gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Zafin Rana Complete Hausa Novel by Aishat Alto Chapter 5 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin tausayawa ta zauna a gefen sa tace  Junaid!

"Shiru yai yana kallanta yana san jin abinda ke faruwa, hawaye ne suka zubo mata ta gogesu tace"

 kasan kullum dakai nake kwana nake tashi? Amma Junaid kana ganina kaki sanar dani kai wanene?

"Abinda ke bakinsa ya hadiya, kallanta yai kamar zaiyi magana ya fasa, mikewa ya shiga kokarin yi"

yana cewa  ni zan wuce ni da Binta.

Hankali a tashi ta mike tace  Junaid zaka koma ina?

Kallanta yai yace  yanda kike rayuwarki hankalinki a kwance nima a can hankalina a kwance

"yake, tunda kin gani na ganki zan koma. "

Da sauri tace  kana tunanin zan barka ka koma wani gun? Junaid? Baka tausayin mahaifiyar

data rasa danta tun baigama wayau ba? Shekarata nawa rabona dakai? Ka rasa abinda zakacemin

sai zaka tafi?

"Juyowa yai ya kalleta, zuciyarsa ce ta karaya, shi kanshi yana kewar mahaifiyarsa amma gani yake"

kamar mantawa sukai dashi.

"Karasowa tai inda yake tace  ka koma ka huta na sa akira wanzami ya dubaka, Junaid bansan"

"meke yawo a ranka ba anma ni mahaifiyarka ce, babu uwar dazata ajiye danta a wani gun tai"

rayuwar datakeso.

"Shiru yai baice komai ba, ganin haka yasa tace  kana san wani abu ne? "

Kai ya girgiza alamar a a yace  Binta tana ina?

Kallansa tai tace  Junaid 

Sai kuma tai shiru tace  ka huta inka tashi sai a kirata.

Kai ya jinjina sannan yace  ina bandaki?

Nuna mai tai da sauri sannan tace  nasa a kawo ma kaya.

"Kaya? Ya tambaya cikin mamaki, tace  eh na tura gun masu dinkin mu na masarauta, nasan"

baza a rasa wanda suka ma Zubair ba.

"Baice komai ba dan baisan ma me zaice ba, juyawa tai ta fita, zama yai a bakin gado yai shiru"

"yana tunanin wannan lamari, wai meya faru ne daga sanda aka kulleshi?"

"Azeema ce ta turo kofa dauke da kaya, mika mai tana cewa  me kake tunani? "

"Shiru yai yana kallanta, murmushi ta saki tace  inada abubuwa dayawa danake san tambayarka"

sai dai ganin yanayin da kake ciki yasa nake jurewa.

"Yanzu kam shima murmushin yai, tace  Junaid! "

"Kallanta yai tace  Nagode daka jure abinda ya faru,nagode wa Allah daya barmin kai da rai. "

"Tausayinta ne ya kamashi, juyawa tai da sauri tabar dakin."

"Junaid ya dafa kansa, lalai bai kyauta ba da yake jin zafin mahaifiyarsa bayan abar tausayi ce."

"Mikewa yai jikinshi duk ba karfi, wanka yai tare da alwala sannan ya fito, kayan ya saka sannan"

ya tada sallah.

"Bari ce ta kwankwasa jin shiru yasa ta koma, kara dawowa tai ta kwankwasa Junaid ya bata izinin"

shigowa.

"Abinci ta shiga jerawa a kan karamin carpet din dake dakin, haka tai ta shigowa dashi tana"

"jerawa, data ajiye na karshen ne ta zube a kasa tace  yarina barka da dawowa. "

Kallanta yai yace  ina Binta?

"Tana dakinmu, taci abinci ne?"

"Cikin mamaki ta kalleshi, tace an kai mata."

Ki duba nasan bata fara ci ba kice mata ta dawo nan.

"Cikin tsananin mamaki ta kalleshi, shima kallanta yai yace  da wani abin ne? "

Da sauri tace  a a

Mikewa tai ta fito kilisar Gimbiya Azeema wacce ke bada sako akan a sanar wa Safiyah halin da

ake ciki.

