gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Zafin Rana Complete Hausa Novel by Aishat Alto Chapter 11 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dan sarakunan da suka shid'e sun k'aru da sirrika masu yawa a cikinsu, to lallai nasan kaima zaka k'arun""."

"Junaid yad'an murmusa, ""lallai Na gode da gudunmawarka agareni, zankuma nazarcesu, idan ina"

"buk'atar fad'ad'a ilimi Zan tuntu6eka""."

"""To Masha ALLAH""."

Sun dan sake yin hira kafin suyi sallama.

**************

"Azeema ta kalli barira dake durk'ushe gefenta tai d'an murmushi, ""Barira daga yau kar a sake"

"saka binta aiki""."

"Cike da mamaki barira tace, ""ranki ya dad'e miyasa?""."

Azeema ta gyara zamanta cikeda k'asaita tana wani murmushin da ita kad'ai tasan fassarar

"kayanta, ""karki damu da sanin dalili, kawai inason daraja duk abinda ya shafi Junaid "

"Barira ta jinjina kai cikeda mamaki, tasandai ba banzaba, akwai shirinda uwar d'akin nata keyi ta"

"k'ark'ashin k'asa, dan tasan haka kawai Azeema bazata sauko ta nemi daraja Binta ba."

Harzata mik'e Azeema ta dakatar da ita.

"""Inason ganin jakadiya""."

Barira ta jinjina kai tare da amsawa da to.

****************

"Yau sarki Abdussalam ya gagara fita fadanci, sai aiken yana buk'atar hutawa yay"

"musu, sannan yabuk'aci ganin Shamaki da wambai da waziri."

"Babu 6ata lokaci suka iso, bayan jakadiya ta nema musu Iso suka Shiga."

Duk suka gaida sarki cikin girmamawa.

"Sarki Abdussalam yay gyaran murya idonsa a Kansu, ""kunsan miyasa na aika a kiraku? "

"Wambai yace, ""ALLAH ya k'arama sarki lafiya bamu saniba, sai dai ganin yanda ka kiramu tabbas"

akwai abinda ke faruwa.

Sarki Abdussalam ne yadan sauke ajiyar zuciya ya cigaba da fad'in  me kuke tunani a game da

Junaid?

"Fuskarsu dauke da mamaki suka kalleshi, Junaid?"

"Abdulsalam yace  duk d'inku kunsan minene ma'anar dawowarsa garemu, sannan kunsan"

"makomar hakan, to yarage ruwanmu Neman mafita, domin yaron yawuce zatonmu, na rasa me yasa nakejin ba daidai ba, me kuke tunani zai faru in ya san abinda ya faru a baya? Wanda"

idanunsa sun sa na fara tunanin dole mu san abinyi.

"Hankalinsu ne ya tashi, dukansu suka shiga nazari."

Shamaki ne ya kalleshi cikin mamaki yace  ALLAH yabaka nasara mizai hana mu tuna baya

"kawai?""."

Da sauri Sarki Abdussalam ya kalleshi yace  Baya?

"Idanunsa ya zare da sauri yace  Bazai yiwu ba, kun manta wacece Azeema a gareni? bazanso"

"aikata hakan ga jininta ba, anema wata mafitar. "

Shiru suka karayi.

"""Mafita d'ayace"" cewar Waziri wanda ya fada yana gyara zama."

"""Wacce kenan?"" Sarki Abdussalam yafad'a yana maida kallonsa gareshi."

"""kayi taron nad'ashi Matawalle ko Galadima, sannan kabashi auren y'arka Zeenatu, hakan zaisa"

yai tunanin kafi kowa sanshi sannan yarka zata lura da duk al amarinsa.

"Wani zazzafan huci Sarki ya sauke, ""shawarar k'arshe dama burinace, dukda ban yanke hukunciba,"

"amma jin kalamanka yasa ka k'aramin k'warin gwiwa, ta farko kuwa kasan dai galadima nada ransa da lafiya, zamu sakashi yin murabus ne ko me? Zubair kuma shike rik'e da sarautar matawalle""."

