gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Zafin Rana Complete Hausa Novel by Aishat Alto Chapter 21 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bai bude idanunsa ba.

Can sai ga Hajjo wacce yasa itama a kirata daga baya.

"Ajiyar zuciya yai sannan ya bude idanunsa a hankali, kallan Abdulsalam yai sannan ya kalli"

"Azeema yace ""daga wannan lokacin na haramtawa Azeema da Abdulsalam shigowa cikin gari, zasu koma kauyen dana nemi su zauna, a kuma can zasu cigaba da rayuwa har karshen ransu, sannan dole su zasu nemi abinda zasu ci su sha, hadima daya da hadimi daya na amince su tafi dasu, sannan idan har Hajjo ta nemi ta bisu itama da hadima daya zata tafi, in kuma mijinta ya nemi zamanta anan ko kuma yana neman sauwake mata? zata koma can karshen ginin kewaye, gefen da Hajiya Inna take ta zauna, sannan itama gudun fitina mai tasowa zata bar shiga duk wani"

"sabga data shafi cikin masarauta."""

"Kallan Hajjo yai sannan yace ""sannan Zubair zan nadashi Hakkimi zai bar cikin masarautar nan ya"

"koma Hakimin garin da na bashi."""

"Maida idanunsa yai yadan lumshe sannan ya sake budesu yace ""inaso a cikin gurin nan maganar"

"abinda kuka aikata ta tsaya, wannan ne kadai abinda xan iya muku."

"Abdulsalam ya kalla yace ""kafin ka tafi gobe kaga nemi ganin 'yarka."""

"Da sauri yace ""to"""

"Yana kaiwa nan yace ""nagama magana."""

"Abdulsalam ya sake zubewa yana godiya, Azeema kam hawaye ne ya zubo mata saboda harta"

"fara rashin dan nata, ita kuma kaddararta kenan, bata taso da shi ba yanzu kuma shn hadu gashi zasu sake rabuwa."

"Kwallarta ta share sannan ta mike ta fita, Abdulsalam yabi bayanta da sauri har yana tuntube."

"Hajjo Junaid ya kalla wacce ta sauke kanta kasa ko tofa kalma daya batai ba, kallanta yai, kallansa"

"tai ta daure tace ""Zubair laifin me yai?"""

"Kallanta yai yace ba laifin dayai sai dai zamanshi kusa dake zaisa ki sashi, in ba abinda zakice zan"

"shiga ciki, sannan kema kiga yarki ta damu."

Ya wuce ciki.

"Haka tafito gaba daya danta a bace, yanzu kam ba yanda ta iya inba so take a turata kauye ba"

"bayan ba ita ya kar zomon ba, rataya aka bata, bataga abinda zaisa tabishi wani kauye ba."

^****

"Abdulsalam ne yabi Azeema da sauri, hannunta ya kamo yace ""Azeema nagode sosai """

"Tari ne ya kwace mai, kallansa tai tace ""karkai tunanin zan bika ne saboda soyayya ko kiyayya,"

"zan bika ne saboda ma kare mutunci da darajar d'ana."""

"Kai ya daga da sauri yace ""koma menene nidai nagode Azeema ke kadai nake bukata a"

"rayuwata."""

"Hajjo wacce ta taho tana jin karshen kalamansa ta tabe baki tace ""sai ka dauki abinka."""

"Kallansa tai bayan ta karaso tace ""kasan dai ni ina nan ko?"""

"Yace ""nasani."""

"Ta maka mai harara ta harari Azeema ta wuce, dan inba su ba da duk wannan abin bakin cikin bazai sameta ba, taga samu taga rashi."

*******

Washe gari a fada.

"Junaid yai gyaran murya wanda yasa kowa sake nutsuwa, kallansu yai dukansu sannan yace"

"""inada muhimmiyar sanarwa, da farko dai Sarki Abdulsalam da matarsa Gimbiya Azeema zasu bar masarautar nan sakamakon izinin hutawa da sukesan yi, abu na biyu kuma Waziri, Shamaki da Galadima."""

