gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading FAHIMAH Gaskiyar Da Aka Ɓoye book 1 By Takori Kabara Chapter 10 | ArewaNovels google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

za ta ba shi budurcinta ba alhalin ta san ba ya sonta.

"Sai ya hau lalubawa sako-sako wai ya nemo rashin son nata daga zuciyarsa a daidai wannan tsakanin, inda ya fahimci ya yi decreasing gradually da 50% a lokutan da suka kasance tare a Ikko. Amma ya fi karfin ya yi fyade ga matarsa, ko da hakan na nufin ya koma yin azumin tadauwa i kullum."

"To amma a yau akwai babbar matsala tare da shi da Fahimah bazata gane ba, da ta tausaya"

"masa koda itama bata son nashi, da ta yi don ceto da neman aljannah, azumi kuma sai gobe zai iya daukar sa."

"Cikin dare Fahimah ta ji sanyi na kada ta, sanyin da ba ta san daga inda yake ba. Tashi ta yi ta"

"kashe A.C amma ko da ta koma ta kwanta sai ta ji hakoranta na haduwa da junansu. Cikin abin da bai wuce minti goma ba wani irin zazzafan zazzabi ya rufe ta. Ga mayafin da ta rufa da shi ji ta yi kamar babu shi, ta rasa inda za ta sa kanta da sanyin da ta ke ji, sai kakkarwa ta ke. Ta ga cewa in ta yi shiru ta kuma kwana a haka, to da safe kam gawarta za a kai wa Ammi. Bargo ta ke so ko ta halin kaka don haka ta mike da dafa bango ta shiga dakin da ta baro Uwais da zummar dauko bargo ta dawo."

"Ashe da rabon za ta yi mummunan gani, ganin abun da ya narkar da duk wata soyayyar Uwais daga zuciyarta. Duk wasu emotions ? duk wasu dadaddun mikin soyayya na shekara da shekaru suka ware, suka kama gabansu. Fahimah ta ambaci innalillahi wa inna ilaihi"

"raji un, sannan ta sakar masa kofar da gudu ta juya zuwa falon da ta fito."

"Uwais ya razana, ya kuma ji kunya irin wadda bai taba ji a rayuwarsa ba. A zatonsa ta jima da yin barci, kuma ko ma me ya yi daga ita har Amrah sune masu babban kamasho. Gara ita Amrah a bisa yarjejeniyar da ya aure ta kenan, daga baya ne ya ga ba zai iya ba, ita kuma ta yi kan gaban kanta, amma ita fa? Ita Fahimar fa? Hujjarta ta fi ta Amrah rauni, hujjarta shi ne ba ya sonta, don haka ba za ta ba shi kanta ba, to ko yana sonta ko ba ya sonta yana da wannan hakkin a kanta. Allah ya bashi. Amma ta yi rantsuwa sai ranar da ya furta mata kalmar so ? an gaya mata son kirkirarsa ake yi, ko ana karyarsa???"

"Bai jin sonta, amma a halin yanzu bai jin kiyayyar ta, ya fara sabawa da ita, sannan yanzu abin da ta gani ya sa ya ji nan duniya babu wanda yake jin nauyi da kunya kamarta."

"Wane tsautsayi ya kai shi? Abu ne da bai taba yi ba ko a lokacin samartaka, sai yanzu da ya mallaki matan sunnah har guda biyu?"

"Ya mike yana maida jallabiyar jikinsa, har ya sauko daga gadon da niyyar binta, wata zuciyar ta dakatar da shi. Yanzu ko me zai ce mata zai zamo ihu ne bayan hari, ko ko ta ce borin kunya ne. Wanda a zahiri haka ne. Ka kasa jin kunyar Ubangijinka sai kunyar Fahimah?"

"Komawa ya yi bakin gado ya zauna ya dafe goshinsa da hannun damansa yana fadin, Astagfirullah Ya Allah! Wa'atubu ilaik ?"

"Fahima saboda kidima bandaki ta shige ta kulle kanta. Tuni ta nemi zazzabin da ta ke ji ta rasa,"

"ji ta yi ta tsani Uwais ba ta ko son sake ganinsa. Ba ta san ma anar abin da idonta ya gani ba, amma jikinta ya ba ta ba abu ne mai kyau ba, abu ne na haramci ko daga yadda Uwais ya yi da ya ganta duk da cikin dim-light ne. Kuka ta saki mai sauti, ta kwantar da kai a jikin sink tana ta yi. Kukan da ya je har kunnen Uwais, ya rasa inda zai sa kansa, ba damuwar Fahimah ce damuwarsa ba, a ah, mutuncinsa da girman sa a idanunta."