"Wambai yay wata Y'ar dariya ""Ranka ya dad'e anzo dai-dai wajen kenan ai, dan inhar ka tu6e"

"Yarima Zubair ka d'aura Junaid lallai kowa zaikuma girmama adalcin mulkinka, a lokacin kowa zai fahimci kanasan Junaid fiye da yanda kake san danka, uwa uba Gimbiya Azeema wacce zata kara"

ganin girma da darajarka.

"Kai ya jinjina cikin gamsuwa, da alama. Kowa yayi na'am da hakan, nantake suka fahimci matsalar"

"ta warware, suka cigaba da tsara abinda suke tunani."

****************

"Fure dake zube gaban zeena a d'arare tace, ""ranki ya dad'e Azi hadimin yarima ya tabbatar"

"min yaci abincin""."

"Cikeda d'oki Zeena tace, ""da gaske?""."

 Sosai kuwa ranki ya dad'e

"""Kai fure baki ta6a sani farin ciki irin yauba, lallai kinata tukuycin albishir mai tsoka""."

"Fure ta washe baki tace  godiya nake ranki ya dad'e, ALLAH ya mallakama yarima Junaid ke""."

Zeena ta dan harareta tace  me kika sani?

Fure tai kasa dakai tana murmushi.

"Sosai Zeena ke tsallen murna ita kad'ai a d'aki, jitake kamar anmata albishir da aljanna yau."

"Haka ta fito ta gangaro bangaren Hajjo, Hajjo wacce ke kwance duk batajin dadi ta kalli Zeena,"

"kallo daya ta mata ta fahimci Zeena nacikin farin ciki, saidai bata tambayeta ba balle tasani saboda abinda ke damunta ya wuce wannan."

"**************"""

Tunda ya dawo sashensa yake cikin nazarin zamansu da Mahmud da yanda mahaifinsa ya

"gudanar da mulkinsa zuwa sarki Abdussalam. Lallai lokacin dazai fito ainahinsa Na jinin sarauta yayi, yakamata kowa ya fahimci sarauta a jini take ba a ayyukaba."

"Sabon shiri yasake, kafin ya aika Azi sashen mai martaba Neman ison ganinsa. Anyi sa'a shima mai"

"Martaban yana muradin ganinsa, dan haka babu wani janjani yasamu izini."

"A yanda Junaid ya fito dolene kowa ya kallesa, ya rikid'e ya canja gaba d'aya, saika rantse a"

"madarautar ya girma, harira kanta galala tai tana kallonsa, lallai ta yarda mulki a jini yake ba'a ayyuka ba."

"Shi kansa Zubair dake k'ok'arin shiga sashensa la6ewa yai yana kallon Junaid, gaba d'aya saiyaji ya"

"raina ajinsa da girmansa, wai harma yaushe Junaid d'in yagama fahimtar shi jinin mulki ne? Jibifa yanda yake wani shak'ar iska da fesar da ita tamkar shine sarkin, lallai aikine babba agabansu, dan wannan yaron idan basu risinar dashiba to zai 6allo musu ruwa."

Oho Yarima Junaid baisan yanaiba.

"Itama Hajjo tuni labari yakai Mata, ba k'aramin girgiza tayiba dajin batun, zeena dake gefenta ta"

"mik'e da hanzari tafice, saidai tana fitowa Junaid Na shigewa turakar mai martaba."

"Takaici yasata cizon yatsa, takoma da alwashin jiran fitowarsa."

****************

"Sarki Abdussalam dake kishingid'e ya zubama Junaid idanu, mamaki yake a ransa yaushe"

"junaid d'in ya koma haka? Koda yake ba abin mamaki baneba, yasan wacece Azeema sarai, komai zata iya aikatawa akan d'anta domin mulkin nan, amma bai tdammaci hakan da wuriba....."

