google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ita nake so ba ubanta ba”

Ya faɗa yana fesa turare a jikinsa. Sannan ya ɗauki glass ya saka ya ɗauki makullin motarsa ya fice. Kai tsaye gidan ƙanen Babansa ya nufa, daman yasan a irin wannan lokacin yana gida kamin yaje gurin da yake aikin ƙira. Har ciki gidan ya shiga, sai qani ƙyaƙƙyami yake da ginin ƙasa, ya gaisa da matansa sannan suka fito waje suna tattauna maganar auren da Asim yake labarta masa na Mardiya akan maganar tura magaba, a nan suka kitse maganar sati mai zuwa sai nemi sauran ƴan'uwa suke je su nema masa aurenta, sannan kuma ya ɗora masa da maganar gidan da aka ce masa akwai amman milinya takwas ne.

Gidan ba shi da nisa sosai da unguwar hakan yasa suka ƙarasa da mota aka kira Mai gidan ya shiga da Asim ciki ya ga komai. Ya yaba da gidan sosai, komai na cikin gidan sabo ne ga sabo fenti ga fulawowi daman irin gidan nan ne da ake ginawa sababbin a saida. Ko tayawa Asim be yi ba, suka kutse magana akan idan ya dawo daga sokoto zai zo tare da shedu a bashi makulin gida takardu shi kuma ya bada kuɗi. Mutunen sai godiya yake ganin Asim be taya ba ya amince zai ba shi kuɗin. Bayan sun dawo ya aje Ƙanen Baban nasa ya miƙa masa dubu ashiri, sannan ya kama hanyar gidan Hajiya Sadiya yana aikawa Namra kira.....


Tsaki yaja bayan ya kashe wayar, lallai ma yarinyar nan ta raina masa hankali, shi zata yi ma ɓoyun ɗansa? Allah yasa ma da gaske ta zubar da cikin nan ta ga yadda zai yi da ita ƙut! ya yi ƙwafa.

Yayi mamakin ganin Hajiya Sadiya a gidan nata, bayan yasan a wacan take zama saboda ƴarta. Bayan sun gaisa ya zauna saman kujera yana kallonta.

“Mun yi waya da Alhaji yace na same shi sokoto, kuma na samu labarin Namra tana sokoto har ma na yi waya da ita, amman kin san ba lallai ba ne ta amince ta dawo gidana ba ko?”

“Nasan da hakan shiyasa ka ga na dawo nan gidan ai, nasan zaka zo nema na, abunda nake so da kai ka yi ta try har sai kaga ta aminci, idan kuma hakan be samu ba, to zan baka abunda zaka bata, kuma ka tabbatar ya kai ga bakinta, ma'ana ta ci”

“Mi zaki ba ni?”

“Ina zuwa”

Ta miƙw tsaye ta nufi wani bedroom. Shi kuma ya ƙurawa pop ido kamar yau ya fara ganinsa.

“Wallahi duk kika zubar min da ciki ko? Hmmm, Allah yasa ma Ubanki ne ya zubar da shi ta yadda zan fi jindaɗin shari'ah da shi...”

Fitowar Hajiya Sadiya ce tasa ya mai da dubansa gareta yana kallon farin ƙyalen da ke hannunta. Tana ƙarasowa ta warware ƙyalen ta miƙa masa apple ja.

“Ka tabbatar ta ci wannan apple ɗin ko da kaɗan ne, amman sai idan ta ƙi yarda ta koma ɗakinta”

Ya ƙurawa Apple ɗin ido

“Kar fa wani abu ya same ta, i mean kar ta mutu, akwai baby na a jikinta”

“Babu abunda zai same ta, ka yi yadda na ce kawai”

“Okay”

Ya miƙe tsaye tare da saka apple ɗin a aljihu, ya fice. Be yi nisa da barin gidan ba Nably ta kira shi, amman sai ya samu kansa da ƙin ɗauka shi kwata-kwata yanzu ta fita ransa, Mardiya ce on top.





KU YI HAƘURI DA WANNAN🙏

*Ku yi ta yaudarar kan ku da sunan wata ta siya ta ara muku ku karanta, idan mun je can inda baki be magana zamu tsaya gaban Allah ni da ku ya mana hukunci.*

HILAL POV.