"A haka suka wayi gari, hasken asuba ya ratso ta tagar toilet din, tana rangaji ta yi alwallah ta fito ta yi sallah, tana idarwa ta yi lullubinta sannan ta shiga inda Uwais yake."

"Yana kwance saman gado, ya dafe goshinsa da hannun damansa. Nadama goma da ishirin ta damesa. Kafafunsa zube a kasa."

"Ya yi nadamar abin da ya yi din a daren jiya, kuma tun jiya yake istighfari, a fili da boye, zuciyar sa na mai sakancewa da cewa Ubangiji ya amshi tubansa, tunda shi Yace ""ku tuba da niyyar bazaku sake komawa izuwa zunubi ba""."

Kallon da Fahimah za ta ke masa shi ne babbar damuwarsa. Dauka zata yi tuntuni rayuwar sa kenan.

"Daga bakin kofa ta tsaya, muryarta ta dushe don kuka har ba ta fita sosai, ta ce."

Ka zo ka maida ni wurin su Ammi ?.

"Ya daga rinannun idanunsa ya dube ta, ta kauda kai. Jin wani abu kamar kibiya ya fito daga idonsa ya shiga nata. Uwais ya taso daga kwanciyar gaba-gadi ya tako ya tsaya a gabanta har tana iya jin hucin sassanyar numfashinsa."

Da ni na kawo ki? Ko ni nace ki biyo ni? Ban ce ki bi Mahdi ku koma ba kika ki? Ban gaya

"miki zuwanki baya amfana min komai ba? Ya tambaya a jere, da wata murya tamkar zai doke ta. Sannan ya sa hannu ya dago habarta."

" You can tell the whole world kin gan ni ina abin da ki ka ga ina yi, amma in mahaifiyata ta ji,"

"na rantse sai na sauya miki kamanni, yadda in na sake ki ba wanda zai yarda ya kwashe ki, don ba za ki ganu ba wallahi Fahhimah ?."

"Fahimah ba ta san sanda ta buge hannun Uwais daga habarta ba, duk wani shayinsa da ta ke ji ada, ai yanzu babu shi, ya gama bata rawarsa da tsalle a idanunta, ta ce,"

" To ka sakenin mana, sai me in ka sake ni? Sai aka ce bazan rayu ba ko a gidan mu na"

"marayu ne? Menene a auren naka banda bakin-ciki? An gaya maka ko ba ka sake ni ba akwai sauran zama a tsakanin mu? Allah ya tsare ni, wallahi ko Ammi za ta min baki yaya Uwais na gama auren ka. I never know this is your habit, Amrahn ma na tabbata bata sani ba wallahi da bazata aure ka ba ?."

Ta saki kukan da ya taho tun daga kololuwar zuciyar ta. Ita kuma kalolin kaddararta ke nan? Daga wannan sai waccan? Uwais da ta bai wa dukkan so da kauna ashe haka yake? Sabon Allah kiri-kiri da aurensa da komai? So ta ke ta gane ko matsayinsa da soyayyarsa sun ragu a zuciyarta a dalilin hakan?

"Ba raguwa kadai ba, komai ya zagwanye hatta shakkarsa da ta ke ji ta kau (istimna'i yana daukewa mai yin sa kwarjini, yana sabbaba illoli ga lafiya da yawa sannan haramun ne a addinance)."

"Uwais ya yarfa hannuwa ya ce, Well, ki gaya ma Ammi ga abin da ki ka ga ina yi, ni ma in"

gaya mata cewa kin yi rantsuwa da ki hada jiki da ni gara kin mutu. Ni ma na mutu kowa ya huta....

"A dalilin ba ni da mafita ne kuma na fita a tunanina, na nema wa kaina relief, amma ko ki yarda ko kada ki yarda ban taba yi ba sai jiyan, kuma inda wanda ya sanya ni a wannan halin to ba wata ba ce, ke ce Fahhimah ?."

"Yana gama fadin hakan ya yi dialling number din Mahdi. Mahdi ya ga kira da sassafiyar Allah, sai ya dauka ba lafiya ba."

"Yana dagawa ya ce, Please Mahdi come and take me to airport, and take this girl to Ammi,"

"ka gaya mata zan kira ta a waya, wani muhimmin uzuri ya taso min a ofis ?. Mahdi ya amsa da, To ga shi nan ?."