"Gaisuwar Junaid ta katse tunanin mai martaba, ya amsa masa da kulawa. Shiru ne ya biyo baya,"

"kowa yana nazarin d'an uwansa, zuwa can mai martaba ya nisa yana gyara zamansa,"

"""junaid akwai matsalane, Ka buk'aci ganina?""."

"Murmushi junaid yayi, yad'an girgiza kansa, ""A'a Abba, dama za6in daka bani nazo fad'a maka""."

Murmushi Abdulsalam yai yace  ina jinka me kakeso?

Ya boye damuwarsa dake kasan ransa.

"""Nayi farin ciki da hakan Junaid, amma kafin sannan gawani albishir"".Abdulsalam ya cigaba yana"

kallansa.

"Kallonsa Junaid yad'anyi, saikuma ya murmusa yana maida kansa k'asa."

"Sarki Abdussalam bai fahimci murmushin Saba, ya danne ya Fara magana,"

" Duba da wasu abubuwa danai na fahimci yakamata kayi aure, kai idan masarauta ne, hankalin"

"kowa a kanka yake kana ganin matsalar data afkou wancen lokacin, hakan yasa yai tunani hadaka"

aure da kanwarka Zeenatu.

 Zeenatu?

Junaid yafad'a yana kallon mai martaba fuskarsa dauke da matuk'ar mamaki. Shi kansa mai

"martaba ya fahimci haka, dan haka ya gimtse fuska yana fad'in,"

 Umarnine Junaid dan dan Sarku matarsa ta farko dolene yabi umarnin wacce aka zaba masa.

Jinjina kai junaid yashiga yi yana wani irin murmushi  Sosai ka cancanci nabi Umarninka domin

"matsayin mahaifi kake a gurina, naji na kar6a da hannu biyu""."

"Sarki Abdussalam ya murmusa, dan aganinsa yasamu nasara a matakin farko. ""ALLAH yay maka"

"albarka Junaid, ina sauraren za6inka. "

"""Abba za6in nawa nima bamai wahala baneba, domin duk bisa bigire d'aya muke""."

Bigire daya?

"Gaban sarki Abdussalam ya fad'i, kardai mulkin?. Kafin ya nemo amsa maganar Junaid ya"

katseshi......

"""Inason izinin Auren yarinyar da muke tare acan, binta!..."""

 Binta?

Sarki Abdussalam yafad'a a harzuk'e wanda yau ne karo ma farko da Junaid yaga yayi magana

haka  Junaid maidamin murtani akan rashin kar6ar za6ina yasaka tunanin had'amin yarinya da Y'ar talakawa marar usul ko me? Ni nai tunanin taho maka da ita saboda ganin kana bukatar

"kwanciyra hankali anan, yanzu kuma ka kawo zancen so? "

"Shiru junaid yai yak'i tankawa, yay kuma kicin-kicin da fuska babu alamar fara'a, danmmi za'a kira"

"binta mara usili? To lallai inhar zai auri zeena sai dai da binta, inba hakaba kuma zai 6allo ruwa gaba d'aya kawai, saiya auri wadda basaso d'in da k'arfin mul......"

"""Dakai nake magana"". Sarki Abdussalam ya katse tunanin junaid."

" Dago ido junaid yay ya kallesa, fuskarsa babu alamar fara'a, hakan ba k'aramin razana sarki"

"Abdussalam yayiba, dan ainahin marigayi sarki Zubair yagani a fuskar Junaid d'in, kasa cewa uffan"

"yayi, saiya samu kansa da sassauta fushinsa, yace,"

"""Nabaka lokaci kayi tunani, bani kad'aiba ko mahaifiyarka bazata yarda da za6inka ba, har gwara"

ni zan iya hakura amma kai kasan Azeema bazata taba yadda ba.

"Junaid ya murmusa, ""Tuba nake Ranka ya dade ba binta kawai ba, ko Zeena bazata aminta ba,"

daga zuwana na shaida hakan.