"Da sauri suka kalleshi gabansu na faduwa, suma ina neman kowa ya kawo sunan dansa wanda"

"zai gajeshi, ya zauna ya huta a gida, lafiyarku itace anin dubawa."""

"""Sannan abu na uku Zubair!"""

"Zubair wanda dama yasan menene saboda Hajjo ta fadamai, Junaid yace ""na nadaka Hakimin"

"Gabas!"""

"Da sauri mai kiran lafiya ya fara yima sarki kiraki, su Waziri kuwa yanda kasan an musu duka"

"haka sukaji abin."""

Da wannan aka shiga wata hidimar.

"Yana fitowa ya hadu da Azi ya dawo, Azi aya kalla yamai alama da ido akan an sameshi?"

Azi ya daga kai alamar eh.

"Bangarensa suka nufa daga gefen kofa yaga mutumin dake tsaye duk kayan jikinsa a kode,"

kafarsa wani sidaden silifas ne.

Junaid ya kalleshi da sauri ya zube kasa yana kwasar gaisuwa.

Junaid ya kalleshi sannan ya nemi ya shigo ciki.

"Da bakin kofa ya tsuguna gaba daya ya rude, sai da Junaid ya nutsu sannan ya kalleshi yace"

"""kaine Malam Kasim?"""

"Da sauri yace ""eh."""

"Junaid ya kalleshi cikin takaici yace ""ka taba tunanin inda yarka take? Ko a wace irin rayuwa"

"take?"""

'Yata?

"Ran Junaid ne ya kara baci, da sauri Kasim ya kalli Junaid yace ""Binta?"""

"Junaid ne ya kalleshi, da sauri ya sake zubewa yace ""Binta? Tanada rai?"""

"Junaid yace ""ka taba dana sanin abinda ka aikata?"""

"Kuka Kasim ya saka yace ""a koda yaushe cikin dana sani nake, san zuciya yasa na wulakanta yar"

"yarinyar da take marainiya."""

Marainiya?

"Kasim yana kuka yace ""Yarinyar mutumin daya taimakeni na zauna a garin ne, babban mutum ne"

"malami yana zaune da matarsa lokacin da mukazo garin, sai dai yana fama da lalurar ciwon daji, a koda yaushe yana zaune saboda kafafunsa, matarsa nada ciki ya rasu, haka almajiransa kowa ya shiga kokarin auranta dan ya biya hallarcin malam, harnima na shiga ciki, sai dai bansan dalilin Hafsa na zabata ba, nazo kuma ganin na samu dukiyar daya bari nai aure har na koresu."""

"Sake zubewa yai yana wani irin kuka, ran Junaid yakai matuka gun baci yace ""wannan wani irin"

"mugun hali ne? Bayan cutar da mahaifiyarta dakai sannan ka sawa yarinyar kiyayar mahaifi?"""

"Kasimu yana kuka yana neman yafiya, Ran Junaid s bace yasa Azi ya sa a kulleshi."

Ba karamin bacin rai bane ya bayyana a fuskarsa.

****

"Abdulsalam da Azeema haka suka bar masarauta bayan kwana biyu da hawan Junaid mulki,"

"Zeena da Binta sunsha kuka sosai dan Binta tunda Abdulsalam ya kirata yake neman yafiyarta take kuka, dakyar Junaid ya lalabata ta bari."

"Binta kam tasha kuka sosai jin Azeema zata tafi, Sai dai tafi tausayin Junaid dan tasan shikadai"

yasan me yakeji zai rabu da mahaifiyar da ya samu bayan shekaru masu yawa yanzu gashi zai sake rabuwa da ita.

*****

"Hajjo haka Zeena ta taimaka mata ta koma can gefen Hajiya Inna, Junaid yasa aka gyara bangaren biyu, Zeena ta koma bangaren Hajjo ita kuma Binta ta koma na Azeema."

