akan 'yan uwankw..

Maganganunta dukan zuciyarsa sukeyi suna yamutsa qwaqwalwarsa tareda zafafa kansa.

Daqyar ya daga qafafunsa zai matso gabanta ta Kuma fasa kuka tana ja da Baya.

Wani nauyi ne ya danne Masa zuciya ya juya ahankali ya shiga dakinsa ya tattaro kayan dazai buqata ya zubo a jaka ya fito.

Su Anty safiyyah na kallonsa da mamaki sosai ya fice gidan batareda yasake cewa komaiba.

Yana fita kuwa hajiya jikinta ya rikice Nan tafara numfashi daqyar
Hankali tashe aka kwasheta zuwa asibiti.

Baitaba sanin haka 'dacin baqin ciki yakeba sai yanzu,

Zafi,ciwo,radadi,nauyi da tiriri zuciyarsa keyi duk lokaci daya,

Gidan Alhaji jamilu ya nufa Amma cin zarafin dayayi Masa yafi Wanda akayo Masa daga gida Dan haka yana baro gidansa Kai tsaye hotel yanufa yakamata daki ya kwantar da babyn tareda komawa gefe ya zube Yana riqe kansa dake neman tarwatsewa.

Babban qunci da dacin zuciyarsa yanda mahaifiyarsa da Yan uwansa dasuke jininsa suka zabi aibatasa da kalmomi mafi muni tareda tsanarsa..

Shin idan da gaske shine qaddarar haihuwar babyn ta sama haka zasu gujesa kenan?

Me yayiwa wannan baiwar Allah dazata ruguza rayuwarsa haka?

Kansa dake Neman bugawa ya juyo ya kalli babyn dake bacci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali..

Wani irin tausayinta yaji tareda qaunarta,
Me tayiwa mahaifiyarta dazata jefar da ita haka ga mutuminda batasaniba,
Batasan halayyarsaba,
Shin idan ga wani mugun mutum ne ta jefarda 'yar Yaya takeson rayuwar wannan 'yar alhakin tayi.

Kansa da kirjinsa sun toshe baida tunani komai.
Alwala yayo yafito yayi sallar magriba da aka Kira.

Yana idarwa babyn ta farka ya taso ahankali ya tsaya akanta Yana kallon yanda take motsawa ahankali tana fidda harshe alaman yunwa.

Numfashi ya sauke a sanyaye kafin ya juya gurin jakar kayan madaranta da nurse ta koya Masa yanda zai hada.

A sanyaye ya hada mata madaran da ruwan roba kafin ya debo ruwan dumi ya saka madaran yayi dumi.

Ajewa yayi gefe kafin ya dauki babyn yafara Bata ta karba take tana zuqa ahankali.

Qura Mata fararen idanuwansa dasuka sauya yayi Yana Jin tausayin kansa da ita,

Meyasa iyayensu zasu zabi jefar dasu akan qaddara?
Meyasa iyayensu suka zabi rabuwa dasu akan abinda suma basune suka samarwa kansuba?

Uwa mace da akafi sani da qawa zucin 'danta Amma su nasu uwayen Mata ne suka fincikesu daga rayuwarsu suka 'yar batareda nazari ko tunanin halinda zasu shigaba.

Shi tasa uwar data fincikesa daga rayuwarsu ta Yar yanada girman dazai kula da kansa Amma ita wannan babyn me tasani.

Har tagama shan madaran tayi bacci bai saniba sbd nisan dayayi a tunani.

Har lokacin sallar ishai tayi Yana zaune rungume da babyn.

Sallar ishai yayi wadda Yana idarwa ya nema guri yazauna tareda rufe idanuwansa yanajin yanda kansa ke tsananin ciwo.

Babban saukin daya samu babyn bamai rigima bace Dan haka har safe batai Masa rigima ba sai Madara datakesha sosai Dan haka baiyi wani baccin safeba.