"Yana gama fad'an hakan yamik'e ya fito cikeda kasaita da izza, wadda tasaka sarki Abdussalam"

kasa d'auke ido daga kallonsa. Har yaushe Junaid d'in yay irin wannan canjawar?.

"Junaid na fita ya tsaya a waje a hankalu ya juyo ya kalli bangaren Abdulsalam, bai taba tunanin"

"shima xai zo mai da magana haka ba, juyawa yai cikin isa ya nufi bangarensa."

******************

"Jakadiya ta kwashi gaisuwa wajen Azeema kafin tace, ""Ranki ya dad'e gani""."

"""Na ganki ai"". Azeema tafad'a tare da zuba mata ido. Takuma gyara zamanta tana kallon jakafiya"

dake gurfane.

"""Jakadiya inason bincike akan y'ay'an sarakunan k'asar zazzau, Gumel, kano""."

"""Angama ranki ya dad'e""."

"Jakadiya na fita Azeema ta kalli barira, ""Naji ance jiya mai martaba yayi zama Na mussaman da"

"waziri da wambai da shamaki""."

"""Eh lallai ranki ya dad'e anyi hakan, amma naji k'ishin-kishin akan auren gimbiya Zeena ne""."

"Baki Azeema ta ta6e, saikuma tayi murmushi"

Barira cikin san gulma tace  Gimbiya yanzu wace d'iyar sarkice a cikin ukunnan tadace da yarima

"Junaid?""."

Azeema ta dan harareta.

"Dariyar farin ciki barira tayi, saboda tunowa da binta tace  ranki ya dad'e mu jirayi tarihin"

"kowaccensu saimu d'ora a mizani, dan yarima yafi dacewa da d'iyar bajimin sarki mai ginannan"

"tarihi""."

"""Wannan gaskiyane barira, shiyyasa nakeson kasancewa dake a komaina, ko mai martaba bazai"

"San komaiba akai saina gama da shikansa junaid d'in""."

"""wannan shawara tayi ranki yadad'e""."

*****************

"""Uwar d'akina ga yariman can yafito daga sashen mai martaba, sai dai kuma ransa kamar a 6ace"

kamar yanda na kula.

Kamar Zeena tana bama fure amsa saikuma ta fasa  A bace? Ko muje bangarensa? Ai yayanane

ba wanda zaice wani abin.

 Amma ranki ya dad'e bak'ya ganin yawan zarya sashensa kamar zai  saikuma tai shiru ta kasa

k'arasawa saboda hararar da zeena ta watsa Mata.

Tace  Gun Yayana zani kinada magana?

Fure ta zube tace  tuba nake Gimbiya.

"A falo suka iske hajjo da Ramlah suna magana sai dai da alama ana jinsu akai shiru, harzata"

"wucesu hajjo ta dakatar da ita ""Ina zakije?""."

"Baki ta turo,  zan d'an fita mik'e kafa mana""."

Hajjo taja tsaki tana d'auke kanta. Zeena kuma tafice fure Na take mata baya.

***************

"Gaba d'aya ran junaid a 6ace take, yayinda zuciyarsa kemasa wani sak'e-sak'e akan mai"

"martaba. Ya tuna wadda akeson had'ashi aure da ita, yarinyar data tozartashi farkon shigowarsa masarautar, wadda batasan darajar d'an Adam ba, zai aminta da aurenta kawai domin yasamu damar kasancewa da kwatarwa Binta  yancinta, Ada ba son binta yake amatsayin masoyiyaba, amma ganin matsayinsa da nata ya kawo tazara a tsakaninsu yayi tunanin aurenta, hakanne kawai zai dai-daita matsayinsu tamkar yanda yake gani a tun farko. Yasan kuma babu Wanda zai amince masa da auren Binta kai tsaye, musamman mahaifiyarsa, amma idan ya jingina akan auren Zeena to lallai zai samu yanda yakeso, yanaji a zuciyarsa mai martaba da manufa yake son bashi auren"

"Zeena, inhar kuma yaga bashida mafita dolene ya yarje masa akan auren binta."