"Da wannan Fada ta samu nutsuwa wanda kowa hankalinsa ya kwanta, sai dai Junaid a koda"

yaushe yana rashin mahaifiyarsa wacce yaso ya kasance da ita sai dai ba yanda ya iya da kaddarar da Allah ya dora musu.

Ba'a dade ba akai rashin Hajiya Inna Allah ya jikanta Ameen

^***********

Bayan watani........

Kwance yake ya juya baya tana matsamai bayansa yana lumshe idanunsa kamar mai shirin bacci.

"Can tace ""Ya Junaid?"""

Hmmmm

Bacci?

Uhm uhm!

"Murmushi tai tace ""ka juyo in ganka tunda ka hau mulkin nan ganinka ma wahala yake mana."""

"Juyowa yai gaba dayansa ya kalleta, idanunsa yana dan lumshe su yana budesu yana saitinta"

"yace ""Binta Allah bacci."" Yai maganar cikin shagwaba"

"Juya mai baya tai tace ""ai bacci lafiya."""

"Murmushi yai sannan ya matso ya rungumeta ta baya a hankali ya sa hannunsa cikin rigarta,"

"idanunta tadan lumshe, hannunta tasa ta rike hannunsa dake kokarin zare mata bra."""

Ya akai?

"Juyowa tai tace ""Yaya Allah Bacci!"" Tai maganar yanda yai dazu, dariya ya saka sosai, sannan yasa"

"hannu ya cakulota bayan ta juya, da sauri ta juyo tana dariya, tana cewa Yaya bari!!!!"

"Ganin yaki bari ta fara ramawa itama, dariya sosai sukai sannan suka kalli juna suna dan numfashi, kan bakinsa ta matso ta sumbaceshi sannan ta koma tana neman kwanciya, hannu yasa ya riko wuyanta sannan ya dawo da bakinta kan nasa, cikin salo da suke sumbatar juna, a hankali yasa hannu ya zare rigarta yana cirewa yana aika mata da sako zuwa bakinta..........."

"Bayan sunyi wanka ne ta kalleshi ta hade fuska tace ""sai yaushe zaka fadamin yanda kukai da"

"Babana?"""

"Idanunsa ya bude yace ""naam?"""

"Ta kwanta itama tana fuskantarsa tace ""Ya kukai?"""

"Bakinsa yadan motsa sannan ya jawota ya rungume nan ya sanar da ita, hawayen dake zubo"

"mata ne sukaki daina zuba, dagota yai yana kallanta."

Itama kallansa take tana kuka.............

"Rungumeta yai yace ""ki mai addu'a daga shi har Umma abinda suke bukata kenan daga garemu"""

"A ransa yace dake da Zeena da alama Allah ya dauramin nauyin zama komai naku, ina rokon Allah"

ya bani ikon kula daku.

"Hannu yasa akan cikinta yace ""sai yaushe zai fito ne wai? Naga na Zeena harya fito."""

Idanunta dasukai jaa ta dago ta kalleshi tasan so yake yasata dariya........

********

Bayan shekara daya.

"A wannan lokaci ansamu canji dayawa, Zeena ta haifi danta namiji aka saka mai sunan mahaifin"

"Junaid Zubair, sai ake kiransa da Baba karami, Binta kuma ta haifi mace aka sa mata sunan mahaifiyarta Hafsa."

"Baba karami yaba Hafsa wata daya, kusan koda yaushe suna bangaren Hajjo wacce zaman kadaici"

"yake neman halakata, shiyasa ana haifarsu ta nemi a dinga kawosu."

"Ramlatu kam ta zama yar sai a hankali, an tasheta itama daga inda take tabar cikin masarauta."

"Junaid ya samawa Azi mata aka auramai suke zaune a nan masarauta, Harira ma tayi aurenta."

"Yau sun tashi ana ta shiri saboda kasancewar yau ranar sallah karama ce, tun safe ake ta hada"

"hada a fada, Zeena ce ta kalli Fure tace ""Zanje na dawo."""

"Da sauri Fure ta taso, Zeena tace ""ki zauna ni kadai zani."""