SIX MONTHS LATER...
Suna jin ƙarar tsayawar Motar Dadynsu suka fita da gudu suna masa oyoyo. Zaune suka same shi cikin motar yana waya, hakan yasa Ezzah zagayawa a front seat ta zauna tana jiran ya gama wayar ta fara masa complain.

“Dady muna dawowa daga makaranta Mama Teema tasa mu wanki”

Yana sauke wayar daga kunnensa kenan, ta soma labarto masa abinda ya faru yau. Wani kallo yake mata, irin kallon nan na ɗa da ƴa, kamin ya kai hannunsa ya kama fuskarta ya riƙe.

“Ezzah kin yi ƙanƙanta da irin abubuwan nan, kullum sai kin ce Teema ta miki kaza bla bla bla, wannan sam be dace da ke ba, babu abunda Teema zata muku sai tarbiya, ƴar'uwarki bata taɓa faɗar an mata wani abu ba sai ke”

Ta turo baki zata masa magana da kuka a lokaci ɗaya.

“Dady ni bana son ta, a kawo mana Mummie mu”

“Ba za'a kawo ba, kuma kar bakin ki ya ƙara furta kalmar ƙi ga matata, ke kowa ai baki so, har Kalsoom ba haka kika mata ba? Saboda ku Hajiya tasa na auri Teema yanzu kuma ki bijiro min da wannan maganar! Kar na sake ji”

Ya fita daga motar ya kama hannun Ulfah, sannan Ezzah ta fito ita ma tana share hawaye ta rufe masa motarsa, ta rufa musu baya.

Teema na tsinkayarsu dan tana tsaye jikin window ne, sai dai ba zata iya jin me suke cewa ba. Tana ganin ya doso ƙofar falon sai ta bar gurin da sauri ta shige bedroom ɗinta ta zauna bakin gado ta soma ƙirƙiro kuka. Tun da ya saka kafarsa a falon ya ji be ji motsin Amaryarsa ba ya saki hannu Ulfah ya doshi bedroom.
Zaune ya same ta bakin gado tana rusar kuka, zama yayi kusa da ita cikin damuwa, dan yasan dalilin kukan nata baya buƙatar tambayarta.

“Sau nawa zan faɗa miki ki yi haƙuri Teema? Wasu ma sai da suka shekara ashiri a gidan miji sannan Allah ya ba su haihuwa, balle ke da baki yi shekara ɗaya ba ma?”

Ta ɗago kai ta dube shi.

“Hilal ina tsoron kar a'ce ba zan haihu ba ne gaba ɗaya, tun da na zo gidan nan ko ɓari ban taɓa yi ba”

“Idan Allah ya ga dama zai baki just be patient, wani lokacin abun mutum nesa yake, na shigo da farinciki kuma kin rusa min shi”

“Ka yi haƙuri rai na ne yake ɓaci”

Ta share hawayenta, har ga Allah wannan matsalar tana damunta, sai dai ta kan yawaita yi ma Hilal kukan hakan ne gudun kar ya zargi ta ci amanar ƴaƴansa, duk lokacin da ya tarar da ita cikin irin wannan halin ya kan kasa mata maganar yaran, ko da kuwa sun je masa sun kai masa ƙararta ne.

“Kuɗin da na faɗa miki muna jira jiya dai Allah yayi sun fito, dan haka yanzu ki shirya muje kasuwa da yara mu yi siyayya, gobe kuma zan je da Kalsoom Hajiya kuma kuɗi zan bata, sauran kuma sai mu ƙara a account, idan na samu hutu sai mu leƙa waje”

Hannayenta ta kama ta riƙe tana murzawa a hankali.

“Hilal ya kamata ka yi tunanin ma kan ka future, kai kake ta hidima da Hajiya duk da tana da waɗanda zasu iya mata beside Abbah ka yana da rai balle ace ko zata rasa wanda zai mata ne, ya kamata ace ka tanada abun ka har sai ranar da zaka nema ko kuma ita Hajiya zata nema sannan ka ɗauko ka yi amfani da shi, ƴaran ka babu abunda suka nema suka rasa, dan me za'ace a riƙa kashe musu kuɗi haka nan kawai a banza? Ka fara ginawa kan ka rayuwa Hilal, yanzu nan kuɗi ba ƙara ka gina gida da shi ba”

“Ina da gida Teema ba ɗaya ba ba biyu ba uku ba, kuma naga yanzu mi zan yi da gida?”