Garin na wayewa guraren qarfe goma Dole cikin ma'aikatan hotel din yasamu wata ta sauya Masa kayan babyn ta shirya Masa ita ya dauketa suka sake koma gidansu.

Wannan karon Yana Isa babban tsaro yasamu a gate akan kada abarsa ya Shiga gidan.

Kiran wayar hajiyar ya ringa Yi Amma Sam Bata dauka daga karshe aka kashe.

Numbern anty juwairiyyah yafara kira itama bata dauka.

Ta anty safiyyah yakoma Kira itama Bata dauka.

Anan ya kusan wuni da babyn cikin Rana ganin Zata wahala yasa yakoma hotel din.

Washe gari haka yakoma gidan Amma saiya samu labarin sun wuce Lagos gabaki dayansu gurin ganin likitan hajiya.

Tashi hankalinsa yayi Dan haka ya ringa Kiran wayar hajiyar Bata Shiga qarshe ya Kira anty juwairiyyah.

Kalaman data fada masa sune yaka saddaqar da duk wani sauran burinsa na zama cikin Yan uwansa da mahaifiyarsa.

Ta sanar dashi hajiya umma Bata kaunar jinsa ko ganinsa,
Idan yakuma zuwa ko kiranta Zata iya tsine Masa.

Wainnan kalaman sun girgiza duk wata jarumtarsa da karfin zuciyarsa,

Amma Kuma sun daskarar da zuciyarsa data tarwatse lokaci daya,
Tabbas zaiyi nesa da Inda Haj umma Zata gansa bare yazama sanadin mutuwarta da 'yan uwansa suke fada.

Yana barin gidan yakoma hotel ya tattara kayansa guri daya,

Yayi wani irin kukan baqin ciki da maraicin rashin mahaifi a duniya,
Yayi kukan rabuwa da uwa wadda yasan itama tana cikin quncin wannan hukuncin nata saidai Kuma bazai taba Zama sanadin ciwonta ba dakuma tsinuwar data ambata garesa.

gari na wayewa ya nufi Tasha yahau motar komawa Yola.

A motar tun agurin Lodi ya sanar masu mahaifiyar 'yarsa ta rasune zai koma gida gurin danginsa.

Da wannan ya kawarda kallon zargin da ake binsa dashi fa babyn.

Wasu sun yarda wasu Basu yardaba ahaka dai akai tafiyar Amma saida wata dattijuwa ta karban Masa babyn sbd ganin yanda yake fama da babyn.
##MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[11/4, 11:05 AM] +234 813 979 4675: *_42_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Wuni cur sukai a hanya kafin suka Isa,
Saida ya sauka mota hankalinsa yayi mummunan tashi sbd baisan yanda zaiyi da babynba,

Baisan wazai tunkara ba,
Baisan tayaya zaiyi rayuwar makaranta da babynba.

Tunanin farko daya fara zuwa kansa shine ya fara Kama hotel na kwanaki sbd bazai iya Zama da ita a gidansaba sbd bashi kadaineba tare yake da friends dinsa ashir da Nuraddeen.

A hotel din daya Kama yakwana da babyn gari na wayeba baida zabi daya wuce yakaita gurin renon marayu sbd bazai iya yawon makaranta da itaba.

Kudin daya bada sosai ne kadai yasa suka karban Masa ita amatsayin 'yarsa da mahaifiyarta ta rasu gurin haihuwa.

Kwana biyu yayi yana yawo tsakanin makaranta da zuwa duba babyn,

Sabon yanayi ya shiga na rashin sauki fa sukuni,
Hankalinsa ya rarrabu,
Ga damuwa da quncin dake maqale cikin ransa.

Ahaka yayi kusan sati biyu
Take kudadensa sukai qasa sosai.

Babban abinda ya sake basa tsoro da firgici ga halin mutanen duniya shine duk kudi da Madara dayake siya na baby metron kashe kudin takeyi Bata siya Mata abubuwan buqata
Ko gyaran jiki dayace aringa Mata da wipes sbd asibiti dasukai masa gargadi akan rage yawaita Yimata amfani da ruwa sbd sanyin daya kamata a baya,

Amma sbd rashin tausayi da imani Ashe ruwa suke Mata amfani dashi ko Pampers basa siya maqale kudin sukeyi ko fitsari tayi ruwa suke saka zuba Mata sosai.