Gaba daya Azeema ta kasa zama sai ake take gun yan uwanta na kusa dana nesa.

Bari ce ta matso kusa da ita ta sanar da ita abinda Yarima yace  shiru tai cikin rashin jin dadin

zancen tace  kice taje

Da sauri Barira ta kalleta tace  Gimbiya.

"Azeema ta juyo ta kalleta tace  ki bar Junaid yai duk abinda yake so, ni zan san abin yi. "

Barira ta jinjina kai sannan tai dakinsu.

"Kamar kuwa ya sani tana zaune sai jujuya abincin take taki ci, Barira ta sanar da ita sakon Yarima"

da sauri ta mike ta dau kwanan tai dakin.

"Barira ta bita da kallo, cikin takaici."

**********

"Hajjo kam sai matse hannayenta takeyi daga zaune, tabbas gaggarumin matsala na neman"

afkowa a tare da ita.

Zeenatu wacce ke zaune itama tayi shiru tana tunanin abinda ke faruwa.

Zubair ne ya daure yace  wai da gaske yaran nan ne Junaid?

"Hajjo tace  da gaske wlh, yanzu ya zamuyi? Dan wlh akwai gagarumin matsala. "

"Zeenatu ta kalla wacce tai shiru kafin wani murmushi ya bayyana a fuskarta, Hajjo cikin mamaki"

tace  ke kuma fa?

Zeenatu ta kalli Hajjo da sauri tace  ya akai bamu gane ba Hajjo? Yaran nan wlh sam baiyi kama

"da bawa ba, ko daga yanayin maganarsa zakasan jininmu ne, ya akai idanunmu ya rufe? "

Ran Hajjo ya baci tace  to ke yanzu ana zancen abinda zai biyo nan gaba wato ke abinda ya faru

a baya kike maimaitawa?

Zeenatu ta sake murmusawa tace  abin ne abin birg 

Uban hararar da Hajjo ta maka mata ne yasa ta kalli Zubair tace  yaya wai meye na damuwa?

Milkin nan fa kowa yasan naka ne meye na wani tada hankali?

Zubair ya kalleta yace  kinba Sulaiman din hakuri?

Tace  kai yaya ana cikin wannan yanayi wake zancen wani Sulaiman?

Hajjo tai dan tsaki tace  aiki Fure ta kiramin Ramlatu.

"Nan Zeenatu ta mike, Hajjo ta kalli Zubair tace  Zubairu karka kuskura adan tsakankanin nan kai"

"laifi, kabi kowa a sannu, kai luf kamar baka nan kafin na samo mafita, dan wallahi barin yaran nan"

daidai yake da ajiye matsayinka.

Zubair ya kalleta yace  Hajjo kisan yanda za ai.

"Tace  karka damu, in ta gama rama abinda aka ma danta sai musan abinda zamuyi. "

Yace  kina nufin sai ta rama?

"Hajjo tai wata dariya tace  bakasan Azeema bane, ita a tarihinta bata barin ta kwana ko a mutu"

ko ai rai amma sai ta fanshe.

Zubair yai shiru yana tunani.

*****

"Suna cin abinci yana tambayeta abubuwan da suka faru tana fadamai, ko mai ya bude sai ya turo"

gabanta yace  binta ga kaza kin taba ci kuwa?

"Dariya tai tace  Ya Junaid nifa bamu shirya bama wlh, ka taho ka barni. "

"Ahhhh ya rike ciki wai ciwo,"

Hankalinta a tashe ta kalleshi tace  Ya Junaid?

Ganin yanda ta rikice yasa ya saki dariya yana cewa  yanzu mun shirya?

Hade rai tai tace  Ya Junaid.

Tai maganar cikin shagwaba.

Azeema dake jikin kofa rike da kofar ta kalli Wanzamin dake gefe kansa a kasa tace  ko zaka bari

sai anjima?