"Har zuwa wannan lokacin Fahimah na tsaye a inda Uwais ya barta kamar mutum-mutuma, tana"

mai tauna kalaman Uwais a bisa ma auni na hankali da tunaninta.

"Ba'a fi minti goma ba da kiran wayar Mahdi ya kira shi, cewa yana reception sannan ya gaya wa Ammi batun tafiyarsa ta ce, lallai ya biya da su wajenta kafin ya tafi."

"Cikin takaici Uwais yake dubansa, Me ya sa ka yi min wannan karambanin Mahdi? ? Mahdi ya ce, Ta ya ya ba zan yi ba? Ka zo da niyyar yin kwana uku, washegari ka ce za ka"

"tafi, don kawai matarka ta bata maka rai, sai in kyale ka ka bar kasar ba tare da sanin Ammi ba? Don ta ce da hadin bakina ko? ?"

"Tsaki ya yi cikin haushin Mahdi, sannan ya wuce gaba, Fahima ba ta yi wata-wata ba, ta rufa"

masa baya harda gudu-gudunta. Fatanta kawai ta bude ido ta ganta gaban Ammi ba tare da

Yaya Uwais ba. Ta tsane shi yanzu kam ba ta ko son ganinsa. Allah wadaran soyayyar.

"Ammi ta tsura musu ido suna sunkuye a gabanta, kowanne fuska ba walwala, da alama Fahimah kuka ta ci ta koshi. Sai ta ji duk farin cikin da ta ke ciki ya koma. Ta dubi Uwais da idanun rahma, ta ce."

" Me ya faru za ka tafi unexpected kuma ba tare da Fahimah ba, ka san ba zai yiwu ta yi har"

"sati biyu a nan ba saboda makaranta, kuma na yi zaton kwana uku aka ba ka? ? Uwais ya ce, Ammi ba abin da ya faru, aiki ne kawai ya taso min ?."

"Ta dubi Fahima, Ke ma ba za ki gaya min ba? Kukan me ki ke yi? In laifi ya yi miki ki gaya"

min kin san ba zan kyale shi ba ?.

"Da kyar Fahimah ta motsa bakinta, ta ce, Ba abin da ya yi min Ammi ?. Tana kallon yadda Uwais ya saki wata boyayyar ajiyar zuciya."

"Haushi ya kama Ammi, ta ce, To tunda haka ne, ku yi ta rikon bacin ranku a ranku, amma ba inda za ku je sai kun yi kwanakin da ku ka zo da niyyar yi, kun zaga dangi kowa ya ganku."

Uwais ina gaya maka ina kara gaya maka Fahimah amanar Allah ce a hannunmu in ka cutar da ita Allah ba zai barka ba ?.

"Uwais bai san sanda ya katse ta ba, In kuma ita ta ke cutar da ni fa? Ita sai Allah ya barta?"

"Ammi na yi kokari na tausa zuciyata na karbi amanarki ko da bana jin sonta a raina, amma ita tana neman halakar da ni, don haka Ammi ki daina jin tausayin Fah-himah don kuwa ba abun tausayi ba ce, muguwa ce ?."

"9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Ammi ta kusa yin dariya don tuni ta je gano ga matsalar tasu. Ta dade da sanin wannan cewa; Uwais irin mahaifinsa ne, in haka ne kuwa ba za ta sha wahalar sanya Fahimah a zuciyarsa ba, wuyarta mu'amalar aure ya gitta a tsakaninsu."

"Ammi ta gyara zama tana murmushi, ta ce, In dai ka hakura da tafiyar a yau, to ka je ku ci"

gaba da karbar gaisuwa. Ni kuma zan yi magana da Fahimah ?.

"Ya tashi ya fice ba tare da ya ce komai ba, sai ma kafar Fahimah da ya kusa takewa, Ammi ta bi shi da kallo tana ajiyar zuciya."

"Uwais na bada baya, Ammi ta ce."

" Yo ke Fahimah, an gaya miki ana hana miji wannan ne a zauna lafiya? It's the greatest"

"weakness of men, sannan hanya mafi sauki ta shigewa sukuf zuciyarsu. Ni dai a matsayin uwa nake miki magana ba suruka ba. Don ni ke na haifa ba Uwais ba ?."

"Idanun Fahimah suka cicciko da hawaye, amma ga mamakinta ji ta yi ko za a dora mata wuka a makoshi ba za ta iya fada wa Ammi ko wani daban abin da ta kama Uwais yana yi ba, which means har yanzu da dan sauran burbushin son, no matter laifukansa a rayuwa. Kuma ai yace ya tuba, bai taba yi ba, na jiyan ma itace sila. Ita ta ja, tunda ta hana shi abinda Allah ya halatta a gare shi. Ba kuma kowanne dan adam ne mai iya tsallake hudubar shaidan a irin wadannan lokutan ba. Maimakon tace komai, sai ta saki kukan da ke cin ranta. Ta kifa kai a cinyoyin Ammi."

Ammi ta janyo ta jikinta ta rungume ta.

" Ammi he keeps on telling me cewa ba ya sona, ta ya ya zan iya sakin jiki da shi? Kalmar"

tana kona min rai Ammi yadda ba kya zato ?.

"Ammi na shafa bayanta cikin lallashi, ta ce,"

" Let him say it... let him say it loudly to the whole world ba ke kadai ba, sai ya gama fada zai kore zafin kiyayyar daga zuciyar sa. Kada ki damu da wannan, tunda har mun samu cewa yana son physical relationship (gamayyar jiki) ya shiga tsakanin ku."

"Wannan ma ba ya zuwa sai da so Fahimah, ki kyale shi ya yi ta fada, watarana da kansa zai janyeta da gwiwoyi a kasa, ko mumbari zai hau yana fadi ba ya son naki ya je ya yi, amma ki barshi ya dabbaqa sunnarsa, sauran ki bar wa Allah ki kuma zuba ido ki sha kallo."

"Allah fa na sonki da Uwais, shi ya sa ya kautar da hankalin matarsa daga kansa ta nisance shi,da tana nan bazamu taba samun kansa haka ba, don haka Fahimah yanzu lokacinki ne kada ki yi wasa da damarki don sau daya ta ke zuwa a rayuwa kin ji ko? ?"

Fahimah ta gyada kai.

"Ammi ta ce, To tashi mu je mu karya kumallo, na tabbata ba ku ci komai ba ku ka fito. Shi ma zan sa a kai masa nasa yanzu ?."

"Ba su kara haduwa da Uwais ba sai da daddare, ya shigo a gajiye ya yi wa Ammi sallama cewa zai wuce masauki. Ko da abin da ta ke so? Ammi ta yi murmushi ta ce, Tunda ka fasa tafiyar ka ji maganata na gode Uwais, Fahimah tashi ku je, Allah ya ba mu alkhairi ?."

"Fahimah ta yi kicin-kicin da fuska daidai lokacin da Uwais ya dago suka hada ido, harara ya"

"sakar mata, ba ta bata lokaci ba ta rama, sannan ta mike don Ammi ta sake maimaita umarninta."

"Suna tafe a hanya Mahdi ke tuki ba wanda ya kula dan uwansa, sai wakokin (Sudanese singers) da ke tashi a cikin motar cikin harshen larabci ta shahararren mawaki Mahmoud Abdul Aziz. Suna isowa Fundaq Mahdi ya ajiye su ya juya, Uwais sai da ya tsaya a reception ya karbi mukullin sannan suka haura ta lifter zuwa dakinsu."

"Tunda suka shiga dakin bai kula Fahimah ba, ita ma ta kama kanta ba ta shiga sha aninsa ba, amma ta ki barin dakin da yake a kan dalilin da bata sani ba. Mafi rinjaye na zuciyarta ya fi raja a a kan ba za ta kara nesanta kanta da shi ba, ko da kuwa ba za su hada shimfida ba. ""Yaa Allah! May not evil did come again to my husband""."

(Addu'ar Fahimah a zuci ga Uwais).

"Filo ta dauka ta jefa bisa kafet ta kwanta. Uwais yayi duk abin da ya saba yi kafin ya kwanta, sannan ya yi changing zuwa Pajamas ruwan toka, ya yi niyyar kiran Amrah kuma sai ya fasa don har zuwa yanzu ba su shirya can-can ba, ita ke nacin kiransa tana ba shi hakuri yana gasa mata bakaken maganganu ta cikin ruwan sanyi, kuma dai bai son yana kiranta gaban Fahimah a kan dalilin da bai sani ba."

"Amma sai ga nata kiran ya shigo. Da farko kamar ba zai dauka ba, don ya gama shirin kwanciya, ko me ya tuna sai kuma ya dauka."

Habib-Qalby I m missing you terribly ?.

"Ya kyabe baki, ya ce, Amrah how dare you want me to believe this? ?"

"Ta ce, Ka yarda da ni Allah kewar ka nake yi ba 'yar kadan ba. Yanzu haka ga ni nan a cikin jirgi na taho in yi surprising din ka, zuwa asubah zan sauka a Kano, I will stay with you for two weeks ?.. ?."

"Idanunsa suka firfito waje, yana duban center din da Fahimah ta ke, ya ce, Stop joking"

Amrah ?! ?.

" Believe me, I m not kidding Habiby, amma Daddy bai san na taho ba. Don Allah ko Yaya jabeer kada ka gaya wa na zo ?."

"Har ransa ya ji dadi, don ta nuna ta yi nadamar abinda tayi masa, amma sai ya ce,"

" Amrah currently bana Nigeria, ina kasarmu Sudan, Yayan Ammi ya rasu. Amma in kin sauka ki jira ni nan da kwana uku zan iso ?."

"Amrah ta ce, Kai ma ka san tsoro na bai bari na in iya zama a gidan ni kadai. Allah Ya masa rahma ?."

" Hakuri za ki yi Amrah, I ll make sure na dawo in two days. You know how much I missed you baby ?."

"Wani mikakken tsaki Fahimah ta saki, wanda ya sa Uwais saurin toshe wayarsa, gaba daya ma sai ya kashe wayar cike da fargabar ko Amrah ta ji? Tashi ya yi ya kunna wutar dakina fusace, dakin ya gauraye da haske."

Wa ki ke ma tsaki? ?

"Daga kwancen da ta ke ta murguda baki, ta ce, Da wanda ya tsargu da shi nake ?."

"Uwais ya sanya hannu ya dauke mayafin da ta rufa da shi, ya ce, Fahimah ki ke ko Fahummah? You better be careful da ni don a fuska ne nake da kyau, idan ki ka shiga hannuna za ki san na fi ki rashin tausayi."

It s my old principle that I will never rape my wife amma da tuni na goge rainin da na lura ya samu matsugunni tsakanin mu ?.

"Fahimah ta mike zaune ta dubi Uwais cikin ido da hasken lantarkin da ya haska kyakkyawar fuskarsa, ta zama tamkar an kara masa hasken fata, ta ce,"

Raini na nawa kuma Yaya Uwais? Ni da na ganka kana ?.. ?.

"Ai ba ta karasa ba ta ji ta kane-kane a jikin Uwais, jikinsa rawa yake sosai with utmost regret to the fullest, a lokacin da yake magana harda taruwar hawaye cikin fararen kwayar idanun sa,"

" Believe me Fah-himah ban taba yi ba, you caused it all, and I repented to Almighty Allah,"

jiki na kuma na bani ya yafe mini. Shi mai afuwa ne mai jin kan bayin Sa. Ya kike so inyi? So ki ke in halaka? A kan me ki ke so in gaya miki kalmar da ban shirya fada ba? A lokacin da ban shirya mata ba?

"Ki ba ni lokaci mana? Ki yarda ba abin da lokaci ba ya canzawa a rayuwar dan adam, kamar yadda Ammi ta ce."

"Fahimah I hate you before, ba don kalar fata ko zubin halitta ba; bana son kowa ya rabi Ammina, infact kishi ne da ni mai tsanani tun ina yaro, so nake Ammi ta zauna da ni ni kadai, tayi ta so na nikadai, amma ba don abin da ki ke tunani ba."

"A dan zamanmu tare a Lagos, sai na samu al amura da yawa suka sauya min a kanki Fah-himah. Ganewa da na yi cewa ke din; you re extraordinarily different da sauran mata,"

"with exceptional qualities ababen so ga duk namijin da ya san ciwon kansa ? Ina kara rokon ki bani lokaci, kada ki tursasa ni wajen furta abin da ba ni da iko a kansa ?."

"Fahimah ta kwanta shiruu! A jikin Yaya Uwais, tana jin wani irin dadi mara misaltuwa a zuciyarta da ba ta taba jin kwatankwacinsa a rayuwarta ba. Kalaman sa sun gama ratsa ta. Ta kasa cewa komai, ta kuma kasa ko da kwakkwaran motsi sabida yadda kalaman Uwais da zurfin muryarshi"

ke ratsa ta. Uwais ya yi amfani da wannan damar ?