Ciwo yafara Neman kama babyn damuwa tasake kamasa sosai gashi bayajin zai iya miqa babyn har abada gidan marayu.

Haka yanaji Yana gani ya bar babyn hannun metron sbd watanni kadan suka rage Masa ya kammala karatun.

Komai nasa yaqare,
Kudin hannu da account dinsa sun qare tas dan haka yafara shiga yanayi sosai.

Babban sauyin daya samesa na rayuwa shine gabaki daya ya rasa walwala da fara'arsa,

Zancen abinda ya samesa tuni ya yadu tsakanin Abokai da jama'ar dasuka sansa Dan haka Ya tsame kansa ya kame daga hulda da kowa yanzu dama can bamai hayaniyar shiga mutanen ne Shiba,

Cikin tsananin hali ya kammala sauran watannin dasuka ragewa karatunsa bayan ya Saida duka agogansa da wayarsa sun qare ga hidimar baby INAYAH wadda yasawa sunan Da karatunsa.

Yana kammalawa ya tattara sauran abinda ya rage Masa ya fita neman hayar dakin dazai zauna ya nema aikin dazai kula da kansa da Inayah.

Wata irin qauna Mai tsanani yakewa Inayah a yanzu daya Gama tabbatarda batada kowa saishi kaman yanda baida kowa sai itan.

Kiransa da metron keyi da abban Inayah yasa kauna da shauqin abin ya shigesa sosai harya sabarwa kansa da amsa sunan.

Gashi Inayah din tayi girma ta warware kaman kowane Lafiyayyan baby.

metron ce tayi Masa tayin gidan hayarsu
Baida zabi haka ya amince duk tsananin qyanqyaminsa da rashin iya Zama cikin mutane.

Ganin yanayin gidan da jama'a sosai yasa ya ringa karbo Inayah wasu ranakun tana wuni hannunsa kafin ya maidata da daddare.

Rayuwa Tai Masa tsanani sosai sbd baida komai baida hanyar koman,

Ga metron tafara gajiya da renon tunda baida abin Bata yanzu saiya samo daqyar.

Rayuwarsa tagama sauyawa tako Ina,
Baya shiga mutane sbd kusan duk Inda yaje zundensa akeyi akan 'yarsa Inayah wasuma jifansa suke da zargin sai Allah idan ba lalata 'yar tasa zaiyiba.

Girma da tsananin dacin kalmomin ya sanyashi tashi gidan bayan ya hada kudin hayar daki wani gidan daqyar da aikin wahala.

Dayake yaga alaman metron ma ta gaji da renon Inayah kawai karbota yayi ya dawo sabon gidan daya samu mai dakunan haya birjik a jere
Mai daukeda mutane dabam dabam masu halaye daban daban.

Dagashi sai tabarma da abun rufa yadawo gidan sai yan kayansa na sawa dasuka Gama fita hayyacinsu sbd kodewa.

Kayan Inayah ba duka suka basufi kala huduba Dan haka dakin nasu fili fayau ne.

Madara yabata tayi bacci yafara kaida kawon tsakiyar dakin da ita a kafada Yana tunanin yanda zaiyi da ita yanzu.

Zuciyarsa ta qame ta bushe akan Al'amarin mutanen duniya da basusan komaiba sai kansu.

Cikin yardar Allah da zashi masallaci yafito da ita a kafada yana tunanin yanda zaiyi da ita yaje sallah.

Umma yaganah ce ta lura da hakan Kuma tunda ya tare ayau din aka fara tsegumsa tanaji sunayi abinka da gidan haya gulma ba taushe hannu.

Karban Masa ita tayi tace yaje sallar yadawo.

Ba musu yabata sbd Yana buqatan hakan.

Daga masallaci gurin neman aikin qarfi yadan zagaya yi Amma bai samuba sai daya dawo yasamu a anguwar ya samu tsaron shago Amma na idan an siya Kaya yakai mota yace ya amince.

Koda yadawo umma yaganah tayi Mata wanka da ruwan zafi tas ta Goyata sbd itama tanada tsananin sha'awar Yara Amma Allah Bai bataba ga manyanci haryazo.

Godiya yayi tareda bar Mata Inayah din sbd kada a datse mata bacci.

Tun daga ranar renon Inayah yakoma hannun umma yaganah wadda ta fahimci baya tareda uwar Inayah tunda dai shine mahaifinta.

Rayuwa taci gaba da tsananta Masa sbd komai ya qarasa juye Masa,

Aikin tsaran shago da aikin gidan ruwa ya hada biyu yanayi dashi yake daukan dawainiyar Inayah.

Ahaka har lokacin service Dinsu yayi yatafi yabarwa umma yaganah Inayah sati biyu acikin camp ya fito yadawo yafara bautar qasarsa.

Fara service dinsa ya taimake rayuwarsu sosai sbd monthly allowance dinsa dashi yake musu komai.

Kauna sosai ta tsakanin uba da 'da yakewa Inayah,
Duka a lokacin burinsa na inganta akanta yaqare,

Baida abinda yafi Masa Inayah sbd kaunarta ta taimaka gurin danne Masa radadi da ciwon dake daskare cikin zuciyarsa.

Ahaka yagama yake fita aikinsa na service Yana dawowa kuma ya hada Dana aikin gidan ruwa.

Koda ya kammala service dinsa Inayah tayi wayo sosai tasan mahaifinta wasu lokutan daqyar ma take komawa gurin umma yaganah.

Haduwarsu da yagana yazama wani babban taimako daga Allah dan kuwa badan itaba baisan tayaya zaiyi renon jinjirar 'ya shikadaiba.

Bayan Gama bautan qasa komai yasake tsananta alokacin ne yafara aikin wahala da qarfi kala kala Dan inganta rayuwar 'yarsa wadda yanzu a hannunsa take tabar hannun umma yaganah.

Tare suke cin abinci tare suke kwanciya
Wani lokacinma tareda ita yake fita aikinsa na wahala tana zaune cikin inuwa yake aikin yagama sudawo gida.

Ganin kaman sanyin dakin zai Mata yawa yasa yasiya mata karamar katifa shikuma Yana kwanciya a tabarma,

Duk wani abun buqata da Zata buqata baya sanya koda wahala saiya Nemo ya ajiye Mata.

Ita kanta tunda tayi wayo tasan mahaifinta wata irin kauna da shaquwa Mai tsananice ke tsakaninsu,

Batada abinda yafi Mata Abbinta a rayuwarta sai umma yaganah data sani,

Sam Bai taba barin tayi kuka ko kewan rashin uwa ba,
Shine uba Kuma shine ya maye gurbin uwa,

Mata wani irin kallo yake musu na rashin tunani da rashin tausayi da imani shiyasa duk wata mace ta fice Masa arai,
Mahaifiyarsa data qyamacesa sbd wannan qaddarar Bai tabajin ya tsanetaba Amma Kuma yasan tabbas Bata kyautaba Dan batai aiki da ilimin da Allah ya Bata.

Inayah itace tazamo sanyin idanuwansa Kuma qarfin gwiwarsa sbd duka gwagwarmaya dayayi a halin dasuka samu kansu yayisune sbd inganta rayuwarta,

Yayi alqawarin ingata tasa rayuwar da tatane sbd su rayu kaman kowane 'yaya marayu sbd daga shi har ita marayin Allah ne.



**********
Hadiza bayan barinta gidansu majeed hanya tabi tana Jin kanta na juyawa sosai ga uwa uba tafiyar datakeyi kaman Mai koyan tafiya Dan kuwa gabanta tuni yafara zubarda Jini sosai na yamutsin dayake ciki.

Batai doguwar tafiyaba taji tana Neman haukace tuburan Dan haka ta nema bakin wata hanya ta zauna tana rusa kuka sosai tana tasa Inda ke mata sauki a jikinta.

Kukan datakeyi ne tana yagar jikinta yajawo hankalin mutanen dake kusa suka fara kallonta suna tausaya mata wasu Kuma Mai Mata video sbd ganin haukacewa zatai alokacin da alama asiri akai mata suke zargi.

Kayan jikinta take kokarin yagawa wata Mata dake kokarin Shiga motarta tayi saurin zuwa ta tareta tana masifa da masu Mata video.

Cikin kuka da azaba sosai Hadiza ta bude Baki daqyar tana cewa"

Dan Allah ki taimakeni kikaini asibiti su ciremin gabana wlh azaba,
Ciwo,zafi,radadi duka inaji.

Kallonta matar tayi da mamaki tana sake riqe Dan kareta da handbag dinta masu sbd daukanta.

Da mamaki tace"

Me yake Miki azabar?
Me kikeji?

Kasa magana Hadiza tayi tana sake bubbuga gabanta cikin ficewa hayyaci tace"

Dan Allah ku taimakeni.....

Da sauri matar ta tari taxi ta cewa Hadizan ta shiga batareda ta kamataba sbd tsoro da tsaro.

Tata motar tashiga tacewa taxi driver din yabiyota.

Wani asibiti suka nufa tasa aka shigo da Hadiza wadda ta fice hayyacinta tini bayan gurnanin azaba da wahala Babu abinda take.

Da gaggawa suka karbeta zuwa ciki suka fara dubata.

Gaban nata dataketa duka suka fara budewa suka duba.

Wata qara suka ringa saki cikin tashin hankali da tsoro.

Dayake wadda ta kawota asibitin likitace take suka taru suka gano haihuwa tayi gabanta yasamu matsala.

Cikin gaggawa da tashin hankali suka fara taimakonta.

Dayake gurin ya lalace sosai Saida aka hada da yimata Yar qaramar tiyata.

Bayan taimakon data samu sun Gama Mata komai an maidata dakin dazata kwanta tana bacci batareda tasan waye akantaba.

Dr iklimat itace ta biya komai na Hadizan tukuna ta wuce gida.


Kwananta uku a asibitin kafin yadawo cikakken hayyacinta ta zauna daidai tana Jin komai Yana dawo mata sabo yanda yafaru.

Tashi hankalinta yayi tafara kuka Mai tsanani na Dana sani da Neman 'yarta.

Da farko Dr iklimat ta dauka Hadizan nada ciwon qwaqwalwa ne Amma data zaunar da ita ta rarrasheta ta sanar da ita komai sosai hankalin Dr iklimat ya tashi Dan haka Hadizan na samun sauki suka dunguma Neman gidansu MAJEED.

Kasa gane anguwar tayi bare gidan Dan haka suka ringa yawon stations suma Kai report Amma ba wani labari.

Tashin hankalin da Hadizan tashiga yasa take Neman rasa nutsuwa da lafiyarta sbd ahankali yafara taba qwaqwalwarta.

Dr iklimat data fara tsorata da Al'amarin haka ta samu ta lallaba Hadizan takaita Inda tafara ganinta tace tayi tanuni daganan ko Zata iya game gidansu MAJEED din.

Kaman qwaqwalwarta bazata tunaba sai gashi ta tuna suka ringa bin Inda take tunawa har Allah yasa suka Isa kofar gidan.

Basuga tashin hankali ba Saida aka tabbatarda MAJEED da babyn baasan Inda sukeba.

Take agurin Hadiza ta suma,
Haj umma ma Jin maganar dake bakin Hadiza yasata zubewa itama tana dafe kirjinta dake kokarin tashewa da tashin hankali Mai tsanani.

Daqyar su Anty safiyyah da taimakon Dr iklimat ta Dan dawo daidai.