"Yace to ya juya tare da mata sallama, shiru tai tana tunanin wannan yarinyar, itafa danta bazai"

"zauna yana biyewa yarinyar nan cikin masarautar nan ba, wanda tasan yanzu idan kowa kansa zai"

koma.

*Ayusher*

"Dan Allah ku daina min sharing din littafi, ina iya bakin kokarina na ganin an zauna lafiya da kowa,"

dan Allah wannan littafin na kudi ne ku daina yadamin shi.

Nagode

*ZAFIN RANA*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*NA Ayusher Muhd*

Shafi na Goma sha Uku.

"Haka sukai ta hirar su kamar ba wata matsala a gabansu, wanda hakan ba karamin batama"

"Azeema rai ba, zama tai a kilisarta tai shiru tare da zubawa kofar ido."

Barira ta sunkuyo tace  Gimbiya haka zamu barsu?

Kallanta tai tace  kinsa a gyara bangaren Yarima?

"Tace  eh na tabbatar ma sun gama, badai tare zaki bar  "

Wani banzan kallo data mata ne yasa ta yin gum da bakinta.

Azeema ta mike ta shiga dakin.

"Suna dariya suna ganin ta sukai shiru, Junaid ya kalleta, Binta kam saurin mekewa tai tsaye ta ja"

baya.

"Azeema ta kalleta tace  Gashi ganinki yasa Junaid ya ware, angode. "

Binta tai kasa dakai tana kallansa.

Murmushi ya sakar mata.

Azeema ta zauna a bakin gado tace  Junaid!

"Yanda ta kira sunan nashi ne ya sa shi kallanta bayan ya amsa, tace  an gyara maka ban garenka,"

"zamuje yanzu ma kaika, dan gobe za ai taron murnar dawowarka."

Ta danyi ajiyar zuciya sannan ga cigaba  Sai dai inaso kai da Binta ku rage nuna mu amalar ku

cikin jama a.

"Kallan Binta tai sannan ta kalli Junaid, Binta!"

"Junaid ya kirata, nan bamu guri ya fada yana kallan Azeema."

Binta ta mike tai waje.

"Azeema ta kalleshi tace  Junaid kai yarima garin nan ne, idan kowa akanka yake, me kake"

tunanin za ace in aka ganka da mace budurwa?

Junaid yace  menene damuwata akan abinda zasuce? Binta kanwa tace wacce na taso tare da

"ita a lokacin da banda kowa, ban fahimci dalilin da zaisa na ja baya da ita ba dan yanzu na zama"

wani abin.

"Azeema tai murmushi tace  ba haka nake nufi ba, in kana cikin mutane ne sannan Junaid ko ba"

dan kai ba ko dan ita ya kamata saboda inba haka ba mutane zasu takura mata.

"Shiru yai bai ce komai ba, tace  ka barta anan sai su dinga kwana da su Barira in yaso da safe sai"

ta dinga zuwa.

Junaid ya kalleta da sauri tace badai tunani kake ku zauna tare ba?

Yace  me zai haka? Bayan haka muka taso?

Tai shiru kafin tace  Junaid kayi hakuri ka barta anan.

Kamar zai sake magana sai kuma yaga kamar bai dace haduwarsa ta farko da mahaifiyarsa ba ya

dinga bijire mata haka ba. Shikenan.

Azeema tace  Nagode Junaid Nagode.

 Ga amanar Binta nan.

"Tace  ni na taho maka da ita karka damu zan kula da ita, sannan Azi da Hari da ragowar bayin"

da mukace su taho sun iso su suka gyara ma bangarenka.

"Cikin jin dadi ya kalleta, tace  Junaid! "

Naam

" Kai jinin mai Martaba ne karka yadda wani ya kawo ma raini, sannan duk wanda ya nemi yima"

zancen banza. 

Sai kuma tai shiru ganin kamar bayasan maganar duba da yanayin da fuskarsa tai.

Murmushi tai tace  Junaid yaushe zaka ban labarin rayuwar dakai.

" Ba wani labari, mun daiyi rayuwar mu tundaga yarinta har kawo yanzu. "

Kai ta jinjina tace  Alhamdulila.