Ummana fa!?.

Wani sashen zuciyarsa ya ambata. Kafin samun amsa sallamar Azi ta katse tunaninsa. Azi ya

rissina yana sanar masa da neman iso daga Zeena.

"Wani kallo ya watsama Azi, kafin yace, ""Bana bukatar hayaniya""."

Azi ya jinjinamasa kai cike da girmamawa.

"Takaici ya kama Zeena jin amsar da Junaid ya bayar abata, wannan wulak'anci har ina, takula"

"yarima Junaid yacika tsauri da rik'o, yakamata ya yafe mata inhar akan laifin data aikatane bisa rashin sani, ita ta rasa meyasa take san ganinsa."

Ranta a 6ace tabar sashen.

***************

"Mamaki yakama Binta jin zancen da barira take Mata, wai gimbiya Azeema tace kar asake"

sakata wani aiki.

"Kodai Junaid ne yay magana? To amma jifa yanda ya watsar da ita d'azun, hakan bak'aramin k'ona"

"ranta yayiba, dan har kuka tayi, ita gaba d'aya ya Junaid ya canja Mata, tamkar bashine abokin"

nan nata dasuka tashi tare suka rayu tareba.

"""Ya ALLAH kabani ikon jurewa da wannan sabuwar rayuwa mai cike da rashin ya Junaid a cikinta""."

Ta share hawayen da suka ziraro Mata.

*************

"Mamaki sosai ya Kama gimbiya Azeema ganin yau kwanan junaid uku bai lek'ota ba, Anya kuwa"

lafiya?. Kokuma nazarin littatafan tarihi da Mahmud ya bashine suka d'auke hankalinsa?.

"""Inaga hakane"". Tafad'a a fili tana murmushi da kauda zarginta na farko."

"Sai mai martaba da shima a kwanaki ukunnan Sam bai nemeta ba, baki ta ta6e, dan hakan bai"

"dameta sosai ba, ayanzu burin gyara rayuwar d'anta ne a gabanta, dan nan kusa take buk'atar dawowar mulki hannunsa, tunanin yanda zatai da Abdulsalam ne ya darsu a ranta, dolene ta san yanda zatai."

"Nace, ""turk'ashi, wannanfa shine ga akuya ga kura @&""."

***************

Ayusher 27

***************

* ZAFIN RANA *

......................

*Hask e  W rit e rs Ass o ci a ti o n*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*K A$ Іf[€ ŠfV *

{28}

"Bude idanunsa yai a hankali ya daurasu akan Azi dake durkushe a gefensa, Littafin dayake nazari"

na hannunsa ya kulle.

"Azi yai murmushi yace ""yauma bazaka fita bane?"""

"Junaid ya kalleshi yace ""zuwa yamma."""

"Azi ya jinjina kai cikin gamsuwa sannan ya mike, haryaje kofa ya juyo ya kalli Junaid, Junaid ne ya"

kalleshi kallo mai dauke da tambaya.

"Azi ya kara rusunawa yace ""Binta fa ta zama 'ya, jiya dana ganta, da alama Gimbiya ta zareta"

"daga gun bayi."""

"Kai Junaid ya jinjina bai ce komai ba, Azi wanda ya fahimci jin dadin Junaid ya fita daga falan."

"Shiru Junaid yai a hankali kuma wani lalausan murmushi ya zagaye fuskarsa, baiyi niyyar fita ba"

saboda yana jiran aike daga bangaren Mai Martaba sai dai jin haka yasa ya mike.

"Ciki ya shiga ya fara shirin fita, harya gama shirya wa sai kuma ya koma ya zauna."

************

"Kallan Barira tai tace ""Anji daga gun Junaid?"""

"Barira tace ""tuba nake ranki ya dade amma haryanzu ba labari."""

"Shiru Azeema tai, tace ""Binta fa?"""

"Dazu wai zata fita, Azeema ta kalleta tana mata alamar ina?"

"Kai Barira ta girgiza tace ""bansani ba Gimbiya."""