“Baka mafarki tara zuri'ah kamar ta Mahaifinka? Baka fatar haɗa ƴaƴan da matanka guri ɗaya yanzu? Ni abun da naga ya fi kawai ka kawo ko 150.000k ne asiya mata lace da atamfa, sauran kuɗin kuma ka ba ni nawa ita kuma Kalsoom ka bata ta siya abinda take so, Hajiya na san idan ka bata kuɗin kashewa zata yi amman idan aka siya mata kaya, ko sakawa ta yi ai ka ji daɗi, ni k8ma ina son na fara business”

Miƙewa yayi tsaye.

“Zan yi tunani akai, bari na je na duba Kalsoom ta ce min kan ta na ciwo”

“Ka gaishe min da ita, tun da ka ƙi yarda na ganta, amman ba zaka bari ka ci abinci ba”

“A'a sai na dawo kinsan matsalar mai ciki”

Ya faɗa da murmushi a fuskarsa sannan ya juya ya fice, zuciyarsa da kwankwato, ya lura duk lokacin da ya shigo da zimmar yi ma yaransa ko Hajiya abu sai Teema ta nuna masa ba haka ba, abunda Kalsoom da Rashida ba su taɓa masa ba kenan. Duk da yana tunanin wannan karon ta yi magana mai ma'ana kuma da bada dalili. Miƙewa ta yi ta rakoshi har gurin mota, ya shiga ta maida ganbun motar ta rufe tana ɗaga masa hannu har ya fice.

Ajiyar zuciya ta sauke, ta gaga mallakar mijinta har yanzu, iya shige-shigen da take tunanin zata yi ta yi amman kan Hilal ya gagara mallaka, bata da ƙudiri raba shi da mahaifiyarsa, sai dai tana ganin kamar hidimar da yake mata yayi yawa, tun da ba shi kaɗai ta haifa ba.

“Ulfah, Ezzah..!”

Sai ga su da gudun su, bama Kamar Ulfah da hanjin cikinta ke kaɗawa, dan jikinta har rawa yake kamar zata saki fitsari.

“Uban mi kuke faɗawa Baban ku ɗazu...?”

Ulfah ta yi sauri ɗaga hannunta sama.

“Wallahi ba ni ce ba, Ezzah ceta faɗawa Dady wai kin sata wanki”

Teema ta miƙa hannu ta kama kunnenta har sai da ta yi ƙara.

“Wato dan na saku wankin uniform shine abun magana? Ke komai sai kin kwashe kin faɗawa Dadynki? Sau nawa nake ja miki kunne akan faɗawa Dadynki magana idan na miki abu?”

Ta nuna mata wani ɓangare na gidan inda rana ta baje a gurin, kamar an hura wuta.

“Oya wuce can ki kama kunnenki, kuma karki taso sai na ce ki taso”

Da sauri ta ɗuka ƙasa ta riƙa kafafun Teema.

“Dan Allah ki yi haƙuri ba zan sake ba”

“Wannan tsinin bakin na ki ba, ke me baƙi hali tun da kin yi mugun gado ko? Kije ki kashe min aure! Ke ce uwar rashin kunya uwar gulma ko? Zaki ci ubanki a gidan nan ba dai duk lamanin da na ke miki baki gani ba”

Ta faɗa tana matsar bakinta. Daman ta saba yi mata irin wannan horon a duk lokacin da ta yi mata ba daidai ba. Ta buge mata hannu.

“Ba zaki wuce ba sai na yi ƙwallo da ke?”

Ulfah ta sa kuka.

“Mama Teema Wallahi ba da ni ba”

“Ai ba da ke ba ita kaɗai, ki ki wuce ki gyara min kitchen”

“Tau”

Ta wuce da gudu idonta cike da ƙwalla. Ezzah kuma ta tashi tana kuka ta nufi gurin da ta saba tsayawa kama kunne ta kama kunnenta.

