You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
fa kamar bata da kuɗin nan”
Cewar Hajaru, Mama ta kai mata wani mugun zungura
“Duk naji bakin ki yayi maganar adashen nan sai na kusa halaka ki, taya zata ba mu kuɗi bayan mun riga mun zuba, kina ganin kullum zogaron kuɗin zubi take mana. Ai ita ta fimu sanin hanyoyin samo kuɗi, ta nemo ta biya a itace silar komai tun da tasan be wani iya mota ba, tasa ya jawo ta tun daga sokoto har katsina dan kawai su ga bayan shi.
Ni Wallahi ɗana ko mutuwa yayi sai nayi ƙararsu”
Hajaru dai tayi shiru bata sake cewa komai ba, Mama kam sai cika take tana barsewa, ita mai ɗa.
KALSOOM POV.
Babu abunda ta ɓoye Salma na zamantakewar auren da suke yanzu da Hilal.
Ita tafi raja'a akan Hilal baya son haihuwa, daman Asmee takan nuna mata alamun hakan tun lokacin data shigo cikin gidan. Sai dai tunaninta ya sha banban lokacin da Salma take nusar da ita akan wasu abubuwan data manta.
“Haba Kalsoom ke kan ki yanzu ba zaki iya gane wani abu a tare da shi ba? Taya za ace dan kin yi ciki sai ya sauya miki? Baya son haihuwa zai bar matarsa ta haifi yara uku kuma tana aiki?Sherin kishiya yana da yawa Kalsoom musamman na zamanin nan”
“Naga sauyi a ɓangarenta dan duk wani kishi data ɗauka yanzu ta aje shi, bana da matsala da ita”
“Wannan ma kaɗai ya isa ya nuna miki akwai abun da tayi, ki bita a sannu kuma ki yi taka tsantsan da ita. Sannan a duk lokacin da mijinki yake fushi yana hawa sama karki tanka shi, kisa mishi ido, saboda maganar zai iya zama miki illah.
Cigaba da addu'ah, idan zaki iya kiyi alwala a zama ɗaya ki karanta Yasin ƙafa goma sha biyar, ki roƙi Allah, ko kuma ki karanta ayatul kursiyu ɗari uku da sha uku Wallahi duk kika roƙi Allah sai ya amsa miki, ki daure kiyi na tsawon sati acikin kwana uku Allah zai biya miki buƙarta ki.
Sannan ki samu ruwa mai kyau ki watsa a saman rufin ɗaki, idan ya gangaro ki tara abu ya zuba a ciki, ki taceshi ki sha ki wanke kanki, Wallahi indan Asirine akayi miki sai ya karya kuma sai Allah ya nuna miki wanda yayi miki haka a bachin ki, maƙukar kika yi har sau uku”
“Na gode sosai Salma, Allah ya bar zumunci”
“Amin Allah ya baku zama lafiya”
Daga haka ta aje wayar, ta jingina da gadonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Kai kayi auren baka huta ba, idan kuma baka yi baka huta ba, da wannen zaka ji”
Yadda ya turo ƙofar ɗakin ya shigo ne yasa ta zabura ta tashi zaune, tana kallon yanayinsa.
“Ina kuɗina dake cikin closet?”
Wani kallon mamaki tayi masa.
“Kuɗi kuma? Ni ban ɗauki kuɗin ka Doc, ban ma san ka aje kuɗi a gurin ba”
“Babu wanda zai ɗaukar min kuɗi bayan ke, dan ke kaɗai kike goge gurin”
“Amman ai ba ni kaɗai bace a gidan nan”
“Mata ta bata taɓa min sata ba, ƴara na kuma basu ɗaukar min kuɗi, sannan basa da wayon da zasu iya ɗaukar dubu ɗari uku da hansi”
Hawaye ya silala a idonta. Ta nuna kanta
“Ni kake zargi kenan, ni na ɗaukar maka kuɗin ko? Haba Doc taya zan ɗaukar maka kuɗi abunda ban taɓa yi ba”
Ƙara haɗe fuska yayi kamar an aiko masa da mutuwa, ya ɗaki mirror ta yana ƙara jadadda mata.
“Bari kiji na faɗa miki, ko ki nemo dubu ɗari uku da hansi ko kuma a bakin auren ki!”
Bata san lokacin data kwantar da kanta gefe tana masa kallon da ita kanta bata san tana masa ba, ta kasa tantancewa shi ne ko ba shine ba.? Fuuuu ya bar ɗakin kamar walƙiya yana wani irin huci.
________________________________
I need more and more comments. 🙌
Bari na ga suwa suke son nayi long chapter gobe 🤔
BEST REGARDS 💖
Khadeeja Candy 😘🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Masu Tambayar Labarin Uzair da Amira zai zo muku a gaba, tare da nasu Zagon ƙasa. Just keep moving komai zai zo daki-daki.
*PAGE - 25*
NOT EDITED ⚠️
KALSOOM POV.
Ta daɗe a gurin tsaye duniyarta na juya mata, kunnuwanta sun kas ɗaukar abunda suka ji Hilal ya faɗa mata, idonuwanta kuma sun kasa yarda da ba mafarki take ba.
Makomar aurenta take tunani, yadda zamanta a gidan zai kasance yake mata yawo a ƙwaƙwalwa, taya zata biya abunda bata ɗauka ba? Akan me zai nuna dubu ɗari uku sun fi aurenta daraja a gareshi? Dan me idonsa zai rufe har yayi mata wannan furucin?
Ta kasa zaɓa tsakanin igiyar aurenta da kuɗin da idan har ta bashi zai iya tabbatar masa da lallai ita ɗin ce ta ɗauka.
Hawayen dake idonta ta share, ta tashi ta ɗauko akwati ta buɗe wardrobe ta ɗauko tufafinta ta saka aciki, ta ɗauki jakarta ta saka wayarta da duk wasu abubuwa da tasan zatayi saurin buƙata, ta zari mayafin ta yafa ta jayo akwati ta fito. A lokacin Hilal yana zaune falon ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya.
“Ina zaki je?”
“Gidan mu, ba kace na kawo kuɗi ba ko kuma a bakin aure na? Ni ba zan iya biyan abunda nasan ban ɗauka ba, amman Allah yana nan baya bachi baya angaje zai bayyana gaskiya, amman ni ba ɓarauniya bace”
Tasowa yayi ya ƙaraso kusa da ita.
“Look Kalsoom ...”
Sai kuma yayi shiru ya kasa magana, ya kuma kasa kallonta. Ganin hakan yasa t share hawayenta ta cigaba da jan akwatin. Sai ya riƙe ya kai hannu ya riƙota, kuma ya kasa mata magana, shi dai ji yake babu daɗi ya rasa abunda ke damunsa, sai yanzu yake jin nadamar furucin da yayi mata, mamakin yake yadda ya alaƙanta sakinta da kuɗin da basu taka kara sun karya ba a gurinsa, bayan kuma baya da tabbacin ita ɗin ce ta ɗauka.
“Ban aureka dan dukiyarka ba, balle har ya kai ni ga yi maka sata, nayi tunanin kasan darajar aure, ashe na yi kuskure, daman an faɗa min baka son haihuwa kana son kayi amfani da wannan damar ne ka wulaƙanta ni ko? Zan bar maka gidan ka sai ka zauna da wanɗanda ba ɓarayi ba!”
Kalamanta sun harzuƙa shi matuƙa, sai kawai y saki hannun nata.
“Kije duk inda zaki je, amman bari na faɗa miki duk wani abu ya samu cikin nan na ki, Wallahi sai kin yabawa aya zaƙinta”
Cikin wani irin ɓacin rai ya nufi ɗakinsa, ita kuma ta bishi da wani kallo na takaici na baƙinciki, kamin ta saka kai ta fice.
Ɗakinsa ya koma ya zauna, rasa yayi abund ke masa daɗi, dawowar da yayi ɗaukar kuɗi sai ya kasa komawa. Ba shi ya fito ɗakin ba sai da lokacin ɗauko yaransa daga makaranta yayi har ya gota, sannan ya fito daga ɗakin.
Kukan Rafiq yaji da yaji yasa shi ya nufi ɗakin Kalsoom dan shi sam ya manta da Fariq na bachi.
Ɗaukarsa yayi ya ɗora a kafaɗa yana jijjigashi, ya fito ya buɗe motarsa ya saka shi gidan gaban, sannan ya zagaya ya shiga ya tashi motar.
Ko da ya isa ɗaukarsu duk sun ƙosa, ga Rafiq sai kuka yake masa, har suka dawo gida.
Da gudu suka shiga falon, sai suka tsaya a gurin da Kalsoom ta saba nuna musu su aje safunan su suka aje sannan suka nufi ɗakinta suna rigangan.
Ganin bata ɗakin yasa suka fito suka nufo kitchen da gudu, nan ma basu ganta ba, sai suka nufo dinning gurin da Hilal yake tsaye yana haɗawa Rafiq madara.
“Daddy ina Anty?”
Yi yayi kamar be ji su ba, har sai da suka ƙara tambaya sannan ya kalli Ezzah kasancewar ita ce babba.
“Anty ku taje unguwa”
“Yaushe zata dawo?”
Ulfah ta tambaya. Sai da ya sawa Rafiq madara a baki sannan ya amsa musu.
“Ni ma bata faɗa min ba”
“Daddy ta dafa mana abinci?”
“A'a bari Rafiq ya gama zan muku takeaway yanzu”
“Anty tace mu daina cin takeaway sai abincin gida”
Kallonta Ezzah yayi da kyau.
“Amman yau Anty ki bata nan na ce zaku ci takeaway”
“Daddy ka dafa mana Indomie”
Ulfah dake ƙoƙarin cire uniform ɗinta ta turo baki tace
“Ba za mu ci indomie ba ai da safe Indomie muka ci, Daddy ayi mana takeaway”
Ezzah ta nufo a fusace tana faɗin
“Allah kuwa duk Anty ta dawo sai na faɗ mata nace kin ci takeaway”
Ita kuma sai ta taɓa hannayenta alamar ma shiryawa masifar.
“Nima na faɗa mata na ce kin yi faɗa da wata a makaranta, ai ta ce ki daina faɗa a makaranta”
Hannu Ezzah ta kai zata daketa sai Hilal ya katsa mata tsawa.
“Ezzah karki dake ta, zan dafa miki indomie, ke kuma zan miki takeaway is that okay?”
Duk suka haɗa baki gurin amsa masa.
“Yes Daddy”
“Come and take your brother”
Ezzah ce taje ta karɓe shi, sannan ya nufi ɗakinsa kansa na masa wani mugun zafi.
NAMRA POV.
Tare suk kwana a gidan ita da Mardiya. Sai dai ita batayi bachi ba, har safe Asim take tunani da halin da yake ciki.
Tasan ita kaɗaice a duniyar nan zata iya taimakonsa, idan kuma har bata masa ba waye zai masa, tun da mahaifiyarsa bata da hali.
Babu abunda ya fi ɓata mata rai kamar abunda Anty Amarya da Maryam suka mata, kuma bayan su bata tunanin akwai inda zata iya zuwa ta kai kukanta.
Tun da tayi sallah asuba ta shiga kitchen ta haɗ ma Mama abun kari, sannan ta shigo ɗakin da suka kwana da Mardiya ta tasheta.
Tashi tayi zaune tana murtsikar ido.
“Ina kwana har kin tashi?”
“Ba dole na tashi ba, har na haɗa muku abun karyawa,dan Allah shiga ki wanke bakin ki ki karya, idan kin san gidan wat dillaliya ki kai ni ko kuma ki kira min ita ta zo ta siye gadona”
Mardiya ta daki ƙirji
“Gadon ki kuma? Haba Namra karki siyar da gadon ki mana”
“Idan ban siyar da shi ba, kai na kike son na siyar ? Ko sata zan yi? Ba ki ga hali da mijina yake ciki ba”
“Amman ba ku da ƴan'uwan ne da za su iya taimaka muku?”
“Ƴan'uwana sun juya min baya, shi kuma ƴan'uwansa ba wani hali ne dasu sosai ba, nasan ko da za a samu ba zai wuce ayi karo karo ba, kuma kin ji abunda likita yace kar ya wuce kwana biyu ba'ayi masa aikin ba”
Sosai Mardiya ta ɓata rai tana nuna mata rashin jindaɗinta akan siyar da Gadon da Namra zata yi.
“Gaskiya ni ban jidaɗin haka ba”
“Ba komai Allah zai bani wani, tashi ki shirya ai kin san wata mai siye ko?”
“Eh akwai wata a nan unguwar mai siye sosai”
“Dan Allah ki min magana da ita yanzu kar rana yayi, kuma ina son kije ki kai musu abincin su”
“To bari na tashi”
Ƙoƙarin tashi take tana wani kare-karen zane, kar sarƙar dake jikinta ta faɗo. Ita kam Namra bata ma kula ba sai ta tashi ta bar mata ɗakin.
A haɓar zanenta ta ƙulle sarƙar sannan ta shiga banɗakin, ta wanke fuskarta, koda ta fito har Namra ta kawo mata taliya a plate da ruwan sanyi ta aje mata.
Haka ta riƙa aika abincin kamar wata tsohuwar mayunwaciya, nan da nan ta ƙare ada plate ɗin, ta sha ruwa sannan ta fito falon tana faɗin
“Bari naje na kira miki ita”
“Toh dan Allah ki yi sauri”
Namra ta faɗa tana shan tea ɗin dake hannunta, idonta duk sun wani zurun-zurun kamar ita ce marar lafiyar.
Mardiya bata ɗauki dogon lokaci ba ta dawo tare da matar, sai da suka gaisada Namra sannan Namra ta ta shiga da ita cikin ɗakin ta nuna mata gadon. Tana ganinsa tasan sabo ne, amman duk da haka sai da ta gama duba ko ins nasa sannan ta kalli Namra tace
“To nawa aka masa kuɗi?”
“Babu wanda ya taya, ki siya kawai”
“Toh ai ba siyen ba, kin san irin wannan manyan kayan ba ko wace mai keya ke siyen su ba, sai su daɗe baka sai da ba amman ke nawa kika ga zaki iya sai da su?”
“Ni dai miliyan ɗaya har da wani abu Abbah ya siya min su, ke kuma sai ki kwatanta”
“Kai kai aiko an daki hancinsa, dan wannan kayan yanzu wasu ma sun daina yayinsu, ai sun faɗi sosai. Sabin ma ba zasu wuce ɗari bakwai ba”
“Tau ki bayar da haka ɗin”
Tayi ma Namra wani kallo tana taunar goron dake bakinta.
“Ni ko ai ba zan ci riba ba, magana ta gaskiya zamu yi, dan ni bana son nakkasa mutum, ƙara ayi ciniki babu cuta babu cutarwa, indai zaki iya bari ɗari, shima dai ƙoƙartawa zan yi dan ba duk dillaliya ke zuba kuɗi da yawa ta siye kayan data san ko ta sai da ko karta sai da ba”
“Haba baiwar Allah, Wallahi lalura ce tasa zai sai da abu na, ba kiga sabo ba ne”
“Na gani amman ai kin san duk abunda aka riga aka fitar indai kuɗi kake so sai ka faɗi, amman yanzu zan yi miki magana ɗaya idan yayi miki na siye ɗari uku da ashiri”
Kallon gadon Namra tayi ta sake kallonsa ta kalleshi sannan ta kalli Matar tace
“Kawo kuɗin”
“Amman fa sai naga mai gidan ki, dan wani lokacin ana siyen kaya sai kuma miji ya zo yace shi ba za'a siyar da kayan matarsa ba”
“Mijina ba shi da lafiya kuɗin magani nake nema shiyasa zan siyar da wannan gadon, yanzu haka yana asibiti aiki za a masa”
“Allah sarki, Allah ya sauwaƙe, amman duk da haka zan zo da ɗana sai yayi mana takarda guda biyu saboda gudun matsala”
“Ba matsala, kuɗin fa?”
“Kuɗi gaskiya sai zuwa gobe na kawo miki sai na ɗauki gadon, dan yanzu ƙuɗin da suke hannuna ba su wuce ɗari biyu ba”
“Bani haka gobe sai ki kawo min sauran ki ɗauki gadon”
“To ba matsala amman sai kin biyo ni gida na baki ga ban ƴan gidan mu saboda shedu”
Sai da Namra ta bawa Mardiya abincin da za a kai ma Mama sannan ta saka hijabinta ta kulle gidan suka fita tare.
Gida matar suka shiga, ta ƙirgo kuɗin gaban mutanen da suke gidan ta bawa Namra bayan ta faɗa musu yadda suka yi, da Namra tun a gida. Sannan tasa ɗanta ya ɗauko takarda yayi shedu guda biyu ya bata ɗaya ya bawa Namra ɗaya.
Tare da Mardiya Namra ta fito gidan, suka tare napep ta kai su Asibiti. Mardiya ce ta wuce kai musu abincin Namra ta nufi gurin biyan kuɗin magani. Dubu ɗari da talati ta biya na aikin, sannan ta biya na magani suka zo suka ɗibi jininsa suka auna sannan suka tura ta lab gurin siyen jini, tayi sa'ah an samu irin wanda ake so, gora uku ta siyo sannan ta dawo ta kawo musu.
Cikin dubu ɗari biyu, kuɗin daya rage be wuce dubu bakwai da ƴan canji ba. A kasale ta shiga ɗakin da yake, sai ta tararda shi cike ƴan'uwan Asim na Sokoto da Bakori sun zo dubiya.
Cikin far'ah da ƙarfin hali ta gaisa da su, sannan tayi ma Mama ina kwana. Sai kusan azahar wasu suka koma aka bar mutum biyu su wai ba yau zasu ba.
Ganin azahar tayi yasa Namra ta ba Mardiya makulli taje ta girka mata abincin rana, ita kuma ta dawo kusa da Asim ta zauna, ta zuba masa ido kamar ba gobe. Daker ya ɗaga ido ya kalleta ya sake rufewa ji yake kamar ba duniya yake ba.
Ita kuma wani irin tausayinsa take ji take ciwon kamar a jikinta yake.
Uku dai-dai nurses suka shigo suka fita da shi zuwa ɗakin da za'ayi masa aikin.
ABDOOL POV.
Hannu ya kai ya kunna air conditioner dake ɗakin sannan, ya rage tufafin jikinsa, ya buɗe freezer ya ɗauko power horse ya sha.
Sai ya dawo saman sofa ya zauna, yana kallon window. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ya miƙa gurin windowdake garden yana sauraren birds singing.
Yana jindaɗin saurarensu sosai da sosai, hakan yasa lokuta da dama idan ba shi da wani aikin ya kan tare a garden dan kawai sauraren sautin na su.
Hannayensa ya zuba a aljihu ya tashi yana wani irin taku na sarauta da ƙasaita ya nufi window, Peacock ɗin dake ƙarƙashin apple tree yana sha'aninsa ya tsurawa ido. Kamar wanda ya tuno wani abu sai kawai yayi wani ƙayataccen murmushi ya wanda ya sanya dimples ɗinsa fitowa, lumshe ido yayi yana shafa fuskarsa.
“Because of her, half the time I don't even know that I'm smiling, she insult me but i still need to see, who's she?”
Abund ya furta kenan a fili sai kuma ya bawa kansa amsa.
“The Unique one”
Murmushi yayi mai sauti, ya rumgume hannayensa yana ƙara saita tunaninsa.
Taya akayi ya zure haka? Mema ya kai shi kula wata har yayi ƙoƙarin mata magana, shi da bay da lokacin wasu mata. Hannu yasa a aljihun wandonsa na Army, ya ɗauko wayarsa ya kira wata number, bugu ɗaya ya ɗauka.
“Ali ya ake ciki?”
“Naje har gurin shugaban masu Napep ɗin na bincika, sai aka kawo min mutumen yace shi be santa ba kuma a bakin babbar asibitin funtua ya sauke ta, wai yana ganin jinya take”
“So what's the solution?”
“Sir want i think is better mu shiga cikin asibitin mu bincika”
“No”
Ya girgiza kai alamar shawarar bata masa ba, ya ɗan ɗauki dogon lokaci, be ce masa komai ba, ba dan kuma baya da abun cewar ba, sai dan isa da izza.
“Ka cire kuɗin da zai isa, a shirya takeaway da five thousand sai muje mu raba ma Patients ko Allah zai sa mu samu ganinta”
“Okay but Sir Akwai meeting da zaka je gobe Abuja, kuma the next day akwai meeting ɗin Mr President ya shirya za ku yi akan matsalar tsaron nan na Maiduguri da Zamfara”
Lumshe ido yayi ya buɗe.
“I know that, nasan end of this month ina da free days, a cikin wannan rana ku zamu je, sai ka saka mana date”
“Alright Sir zan duba the most expensive free day na ka”
“Good of you”
Sai kawai ya kashe wayar, ya mayar aljihu. Da ƙarfi aka banko ƙofar ɗakinsa, sai kawai yayi murmushi.
“Hey Dude”
Wanda ya kira da sunan ta fito daga cikin labule tana dariya, yarinya matashi wanda ba zata wuce fourteen to sixteen years.
“Yarima Ummi na kiran ka”
Ta faɗa tana taɓa hannayenta. Hannayen nata ya riƙa yana murmushi.
“Dude Yarima has finally found his princess”
Ta zaro ido
“Wow, when? How? Who?”
“At funtua i don't know who's she”
“Is she really cute?”
Wa wara manyan idanuwansa.
“Yeah she's so pretty, she had that diamond eyes, her lips is so cute, i like her face, she's tall, she wearing Hijab and she's black, Dude you know how i love black girls huh?”
“Yes Dude so how are we going to meet her?”
“I don't know, she slap me Dude”
Ya wani ɓata fuska kamar ƙaramin yaro. Itama ta ɓata fuska kamar tayi kuka.
“So heart touching”
“Don't worry i will slap her heart when i have a chance, but i still feel her soft fingers on my cheek”
“ I will be the first one to tell Ummi”
Ta faɗa tana dariya. Sai yayi saurin rufe mata baki
“No Dude wannan sirrin mu ne, no one will ever know”
“Yes I won't tell”
Ta faɗa tana ɗaga hannu sama alamar tayi alƙawari.
“So tell me why Ummi take son gani na?”
“She want you to go and meet Cute Eysha, daughter of Hajiya Saratu”
“What? Please tell her I'm sick”
Har ta buɗe baki sai kuma ta rufe ta saki hannunsa ta fita. Batayi minti biyar da fitar ba yaji alamun shigowar Ummi.
Da sauri ya haye saman gado yaja bedsheet ya lulluɓe ya makore kamar da gaske ba shida lafiya.
“Ai dole ka riƙa ciwo, kullum baka da hutu kai ne agogo sarkin aiki, idan an maka maganar aure kamar ance ka faɗi ka mutu, duk yaran garin nan kace basu maka ba, ko so kake ni da Mai martana mu mutu ba muga auren ka ba?”
Ɗan ɗagowa yayi kaɗan yana pretending like he's really sick.
“Ummi yanzu kuma miye nawa? ”
“Ƴar wajen Hajiya Saratu nace kaje ka gani, tace min jiya ta dawo daga Kaduna”
“Ummi ko na yi aure babu wanda zata zauna da ni, saboda ina da lalura ta rashin lafiya yanzu haka Dr Alex ya ɗora ni akan magani”
Ya faɗa yana ƙoƙarin mayarda ƙaryarsa ta zama gaskiya. Ita kuma sai ta amsa da ƙarfi.
“What?”
Sai kuma ta kalli ƙanwarsa.
“Afrah go and watch your favorite channel”
Sai da suka yi ido biyu da yayan nata sannan ta fice.
ANTY AMARYA POV.
Ji take bata kyautawa Namra ba, idan har bata mata ba babu wanda zai mata sai Allah, soyayya irin ta ƴa da uwa ta hana Anty Amarya ƙyale Namra har sai da tasa Maryam ta tura mata dubu ɗari da Hansi.
A gajiye Maryam ta shigo falon ta zauna kusa da Anty Amarya tana miƙa mata atm ɗin ta.
“Kai yau nasha wahala Wallahi, sai kusan 4 muka tashi lacca, naje back kuma na tararda layi”
“Kin tura mata?”
“Eh but her phone is still switch off ”
“Maybe ta siyar ita ma”
“Kai why not su dawo nan garin? Zama acan zai mata wuya”
“Leave here ita ta so ai, sai taje tayi abunda take ganin yafi mata”
“Amman Anty Namra zata sha wahala tun da tana gudun zuciyar mutane”
Ajiyar zuciya Anty Amarya ta sauke, tana wani nazarin na daban.
_________________________________________
Five words for this chapter... 😻
Waiting for your comments... 😘
Best regards to you all... 💖
CANDY🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
This page is for Birthday Girl Salwees. Happy Birthday Dear 💖
*PAGE - 26*
NOT EDITED ⚠️
Hankalin Namra be kwanta ba har sai da aka fito da shi daga ɗakin da aka masa aikin.
Sai suka dawo da shi, ɗakin da yake, anyi aiki cikin nasara da taimakon Allah.
Sai da yamma Mama ta je gidan Namra ita da Hajara dan yin wanka ta kuma ɗan huta, Mardiya Namra ta bawa keys ɗin gidan dan ta taba musu abinci kuma ta taya su zama. Ita kuma ta kwana da Asim a asibitin.
Babu irin inda Mama bata shiga ba a gidan, sai baya kyau gidan take da girmansa. Mardiyace ta faɗa mata Namra ta siyar da gadon har an bata wani abu daga ciki.
Babu irin tsinuwar da Mama bata yi ma iyayen Namra ba, a zatonta sune suka turo mata da kuɗin aiki dana magani, a nan ne Mardiya ta ƙara fayyace mata matar data taimaka ta kawo Asim asibiti ba yar'uwarsu bace, nan ma Mama ta cika da mamaki, dan a zatonta ita yar'uwarsu.
“Kai tirr da wasu mutune Wallahi, wato su babu ruwansu da lamarin mijinta tun da ba ita bace ko? Hmmm ni ban taɓa ganin iyaye irin nata ba, daman ba son auren su ke”
Taja wani godon tsaki sannan ta fito daga ɗakin, ta shiga kitchen ta fito ta shiga ɗayan ɗakin. Mardiya dai na biye da ita har ta gama duba gidan. Shikafa da miya Mardiya ta dafa tare da Hajara.
Washe gari ma wani abincin Mardiya ta sake dafa musu, bayan sun ci ta zuba wanda zasu tafi dashi a asibiti, sannan suka wanka suna cikin shiri Dillaliyar ta zo Mardiya tace mata bata nan, sannan ta rufe gidan suka nufi asibitin.
Namra suka tarar zaune a kujerar dake ɗakin tana bawa Asim tea. Ba laifi alamun sauƙi ya bayyana a yanayinsa, wanda a ada ma idan ya ɗaga ido sai yayi saurin rufewa yanzu kuma gashi har yana shan tea.
Farinciki gurin Mama ba'a magana, sai ta zauna saman gadon kusa da shi, tana murmushi
“Mashallah Ibrahim, Allah ya ƙara maka lafiya”
Ɗan murmushi yayi kaɗan irin yana jin zafin ciwon nan yana ƙarfin hali. Mama ta kalli Namra
“Yaushe ya farka?”
“Tun da asuba, har likita ya duba shi ya bada wata takardar ta gani yace allura ce za a masa guda bakwai, kullum ɗaya saboda jinin daya bugu a kansa”
“Allah yasa dai babu tsada”
“ Pharmacy asibiti sun ce duk ɗaya, dubu tara ne, ga kuma maganin da suka rubuta shima sai yaci dubu biyar”
Mama ta rafka uban tagumi.
“Tau ai fa kaji matsalar babbar asibiti, yanzu ina za a samu wannan kuɗin kuma? O Allah”
Namra ta saci kallon Mardiya da idonta ke kansu, tace
“Mardiya kuje waje ke da Hajara”
Tashi tayi ta fice ita da Hajarar. Sannan Namra ta kalli Mama tace
Book Chapters
Chapter 14
Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71