"Shiru Azeema tai tana dan kada hannunta, badai dan ta bata matsayin 'ya ba take neman"

zagayewa ta dinga zuwa gun Junadi ba tare da saninta ba?

**********

"Mikewa naga ya sake yi sannan ya fito daga cikin dakin nasa, da sauri Azi ya matso yace ""Yarima"

"zaka fita ne?"""

Kai Junaid ya daga cikin kasaita ba tare da ya amsa ba.

Da sauri suka matso dan yima Junaid rakeyi.

"Zeena wacce ta nufi bangaren Junaid ce ta tsaka cak, daga nesa wanda akala yakai taku goma"

sha biyar tsakaninsu.

Itama ja tai ta tsaya daga inda take.

"Zeena ranta yakai matuka gun baci, tun daga sama ta kalleta zuwa kasa, da alama kenan ta fita"

daga matsayin bayin da take?

Cikin isa ta daga hannu tayima Binta alama da ta zo.

Binta ta kalleta sannan ta karasa inda take.

"Wani banzan kallo ta sake mata sannan tace ""daga ina?"" Binta ta kalleta tana tunanin wannan tambayar fa?"

"Zeena ce ta katseta da cewa ""ina zaki kuma? A iya sanina kin bar bangaren Ya Junaid."""

"Binta ta dago ta kalleta sannan tace ""zanje gun Harira ne."""

"""Harira? Wace kenan?"""

"Shiru Binta tai ganin batasan me zata ce ba, Zeena jin bata tanka mata ba yasa tace ""banaji dai mace wacce tasan mutuncinta zata dinga zirga zirga bangaren namijin da batada alaka dashi ba."""

"Binta ita kanta batasan sanda ta kalleta ba, hatta Fure sai data guntae dariyar data taso mata."

"Ganin yanda Binta ta kalleta ne ya harzako Zeena dan dama neman abinda zata mata takeyi,"

Binta bata nufa ba taji an wanketa da mari.

"Kallanta tai cikin tsananin mamakin laifin datai, Zeena tace ""me? Zaki rama ne?"""

"Binta tai shiru, ke yanzu in har kinada hankali ba tattarawa ya kamata kiyi ki dau kafafunki ki"

koma mahaifarki ba?

Binta yanzu kam ta fara zargin san shi Zeena takeyi.

"Junaid wanda ya fito yana tsaye daga bayansu yanajin abinda ke faruwa, ransa yakai matuka gun"

"baci duk da a fuskarsa bazaka gane ba, Binta ce ta dago zatai magana ta ga Junaid, ido ta kuramai ta kasa cewa komai."

"A kufule Zeena ta juya dan taga meke faruwa, Junaid suka gani a tsaye yana kallansu."

"Gaban Zeena ne ya fara dukan uku uku, wanda idanunta suka firfito waje, a hankali cikin kasaita"

da takama ya fara taka kafafunsa zuwa inda suke.

"Binta kam kallanshi kawai take gaba daya ya canza, ya sake kwarjini, dama haka Junaid yake ko"

dan ya dawo inda ya dace dashi ne?

"sauke idanunta tai daga kansa ganin ya nufo daf da inda suke, Zeena a rude tace ""Yaya."""

"Kallanta yai yace ""Zeena? Me kikeyi a nan?"""

"Ta kalleshi cikin fargaba tace ""dama nayi tunani zuwa ne gunka."""

"Guna?"""

"Kai ta daga,yace ""me kike anan to?"""

Kallan Binta tai wacce ganin bai kalleta ba yasa gaba daya taji kafafunta sun fara rawa.

Idan na kasa dake ya miki laifi me zai sa ki kaskantar da kanki a ciki mutane?

"Mamaki ne ya kamata ta kalleshi da sauri, Binta kam gaba daya jitai kanta ya fara wani sarawa,"

"juyawa yai zuwa bangarensa, Zeena ta kalleta ta dafa kafadarta tace ""dan an sa saban kaya ba'a canza asali."""

"Tabi bayansa, Azi kam wannan lamari shi kanshi ya daure mai kai, meke faruwa?"

"Suna shiga cikin falansa kallo kadai yama Azi, suka bar falan dukansu."

"Yana tsaye dama bai zauna ba, ita kanta Zeena a tsaye take, cikin salo tace ""Ya Junaid."""

"Bai juye daga inda yake ba yace ""ke kika nemi hadin aure tsakani na dake?"""

"Gabanta ne ya cigaba da faduwa, ta rasa me yasa yau take jin shakkar Junaid haka."

Juyowa yai ya kalleta sai kuma taga ya saki wani murmushi wanda ya kara sata cikin wani yanayi.

"A hankali ya tako zuwa inda take yace ""me? Bake bace?"""

"Kallansa tai idanunta duk sunyi jaa, kai kace marinta akai, a hankali tace ""nice."""

"Murmushi ya sake yi yace ""kinasona da har kike tunanin zaki jure duk matsalar da zata fito ta"

"bangaren Hajjo da Ummana?"""

"Yawun bakinta ta hadiya sannan tace ""Eh."""

"Yadan jinjina kai a hankali yace "" hakan yayi, sai dai in har kinaso na aure nima sai kinbi sharadi na."""

Sharadi?

"Ta fada a dan tsorace, yace ""eh sai dai in zan aureki tare da kawarki."""

Kawata?

"Cikin mamaki tai tambayar, yace ""wacce kuke hira da ita a waje dazu, na tabbatar yanda kike yar"

"sarki bazaki daga hankalinki akan hakan ba."""

"Rainin wayau, bayan yasan abinda sukai a waje harya tambayeta yanzu kuma yazo mata da wani"

rainin hankali? Wai kawarta? Sannan me? Ya hadasu da wannan yar iskar da ba'a ma san tsatsonta ba?

"Junaid ne ya kalleta yace ""kina so ki aureni wannan ce kadai hanya in kuma baki amince ba kowa"

"yasha zamansa."""

Shiru gai tama rasa ta ina zata fara kamo abinda ya kamata.

"Junaid yace ""ki sanar da Mahaifinki haka dan nasan zai kira ya tambayeki, in kuma baki amince"

"ba kowa yasha zamansa."""

Yana kaiwa nan ya fita daga falan ya barta a tsaye kamar gunki.

"Binta kam kasa ma shiga gun Hari tai tana tsaye a gun kamar wacce bata numfashi, abun daya"

faru sai kara dawo mata yakeyi.

"Ganin Azi ya fito yasa ta fahimci sune, da gudu tai kwana ta labe, sai dai kafin ta karasa kwanar"

"Junaid ya hangota, tsoransa ma kartaje garin gudu ta fadi taji ciwo."

"Haka suka zo ta saitin inda ta boye ya dan kalleta ta gefen ido ya basar, kiyi hakuri Binta idan har"

banyi hakan ba bayanda za'ai na dawo dake gareni.

Bangaren Azeema ya nufa wacce ganin Junaid baizo ba yasa tasa a kara kiran Jakadiya.

"Suna zaune Jakadiya na mata bayani akan binciken da akai, Azeema kowacce aka nuna mata aka"

mata bayani sai tadan kushe.

Jakadiya tasa dariya tace  Gimbiya taya za a samu wacce zata dace bayan duk wacce aka baki

bata miki ba?

Azeema tai murmushi tace  bawai basumin bane Junaid dine kamar basu dace dashi ba.

"Barira ce tai dariya tace  A idanun Gimbiya, Junaid ne kadai ya cika yanda ya kamata . "

Azeema ta kalli Jakadiya tace  Me Takawa yake a  yan kwanakin nan?

"Jakadiya tace  nikaina bansan meke faruwa ba, da alama wani nazari yakeyi. "

Matsowa tai cikin gulma tana san sanar da ita har Junaid ya kira bayan sun zauna dasu Shammaki

aka sanar da isowar Junaid.

