You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ganganro Mata.

Kai tsaye Bai tsaya komaiba yace"

namiki alqawarin sauke Miki wannan auren daga lokacinda kika yarda da qaddara kika San aure tsakaninki da Abdul ya haramta,

Zan sauke Miki auren ki koma hannun mahaifiyarki da Abdulsamad kimun alqawarin bazaki Bari shedan ya Shiga zuciyarkiba kiyi watsi da tarbiyar Dana Baki.

Dago jajayen idanuwanta tayi da basa iya budewa sosai ta kallesa Jin Zata bar hannunsa Wanda ita Batasan wannan yarenba kwata kwata bazata taba barinsa Koda Zata rasa kowa a duniya.

Juyawa yayi ya kalli umma yaganah zaiyi magana
umma yaganah tayi saurin zubewa qasa tana neman fashe Masa da kuka tace"

Dan girman Allah MAJEED kada ka furta kalma daya data danganci rabuwar wannan auren.....

Rintse idanuwansa yayi Yana sake hadiye yanayin dayake ciki ya kalli Inayah dake kallonsa Ido na tsiyayar hawaye tana jiran kalamansa da zasu warware auren su koma matsayinsu na uba da 'ya.

Tunda umma yaganah take Bata dukan Inayah ba bare ma agaban Abbi sai yau dataji kaman tayiwa Inayah din duka tashi Kisha ruwan gishiri Dan haka Batasan lokacinda ta ringa dukan Inayahn da mayafin Jikintaba tareda damqar hannunta tayi ciki da ita bayan ta kalli cikin tsakiyar idanuwan Dr Abdul dake zubarda hawaye shime ta buga Masa wani irin mummunan gargadin dayasa shi kallon Abbi Wanda yakasa cewa komai sbd kansa daya toshe Yana sake daukan zafi.

Wucewa yayi yabar Dr Abdul din a tsaye gurin Yana bin hanyoyin dasuka bi da idanuwa cikin tashin hankali sbd Koda yasan bazai taba auren Dan Inayah ba zaifi samun nutsuwa da sauki idan yasan ba auren kowa kanta.


Umma na shiga daki da Inayah tayi wurgi da ita tsakiyar dakin tareda kallonta cikin tsananin takaici da bacin Rai tarasa wane irin duka zataiwa bakin Inayahn,

Cikin kuka Inayah ta cusa kanta cikin tsakiyar qafafunta tana jin hankalinta Kuma na tashi da kalman Abbi na miqata ga matarda ake Kira da mahaifiyarta wadda haryanzu basu sake haduwaba tun ranarda tazo gidan komai ya lalace.

Daqyar umma yaganah ta samu danne zuciyarta Takoma palon Wanda dama MAJEED ake jiran yazo afara maganar da zaayi.

Koda Isa palon zaman taron yaqara yamutsewa sbd Dr Abdul da jikinsa ya rikice Dole suka bar gidan.

Umma Hadiza kaman zata Dora hannu akai tayita rusa ihu takeji sbd wannan masifar dake Neman dawo Mata,
'danta daya Wanda take ganin ta Kama qwaqwalwarsa na Neman juyewa sbd son 'yar uwarsa
Gashi tana neman rasashi batareda wannan datake ganin tasamoba Bayan shekaru tazo hannuntaba.

Bataso tafiyaba saita hadu da Inayah Amma MAJEED ya hanata ganin 'yarta sbd yaqara nuna Mata ikonsa akanta.

Bayan barinsu gidan umma yaganah qin zuwa Inda Inayah take tayi sbd wannan karon tayi mummunan Kona Mata Rai.

Matuqar auren MAJEED yabar kanta Bata tunanin Inayah Zata samu mijinda zai kaisa agurin kulawa da ita Dan haka zatai iya kokarinta gurin ganin wannan auren baitaba rabuwaba Koda hakan na nufin da qarfin hali ta cusa Inayah gun MAJEED ya dirka Mata ciki taga yanda auren zai rabu kowama ya huta har Hadizan da 'dan su huta dasu akan raba auren.