Juyawa Teema ta yi ta koma cikin falon, har ta zauna sai kuma ta miƙe tsaye ta nufi bedroom ɗinta tana ta saƙe-saƙe a ranta. Wani irin ihu ta ji da muryar Ulfah ba shiri ta zaɓura ta fito daga bedroom ɗin a firgice ta nufi kitchen.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Na shiga uku uban waya aike ki taɓa miya?”

A razane ta yi furucin kamin ta ƙarasa gaban Ulfah da ke kwance ƙasa lame-lame tana murje-murje da ihu kamar bata san inda take ba, jikinta har ya sale.
Har ta ɗaga ta tasheta sai kuma ta saketa ta fita a firgice tana kiran Ezzah.
  Karo suka yi ita da Ezzah duk ta haɗa uban gumi.

“Mama Teema ga ni”

“Je ki Kitchen ki kama ƴar'uwarki yi sauri”

Ita kuma ta juya da sauri ta koma ɗakinta dan kiran Hilal.

KALSOOM POV.

tana zaune falo Hilal ya shigo bakinsa ƙunshe da murmushi da kuma sallama a lokaci ɗaya. Itama da murmushin ta amsa masa tana ƙara miƙarda ƙafafunta. Kusa da ita ya zauna daman tana zaune ne saman carpet ya kai hannu ya shafa ƙananan kitson da ke kanta yana murmushi.

“A bani canji na na kitso”

“Ba wani canji mai kitson ma ta ce sai an ƙaro”

Dariya yayi ya kai hannu ya shafa cikinta.

“Sai kice mata ai ke mijinki bawan Allah ne, ba mai kuɗi ba ne”

“Ba wani nan, ni sai ka ƙaramin”

“Baki da matsala yarinya ko nawa kike so za a ba ki, ƙuɗin da na ke faɗa miki ina jirajiya sun fito”

Ta zaro ido.

“Da gaske Alhamdulillahi”

Ya lanƙaci hancinta.

“Yes”

“Allah yasa musu albarka”

“Amin mi kike so a siya miki?”

“Ka fara cirewa Hajiya nata, sannan mu sai kuma ƴaƴanka, kai ai ko baka samu ba, ba matsala”

“Sai dai na ɗauki na ki”

“Ba matsala ai daman ni bana siyen komai yanzu”

“Ko da kin haihu?”

“Hilal anya zan haihu?”

“Haba ki daina wannan maganar mana, ke da Teema maganar haihuwar nan na ku ya ishe ni”

“Ƙara ita ai bata yi cikin ba, ni kuwa shekara har da wata huɗu ban haihuwa ba, cikin nan ya ishe ji nake kamar na cire shi na aje”

“Zaki haihu inshallah, tun da an bincika babu wata matsala”

“Allah yasa”

“Amin. Zaki haifa min Baby girl mai kama da ke”

“Baby Boy dai zan haifa mai kama da kai”

Bakinshi ya kai zai yi kissing ɗinta sai wayarsa ta yi ringing, kawar da fuskarta ta yi dan ta bashi damar picking ɗin wayarsa.

“Hello...”

Ya miƙe tsaye da sauri.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, gani nan zuwa”

“Miya faru? ”

Kalsoom ta tambaya a firgice.

“Wai Ezzah ne da Ulfah suka yi faɗa shine Ezzah ta watsa mata miya”

“Subhanallah miya haɗa su haka, ko na ɗauko hijab ɗina muje tare?”

“A'a zauna duk yadda aka yi zan kira ki”

Ya fice a firgice. Daker ta unƙura ta miƙe tsaye da tulelen cikinta.

Yana isa ya ɗauke ta suka yi asibiti tare da Teema, Emergency ya wuce da ita surgical Ward, wata Dr Khadija ce ta shiga bata taimakon gaggawa, dan Dr Hilal tsaye kawai yayi yana kallo saboda jikinsa duk ya mutu ko da suka kawo ta asibitin ma ta suma.


AMIRA POV.

Tun da suka kamo hanyar sokoto take ta aikinki kuka, har suka iso sokoto idonta ya kumbura sosai. Direban na yin horn a bakin gate ɗin gidansu, ta jita cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, wani sabon kuka ne ya sake rufeta, musamman lokacin da ta ji muryar mai gadin su yana tambayar wa suke nema.