Kuka tafara tana yiwa Hadiza Allah ya Isa akan abinda tayiwa MAJEED ta rabasa da uwarsa akan 'yarta Mara uba da asali.

Hadiza Kam saidai akai asibiti da ita.

A asibiti tana farfadowa Bata iya kukaba sbd zuciyarta dake barazanar daina bugawa.
##MAMUH#





_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107*_43_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Daga gidan Dr iklimat Hadiza sake komawa tayi gidansu hajiyar MAJEED wannan karon tana kuka tana komai Amma irin wulaqanci da tozarcin dasu anty juwairiyyah sukai Mata baisa ta hakuraba haka ta ringa zuwa rokonsu su fada Mata Inda MAJEED ya tafi da yarta.

Tun tana zuwa tana samun ganinsu har takai idan tazo Mai gadi ke yimata korar wulaqanci yana zaginta.

Daga qarshe police suka saka aka kamata daqyar tasamu Dr iklimat ta karbota bayan ta sanar dasu Hadizan nada matsalar qwaqwalwa.

Tun daga lokacin tashiga wani mawuyacin hali na ciwo da nauyi a zuciya.

Gabaki daya bata gane komai batajin komai sai kukan jaririyarta,
Kuka tuninya Dena zuwan Mata ya qafe..

Ta dan samu lokaci ahakan cikin masu aikin gidan Dr iklimat kafin Dr iklimat tafara janta ajiki Dan ta warware tafara dawowa daidai.

Da fari Al'amarin yayi wuya Amma da dr ta dage sosai Kuma lokaci yaja sai gashi tafara sakewa sbd kyautatawa Dr iklimat dataketa dawainiya da ita.

Itama aikin ta dauketa cikin gidan na abinci data iya.

Ganin qwarewarta a iya abinci yasa Dr iklimat ta maidata restaurant dinta sbd taga qaruwar da zatai da Hadizan.

Dayake tasaba aikin restaurant sai Bata wani Sha wuyaba tasaba da aikinta sbd Sam yanzu Babu wani digon farin ciki ko daya a rayuwarta,
Zuciyarta rufe take ruf da tarin baqin ciki da damuwa Amma a fili tana iya kokarinta gurin mu'amala me kyau da mutane.

Dr biyanta albashinta takeyi Mai kyau ba gayya Kuma kullum ta gamo aiki a can da daddare gidanta take dawowa ta kwana Saida sassafe ta koma.

Ahaka yayi fiyeda shekara daya a tareda Dr wadda Takoma tamkar wata babbar yayarta sbd sabo da kulawa,

Fes Takoma tayi fresh abinta sbd nutsuwa da cigaban data samu sosai.

Ana hakan abokin babban yayan Dr wani soldier yaganta yayi shaawan aurenta sbd yafi shaawan auren macenda batada kowa ganin yakeyi tafi maka biyayya hakama Zata riqeka amatsayin kowa nata tabika duk Inda kakeda ra'ayin juyata ko kaita.

Dr iklimat tana duba ribar da Zata samu a komai na rayuwa Dan haka MJ Muhammed na bayyanarda buqatansa na auren Hadiza tasan cigabansu sbd yanada arzikinsa sosai saidai yawan auri saki Amma yanzu kila ya daina tunda ya samu irin wadda yakeso wadda bazata iya Musa Masa komaiba sbd batada kowa.

Hadiza batada ra'ayi ko shaawan aure yanzu ko kadan aranta Dan haka Bata boyewa Dr iklimat ba ya fada mata batada ra'ayi.

Dr batai qasa a gwiwa ba ta ringa lallaba Hadizan tana cusa mata ra'ayin da auren kawai Zata samu sukuni da nutsuwata rayuwa tareda komawa cikin 'yan uwanta dasuka gujeta,

Aure ne kadai rufin asirinta Kuma shine zai Bata Daman sakin kudi ta nema majeed da 'yarta duk duniyar daya gudan Mata da 'ya.