Ranar gidan ko abincin dare Babu Wanda ya fito ci sai Neesah kawai data fito itama snacks kawai taci takoma daki ta kwanta.

Acikin daren Abbi yayi booking ticket na zuwa Abuja akwai Wanda zai gani daga can zai wucewarsa Dan Yana buqatan kansa ya sake.

Washe gari qarfe 8 na safe yayiwa umma yaganah txt driver ya wuce dashi airport jirginsu ya tashi qarfe Tara.

Koda INAYAH ta tashi da safe jiki a mace tasan Bata kyautaba Musamman da umma yaganah ta matse fuska sosai Bata wani sake Mata ba
Duk saitaji tasake Shiga damuwa dan haka ko wanka bataiba da Riga da wandon bacci masu tsantsi ta wuce palon Abbinta Dan basa hakuri sbd Bata iya juran fushinsa akanta ko kadan,

Kuma ta wani bangaren gaskiyarta ce tafada bazata iya rayuwar aure da Abbinba sbd asalin life takeso arayuwar aurenta wanda Zata iya nuna soyayyar mijinta agaban kowa Kuma shima zai iya nunawa agaban kowa Dan haka Babu ta Inda Zata iya wannan rayuwar da Abbi Wanda takewa kallon ubanta Kuma uwarta.

Shine ya koyar da ita yakuma Bata tarbiyar fadar Gaskia komai dacin dazata kawo shiyasa koyaushe ake ganin wautarta Dan ita tasaba gaskiyarta take fada daga zuciya ba boye boye ko munafurci.

Kayan jikinta umma yaganah ta kalla lokacinda ta gaisheta tareda juyawa Zata nufa sashen Abbin.

Floral pyjamas ne na bacci ajikinta masu santsi farare,
Babu bra ajikinta Dan haka kirjinta dasuke tsaye qyam suna bayyanarda basa cikin bra din.

Ko hips dinta sosai suka fito a wandon kayan sbd santsin kayan yasa suka Dan lafe a jikinta.

Da adah ne umma yaganah hanata zuwa takeyi gaban Abbinta da kayan bacci sbd kusan rayuwar Inayah din babu ruwanta kusan koyaya tana iya zuwa gaban mahaifinta da towel ne kawai Bata iya zuwa gabansa sai guntayen Kaya Amma Dan kayan bacci dasu leggings duk ba komai bane agunta.

Umman na sane Sarai ta qyaleta ta Kama hanyar palon nasa batareda tace Mata taje ta sauyaba kokuma sanya wani Abu akai.

Ja'irar yarinya Allah ya nunan ranarda wannan bakin naki zai mutu yayi hankali.

Shima MAJEED din da haryanzu yake biye Miki yaqi bude Baki ya magantu dakyau ki dawo hankalinki.

Inayah nakaiwa kofa massage din MAJEED nashigowa wayar umma na cewan yayi tafiya.

Sanyi jikinta yayi tanajin tausayin MAJEED din sbd abubuwan sun Masa yawa gashi wannan Yar banzar na Neman qara zafafa Masa kai da haukarta.

Cikin gatse tace"

Hajiya saiki dawo MAJEED din yayi tafiya yace
Saiki dawo kici gaba da kuka tunda Baki aura Dan rayuwar dakike burin samun aureba.

Maganar umma na cewan abbin yayi tafiya yasa hankalinta sake tashi saidai Bata nunaba sbd umman karta cigaba da Mata wannan fadan na baqar magana Dan haka ta juya jiki mace Takoma dakinta.

Tana shiga daki ta zauna tareda daukan wayarta Kai tsaye tasaka kiransa tana sake Shiga damuwa Mai tsanani,

Abbinta akaron farko dasuka kwana suka wuni basuyi wayaba basuyi maganar arzikiba,
Yanzu Kuma yayi tafiya batama saniba hakama umma yaganah kawai ya fadawa.

Hawaye taji idanuwanta na cikowa dasu indai kuwa akan Abdulsamad Abbinta zaiyi irin wannan fushin da ita Zata hakura dashi...
Tama hakura dashi
Zata bawa Abbi hakuri bazata sake ko maganar Abdul dinba barema ummansa.