"Nan ta fito ta nufi hanyar bangaren Junaid, yana zaune yana duba littafin dake gabansa Zeena ta"

shigo.

"Kallanta yai yace ""Zeena?"""

"Zama tai kusa dashi tace ""me kake gani game da yau?"""

"Yau? Ya tambaya, tace ""maganar da mukai"""

"Yanayin fuskarsa ne ya canza yace ""kina ganin yaune kuma ya dace?"""

"Tace ""naga yanzu kowa na hidimar shiryawa, sannan hankalin kowa baya fada har dai zuwa"

"yamma idan za'ai hawa."""

"Yanzu ya fahimci manufarta yace ""na gane, zamuje taren?"""

"Idanunta ne suka dan canza ta girgiza kai tace ""kaje kai kadai yaya ni zan zauna anan harka dawo"

"saboda kauda kokonto."""

"Murmushi ya saki cikin jin dadi, sannan ya rungumeta yace ""nagode Gimbiya."""

"Fita yai ta kofar baya bayan ya kira Azi, suna fita Azi ya zagaya ya fita da mota Junaid ya hau suka"

nufi kauyen.

"Azeema na zaune tana tsince shinkafa, gefenta kuma Barira ce tana fifita ruwan dake kan wuta,"

"Abdulsalam dake cikin dake a kwance rai a hannun Allah ne ya fara tari, mikewa tai ta shiga dakim, tari yake sosai hadda amai, ta rikeshi ya gama sannan aka gyara gun, duk sun canza in ka gansu abin tausai, dan ma Azeema ta taho da kadararta da kayanta su suka saida suka yar gona suna noma."

"Sai daya kwanta ya kamo hannunta yana lumshe idanunsa, yau kam tun safe yake kwara amai"

tsoron halin nan da yake ciki take gashi yasha magani amma abin karuwa yake.

Gimbiya!

Yanda Barira ta kira sunan ta a razane ne yasa ta sakeshi ta fito.

"Daga bakin kofa ya tsaya gaba daya jikinta ya hau rawa, Junaid wanda ke tsaye ne ya mata"

murmushi.

Shigowa yai ya zauna kusa da Abdulsalam.

"Kallansa yai sannan ya kalleta yace ""jikin ne?"""

"Jin muryar ne yasa Abdulsalam ya bude idanunsa, yana ganin Junaid ya fara kokarin mikewa sai"

amai.

Junaid ya maidashi ya kwanta sannan ya kalleta.

"Abdulsalam ya kamo hannun Junaid yace ""Junaid ka yafemi """

"Amai ya shiga kara yi kai kace kayan cikinsa zai amayar, nan hankalinsu ya tashi, Junaid ya rikeshi"

"yace ""na yafema kai shiru ka kwanta."""

"Sai dai ina, jikin ne ya sake rikicewa anan rai yai halinsa."

"Bakaramar firgita Junaid yai ba ganin baya numfashi, hankalinsa ya tashi matuka."

"Azeema kam kasa ko kuka tai, haka Junaid suka mai sallah suka kaishi, nan ya nemi su koma da"

"Azeema amma tace anan take san zama, dole ya taho ya barta."

"Tunda ya shiga moga idanunsa sukai jaaa sosai, tausayin Zeena da Binta su kara kamashi, dole ne"

"ya zamar musu uba, yana fatan Allah ya tayashi rekesu cikin adalci."

"A haka ya isa akai hawa, sai daga baya akaji rasuwar sa......"

Allah ya mana mai kyau Ameeeeeen

****

Ayusher

Ina mika godiya gareku gaba daya wadanda suka sai littafin nan nagode da karamci da kuma

"kauna, kura kuran dake cikin littafin nan Allah ya yafe min su, wanda na fada daidai kuma Allah ya bani ladansu."

"Muna nan haryanzu a tare tunda bamu karasa A GIDANA ba. mu cigaba daga can muji Goggo,"

"Adamu, Zainab da Khalid da kuma Razy "

Love you soooo much

Onelovec'


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment