You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
mu ga Allah muka fito kuma a gare shi za a maiyardar mu. Wanɗannan gafara da kyakkayawan yabo daga Ubangijinsu sun tabbata gare su, da rahama kuma waɗannan sune shiryayyu.” (Baƙara: 155-157)
Tuna waɗannan ayoyin ya ankarar da ita abubuwan data manta, ji tayi kamar an tsikareta, gashin jikinta ya tashi, a nan ta soma tambayar kanta, dan me zata yarda zuciyarta ta rinjayeta ta tsaɓi Ubangijinta? Ta fita daga waɗancan bayin da Allah ke yabo? Ashe Ubangijinta be mata dukan gata ba? Ashe daman Imaninta ƙanƙane ne?
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta furta a fili, har sai da mai Napep ɗin ya kalleta.
“Hajiya lafiya dai?”
“Lafiya ƙalau dan Allah juya da ni ka kai ni babbar Asibiti”
“To amman fa wasu kuɗin zaki sake biya”
“Na ji mu tafi”
“Tau Hajiya lafiya kike kuka?”
Sai a lokacin ta tuna da hawayen dake fuskarta, sa sauri ta share hawayen ba tare data ce masa komai ba har suka isa asibitin, sannan ta fita ta ciro kuɗinsa ta ba shi.
Ko da ta shiga cikin ɗakin Asim na zaune, kamsa ya kumbura sosai har idonsa ɗaya ya liƙe, hankalinta ya tashi dan yanzu wannan kumburin ya fi na jiya.
Kusa da shi ta zauna zuciyarta cike da tausayinsa, har idaniyarta na ƙoƙarin zubar masa da ƙwalla.
“Asim kaga har yanzu Anty bata kira ba, kuma bata aiko ba, ni kuma bana da wata mafitar, ga kuɗi da ake bina ma ban san yadda zan yi ba, wannan kumburin naka yana tsorata ni”
Ya matse ƙallah data cika masa ido.
“Namra ko gida za mu koma ne?”
“Idan mun koma za su ce mun kwaso ciwo mun dawo”
“Likita yace idan ba allura nan aka min ba yana da wahala naji sauƙi da wuri”
Hannayenta tasa ta rumgume shi tana kuka. Shi kuma a take yaji sha'awarta ta saukar masa, ya kai hannu yana ɗan shafa ta. Data anƙaro da abunda yake nufi da ita sai tayi saurin ɗagowa daga jikinsa.
“Ina Mama?”
“Tana waje”
Ya sake miƙa hannu yana shafa fuskarta, yana ƙoƙarin ɗaga hijabinta ya zura ɗayan hannunsa ciki.
“Asim asibiti muke fa, kuma dubi halin da kake ciki”
Yawun bakinsa ya haɗe, ba tare daya daina abunda yake mata ba. Ana taɓa ƙofar ɗakin tayi saurin tashi tsaye, shi kuma ya bita da kallo idonsa har sun fara canja kala.
“Mama ina wuni?”
“Lafiya ƙalau ya rana?”
“Alhamdulillah”
Ta ɗan kalleshi cike da kunya, dan gani take kamar Mama ta lura da abunda suke.
“Bari naje gurin Hajara”
Bata jira abunda zai ce ba ta fice. Sai Mama ta zauna a kujerar dake kusa da Asim tana faɗin
“Lamarin nan naka fa ƙaruwa kawai yake yi”
“Tau Mama nayi maganar kuɗin adashen nan kin kawo wasu hujjoji na daban, ko mutuwa na yi ai ke kika rasa ni tun da su ƴar su wani zata aura”
“Shawara da nake kenan a zuciyana, zan je nayi mata bayani sai na karɓo kuɗin daman dubu ɗari uku ne, idan Allah yasa ka samu sauƙi sai a shiga wani kuma”
“Haka yafi, tun da kin ga har yanzu basu saje kira ba ma balle su aiko. Yaushe zaki je?”
“Gobe nake son naje, nima kuɗin da suke hannun na duk sun tafi gurin siyen abinci, ga tufafin nan ƙala ɗaya kullum ƙara naje ya ɗauko wasu tun da waɗanda muka zo da su sun ƙone, da Hajara zan koma in yaso sai na dawo ni kaɗai, daman Haruna ya matsa da maganar yaushe zata dawo”
“Ni Wallahi inda da hali ma da kin tafi yanzu, sai ki dawo gobe da wuri, dan ni kaɗai na san halin da nake ciki, kuma kin ga yanzu aka yi ƙarfe ɗaya, nasan zuwa yamma kin isa”
Ta ɗan yi shiru tana nazari.
“Rana be yi ba?”
“Be yi ba Wallahi, tun da kin ga ma Namra ta zo sai ta zauna nan har ki dawo”
“Tau bari na gani, ai duk na natse ma da wannan kumburin na ka”
Ta tashi ta fita cikin yanayin damuwa. Wayar Asim dake hannun Hajara Namra ta karɓa, ta saka number Babban Yayansu ɗan Hajiya Barau, sai ta matsa can nesa da Hajara ta kira shi.
KALSOOM POV.
Ba itace da girkin ba, amman sanin halin Rashida yasa bata tsaya jiranta ba ta shiga kitchen ta ɗora musu breakfast, daman wani lokacin ita take shirya musu tun da Rashida aiki take zuwa.
Sai da ta shirya komai, na karyawa sannan ta ɗauko kulolin su ta zuba musu abincin su, sannan ta kira su ɗaya bayan ɗaya ta miƙa musu kulolin.
“Ku je gurin mota zan tashi Daddyn ku yanzu”
Ta nufi ɗakinsa, tana buɗe maɓallan rigar bachin ta. A tsakiyar gado yake kwance yana lulluɓe irin yana jin tsayi ɗin nan.
Air conditioner ta fara kashewa sannan ta nufi window ta buɗe su duka ta ɗage labulayen sannan ta nufo inda yake kwance ta yaye bedsheet ɗin tana taɓa masa kunne.
“Likita tashi safiya yayi fa”
Hannu ya kai ya janyo ta saman gadon ya rumgume ta
“Ban gaji da bachi ba”
“Yara suna gurin mota suna jiran ka”
“Ya salam”
Ya ƙara rumgume ta tsamtsam ƙirjinsa, kamar ba zai tashi ba, sai faman lumshe ido yake alamar bachi na masa daɗi.
“Doc. Doc. Doc”
Shiru be motsa bama balle ya amsa ta, hannu ta kai ta murɗa masa kunne, har sai da tayi ƙara ya kama hannunta ya ciza sannan ya tashi, yana jan kitson ta.
“I hate dis Morning”
“Really”
Ta tsire baki tana koyonsa.
“I hate dis Morning”
Ya zare ido, lokacin da idonsa suka kai kan ƙirjinta.
“Wow”
Ya kai hannu zai taɓa ta, ta fisgi kanta cikin zafin nama, ta sauka saman gado ta fice daga ɗakin tana masa dariya.
Tashi yayi ya shiga bathroom ya wanke bakinsa da fuskarsa sannan ya fito ya kai yaran makaranta. Ko da ya dawo babu kowa falo, sai kawai ya nufi ɗakin Rashida dan yaga motarta waje alamar yau bata fita da wuri ba kenan.
Tana ganin ya shigo ta juya kwancinta ta bashi baya. Hakan be da me shi sai ma dariya da yayi ya ƙarasa kusa da ita ya juyo da ita, hawayen daya gani a idonta ya tashi hankalinsa.
“Lafiya Pyar?”
“Bana jindaɗi ne”
“Me ke damun ki”
“Nima ban sani ba”
“Amman miyasa baki faɗa min ba?”
“Taya zan faɗa maka bayan ta shiga haƙƙina taje ta tashe ka, kuma ta san yau ba girkin ta bane”
“Ta riga ta saba ne, saboda kina fita sa sassafe ba tare da kin damu da tashi na ba, balle haɗa mana abun karyawa”
“Ni gaskiya ta daina shiga min haƙƙi bana so”
“Shikenan zan mata magana, amman yanzu faɗa min me kike ji yana damun ki”
“Fever, sneeze, headache and nauseous”
“Zan diɓi jininki da fitsari idan zan fita, yanzu tashi mu karya sai ki sha magana”
Ta ƙara manne masa a jiki.
“A'a ni bana so cin komai”
“Tea fa?”
“Sai dai idan kai zaka haɗa min da kan ka”
“Yes ni zan haɗa miki ai”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya tashi ya fice. Ajiyar zuciya Rashida ta sauke, ranta yana mata ba daɗi, idan har zarginta ya tabbata gasjiyar tana da ciki, tana cikin matsala dan bata iya tantance na waye ne,
‘Taya wani zai gane idan ba ni ma faɗa ba?’
Tambayar da tazo mata kenan a zuciyarta, sai kawai ta tashi ta shiga banɗaki.
Hilal sai da ya shiga ɗakinsa ya ɗauko maganinka sannan ya nufo ɗakin Kalsoom, a lokacin tana zaune gaban madubi tana shiryawa dan fitowarta daga wanka kenan.
Daga bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yace
“Wifey Yau madam babu lafiya, ba zata fito ba tea kawai zata sha, ni ma kuma bana jin cin komai”
Kai ta ɗaga masa tayi murmushin da be kai zuci ba. Har ya wuce, sai kuma ya dawo ya tsaya bakin ƙofar ya miƙa mata hannu.
“Taso na haɗa miki breakfast”
Ba musu ta taso ta miƙa masa hannun ba dan ranta na mata daɗi ba. A kujerar data saba zama ya zaunar da ita, ya ɗauki kofi biyu ya haɗa tea, ya aje mata ɗaya gabanta ya zuba mata ƙwai da sauran abubuwan da suke gurin, sannan yaƴi mata kiss ya ɗauki tea ɗin ya nufi ɗakin Rashida.
Da kallo ta bishi, zuciyarta na sosuwa da lamarinsa, tabbas yana son matarsa fiye da yadda yake son kansa, yanzu ya kasa karyawa saboda bata da lafiya, ta lura da yadda yanayinsa ya canja a take, taya zata shiga rayuwar irin waɗannan ma'auratan sannan tace zata samu farinciki?
Hannu ta kai ta shafa cikinta, hawaye masu zafi suka silalo daga idonta.
Sai da ya bata tea ɗin tasha sannan ya bata magani, sai ya sake fita yaje ya ɗauko wasu robobi guda biyu ya miƙa mata babbar.
“Kiyi fitsari a wannan”
Hannunsa sanye da safa, ya ɗibi jininta ya zuba a ƙaramin robar sannan ya manna mata kaɗa ya lunda mata, ya kwance robar daya ɗaure mata hannun da shi, kwashe kayan yayi ya fice. Bayan kamar thirty minutes ya dawo ɗakin da shirinsa na zuwa office.
Robar fitsarin ya ta bashi, ya karɓa yayi mata kiss, sannan ya fice. Ɗakin Kalsoom ya shiga, tana jin motsinta ta lafe kamar tana bachi, itama kiss ɗin yayi mata sannan ya fice.
Rashida na jin tashin motarsa ta janyo wayarta ta danna number Asmee, ringing huɗu tayi sannan ta ɗauka.
“Asmee an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau ya gidan?”
Ya amsa mata muryarta da alamar damuwa.
“Asmee yau ba zan samu fita ba, bana jindaɗi, sai dai kr kije idan da hali”
“Me ke damun ki?”
“Abubuwa da yawa ga jikin duk ya min nauyi”
“Ko dai ciki ne?”
“Haka nake tunani nima”
“Allah ya raba lafiya”
Jin ta faɗa ba da wani jindaɗi ba yasa Rashida Tambaya.
“Ya naji muryar ki ba daɗi?”
“Ba komai, nima bana jindaɗin ne, amman zan daure a haka naje”
“Yauwa na gode sosai, kin ce dai yana aiki sosai ko?”
“Sosai Wallahi kamar yan kan wuƙa, duk yadda mu kayi zan faɗa miki”
“Okay na gode”
Rashida na kashe wayar Asmee ta fashe da kuka.
‘Allah kasa ba gaske bane Allah, idan har da gaske ne ya ci amanata, tun da yasan yana da shi kuma ya nemi ya kwana da ni, Wallahi dana sani ni dama ban je gunsa neman magani ba, mugun Malami kawai’
Abunda take ta tunani a zuciyarta kenan, a fili kam kuka kawai take, kamar ta cire idonta.
_________________________________________
Kuyi Haƙuri da wannan idan Allah ya bani iko zan kara muku wani anjima.
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Godiya marar iyaka gareki Daughter, na gode na gode I really did not expect this awesome surprise from your side
Allah ya kara arziki 😘
*PAGE - 31*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan seconds ya rage wayar ta fara ringing sai kawai ta kashe, tana tunanin yadda za fallasawa kanta asiri idan har ta yarda ta faɗa masa danuwarta, ba duka ɗan'uwane yake taimako dan Allah ba, ballanta shi data san dole ne ya faɗawa Hajiya Barau, ita kuma fitar da maganar zata yi, sai a fara cewa tana roƙon dangi.
Juyowa tayi ta nufo gurin da Hajara take zaune, ita ma ta zauna tana miƙa mata wayar.
“Har kin kira?”
“A'a ban kira ba na fasa ne”
Ta faɗa tana murmushi, isowar Mama yasa ta sadda kanta ƙasa tana watsa da yatsun hannunta.
“Wai gida za mu koma yanzu”
Daga Hajara har Namra kallonta suka yi
“Gida kuma? Ina ba dai sokoto ba ko?”
Namra ta tambaya cike da mamaki.
“Can fa, wai so nake muje yanzu kamin yamma mun isa sai da gobe kuma mu juyo”
“Amman zuwa lafiya ne?”
Mama ta ɗan yi shiru kamar mai tunanin abunda zata ce mata.
“A'a wai kuɗi zan je na ranto idan har Allah yasa an samu sai a siye maganin da likita ya rubuta ta, tun da naga alamun sauƙi a jikinsa amman kumburin nan na kansa yana bani tsoro. Kuma ina son naje na ɗauko wasu tufafin gashi mai son Hajara shi ma ya damu yaushe za mu dawo”
Namra ta sauke ajiyar zuciya cike da tausayawa, ji take kamar ace tana da mafitar su ta ɗauka ta bada, ba sai taje neman rance ba.
“Amman Mama da zaki yi haƙuri har gobe, saboda yanzu rana yayi sosai, kuma zaku iya zuwa ku tarar da jira a tasha, ƙara ki haƙura har da safe sai ki tafi, amman tafiyar dare ba kyau, musamman lokacin nan na muke cikin matsalar tsaro”
Mama ta ɗan yi shiru, tana nazarin maganganun Namra.
“Nima haka nake gani, ƙara na haƙura har zuwa goben”
Ta faɗa daga tsayen da take tana gyara ɗaurin zanenta, sai kuma ta juya ta koma dan faɗawa Asim zancen canjin tafiyar.
Sai da wuce sannan Hajara ta kalli Namra tace
“Tafiya yanzu sai kace waɗanda aka kora daga gari”
“Nima ai shi na gani, ƙara dai a haƙura har da safe, yau da gobe a duk ɗaya ne wajen Allah”
Namra ta faɗa tana ƙoƙarin tashi
“Lallai kam, nima bana son tafiya irin wannan”
Murmushi kawai tayi ta nufi ward ɗin da nufin ƙara tausasa Mama ta haƙura da tafiyar har gobe.
A bakin ƙofar ta tsaya cak! Tana sauraren muryar Mama da kunnuwanta suke sato mata.
“Na ce amman ai dubu ɗari sun isa ko? Kar mu karɓo kuɗin duka ya zama ba muna da komai gurin mai dashen”
“A'a Mama ki karɓo gaba ɗaya, kin san dole ne mu siye abinci, kuma wata ƙila ba wannan maganin kawai za a siya ba”
“Amman Ibrahim idan muka karɓi kuɗin duka mun fita daga adashen kenan fa, abinci idan har taga babu shi ai dole ta faɗa ma iyayen nata, ni ina mamakin ace ƴarka ta yi wuta irin haka ka kasa taimaka mata, anya wai ƴar su ce tagaske kuwa? Ni bana ganin a kashe kuɗi dika fa”
“Haba Mama lafiya na kama da me? Idan har Allah yasa na ji sauƙi, ai sai a samo wasu a ake shiga kuma”
“Ina za'a samu wasu Ibrahim? Kana ganin yadda suka juya maka baya, Wallahi bana tunanin zaka samu wani abu a auren nan, duba kaga ko fa ƴar garar nan da ake ba su maka ba, yanzu dubi halin da kake ciki ai ko basu fitar da kai waje ba, sa maka iya ƙoƙarin su amman suja ƙyale ka”
Wani dogon numfashi Asim.yaja ya sauke zuciyarsa cike da jin zafin abunda iyayen Namra suka masa.
“Allah dai ya bani lafiya, idan kiɗa ya canja rawa ma dole ta canja, idan su yi dan Allah ba sa yi dan ƴar su”
Kamar an jefar da gilass a ƙasa ya tarwatse haka taji a zuciyarta, lokacin da maganganun Asim suka daki dodon kunnenta.
Da sauri tayi baya tana maida numfashi, tare da haɗiye yawu a lokaci ɗaya. Wani irin mamaki take tana girgiza kai, kamin tayi haramar barin gurin.
Da sauri-sauri take tafiya kamar zata haɗa da gudu, ji take kamar tayi tsalle ta ganta a wani wajen, ta kasa yarda da kunnuwanta sun ji abunda Asim da Mahaifiyarsa suke faɗa.
Ta tari mai Napep tana haƙi kamar wanda aka janye wa numfashi.
“Nasarawa zaka kai”
“To ɗari da Hansi, kuma sai na bi ta Yarima Estate na sauke wannan matar”
Kai kawai Namra ɗaga masa, ta shiga Napep ɗin ba dan hankalinta yana jikinta ba. Yarinyar dake kusa da ita taja wani dogon tsaki, tana matsawa can gefe irin tana ƙyaƙyamin Namra ɗin nan.
“Mtswww ni dama zaka sauke ta, ta nemi wani sai na biya ka kuɗin duka”
“A a haƙura dai zaki yi Hajiya, ai da kamin a ɗauke ta kika ce haka, amman yanzu na riga na ɗauko ta kyayi wannan maganar kuma”
Mai Napep ɗin ya faɗa, yana mai cigaba da tuƙinsa. Sai a lokacin Namra ta kalle ta da kyau.
“A'a ka sauke ni mana ka kaita ita kaɗai saboda ni ba mutum bace, ko kuma Napep ɗin ta gidan ku ce, idan har kin isa miyasa ba'a siya miki mota ba? Ko kuma ayi miki direba na ki na kan ki? Wallahi ƙaryar arziki kike tun da har kika iya shigo Napep”
Ƙasa-ƙasa ta kalli Namra tana wani yamutsa fuska, ita har ga Allah ƙyaƙƙyamin Namra take. Wayarta dake jaka tayi ringing, tayi saurin fidɗo purse ɗin dake cikin jakar ta cire wayar tare da yin picking ta kara a kunne.
“Hello Dude”
Ta ɗan yi shiru kamin ta sake cewa.
“Ni na baro motar can, Ummy ce na faɗa mata, wai bata turo direba tun da ban faɗa mata zan fita ba”
“Eh ina kam Napep n kusa isa, okay bye safe trip Dude”
Ta kashe wayar kamar ta fasa kuka, kamin a isa Estate ɗin nasu har ta tsawala.
Har bakin gate ɗin gidansu ya sauke ta, ta ciro 1k ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canji ba ta nufi gidan, da sojoji suke gadi, da sauri suka buɗe mata gate shige cikin, sai ƙyaƙƙyamin kanta take.
Kai kawai mai Napep ɗin ya kaɗa ya wuce da Namra Nasarawa road.
A ƙofar gidan su Mardiya tace a sauke ta, ta ciro ɗari biyu ta miƙa masa ya karɓa ya bata canji sannan ta juya ta nufi cikin gidan, zuciyarta na dawo da maganganun da kunnuwanta suka joyo mata.
A zauren gidan ta tsaya, ta jingina da ginin gurin ta lumshe.
‘Miyasa Asim yake ƙoƙarin ɓoye min sirrin sa? Me suke shiryawa shi da mahaifiyarsa? Kar zancen Anty ya zama gaskiya, kar dai ace rayuwar Asim ta canja, da biyu ya aure ni kenan? Soyayyar daya nuna min a baya ta ƙarya ce?’
Hawaye ya silalo daga idonta, dake lumshe, sai kuma ta girgiza kai tana cigaba da zancen zuci.
‘Amman ya so ni a baya kuma so na gaskiya, miyasa yanzu zai canja? Na juyawa kowa baya saboda shi, ba zai min haka ba, what if i choose the wrong person? No no no it's Asim mutumen da yake son ki so na haƙiƙa mutumen da yace min miki ba dukiyarki ce a gabansa ba’
Ta buɗe ido tana share hawayenta.
“Amman mi yake nufi da idan ba suyi dan Allah sa yi dan ni? Me yake nufi da idan rawa ta canja, Allah ka fahimtar da ni, Allah ka amintar da ni, Allah kar ka saka zancen Anty ya zama gaskiya, Allah kar kasa Asim ya zama cikin mutanen da za su min Zagon Ƙasa, Allah kar kasa ayi ma auren nan na mu dariya”
A fili tayi furucin tana kuka, zuciyarta a karye, tana ji a jikinta ranar nadamar ta tana daf ta ita.
Ganin wata zata fito daga cikin gidan yasa tayi saurin ɓoye kukanta.
“Namra ce a nan tsaye?”
“Eh yanzu na shigo ina wuni?”
“Ya jikin mai gidan na ki?”
“Da sauƙi sosai”
“Allah ya ƙara sauke, har yanzu dai ba mu samu mun koma mu ƙara dubashi ba”
“Ba komai ai, kuna ta sana'ah ba zama”
“Ba zama fa Allah dai ya ɗauƙe Wahala”
“Amin”
Namra ta kunna kai cikin gidan, ita kuma ta fice tana gyara hijabinta.
HILAL POV.
Yau one day da gwajin da ya kai ayi ma Rashida, dan haka yana buƙatar karɓo result ɗin dan tabbatar da zarginsa, duk da alamu sun nuna cikin ne amman ya fi son ya ƙara tabbatarwa.
Lokacin daya gama duba Patients ɗinsa sai ya nufi lab dan karɓar sakamakon.
To his surprise ba abunda yake zato ba kawai ya gani, a cikin result ɗin akwai symptom ɗin HIV. Haka ya riƙa karanta result ɗin ba daɗi, but still abu ɗaya yake gani da biyu yake gani.
Ciki da kuma symptom.
Ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yayi, kar mutanen da suke gurin su zargi wani abu. Cikin rashin kuzari ya dawo office ɗinsa, har ya zauna sai kuma ya tashi tsaye, sai karanta takardar yake numfashinsa na yawo, wani zafi ya riƙa jin yana masa yawo tun daga cikin cikinsa zuwa ƙwaƙwalwarsa.
“Ko dai mistake suka yi? How could this happen?”
Ya kasa yarda, mamaki yake har yanzu, shi dai yasan yana yawan gwada kansa every 6 months da kuma iyalansa, kuma lokacin da aka auna jinin Kalsoom be nuna haka ba, why Rashida?
Gani yake mistake ne suka yi, sai dai baya jin zai iya koma ya tambayesu, abunda kawai zai iya, shine ya sake ɗibar jinin nata, da na ƴaƴansa da kuma na Kalsoom ya kai ward ɗin da ake gwajin cutar, dan tabbatar da zarginsa, idan har da gaske ne ai zai nuna yadda ta samu ciwon da kuma daɗewarsa a jikinta.
Be iya ƙarasa aikin ba ya haɗa kayansa ya ɗauki ƙaramin box ɗinsa ya cire labcoat ya riƙe a hannu ya fice, ba tare daya tsaya kulle office ɗin ba.
Ko da ya isa gida kansa har wani zafi yake kamar an kunna masa wuta, gaba ɗaya kalar idonsa, da fuskarsa ta canja irin kana kallonsa kasan yana cikin damuwa.
Rashida na zaune falo riƙe da plate tana cin abinci, ba laifi yanzu kan ta ɗan samu sauƙi dan ita ma tayi girkin sa kanta. A bakin ƙofar falon ya tsaya yana kallonta wani tausayinta yaji ya lulluɓe shi har idonsa suka cika da ƙwallah.
Ita kuma ta ɗan kalle shi kaɗan ta kauce kai, ba dan bata son kallon nasa ba, sai dan baƙin kishi daya rufe mata ido, gani take yanzu ai ba ita kaɗai ce da shi ba.
Yana sako ƙafarsa a first step ɗin falon, sai ta tashi ta nufi ɗakinta. Shi kuma ya tsaya a gurin ya bita da kallo zuciyarsa cike da tausayinta.
______________________________________________
Assalamu alaikum Habibaties 🌺
Ina fatar kuna cikin koshin lafiya? Allah yasa haka Amin
My dear readers idan Allah yasa muna cikin masu rai da lafiya, idan na yi page 35 tau ZAGON ƘASA na Khadeeja Candy ya koma na siyarwa, daga bakin Page 35 har zuwa karshe na kudi ne, daga page 1 zuwa 35 free ne. Nasan zaku ga chanji yazo muku ba ta yadda kuka zata ba, ku yi hakuri ku min uzuri, haka sauyin ya zo. Kuma ina fatar zaku goya min baya, fiye da yadda kuke min a da, soyayyar ku da haɗin kan ku, shi na ke fata a kullum, Allah yasa ku min kyakkyawar fahimta. 😊👌
Ga waɗanda suke sha'awa. Naira ɗari biyu ₦200 zaku turo ta wannan account ɗin 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Ga wanɗanda basa da account kuma za su iya turo katin waya na line mtn na dari biyu da hansin ₦250 ta wannan number 08036126660
Idan kun tura. Sai ku turo da shaidar biyan kudin wato screenshot ta wannan number 08036126660.
NA GODE 😊
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 32*
NOT EDITED ⚠️
Ɗakinsa ya wuce ya aje kayan da suke hannunsa, sannan ya fito ya shiga ɗakinta. Zaune ya same tana taunar naman abincin data gama ci, kusa da ita ya zauna yayi mata ƙuri da ido, kamar mai tunanin abunda zai faɗa mata.
“What?”
Ta tambaya shi sam be san ta lura da kallon da yake mata ba har sai da tayi magana.
“Bana da ikon kallon ki ne?”
Ya faɗa yana murmushin ƙarfin hali.
“Kallo na nawa kuma, ai na gaji da kallon nawa ne shiyasa kaje ka ɗauko wata, kuma ni ka faɗa mata ta daina zuwa min yawo da yara karta lalata su”
“Uhmm, Pyar ki daina sawo zance Kalsoom a gurin da muhallinta ba, ke da ita duka ɗaya kuke a guna, wani abun da kike faɗa akanta ba daɗe yake min ba, and you know what ita bata taɓa wani mugun furuci akan ki ba, balle kuma akan ki ba, sannan tana kula da ƴaƴanki”
Ta taɓe baki ta aje plate ɗin ƙasa.
“Wallahi duk son ƙarya ne, babu kishiyar data zata so ƴaƴan kishiryarta, wannan duk Zagon ƙasa ne”
Ya kai hannu ya riƙo hannunta.
“Naji pyar faɗa min when last nayi miki gwajin jini?”
“I can't remember, ba kai kake min ba?”
Ya ɗanyi shiru.
“Ina ganin anyi shekara biyu yanzu, saboda ba samun zama nake ba, miya faru?”
“Ba komai, zan sake ɗibar wani ne, wacan a mota ya ɓata fitsarin kawai na auna”
“Okay amman yau zaka ɗiba, dan gobe zan je aiki”
“Daga jin sauƙi sai kuma zuwa aiki?”
“Kasan matsalar banki tun yau ma aka so na koma”
Hannu ya kai ya shafa gefen fuskarta.
“Pyar i love you so much ki sa wannan a zuciyarki, mijinki yana son ki sosai”
“Yana son mu dai point of correction”
Ta faɗa tana wani yatsina fuska, shi kuma yayi murmushin da be kai zuci ba, ya tashi tsaye.
“Bari na yi wanka”
“As you wish”
Bayansa ta bi da kallo zuciyarta na mugun tafarfasa, duk yadda take so mijinta idan ta tuna da ba ita kaɗai yake so ba, sai ranta
Book Chapters
Chapter 17
Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71