Zancen Ayshatouh da Dr tasaka yayi tasirin sauya Mata raayi Akan yin auren.

Ba bata lokaci kuwa Dr tafara karban kudi sosai gurin MJ Muhammed aka fara gyaran Hadiza daman gata da sauran kuruciyanta.

Gaggawa Dr iklimat tasaka akan auren Wanda yasa Hadizan kejin damuwa Amma Kuma bazata iya fasawaba tunda tabbas batada qarfin dazata nema 'yarta sai tana tareda Mai qarfi.

Batada ra'ayin komawa gida Amma Dr iklimat ta dage akan suje gidan a daidaita Yan uwanta su daura Mata auren da kansu sbd kaucewa wata fitinar gaba.

Bayan ankai ruwa Rana itada Dr da Yan uwanta suka karbeta Bayan sun tabbatarda Mai kudine sosai Wanda zata aura.

Tunda Hadiza tadawo gida Babu Wanda ya tambayi Inda yarta takeba sai Inna wadda take fushi sosai dasu kabiru tun Bayan barin Hadiza gidan.

Ita kanta hadiza Bayan dawowar tata bayan gaisuwa Babu abinda yake hadata da Yan uwanta da matansu da 'yayansu,

Ta kebe kanta ta tsame daga cikinsu sbd tasakawa kanta Bayan Inna da Dr iklimat batada kowa a duniya.

Wata biyu tayi da dawowa gida akan daura aurenta da MJ Muhammed ta tattara Takoma Abuja gidanta itada Mai aikinta guda daya.

Tunda akai auren hankalinta baya kan mijinta sai akan Neman 'yarta wadda idan ciwon rashinta yataso Mata kaman zautuwa takeyi.

Tun mj na daurewa har abin yafara damunsa sosai auren ma yafara fice Masa akai.

Rawa auren yafara tun Bai Gama cika shekara ba
Dr na ganin hakan ta tashi tsaye akan Hadiza da fada sbd idan tayi gangancin rasa auren tayiwa kanta.

Ga rayuwarta tuni ta sauya tasamu wadata da Jin Dadi Amma zuciyarta takasa nutsuwa ta rungumi qaddara.

Inna Dr iklimat ta daukowa Hadizan wadda ta zauna tareda ita tana lurar da ita illar datakeson yiwa rayuwarta idan Bata dauki qaddara ta rungumaba.

Ba kunya hardasu Yaya Umar suka ringa kawo Mata ziyara akai akai suna Mata nasihan riqe aurenta.

Tayi iya kokarinta gurin danne damuwarta cikin ranta tafara kyautatawa mj Wanda yake tsananin kaunarta da Gaskia yanzu.

Rayuwar aurenta ta gyaru sbd ganin yanda dangi da Yan uwa kowa nayi da ita sosai sbd abun duniyar datake dashi yanzu Dan haka saita sake nutsuwa da kulawa da mijinta sbd koba komai auren yazama rufin asirinta dayasa kowa ka binta a Yan uwa.

Duk yanda taso cire damuwar yarta Bata iya cirewa duka Wanda hakan yasa mj ya dauketa daga Abuja Inda take tuna babyn ya maidata Lagos yadawo da uwar gidansa Abuja.

Rayuwarta a Lagos tafi ta abujan kwanciyar hankali da nutsuwa sbd ta rage damuwa sosai ta fuskanci gabanta.

Kaman yanda ake cewa dukiya daban take to kusan ta tabbarda hakan,

Yayunta dasuka fara aibata 'yarta sundawo sune suke gwagwarmaya sosai gurin bincike da Neman Ayshatouh wadda suka yarda da cewan ba shegiyar bace yanzu idanma da Allah suka yarda ko Dan quncin dasuka luradashi kwance qasan ranta Wanda suka tabbatarda har abada bazai goguba,

Kokuwa Dan kudin datake sakar musu sosai gurin binciken Neman 'yar ne?

Kwadayi da dukiya sunsaka

Please Login or Register in order to submit comment