“Amira na kawo ka min magana da iyayenta zan danƙata hannun Mahaifinta ko mahaifiyarta”

“Amira...!”

Mai gadin ya daki ƙirji. Kamin Direban ya sauke gilashin motarsa ya hango Amirar ce da gaske. Jiki na rawa ya wangale musu gate sannan ya shiga cikin gida da gudu.
Sai ga Mahaifiyarta da duka ƙanenta sun fito har da Baban yayanta. Duk motar suka nufa. Ammy ce ta fara buɗe motar sai ga Amira ta fito daga ciki tana kuka, suka rumgume juna, ƙanenta kuma suka daka tsalle suka yi kanta, Big bro ɓata ne ya tsaya a gurin ya dake yana kallon ikon Allah.

“Ke ce Mahaifiyarta?”

Ammy bata iya amsawa ba sai kuka take, Babban yayansu ne ya amsa da.

“Eh ita ce, waye kai?”

Ya fiddo id cart ɗinsa ya nuna masa,sannan ya miƙa ma Ammy waya.

“Zaki yi magana da Ogan mu”

Cikin muryar kuka Ammy ta ce

“Hello”

“Ke ce Mahaifiyar Amira?”

“Eh nice”

“Kina magana da Major Abdallah Ahmad Mai-doki, da ga rumdunar bada tsoro ta Kasa wato Nigerian Army, da fatar ƴar ki ta shiga hannun ki”

“Ta shigo na goɗe muku”

Daga hakan ɗireban ya janye wayarsa ya buɗe motarsa.

“Wait...”

Big bro nata ya faɗa sannan ya ƙaraso kusa da shi.

“Ina kuka haɗu da ita?”

“Ba ni da wani abun da zan ce ita zata muku bayanin komai da bakinta”

Ya shige motarsa ba tare da ya tsaya jiran abunda zai ƙara tambayarsa ba ya juya a guje ya bar gidan. Sai da Ammy da Amira suka ci kukan su sosai a gurin sannan suka shiga cikin giɗan still suna kuka ita da ƴarta.

NAMRA POV.

“Miya haɗa ki da Yasmin?”

Anty Amarya ta tambaya.

“Ba komai saboda kawai na ƙi amincewa ta maka Uzair kotu ne”

“Kotu a wane dalili?”

A nan Namra ta labarta mata yadda suka yi da Yasmin.

“Karki yarda da ta sa sake jefa ki cikin halin da mahaifin ki zai tsane ki”

“Nima ba zan yarda ba Anty idan munje lahira Allah zai mana hukunci ai”

“Wannan shi ya fi, kin samu kin dawo gida kuma za su kawo miki wani ruɗani, qaya sani ko da mijinta aka haɗa kai ta aikata miki haka”

“Ƙoma ba da shi ba ne babu ta yadda zan yarda ta kai mijinta kotu saboda ni”

“Hakan ya yi ki karya kije ki gaishe da mahaifinki, breakfast ɗin ki na nan dinning”

“To na gode”

Tare suka fito da Anty, suka zauna dinning sai tattauna maganar suke, bayan ta gama karyawa ta koma ɗakin Anty ta ɗauki Hijab ta saka ta nufi part ɗin Abbah.

“Assalamu alaikum”

Ta faɗa yayinda ƙafafunta duka biyu suka tsunduma cikin falon Abbah. Abbah dake dinning area ya ɗago ya kalleta idonsa sanye da farin gilashi fuskarsa kuma ɗauke da murmushi.

“Mamana”

“Na'am Abbah ina kwana”
Ta duƙa har ƙasa ta gaishe shi tare da Hajiya Barau dake ƙoƙarin barin dinning ɗin, kamar zata fasa ihu tace wayyo haka ta bar falon. Sai Abbah ya nunawa Namra kujerar da ke kusa da shi.

“Zo nan ki zauna Mamana”

Ta zauna cikin wani irin jindaɗi marar misaltuwa.

“Kin tashi lafiya, kin karya ko?”

“Na karya”

“Mamana ina son na tunatar da ke akan rayuwa. Ki riƙa haƙuri da abunda ya same ki, kar hakan ya saka ki sakewa ko kuma wani tunani, ko wane bawa da irin ƙaddararsa, dukan abunda ya faru ga bawa zai zamo masa darasi ne ko kuma izna ko wata hanya ta samun cigaban rayuwa, ko da kuwa abun nan mai daɗi ne ko akasin haka, dan haka bana son ki saka damuwa a ranku ni dai na yafe miki, kuma ina son idan kin ɗan hutu kin samu sawaba sai kuma ayi maganar karatu, ina tunanin idan kika koma makaranta sake fi sakewa ki manta da komai”

“Na gode sosai Abbah Allah ya saka maka da alheri, kamin abunda ban taɓa mafarkin zaka min ba, ni kuma na maka alƙawarin va zan sake tsallake zaɓinka ba har a bada ko da kuwa a tufafi ne”

“Allah ya miƙe albarka, ni zanje na shirya akwai inda zan je kwana biyu nan ban samu na fita ba”

Ya miƙe tsaye yana faɗar hakan, ita ta miƙe tsaye.

“Tau Abbah Allah ya tsare”

“Amin”

Ya nufi hanyar da zata sadashi da bedroom ɗinsa, ita kuma ta juya ta fice zuciyarta cike da farinciki.
Ko da ta dawo part ɗin Anty ta tararda su Maryam sun dawo, ga manyan ledoji a gabansu amman sun riƙe baki sai mamaki suke, da alama akwai abunda ya faru.

“Lafiya?”

Maryam ta riƙo hannunta.

“Ke ƴar gidan Abbah wai Amira ta dawo”

“Amira kuma? Daman tun tafiyar da ta yi bata dawo ba sai yanzu?”

“Wallahi sai yanzu, kuma jiya ita ma ta dawo kamar ke”

“Amman kun ji wani abu game da ita?”

“A'a nima Iklima ce take faɗa min ta dawo”

Anty Amarya ta ce

“Allah ya kyauta”

Duk suka amsa da Amin.

UZAIR POV.

Yana shiga bedroom ɗinsa ya fito ya nufi na Yasmin dan yana son ya bincika ko da akwai sauran abunda ta boye, jikinsa na bashi ba saƙon wasiƙar ne kawai ba. Bincike ya fara mata cikin durowoyin ɗakinta kama ya koma gurin wasu takardu da suke gefen gadonta, be samu abunda yake so ba, sai kaiwa ya juya ya fita ya nufi wata ƴar ƙaramar durowarta da take aje takardun aikinta da littafanta duk ya bi ya watsar sai bincike yake mata. Wani abu ya ji ya tsoki tsararsa, kamar an soma masa mashi a kunkuru, tun yana juriya da riƙe kunkurun nasa har ya ji abun ya ƙara sukarsa da wani mugun zugi, wata zarananniyar ƙara ya saki yana jin abun masa ƙasa cikin ƙashin ƙafafunsa, ihu kawai yake yana mirgina, abun ba kyau maza a ƙasa😖

Da gudu mai aikinsu ta so kansa tana tambayar ba'asi. Ganin abun ba na banza ba ne ƴasa ta fita neman mai gadi ko zai iya taimakawa. Ko da Mai gadin ya shigo Uzair wani abu yake kamar mai ɗaukar rai. Da sauri Mai gadi ya kira Yasmin ya faɗa mata abinda yake gudana.

YASMIN POV.

“Zan turo maka number ka kira mahaifiyarsa ka faɗa mata”

Amsar da Yasmin ta mayar masa kenan ta katse kiran, ta aika masa number sannan ta cigaba da kuka tana zanawa mahaifiyarta abubuwan da Uzair yake mata wanda hakan kawai ya isa ya tabbatar da gaskiyar abunda ya yi ma ɗanta, bayan ta fito gidansu Namra ta nufo gidansu dan ta na jin bata buƙatar komawa gidan a yanzu.

