You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ÿþ 5ØÜ5ØÜ5ØÜ5ØÜ5Ø
Ü 5ØÜ5ØÜ5ØÜ5ØÜ

LABARI ME CIKE DA

"BAN TAUSAYI, "

"MATSANANCIYAR DAMUWA, KUNCIN CUZIYA, "

"SADAUKARWA, "

ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.

WRITING BY

MARYAM STAR YAR BAIWAR JJRT.

MARUBUCIYAR

RAYUWAR SAMHAD DAFIN MACIJI

A DAREN AURENA AND NOW

ZAFIN WUTA

PAID BOOK

SEASON ONE

Chapter 1-5

EJ-1D' FE-1D' 'DDG E3(.

LEGOS NIGERIA

UNGUWAR AGEGE

"Wani ™wararaSaSSen gida ne ginin ™asa wanda ko arzikin shahen siminti bai samu ba, gida ne ™arami sosai kuma marar tsayo dan dama waje za'a iya hango kaiwa da komowar mutanen gidan."

Da gudu na fito daga cikin kurkukun gidanmu wa ni dattijo biye da ni hannunshi ri™e da zabgegiya bulala irinta

"dukan dawakai, gudu ni ke iyakar ™arfina tare da ihun neman agaji dan saura ™iris Dattijon ya kama ni damma ina zillewa."

"Shawo kwana yai hannu shi ri™e da jakar bakko, lokacin da ni ke ™o™arin bige shi insha kwanar nima, caraf na ji anri™e hannuna da mugun ™arfi, wa ta iriyar ™ara na saki tare da gantsarewa jin saukar duka a jikina, kafin in aje numfashi na sake jin saukar wa ta bulalar a bayana aiko na sake gantsarewa tare da kai gwuiwoyina ™asa saboda yanda zafin bulalar ya ratsani, rufe ni yai da duka babu ™a™™autawa yayinda har lokacin ba'asakarmin hannuna ba, birgima ni ke a ™asa ina bayarda ha™uri tare da neman agajin jama'a amma babu wanda ya kula ta kaina."

Sai da wannan dattijon yai min lis yanda ko hannuna ba na iya Wagawa saboda tsabar yanda na daku sannan ya rabu

"da ni, wannan matashin kuma wanda ya ri™e hannuna bai sake ni ba har aka gama dukana, bayan dattijon ya juya ya na sababi kamar ze haWe harshenshi saboda masifa ya koma ya shige cikin gida ba tare da ya kula da ko hijabi"

"babu a jikina ba, daga ni sai doguwar riga irinta shan iska wacce duk ta jeme ta ji jiki, kaina ko atzi™in Wan kwali babu"

"sai ba™in sisilkan gashina da ya sauka har tsakiyar bayana, sanadiyar burkiWa da nai duk ™asa ta cika min gashi da jiki. Cike da raWaWin zuciya na tashi ina karkaWe jikina har lokacin ban daina kuka ba kuma hannuna na ri™e da na wannan matashin."

"Baice da ni komi ba ya ja hannuna ina turjewa amma bai tsaya ba sai da ya sada ni da cikin gidanmu, a gaban"

wannan dattijon wanda ya yi min duka ya sake ni tare da komawa gefe inda wa ta farar matashiyar ma ta ke zaune ta yi tagumi hannu biyu.

"""Mama barka da wuni, munsame ku lafiya."""

Matashin ya katse ta daga tunanin da ta ke.

"""Lafiya lau Hashim fatan ka dawo lafiya ya hanya ?""."

"""lafiya lau Alhamdulillah, ga wannan."""

Yai maganar ya na mi™o ma ta bakkon hannunshi.

Cikin sassauta fuska ta amshi ledar tare binshi da addu'a.

Amsawa yai tare da tashi ya koma wajen wannan dattijon shima ya gaida shi tare da zaro kuWaWe daga cikin aljihunshi ya ba shi tare da faWin.

"""Abba ga wannan babu yawa anyi cefane, kuma idan andawo daga sallah idan baku komi ina son muWan tattauna."""

"""Ah bakomi Hashimu yaron albarka, ina gaya maka kaf gidannan babu me hankalinka ubangiji Allah ya biyaka da"

"gidan aljanna."""

Ya faWa tare da zuran kuWin a aljihun rigarshi.

Kallo Hashim yai tare da faWin.

"""Mubeenah ki tashi ki yi alwala lokacin sallah ya gabato."""

Cikeda masifa Abba yai caram ya ce.

"""Yauwa Hashimu gara da Allah ya kawoka a daidai wannan lokacin, wallahi na gaji da halin wannan yarinyar, na gaji"

"da nunamin ita yanzu ta kangare ta balage, kullum cikin janyomin hasifa da tashin hankali ta ke, ace yarinya rai Waya amma ta addabi rayuwata ta hana ni sakat, banda damar gindaya doka a gidana sai wannan masifatattar ta nuna ban isa da ita ba, to na gaji wallahi ta kaini ™arshe na ™ure da bango, kodai ta nemi aiki inda za ta dinga ciyar da kanta ko kuma ta fito da mijin aure in aurar da ita in huta, Allah yana gani na gaji da ri™on wannan yarinyar."""

"˜a™™arfar ajiyar zuciya Hashim ya sauke, a cikin zuciyarshi ya na karanto A'uziyya jin irin kalaman da Abba ya ke jifar"

´ar cikinashi kamar ba shi ya tsugunna ya kawo ta duniyar ba.

Fice wa sukai daga gidan zuwa masallacin da ke cikin kayi don gabatar da Sallar La'asar.

Mama ce ta tashi daga inda ta ke zaune ta nufi Mubeenah ta Wago ta tare da kama hannunta suka shiga cikin wani

"Waki me ´ar ™aramar ™ofa, akan wa ta jemammiyar katifa ta zaunar da ita, itama ta zauna tare da kama hannun Mubeena cikin na ta, cikin nuna damuwa ta ce."

"""Mubeenah! tabbas Abbanku baya kyauta, sam abubuwanda ya ke miki ba su dace ba, musamman zafafan kalaman"

"da ya ke yawan jifanki da su masu kama da ZAFIN WUTA saboda muninsu, bazan ja da baya ba wajen sake jadadda"

"ma ki cewa ki ™ara ha™uri akan wanda kike yi a yanzu, komi zai wuce kamar ba'aiba wuya ko ™unci basa taSa"

"dawwama, bayan wuya sai daWi, kicigaba da ha™uri da ™addararki, jarabawace Allah ya ke jarabtar ki da ita, idan kika jure nan gaba zakiyi alfahari da hakan, tabbas Ubangiji ya na son ki tunda har ya jarabce ki da rayuwa me cike da tarin ™alubale gami da tukitattun al'amurra, ki ci gaba da yin addu'a akan Allah ya zaSa ma ki abin da ya ke alkairi a gare ki, da yardar Allah kina tare da nasara."""

"Zafaffan hawaye ne suke ambaliya akan fuskata, yayinda nike tunanin shi har tsawon wane lokaci zan Wauka ina"

"fuskantar ™alubalen rayuwa, har zuwa yaushe Allah zai dube ni ya sau™a™amin lamurrana kamar sauran mutane, ina so inyi farin ciki kamar kowa, ina so inzama kamar sauran mata sa'annina waWanWa ke rayuwa cike da farin ciki."

"Shafa bayana Mama ta ke alamar rarrashi, a zuciyarta ta na matu™ar tausayamin da irin rayuwar da na tsinci kaina."

Mun Wauki lokaci a hakan gani da Mama tai lokacin Sallah na ™urewa ya saka ta lallaSa ni muka fice a tare dan

"gabatar da Sallah akan lokaci, da kanta ta zubamin ruwa a ™aramar butar da ita kaWai ta rage mana a gidan, kamar talauci a kanmu ya ™are, kullum ina Allah wadai da irin hallayar Abba ta mama™o da bin diddigi, Abba ya kasance cikin irin mutanenan masu hannun ´an dambe, ga son banza muddin zai ™yalla ido ya hangi mutum da Wan mai™o ba shakka sai yasan yanda yai wajen haWa ala™a da shi ta yanda zai yagi rabonsa."

"Shiga banWakinmu wanda ya kasance Wan ™u™ut, sam baya da faWi sai tsawo shima ba canba, raSewa naj gefe na"

"malala ruwa a ™asa sannan na biya bu™atata na fito, alwala na gabatar cikin nutsuwa tare da godewa Allah da ya yo ni cikin hasken musulunci, yanda ruwan alwata ke bin muguji ya na gudana haka damuwar da ta cunkushemin zuciya ke kwaranyewa saboda ™arfafa iymani na da nai a lokacin da nike alwala dan ganawa da mahaliccina."

ZAFIN WUTA LITTAFIN KUŠI NE AKAN NAIRA 500 KACAL.

TA KU HAR KULLUM

MARYAM STAR.

5ØÜ5ØÜ5ØÜ5ØÜ5Ø
Ü 5ØÜ5ØÜ5ØÜ5ØÜ

LABARI ME CIKE DA

"BAN TAUSAYI, "

"MATSANANCIYAR DAMUWA, "

"KUNCIN CUZIYA, "

"SADAUKARWA, "

ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.

WRITING BY

MARYAM STAR YAR BAIWAR JJRT.