"Shiru suka danyi saboda rashin sabon dake tsakaninsu, kafin yace  meye dalilin sarki na kaini"

can?

"Kallansa tai da sauri saboda batai tunanin tambayar ba, tace  bansani ba wlh, sai dai nasan"

yayi hakane dan hankalin ka ya kwanta.

" Bawai ina inajin haushi bane, sai dai haryanzu ina ganin akwai dalili bayan waccan. "

Shiru Azeema tai jin kalamansa yasa itama ta fara tunanin tabbas dan kawai Junaid yai rayuwa

"hankali a kwance bazai zama dalilin da zaisa ya dauke danta bada saninta ba ya boyeshi, tabbas akwai wani abin kenan? To menene?"

Junaid ne ya kalleta yace  karki damu nayi maganarne ba tare da nazari ba.

Murmushi tai cikin jin dadi a kalla yana da dogon nazarin da akesan mai mulki ya kasance dashi.

Mikewa yai yace  Su Harin suna ina?

Tace  bari nazo muje.

"Dakin huta, ta mikr tana cewa muje na fara nunama hanya."

"Nan suka fito, Binta bata gun hakan yasa yace  Binta fa? Barira tace  ta shiga bandaki. "

Yace  bari na jira ta fito.

Azeema ta kalleshi tace  muje Junaid in ta fito sai Barira ta kawota.

Ya kalli Barira wacce tai saurin cewa zan fada mata inta fito.

"Nan suka nufi waje, a hanya sai kallan Junaid ake ana gaisheshi, Suna kokarin yin kwanar dazata"

sadasu da bangaren Junaid ne sukaji ance  Barka da Yamma.

"Juyowa Azeema tai, ta hade fuska tsam tare da binta da kallo, Zeena ta karaso fuska a sake,"

Junaid kam ganin ba dashi ake ba bai ko juyo ba.

Zeena tace  Nazo bada hakuri naga zaku fita.

Azeema tace  hakuri? Laifin me kikai?

Tace  Tuba nake na yi abinda na bata miki rai.

"Azeema ta juya batace komai ba, dan bataji zata hakura tabbas sai ta fanshe."

Zeena ta bi bayanta tana kallan Junaid tace  Yarima kayi hakuri bansan kai wanene ba lokacin.

"Juyowa yai ya kalleta, tsayawa tai tare da kura mai ido, maida kansa yai hanya baice mata komai"

ba.

Shiru tai bata kara daga kafarta ba wanda hakan yasa du Azeema sukai gaba.

Fure ce tace  Gimbiya menene?

"Zeena ta kalleta da sauri sannan ta kalli gun da su Junaid suke, haushi ya kamata tace  uban me"

kike da har suka wuce mu?

Fure tace  tuba nake Gimbiya.

Takaici ya kamata tace  meye ma amfanin fitowar? Ko so kike na bisu kamar jela?

Fure tace  tuba nake Gimbiya.

Cikin takaici ta juya ta koma bangaren Hajjo.

Azeema kam wani irin dadi ne ya kamara dataga kallan da Junaid ya mata wanda ta san hakan

ne ya tsorata ta tabbas jinin sarautar na nan na yawo a jikinsa.

Yana shiga ya hango Azi na gyra harabar waje.

"Azi na ganshi ya matso cikin tsananin jin dadi, kasa yai da kansa yace  Yarima. "

Junaid ya kalleshi cikin jin dadi yace  Azi kunzo lafiya?

Azi yai saurin zubewa a kasa yace  tuba nake yarima na barka cikin wani hali.

"Junaid yai murmushi yace  nina umarceka ka barni ai, ina su Hari? "

Suna ciki hala dan da suna nan.

"Kai ya jinjina sannan suka shiga ciki, yanda aka gyara gun me gashi kato sosai ya birgeshi."

"Azeema tace  Junaid nan asali da bangaren Mai Martaba ne, anan mahaifinka ya zauna, sai dai"

shekaru biyar da suka wuce aka kara fadada masarautar wanda aka sakema Takawa wani ginin

"shine ya tashi, dazu ya turo akan abude maka. "

Junaid ya kalleta yace  amma hakan ba matsala?

Tace  ba wani matsala tunda umarnin Sarki ne.

"Junaid ya jinjina kai alamar gamsuwa yana kara kallan gun, Azeema ta shiga nununamai yanda"

gun yake.

***

Zeena hartaje zata shiga bangaren Hajjo ta kalli Fure tace  Fure ni me zasuje yi bangaren Takawa na da?

"Fure tai shiru, Zeena tace  kin fadamin ko kuwa?"

Fure tai kasa dakai tace  Sarki ya bar ma Junaid.

Ido ta zaro tace  mene?

Kallan Fure ta karayi tace  Hajjo ta sani?

Fure ta girgiza kai alamar a a.

Zeenatu tace mu koma bangarena baza a huce a kaina ba.

*******

"Da sauri Binta ta shigo, sannan ta kalli Kuyangar data jata wai akan an aiketa, Barira ta kalleta"

tace  kun dawo?

Binta tace eh tana kallan bangaren Junaid.

Barira tace  kije ki huta shima ya tafi bangarensa saboda ya gaji wai yana san hutawa.

Binta tai shiru cikin rashin jin dadin ya tafi ya barta ta shiga ciki.

*******

Azeema ta dade acan kafin ta fito ita da kuyanginta.

Junaid ya kalli Hari yace  Hari haryanzu Binta bata karaso ba?

Tace  Yarima!

Itakam Hari girma duk ya fara zuwa mata ta kuma san zamansa da Binta bazai yiwu yanda yake

"tunani na, sai dai batasan me xatace mai ba."

"Junaid ya kalleta yace  Hari ki tura a dubo, dan tazo taga nan. "

Hari tace to Yarima ta fito.

"Shiru tai tare da kallan Azi wanda shima kallanta yake, su sun san yanzu Junaid zai san me ake nufi"

"da sarauta, ilolinta, matsaloli da kums kalubalen dazai fuskanta....."

*********

*ZAFIN RANA*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*NA Ayusher Muhd*

Shafi na Goma sha Hudu

"Har bayan sallar isha i Junaid baiga Binta tazo ba, ga abincin dare an jera mai amma baibi"

"takansu ba, hankalinsa ne ya tashi, fitowa yai ya kalli Kuyangun dake tsaye bakin kofa ya kalli ta"

farkon yace  Ina Hari?

"Tace tana daki, yace  kinsan bangaren Umma? "

Tace  Gimbiya Azeema?

"Yace  eh, kije kice ma Binta tazo. "

Tace  to Yarima sannan ta juya.

********

"Binta zaune a gaban Azeema, Azeema cikin sakin fuska tace  Binta nasan kin damu da Junaid"

"sannan kin shaku dashi ta yanda bama zato a lokacin da bashida kowa sai ke, sai dai ina neman"

alfarma daya daga gurin ki.

"Binta ta kalleta kadan sannan ta maida kanta kasa, Azeema tace  dan Allah ki dan janye daga"

Junaid.

"Gaban Binta ne ya fadi, hankali a tashe ta kalleta, Azeema ganin yanda abin ya shigeta yasa ta"

murmusa tace  ba cewa nai ki janye daga gareshi gaba daya ba alfarma nake nema ki dan bari wannan uwar data rabu da danta shekara da shekaru ta dan samu damar shakuwa dashi na wasu

yan lokuta.

"Idanun Binta ne suka ciciko. Azeema tace  nasan zaki fahimceni, kimin wannan alfarma kinji"

Binta?

"Binta ta daga kai alamar to hawaye suka gangaro mata, Azeema ta rike hannunta tace  nagode"

"kwarai da yanda kika taimaki dan nan nawa, ma tabbatar samunki kusa dashi ne yasa ya iye jure"

rashin mu.

"Wasu hawayen ne suka cigaba da zubo mata, Azeema ta kalli Barira tace  kuje da ita gobe a"

hado mata abubuwan bukata.

Barira tace  to Gimbiya.

"Nan Binta ya mike tai bangaren su Barira, tana shiga ta tsugunna tana hawaye, duk da ta fahimci"

"Gimbiya sai dai tana ganin ba a mata adalci ba ana neman rabata da Junaid wanda bataji ko yini zata iyayi bashi, a yanzu haka ma ji take kamar ta ruga inda yake."

Binta na shiga daki Barira ta kalli Gimbiya cikin jin dadi tace  Gimbiya kinyi maganinta.

"Azeema ta girgiza kai alamar a a tace  matsalar ba ita bace Junaid ne, me kike tunanin zai faru"

in mutane sukasan ya dawo da mace sannan ba matarsa ba? Macen ma mara asali?

Barira tace  ya zamuyi gobe?

Da safe ki kiramin jakadiya.

"Jakadiya? Barira ta tambaya, Azeema ta mike ba tare da ta amsa mata ba, taje shiga daki baiwar"

da Junaid ya aiko ta shigo ta sanar da Barira sakon Junaid.

"Barira tace  wayyo tayi bacci, tun dazu dama take cewa bacci takeji kanta na ciwo. "

"Kuyangar nan da jin haka ta juya, Azeema ta shiga ciki."

"Zama tai a bakin gadon ta kalaman Junaid ne ke mata yawo, tabbas akwai wani dalilin dayasa"

"Sarki ya daukeshi, to menene dalili? Baiso danta yai mulki? Kai ta girgiza da sauri dan tasan ba shi bane, tabbas gobe zata bigi cikin Jakadiya taji ko ta san wani abin, dan da dukkan alamu Abdulsalam ma baisan komai ba."

Ta dade tana juye akan gado kafin ta samu bacci ya dauketa.

***********

"Jin Binta tayi bacci yasa ran Junaid yadan sosu, sai dai baiyi zargin komai ba, yana nan a zaune"

yana tunanin cin abinci Azi ya kwankwasa mai.

Bayan ya shigo ne ya sanarwa Junaid akan Sarki AbdulSalam na san ganinsa.

Tare suka fito da Azi dan dama bai sanshi ba bai taba ganinsa ba.

"Sun isa fadar mai martaba, yana zaune an jera mai abinci a gabansa, Ji Zagi na sanarda isowar"

"Junaid ne yasa ya kalli bakin kofa, har Junaid ya shigo ya zauna daga can gefe idanunsa na kansa, wani sansanyan murmushi ya saka ya nuna masa kusa dashi yace  dawo nan. "

"Junaid ya karasa sannan ya gaisheshi, Abdulsalam ya amsa cikin tsananin kulawa sannan yace"

 Junaid!

Kallansa yai sai gani yai yayi murmushi wanda yasa Junaid din dan murmusawa kadan shima.

Wai kaine ka zama saurayi haka? Wasa wasa in yaro ba agabam mutum ya taso ba saurin girman

sa zaka gani.

Junaid baice komai ba sai dai yanda yake maganar yasa ya dan saki jikinsa.

Abdulsalam yace  bismillah.

"Ya fada yana mikamai spoon, Junaid ya amsa sannan suka fara cin abinci tare, sai turomai gabansa"

"yakeyi wanda yasa Junaid din aake murmusawa, Sarki ya kalleshi bayan sun gama yace  Junaid! "

"Junaid ya kalleshi tare da maida hankalinsa kansa, ka yafemin nasan duk da umarni ne na"

"mahaifinka ban kyauta ba na barinka danai, da alama san kai nane yamin yawa?"

Junaid cikin mamaki tace  san kai?

"Abdulsalam ya jinjina kai alamar eh, yace  kamar yanda kasani mahaifinka ne sarki, ban taba"

"tunanin amsar mulki daga gunsa ba aka sari maban taba kawowa zan mulki kasarnan tamu ba, sai"

"dai daga sanda Yaya ya furta min naji sha awar hakan, sai dai nasan in har kana nan dole wasu sai sunyi tunanin yin amfani dakai gun karya ni. "

Yadanyi shiru kafin ya kalleshi yace  san kai ko?