“Ko ma minene shiru ya kamata ki yi ki rufawa mijinki asiri”

“Irin wannan rufa Asirin ne yasa mata da yawa maza suke cutar da su, idan aka muku fyaɗe ko aka yi ma ƴaƴansu, wannan abun yana cutar da mata da yawa, mu muke faɗar a daina ɓoye abu a riƙa fitowa a ana faɗa yau kuma sai a same ni da wannan aikin na ɓoyewa? Ɓoyewar nan da ake shi kw basu damar ƙara aikata abunda suke aikatawa, at least ko da ba a hukunta su ba, duniya zata kunyata su kuma asan ko su waye, ban ga dalilin rufawa Uzair asiri ba ko da kuwa ubana ne balle mijina, ina yawan faɗar cewa ni dai i would never in my life encourage anyone to live with an adulterer tun da har Allah ya ce a jifasu su mutu, they are as good as useless to be seen alive in this world, sai kuma na zama ni ce zan rufa masa asiri miye amfanin aikina?”

“Nidan indai zaki ɗauki shawarata ban ga abun burgewa ga mace ta kai mijinta kotu ba da sunan wai yayi ma ɗansa fyaɗe, kina da hujja ne?”

“Ko bana da ita dole zan samo ta”

“Ni kam ba da yawun baki na ba Yasmin wannan sam be dace ba, idan ma zama ne ba zaki iya da shi ba, sai ki nemi ya rabu da ke kawai ki hutu”

Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


AMIRA POV.

“ji na yi gidan nan ya isheni ina ta jin kamar idan ban gudu ba wani abun zai iya faruwa da ni. Ban tsaya ɗaukar komai ba sai kuɗi, tun daga lokacin da na bar gidan nan nahau mota na kama hanya ban sake sanin inda nake ba, ban san inda direba ya sauke ni ba ban san ya nayi rayuwa ba, sai a ƴan kwanakin nan da wannan sojan ya tsince ni a bolar gidansu, shine yayi ta min addu'ah da komai har hankalina ya dawo, na faɗa masa inda nake ya saka direba ya kawo ni gida”

Duk kai suka girgiza cike da tausaya musamman Ammy da ke kuka kamar yadda Amira ta ke yi.

“Amman Namra ta ci amanar abota, ai gashi nan ta fara ganin abunta, ɗazu-ɗazu hajiya Haulat ta ƙira ta faɗa min ita ta dawo gida aure ya mutu, kuma ance can gidan auren ta ci kwakwarta”

Salman Big bro nasu ya kalli Ammy dake wannan maganar yana faɗin

“Ai ba laifinta ba ne, ita Amira ai cin amanar ta tashi yi, da yanzu da gaske ne idan an sakawa Namra wannan abun maganin zai kamata ai kim ga ita ta ci amana kenan, waya sani ma ko koma miki ne yayi, a haɗa baki da ke a sace ta har a ayi mata ƙazafi, wallahi kun ci amanar juna ke da ita”

Abban Amira ya ɗaga masa hannu cikin ɓacin rai.

“Idan kasan bakin ka ba alheri zai faɗa ba, ka tashi kawai ka bar falon nan. Allah zai saka miki Amira zura mata ido kawai daga ita har ɗan'uwan na ta”

“Wane irin a sa muku ido? Aja mata haƙƙinta dai, babu irin abunda ba'ayi ba amman yarinyar nan ita da mahaifiyarta suka tsaya kai da fata akan babu hannunsu a ɓatan Amira, aka kiɗa aka raya aka daka yarinyar ta ƙeƙashe ƙasa tace bata san gaibu ba akan ɓatan Amira sai yanzu kuma gaskiya ta bayyana za'ace a ƙyaleta”

Taɓe baki Salim yayi ya miƙe tsaye ya fice daga falon.

“Babu wani haƙƙi da za a ja mata ku zuba musu ido kawai, ko bayan rage kika zagaya kika ɗauki wani hukunci sai na ɓata miki rai Wallahi, tun da na ce a bar maganar nan barinta shine ya fi kawai”

Ya miƙe tsaye ya fice daga falon. Kuka sosai Amira take, sai dai ba kuka dawowa gida ba, kukan rabuwa da Abdool tana jin kamar zata mutu idan ta tuna baya kusa da ita a yanzu.

ABDOOL POV.

Ya ware hannayensa.

“You see Ummi na faɗa miki Mai Martaba bashi da matsala,

Please Login or Register in order to submit comment