Da sauri ta suka tattare Barira ta nunawa Jakadiya hanyar baya ta fita da sauri.

Azi ne ya kalli wacce tai ison ya sake mata alama dan ta sake sanarwa.

"Barirace ta karaso da sauri ta bude kofar, sannan ta basu hanya."

"Junaid ya shiga ciki, kallan Azeema yai wacce ta gyara zama kai kace ita kadaice dama a gun."

Zama yai ya gaisheta cikin kulawa.

"Kallansa tai cikin wani jin dadi tace  Barka da isowa Yarima, har ina tunanin aikawa kazo, ganin"

kwana biyu banganka ba.

Junaid ne ya kalleta yace  Tuba nake Umma na.

"Wani dadi ne ya kamata, tace  Ya zanyi, ai ganinka ya wanke komai. "

Murmushi yai cikin jin dadi.

"Barirace ta sunkuyo tace  Yarima, Gimbiya ta maida Binta matsayin  ya. "

Kallan Azeema yai sannan ya sunkuyo yace  tana godiya Ummana.

"Shikenan? Abinda yazo mata ranta kenan, ganin ba wani farin ciki a fuskarsa yanda ta zata."

Sai dai hakan ya mata dadi ta wani bangaren.

***************

"AbdulSalam ne yai shiru, yau ya gama tattare duk wani hukunci da zai dauka."

"Shammaki ne ya kalleshi su biyu a cikin falan, yace  Ranka ya dade ka gama tunanin? "

"Abdulsalam yace  eh. Dole ne mubi abinda yakeso inhar munasan abinda mukeso ya samu,"

sannan inhar munaso mu binne abinda yake tattare da rayuwarmu.

"Kayi shawara mai kyau Ranka ya dade, kayi hakuri mu bashi abinda yakeso, ni inaga wahala ma"

kadai ya isheta a gadan nan da batada kowa.

Kai Abdulsalam ya jinjina yace  inka fita kasa a kira Zeena.

"Nan Shamaki yai sallama, a waje ya bada sakon Takawa sannan ya tafi."

"Zeena wacce tunda ta shigo bangaren Hajjo ko kala batace ba, duk kuwa da maganar da Hajjo ta"

mata bata iya tankawa ba.

Zubair ne ya kalli Hajjo yace  Hajjo kin bincika mai Junaid suka tattauna da Mai Martaba?

Hajjo ta kalleshi tace  Zubair sau nawa zaka tambayeni ne? Menene matsalar ka ne nikam?

Bantaba ganin ka cikin wannan yanayin ba.

Ya kalleta fuska a kumbure yace  Hajjo bakiga yaran nan bane shi yasa.

Tsaki taja tace kaidai kayi kokarin bin karatun ds akema karka kuskura ka bari yaran nan ya sake

wulakantani dan wlh bazan taba yadda ba.

Baki yadan kara kumburowa sai dai baice komai ba.

Harara ta bugawa Zeena tace  Ke bansan iskamci kinshigo ko kala bakice ba.

Fure ce ta shigo da sallama ta zube tace  Gimbiya Mai Martaba yana nemanki.

Wani murmushin jin dadi Hajjo tai da alama Sarki ya yanke hukunci akan maganar Sulaiman

datamai.

Mikewa Zeena tai kamar mara rai ta nufi kofa.

Hajjo ta sake wani murmushi jin dadi.

Nace Zai zama kuka @&

*******

Zeena ce dukufe a gaban Mai Martaba ya kalleta yace  Zeena!

Kallansa tai tace  Naam Abba.

Shiru Abdulsalam yai kafin yace  maganar Junaid namai magana.

Kallansa ta sakeyi sai dai batace komai ba dan ta riga tasan me zai karasa ce mata.

Sai ji tai kuwa yana cewa  Yace inhar zai aureki sai dai ya hada da yarimyar daya taho da ita.

Shiru tai wanda hakan yasa

Please Login or Register in order to submit comment