Junaid ya daga kai alamaf eh yace  san kai ne.

"Sarki ya kalleshi, Junaid ya murmusa yace  amma san kan mai amfani, akalla bakai kayi tunanin"

"fotar dani ba, sannan baka taba tunanin sauke mahaifina ka hau ba, sannan sai daya furta sannan"

kaji kanaso.

"Ido Sarki ya kuramai cikin tsananin jin dadin kalamansa, kafin yace  nayi mamaki. "

"Junaid yace  kayi hakuri in na bata maka, sau da dama nakanyi magana ne akan abinda raina ya"

bani.

"Sarki yace  hakan akeso ai, ya zama ko za aji haushi ka aji amma a kalla ka fadi abinda ka sani. "

"Junaid ya kalleshi suka murmusa a tare, Sarki yace  gobe za ai taron dawowar ka zakaga"

"mutane da dama da baka sani ba, yan uwanka da duk baka san dasu ba. "

Yace  haka Um 

"Sai yai shiru, sunan nama wahalar fada?"

"Ya kalleshi tare da dan shafar wuyansa, Abdulsalam yace  gashi nima so nake ka dinga kirana da"

Abba ba yanda kakecemin Kawu ba sanda kana karami.

"Junaid ya kalleshi da sauri, dariya sosai AbdulSalam yai wanda har fadawa sukai mamakin"

"wannan lamari, yace  wasa nake ma, wato har ka fara hangowa ko? "

Junaid yace  ya nuna?

"Sarki yace  sosai, sai kayi kokarin gun nuna abinda ke ranka, dan nan masarautace za ai amfani"

da abinda kake so a cutar dakai.

"Junaid ya jinjina kai alamar gamsuwa, me yasa yaji ya sake da mutumin nan daga haduwa daya?"

Lalai y cancanci a kirashi sarki yasan yanda zaiyi yaja mutum jikinsa.

"Sunyi sallama Junaid ya fito fuskarsa a sake, Azi yace da alama Yarima kaji dadin zuwan nan. "

Junaid ya kalleshi yace  ya nuna?

Azi yace  gashinan a fuskarka.

"Da sauri Junaid ya hade fuska yace  Azi, a duk lokacin dakaga ina kokarin bayyana abu a fuskata"

"kamin alama yanda zan gane, kafin na saba. "

Azi yi dariya yace  koyarwar da akai yau kenan?

Junaid ya ce  eh.

Haka suka wuce bangarensa ya zubawa abincin nan ido kafin yasa a kwashe sannan ya shiga ya

"kwanta, kan binta sosai yake mata ciwo? Yaso biyawa daga gun Sarki saidai yana tsoron karya tashesu daga bacci."

***********

"Hajjo ranta yayi mugun baci mikewa zaune tai a kan gadonta cikin tsananin takaici, yanzu"

"bangaren da take so ya barma Zubair har fadamai tayi shine ya ba wa wani Junaid? Fuskar tabta hade ranta yayi mugun baci, dan dama dazu da Ramlatu tazo haushi ya kamata da taga itama"

"Ramlatun yanzu tsoron Azeemar take, yanzu kuma sai taji wannan zance?"

Tayi tsaki yafi cikin kwano kafin bacci ya dauketa.

Da safe tana tashi aka kawo mata labarin cin abinci da hirar da Junaid sukai da Sarki jiya wanda har ana jin dariyarsa har waje.

"Cikin takaici ta cilar da kofin dake hannunta, wanda ya kusa bige Zeena datake kokarin shigowa"

"yanzu, tana ganin haka ta fara kokarin juyawa."

Cikin tsawa tace  ina zaki?

"Zeena ta juyo ta dawo ta zauna, Hajjo ta kalleta tace  kinba Sulaiman din hakuri? Kindai san"

gobe zai koma ko? Da yau dai tafi ma Takawa yace

Please Login or Register in order to submit comment