Kiran wayarsa tahau yi Amma takasa samu Dan haka taji kaman wani zazzabin na neman kamata Dan haka ta silala tayo wanka ta shirya cikin doguwar Riga breakfast dinma Dan Dole ta fito taci tana qarfafawa kanta sbd Abbi yadawo anjima ya taddata ta sake zaifi saurin yafe Mata sbd fushin Abbi shine abinda Bata taba dauka da wasaba.
##MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107[11/3, 10:19 AM] It's Queen Meenali👑: *_37_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Sukuku ta wuni ranar zuciyarta ba Dadi hakama umma har lokacin ta fuske Mata ga Neesah nata shirye shiryen tafiyarta ga abbin sai Kira takeyi takasa samunsa duk saitaji kaman tayita rusa kuka
Gashi umma na fushi ko tayi kukan tasan ba rarrashinta umman zataiba.

Har qarfe biyar na yamma tana jiran dawowar abbin sbd Bata tunanin tafiyarsa Mai nisace kokuma kwana bare barin qasa dazai tafi Bata saniba tana matsayin 'yarsa daya tal......

Shiru tayi daga wannan tunanin sbd tunowa da auren da har lokacin Batajin ta sauko ta karba auren,

Ta hakura da Dr Abdul sbd kaucewa fushin abbin Amma ita maganar aurenta dashi batajin Zata taba karban wannan.

Ganin zaman Yana neman Cinna Mata hauka yasa ta fito Palo tana kokarin nufar hanyar dakin umma yaganah saiga qarar akwai baqi a kofa.

Duk da tasan ba Abbi bane Amma sbd tana buqatan ganinsa yasa taje da sauri ta bude tana adduar Allah yasa shi dinne.

Anty Hafsat tagani da CM da sauri ta rungume anty Hafsat tana Jin hawaye na ciko idonta kawai sbd Daman tana neman Wanda Zata fadawa kukanta.

Cikin kulawa Anty Hafsat ta dago bayan ta zare jikinta tace"

Muna tareda baqi Inayah behave yourself idan mun nutsu mayi magana.

Fuskarta still da sauran hawaye ta juyo ta kalli baqin.

CM tafara kallo cikin nutsuwa tace"

Daddy Ina wuni?

Murmushi yayi cikin kulawa shima yace"

Lfy kalau Inayah,
Yaya umma yaganah?
Ki gaidata idan Kun shiga bazan tsayaba sauri nake saidai idan nadawo.

Anty Hafsat ya kalla yace"

zanje na dauko Alhaji babbah sbd suma su Haj Hadizan suna hanyar qarasowa nan din kafin su iso akai su hajiya suyi sallah su huta sun biyo hanya.

Juyawa yayi ya kalli farar dattijuwar dake tsaye gefe cikin ash Australian lace da lafaya baqa a nade da ita yace"

Hajiya ku qarasa Bara na dauko Alhaji idan kafin Ku huta.

Gyada Masa Kai kawai tayi ahankali tareda maida kallonta kan Inayah data kasa daukewa Ido.

Cikin nutsuwa Inayah ta kalli matar wadda itama tsura Mata Ido yayi sosai sbd haskenta sosai da Kuma ganin kamanninta sosai da Abbinta Dan kuwa kusan Tama fisa kyau sbd tana mace saidai kawai manyancin datai sosai.

A natse cikin kasa boye mamakinta sosai tace"

Ina wuni?
sannu da zuwa.

Sam hajiyar Bata amsaba Wanda ita Inayah Sam Bata luraba juyawa tayi Takoma ciki tana sake saka Kiran Abbi a wayarta.

Cak hajiyar tayi agurin taqi saka kafarta a palon.

'yarta dake gefenta wadda a shekaru tafi anty Hafsat shekaru sosai ta kalli hajiyar zuciyarta na quna kaman yanda ta hajiyar ke quna Kai tsaye ta bude Baki ba boye boye tace"

Hajiya inaga mu koma gida kowai kokuma kokuma muje gidan Alhaji babbahn shida kikazo sbd alfarmar daya nema ta zuwan naki.

Batareda hajiyar tace komaiba kuwa suka juya
Anty Hafsat ta juyo da sauri tareda binsu a rikice tana bawa hajiyar hakurin su dawo.

Hajiyar tafiyar kawai takeyi Amma zuciyarta a rufe take....

Ciwon hawan jininta Dana zuciya daf yake da tashi sbd dacin da zuciyarta ke dauka..

Kasa jurewa tayi ta tsaya cak tana Dan dafe kirjinta.

Da sauri anty Hafsat da 'yar tata wadda anty Hafsat takira da Anty juwairiyyah suka riqota suna Kiran sunanta da cikin kulawa.

Ganin tana neman faduwa agurin yasa ba yanda anty juwairiyyah ta iya suka Jata suka koma cikin gidan.

Umma yaganah data fito palon Jin ance sunyi baqi Bata ga kowaba tana Shirin juyawa suka shigo da hajiyar a rirriqe.

Da sauri cikin kulawa tace"

Subhanallh,
Hafsat baqin namune ba lafiya?
Bari Akira Dr farhat da sauri kafin Nan Bari Neesah ta fara dubata.

Ciki umman tayi takira Neesah saidai Ashe Neesah din ta fita Dole sai dr farhat suka kira da gaggawa.

Agurin wayar anty Hafsat tace"

Umma yaganah ki sanar da ita umman AA MAJEED ce da kanta da Allah ta iso da wuri........

Wuta umma yaganah ta dauke tareda bude dukkanin idonta tana kallon hajiya.

Sai alokacin taga zallar kamannin MAJEED atareda hajiyar dan haka take jikinta Dana Inayah data fito lokacin mutuwa sbd tsananin farin ciki.

Umma na aje wayar kuwa ta kalli anty Hafsat tace"

Mahaifiyar MAJEED ce kikace?

Eh umma itace.

Maida kallonsu kan hajiya sukai itada Inayah lokaci daya fuskar Inayah daukeda farin ciki Batasan lokacinda ta furta"

Yau Naga daya da cikin kakannina kenan...
Ashe munada dangi muma,
Abbi na ummansa na raye..

Da sauri umma yaganah ta Dan kwabeta kada ta sauka layi
Cikin sakin fuska da bayyanan farin ciki tafara yimusu sabuwar sannu da zuwa tana miqewa Anty juwairiyyah ruwan roba da aka kawo Mara sanyi tace"

Bata Tasha Zata Dan ji dama Dama kafin Dr farhat din tazo.

Daga hajiyar har anti juwairiyyah Babu wanda ya iya magana har lokacin sbd Babu Wanda zuciyarsa Bata cikin dacin rai na shigowa gidan.

Ganin yanayinsu yasa umma datake Babba ta fahimci akwai damuwa Dan haka tace Inayah tayi ciki har hajiyar ta samu nutsuwa tukunna.

Babban dakin bakinsu dake gefen na umma yaganah aka gyara take duk da Baya buqatan wani gyaran sbd komai na dakin fes yake Kuma Babbane da toilet.

Dubari su Anty Hafsat suka ringa yiwa hajiyar ana mata firfita duk da sanyin AC sbd asamu Dr farhat ta iso.

Dr farhat na isowa aka Kama hajiyar aka Kai dakin da aka Gama gyara musu sanyin AC da qamshi sai tashi yakeyi.

Ba wata matsalar bace kawai jinintane ya hau take.
Maganinta da batazo dashiba shi Dr farhat tasa aka kawo suka Bata
Cikin Yan mintuna kuwa sai gashi tadan samu tafara dawowa daidai.

Fita akai aka bawa hajiyar da Anty juwairiyyah guri su but suyi sallah da sauransu tukuna.

Bayan fitarsu ganin yanayin hajiyar yasa Anty juwairiyyah data Gama cika da baqin ciki aranta tun na shekarun Dana yanzu datake gani gabanta yasa bataiwa hajiyar maganar komaiba ta nufi toilet tashiga Dan yin alwala.

Hajiyarma saita huta Zata iya sallar sbd tanajin jiri har lokacin da bugawar zuciya da sauri Dan haka rufe idanuwa tayi daga kwancen tanajin zuciyarta na karye fiyeda shekarun data debo bada ABDULMAJEED dintaba sbd Bata saniba Ashe Yana Nan ya Gina sabuwar rayuwa da sabuwar uwa...Jin tayi hawaye na taruwa acikin idonta Amma kaman koyaushe Bata barin su gangaro sbd zubda hawayen uwa akan danta matuqar bana farin cikiba babbar masiface ga 'da.



Inayah kuwa cikin farin ciki take Neman wayar abbin Amma still Bata samuba sai taji murnarta ta Kai sbd duk Wanda Zata samu a rayuwarta matuqar Bata daidai da Abbinta Bata cikin farin ciki da nutsuwa Dan haka take murnar ta sace Mata ta zauna daki tareda zubawa wayarta Ido.

Umma yaganah kuwa hidima tashiga kitchen da kanta tafara yiwa su hajiyar MAJEED din sbd tasan matsayinsu sun wuce abar 'yan aiki da hidimarsu Dan haka tahau aikin abinci Lafiyayye Mai lafiya.


Saida akai Kiran magriba aka Gama komai aka kwasa a jere da kuloli aka Kai dakinsu har lokacin daga hajiyar har Anty juwairiyyah Babu Wanda ya saki fuska ko nuna sakewa Amma hajiyar taji sauki tana zaune tana waya a sanyaye da babbar yarta.

Umma yaganah Bata damu da rashin sakewarsuba bil haqqi take musu hidima tana sake bayyanar musu da mahimmanci dasuke dashi Mai girma a gidan duk da yau suka fara zuwa.

Acan Kuma Inayah nason magana da anty Hafsat Amma anty Hafsat din ta hana sbd Dr farhat na gidan Bata wuceba Kuma Batasan da MAJEED aka daura aurenba a qataice bakowane yasan meye dalilin fasa auren Inayah da Dr Abdul ba hakama bakowa yasan da waye aka daura aurenba sbd duk har lokacin a uban Inayah suka Sansa.

Dr farhat na tafiya saiga su Alhaji babbah sun iso daidai tareda motarsu umma Hadiza da 'yan uwanta.

Dunguma sukai suka shigo ciki gabaki daya babban palonsu umma yaganah.

Tunda umma Hadiza tashigo take rarraba idon Neman ganin Inayah cikin gidan.

Inayah tunda taji su umma Hadiza sunzo gidan taqi fitowa ko Alhaji babbah tanason fitowa ta gaidar Amma batajin Zata iya barin umma Hadiza ta ganta matuqar bada izinin Abbinta ba sbd shine kawai yakeda iko akanta na yanda zaiyi da alaqarta da Hadizan.

Umma yaganah ma Gaisawa kawai tayi dasu Alhaji babban ta miqe Zata komawarta ciki sbd yanzu da mahaifiyar MAJEED take Nan ba buqatan zamanta agurin dama can Dan tana matsayin uwa ne.

Cikin nutsuwa Alhaji babbah yace"

Yaganah dawo ki zauna ai komai dake zaayi kece MAJEED yanzu tunda Baya Nan.

Dan murmushin yaqe tayi tareda dawowa ta zauna tana dan kallon Inda hajiyar MAJEED take zaune fuskarta ba walwala ko kadan.

Kusan kowa ya zauna ya nutsu,

Alhaji babbah ne da CM a gefe daya
Sai umma Hadiza da Haj balaraba a dayan gefen
Alhaji buhari dasu malam Umar ma dasuka matsu dason ganin Inayah duk suna zaune sai Dr Abdul daya rakube cikin yanayi na tausayi da ciwon dake damunsa.

Hajiyar MAJEED ma da Anty juwairiyyah da umma yaganah sai Anty Hafsat gefensu daya.

Cikin nutsuwa Alhaji babbah yafara magana da cewa"

To dukkaninmu dai kusan bamusan junaba anan MAJEED da INAYAH ne ya hadamu anan,

MAJEED yayi tafiya wadda Nima ban hanasa duk da nasan zaayi wannan zaman sbd Yana cikin yamutsin Kai Dana zuciya
Yaron Yana buqatan nutsuwa sbd abubuwan duk sun taru sun ratayane akansa Dan haka gwara abarsa ya samu nutsuwa kada pressure da damuwa din mahaifiyarsa gatanan data matarsa data hajiya Hadiza dama Tamu duka ta sanyasa cikin wani hali.


Hajiya Asma'u wannan itace hajiya Hadiza da 'yan uwanta gasunan mahaifiyar Inayah 'yar MAJEED da kuka sani a baya matarsa Kuma a yanzu.

Hajiya Hadiza wannan Kuma itace mahaifiyar ABDULMAJEED data haifesa.

Ayanzu wannan taron dai na fahimatar junane dakuma warware duk wata damuwa da qaddarar data Riga ta wuce.

Inayah dai ba 'yar MAJEED bace hajiya kaman yanda kike tunani
Amma dai yanda tazo hannunsa ne Babu Wanda yasani sai Allah saikuma MAJEED din da Hadiza gatanan zaune.

Hadiza ki warwarewa hajiya komai sbd kawarda zargi da Kuma damuwar qaddarorin dasuka gifta abaya data rabu da 'danta akan hakan.

Dagowa Hadiza tayi jiki a sanyaye ta kalli hajiyar cikeda kunyar Zama mugun sanadin daya kawo abubuwa da dama.

Kan su Yaya Umar da Yaya kabiru ta maida kallonta sbd kusan suma sune sanadin komai.

Inayah data tsaya bakin kofar dakin umma yaganah sbd tanason taji yanda tazo hannun Abbinta da kunnenta batareda wani ya fada Mata ya rage Mata wani abun....

SHEKARUN BAYA....
#MAMUH##
#LOVE/ROMANCE/LOADING


_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[11/3, 10:19 AM] It's Queen Meenali👑: *_38_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Tana fitowa gidansu rungume da jaririyar tata dake lafe kirjinta tana bacci taji qafafuwanta na Neman sanyi Amma sukasa riqeta sbd wani irin nauyi da kirjinta kemata tareda radadi a maqoshi..

Sake rungume jaririyarta tayi da kyau ahankali kafin ta dago ta kalli hanya da idanuwanta dasuka qafe sukai jajir sbd kuka tuni ya qafe daga Idanuwanta.

Ahankali ta daga qafafunta tafara tafiya tareda kauke kanta qasa sbd Yan anguwa wainda suka lura da ita suke kallonta da ma'anoni da maganganun zunde da zagi.

Bakowane yasan tadwo daga Lagos dinba da ciki saidai sukaji haihuwar tareda rasuwar mahaifiyarta shiyasa kusan duk Wanda ya bude Baki tir da Allah wadai yake furtawa gareta da jaririyar 'yarta.

Ahankali take takawar sbd rashin qarfin jiki dakuma qarin data samu agun haihuwa gakuma rashin abinci ko abinsha Dan haka batada wani babban kuzarin takawa da sauri harta fice daga layin batareda ta waiwayo ba Dan tanajin idanuwan mutane akanta Wanda tasan mummunan fatar rashin ganin me kyau suke Mata a duniyar da Zata shiga.

Kasa hawa titi tayi sbd Batasan Inda ta dosaba,
Batasan gurin waye Zata ba a wannan mummunan halin datake ciki,

Batada uwa Bata uba batada miji waye gareta Mai tsaya mata?

Samun kanta tayi da zaunawa bakin wata bishiya sbd kwakwalwarta datake neman Dena aiki.

Jaririyarta tafara kuka Wanda na tsananin zafin ranar dake dukansu ne

Yaye zanin datake dunqule aciki tayi ta Dan kalli fuskarta taga yanda fuskar tayi jajir take sbd azabar Rana
Sai alokacin taji zuciyarta data daskare tana narkewa da tausayin kanta dana jaririyar Dan haka batada zabi daya wuce ta tunkari gidansu salisu ko ummansa Zata karbesu tunda jikartace su taimaketa ta zauna gurinsu ta Rena Ayshatouh idan ko shekara tayi saita barta takoma gidansu idanma sbd itane su Yaya Umar suka koreta daga gida.

'yar qaramar jakar kayanta ta bude tafara duba kudin datake dasu.,

Dari uku da ashirin tagani take jikinta yakuma mutuwa saidai halinda zuciyarta take ciki Batajin akwai abinda zai fisa daci.,

Miqewa tayi ta qarasa bakin titi Anata kallonta sbd Jin yanda jaririya ke kuka sosai a jikinta Dan haka Bata tsaya juran napep ba ta tsayarda Mai mashin ta hau suka tafi.

Gabanta tsananta faduwa da shiga qunci yakeyi sbd hajiyar salisu ma batasan yaya zata karbesuba...

Mai mashin na ajiyeta kofar gidan ta Ciro dari da hamsin ta miqa Masa ta juya ta shige qaramar kofar gidan tana sake qamqame yarta jikinta.

Tun kafin ta qaraso ciki Yara suka fara Isa gurin hajiyar suka sanar Mata Hadiza tazo.

Dan shiru hajiyar tayi kafin ta kalli yaran ta korasu waje ta dawo da hankalinta kansu balaraba dake gidan ta sallamesu suka wuce inda zasu ta kofar baya batareda sun tsaya Gaisawa da Hadizan ba Dan dama a sama sama suke da ita tun salisu nada Rai bare yanzu da basuda alaqa da ita.

Da wata irin dasasshiyar sallama ta shigo hankali sbd muryarta ko fita batayi.

Da mamaki hajiya ta kalleta idanuwanta na sauka kan jaririyar dake hannun Hadizan.

Idanuwan Hadizan zuwa fuskarta ta kalla dakyau take tagane jegone tareda Hadizan Dan haka ta tattaro hankalinta da mamaki a bayyane kan fuskarta tace"

Hadiza¿
Kece nake gani?
Lafiya da Rana tsaka haka?
Ba zaman karban gaisuwar Aishatu akeba.

Kasa magana Hadiza tayi sbd jirin dake dibanta Dan haka a sukwane ta qaraso ta durqusa gaban hajiyar tareda sunkuyar dakai idanuwanta na sake rinewa.

Sake Shiga firgici hajiya tayi tana qin nuna taga jariri atareda hadizanba tasake cewa"

Hadiza nace lfy kuwa?
Kiyi mgana kikai shiru kina bani tsoro...

Dagowa Hadizan tayi tana kallon hajiyar sbd tasan bazatace bataga abinda ke hannuntaba
Idanma Bata ganiba bazatace batajin kukan da Ayshatouh ke tsalawaba.

Sunkuyar dakai tayi tareda bude jaririyar dakyau agaban hajiyar muryarta na a disashe da tsananin damuwa da qunci Mai daci tace"

Hajiya haihuwa nayi su Yaya Umar sukace nabar gida,
Bansan Inda zaniba sbd ko Abokai banda shine nataho Nan....


Dauke wuta hajiyar tayi daga zaune tana kallon Hadizan Baki sake ko fuskar jaririyar taqi kalla.

Qofa tafara kalla ta leqa tsakar gida taga ba kowa tadawo da sauri ta kalli Hadizan cikin tsananin mamaki, firgici da takaici Kai tsaye tace"

Me Zan Miki anan hadiza?
Haihuwafa kikace kinyi?
Haihuwa ba aure fa?
Wace qaddarace wannan takaiki ga wannan mummunan sakamakon? Shine Kuma Zaki zomun Nan?

Ko kunyar 'danki dake gidan Nan bakijiba kika kwaso jiki da jaririn shege kizomun anan?

To Kinga Hadiza tun kafin Raina ya baci Kuma tum kafin wani yaji tashi ki fice,

Mune mukafi kowa hauka a duniya ne dazamu Baki gurin zaman renon barna......

Rawa hannuwan Hadiza suka fara hankalinta yasake mummunan tashi tana kallon hajiya da idanuwanta jajir tace"

Dan Allah hajiya ki yarda Dani ki fahimceni
Kima kaini a dubani idan ana dubawa wallahi tallahi banyi kowace irin barnaba nasamu cikin Nan,
Wallahi cikin salisu ne......