"It was kind of gentle romance wanda ya gigita duniyar Fahimah Shagari, ta kara dulmiyewa a kaunar Uwais yau, har fiye da tarin shekarun da ta kwashe cikin koshin wahala....."

"And it started from there ? tafi ? tafi har tsayuwa ta gagare su. Abu na karshe da Fahimah ta fahimta shi ne, daukarta da Uwais ya yi kacokam a hannun sa. Sauran al amuran da suka biyo baya masu tsauri da girma ne da suka shallake tunanin su ? A lokacin da Uwais ya maida Fahimah a layin sauran mata, kuka ta saki mai sauti tana kiran sunan Ammi, kai har"

"Baba Talatu yau ta sha kira, tunda su kadai ta ke da su a duniya."

****

"Lokacin da Uwais ya samu nutsuwar da yake matukar son samu kwana da kwanaki, wata da watanni, bai juya mata baya ba, rungume Fahimah ya yi a tsakiyar kirjinsa, yana tambayar kansa was all these not LOVE? Idan ba shi ba ne, mene ne? To ko ma dai ya ya ne ko so ne ko ba so ba ne, shi da Fahimah yau sun zama daya. Duk wani kurarinsa da challenges dinsa a kan Fahimah ya neme su ya rasa, irin matan nan ne da ake kira one in million da sai namiji mai matukar sa a a rayuwa ke sa'ar mallakar su. (Never judge a woman by her skin colour). Inji Uwais Shagari."

"Uwais yake fadawa kansa. Ya ke kuma fadawa sauran maza 'yan uwansa, masu ra'ayi da akida irin tasa."

"Har aka yi kiran assalatu Uwais tunanin da yake kenan, yana rungume da Fahimah, yayin da Fahimah ta yi kukanta ta gaji, barci ya dauke ta."

"Wani irin barci na kwanciyar hankali. Soyayyar shekara da shekaru da ta ke yi wa Uwais yau ta sarrafa kanta ta bada cikakkiyar ma ana, ma anar da daga ita har Uwais, babu wanda ya tsammaci girmanta ya kai hakan....fadinta ya kai hakan.... Tasirinta zai kai hakan haka karfinta"

da zurfinta ya kai har haka !!!

*****

WASHEGARI

"Har karfe goma sun kasa fitowa zuwa gidan gaisuwa, duk da Mahdi ya zo daukarsu sai komawa ya yi, don Uwais ya ce da shi Fahimah ba ta jin dadi ya je ya dawo wajen azahar lokacin ta ji sauki don ta sha magani yanzu ta kwanta."

"Da gaske barcin ta ke tun wayewar gari bayan ya taimaka mata ta yi wanka, ta yi sallah ta sha tea. Shi kuma ya koma kan study table daga shi sai singlet da wando three quarter ya kunna loptop dinsa ya soma rage ayyukansa na ofis."

"Daidai lokacin da kiran Amrah ya shigo, sai da ya saci kallon Fahimah ya tabbatar barci ta ke"

sadidan sannan ya amsa.

" Habiby na sauka a Kano, luckly Yaya Jabeer ba ya gari, don haka ina wajen Aunty Murja, in"

ka iso sai ka zo ka dauke ni ?.

"Ga mamakin Uwais Shagari, duk dokinsa na son ganin Amrah da son kasancewa da ita ya yi decreasing 50% fiye da tsammaninsa. Daren jiya ya samu wata irin gamsuwa a auratayya da bai taba samu ba. Ya kuma gane kyawun fuska ko kalar fata ba shi ne mace ba, matan alfarma daban suke. Daban Ubangiji ke halittar su kawai, don ya baiwa namiji mai tsananin sa'a irin sa. Shi ya san he's among the luckiest cikin mutanen duniya daga kwanaki bakwai a baya zuwa yau."

" Alright Amrah, see you soon ?."

"Abin da ya ce da ita ke nan, sannan ba tare da ya kara cewa komai ba ya kashe wayarsa. Amrah ta yi sakatoto da waya a hannu, lokacin da Aunty Murja ta iso wajen ta sameta, ta mika mata kofin da ke hannunta mai dauke da tatacciyar madarar shanu mai sanyi (fresh milk)."

"Murjanatu ta ce, Lafiya dai Amrah? ?"

"Amrah ta yi rau-rau da ido, idanunta cike da hawaye ta dubi Murjanatu, ta ce, Aunty Murjaj, ni Uwais

Please Login or Register in order to submit comment