Wata irin mummunan zabura hajiyar tayi tana kallon Hadiza a gigice sbd mamaki da baqin cikin zancenta Dan ta Gama raina Mata hankali kokuwa dai mahaukaciya ta dauketa?
Amma dai Bari ta tabbatar...kallonta tayi a Rikice tace wane salisun Hadiza?


Muryarta Bata fita sosai sbd shaqewar maqoshi tace"

Salisu baban Abdul....

Kasa magana hajiyar tayi ta rufe idonta daya fara sauyawa sbd tsananin bacin Rai da masifar Rainin da Hadiza tazo dashi Dan haka Bata buqatan ma Jin komai ta nuna Mata hanya tace"

Fice Hadiza kibar gabana Dan Allah.

Dagowa Hadiza tayi ta kalli hajiyar sai alokacin hawaye suka ciko jajayen idanuwanta suka fara gangarowa.

Magana takeson yi Amma zuciyarta tayi nauyi bazata iyaba sai wani irin quntataccen kuka Mai ciwo daya zuwar Mata.

Ganin ba tashi zataiba kada wani yashigo yagantama kokuma yaji haukar datake fada yasa hajiyar Kama hannayenta ta miqar tsaye tareda janta takaita har waje ta Kuma gargadeta akan sake zuwa da wata jaririyar gidan da sunan salisu abakinta.

Kuka sosai Hadiza keyi tanajin wani irin azababben ciwo a zuciyarta,
Jin takeyi kaman zuciyarta zata mutu,

Ganin mutanen dake wucewa sunfara Mata kallon mahaukaciya yasata Jan jiki tabar kofar gidan.

Tafiya kawai takeyi sbd Batasan Inda zataba,

Jin jaririyar tayi baccin wuya itama yasata tsayawa ta goyata taci gaba da tafiya.

Tafiya Mai nisa tayi wadda batamasan tayiba har Saida yamma tayi sosai ta nema bakin wani gidan abinci ta zauna tareda sauke jaririyarta ta saka cikin hijabinta tafara Bata nono.

Kasa Shan nono 'yar tayi sbd tuni ciwon zazzabin wahala ya rufeta sbd ba qaramar Rana sukashaba.

Fara jijjigata tayi tana sake cusa Mata nonon Amma Bata amsaba Dan haka ta maidata ta goya.

Shagon dake gefen gidan abincin ta qarasa ta siyo ruwan roba na sauran canjinta dasuka rage Takoma Inda ta baro ta zauna tasake saukoda 'yar ta bude ruwan ta ringa zubawa a murfin robar tana Bata.

Ruwan ma batasha saidai wasu sun shiga cikinta kadan...

Kuka jaririyar keyi sosai Wanda ya qarasa gigita Hadiza..
Batasan ya zataiba sbd kanta zazzabi da ciwone Mai qarfi a jikinta.

Gabanta radadi yake Mata sbd qarin haihuwa da rashin ruwan zafin gasa gurin ga doguwar tafiya cikin azabar Rana Dan haka itama take a gigice.

Kukan 'yar yasa Dole tabar gurin ganin hankalin jama'a yafara yawa kanta.

Cikin wasu mabarata dake gaba kadan bakin wasu super market taje ta zauna tana sake fama da Yar dake kuka har lokacin.

Nanma bata tsiraba sbd anfara Mata kallon zargi da 'yar
Silalewa tayi tabar gurin kafin ayi Mata dukan Satan 'ya takama hanya taci gaba da tafiya gashi duhun dare yafara Dan har anfito sallar magriba.

Tafiya Mai Dan tsayi takuma Yi taji bazata iyaba sbd radadi da azabar da tsakiyar cinyiyinta ke Mata,

Azabar datakeji tafi Mata naqudar haihuwar datayi sbd gurin ya goge sosai sbd tafiya Dan haka tasamu wasu shaguna da Yan gudun hijira suke ta zauna daga can gefe itama.

Ruwan robar data siyawa yarta itama taciro daqyar ta iya karban kadan ta

Please Login or Register in order to submit comment