MARUBUCIYAR

RAYUWAR SAMHAD DAFIN MACIJI

A DAREN AURENA AND NOW

ZAFIN WUTA

PAID BOOK

Season two

Chapter 5-10

"Bayan na kammala alwalar na yi addu'a kamar yanda manzo ya koyar, sannan na tashi na zubawa Mama ruwa na kai ma ta butar bakin ™ofar bayan gida na juya na wuce Wan tsukakken Wakina me kama da gidan Tantabaru, yamusashe abin Sallah na shimfiWa sannan na janyo daguwar linkakkiyar hijabina wacce ta ke a tsarkake fes sai zuba ™amshin turare Wan Wure ta ke, zura hijabin nai tare da kabbara Sallah na fuskanci Mahaliccina cike da ™an™an da kai, wani irin rauni ne ya ziyarce ni lokacinda gaSoSin jikina suka taimaka mani wajen yin Sujjada ina ganawa da Ubangijina, addu'a nike jerowa cike da fata da ya™inin Allah zai kalle ni ya amsamin ro™ona."

"Bayan na sallame Sallar nai tazbihi gami da azkar wanda Manzonmu ya koyar, na jingina da bangon Wakin ina"

"tunanon irin ™alubalen da ke baibaye da rayuwata tun tasowata har zuwa yanzu, ko a labaran hausa da nike bibiya ban taSa cin karo da makamanci labari wanda yai shige da nawu ba, kullum cikin fuskantar sabon babin ™alubale da littafin ™addarata ke buWe min nike, sam bansan farin ciki ba a rayuwata, abu Waya na sa ni shine, tarin ™alubale da wahalhalun rayuwa."

"Ina a zaune ina tunanin yanda rayuwa ke gara ni kamar kwallon ™afa na jiyo maganar Abba tun daga waje, Abba irin"

"mutanen nan ne masu hayaniya waWanda ba'a sirri da su, idan ya na magana muryarshi na fitowa da ™arfi sosai, tumbama ace faWa ya ke wayyo Allah wallahi inada tabbacin har masu wucewa a bakin hanya su na jiyo amon sautinshi, kafin in ankare na ji Sallamarsu a cikin gida shi da Hashim, runtse idanuwana na yi da ™arfi jikina yahau tsuma kamar yanda nike tsintar kaina aduk lokacinda Abba zai shigo gida, ina jingina shigowarshi da tashin hankalina saboda da zarar ya sako ™afarshi ya ke fara ™ir™irar abin da zai saka ya kira ni ya yi min faWa wa ta ranama harda duka."

"Zagi, gori, cin mutunci sune abubuwanda ke maimaita kansu a bakin Abba akaina, nakan cintsi kaina a cikin wasiwasi lokuta dadama idan nai Abba ya jefe ni da mummunar kalma, zuciyata na raya ma ni cewa ba shine wanda yai silar zuwana duniya ba, musamman idan na natsu ina tunani akan yanda ya ke ina nakasa ina naka aje da Sumayya da Habiba, Sumayya da Habiba yayena amma ba uwarmu Waya ba, Sumayya Mamace wacce ta haifeta ita kuma Habiba Wiyar Umma ce abokiyar zaman Mama wacce ayanzu ta tafi da Habiba da Sumayya ganin gida acan Katsina."

"""Mubeena! Mubeenah!! ke Mubeena wannan wane irin iskanci da raini ne ace kina ji na sai faman kwaWa kira nike amma kiyimin banza saboda ke ba yarinyar arzi™i ba ce, idan kika bari da™i™a biyu ta shuWe ba tare da kin fito ba"

"Wallahil'azim na iske ki a Wakinan sai jikinki ya gaya ma ki."""

"Tsulum na fito kamar wacce aka hankaWo na isa gabanshi tare da du™awa na ce ""Dan Allah ka yi ha™uri Abba wallahi Sallah na idasa, kafin in kwashe abin Sallar ne ka kira ni."""

"""Mtswwwww aikin banza da wofi, da anyi magana ki kama sunne kai ke ala dole ta Allah, ki buWe kunenki da kyau ki ji abin da zan gaya ma ki, Allah ya so ki yayanku ya ceceki daga hukuncin da na zartar a kanki, ya tsaya tsayin daka ya"

"nemo ma ki aiki a gidan wasu manyan mutane shahararrun attajirai waWanda kowa ya san da zamansu a Legos ke harma da sauran ™asashe da garuruwa, idan kika natsu kika yi aiki me kyau to ba shakka mun warke daga wannan addababen talaucin, idan kuma bakiyi abin da ya dace ba har suka gaji suka koroki kamar yanda akai ma ki a gidan Alhaji Šan Gaske to babu makawa zaSi biyu ne ya rage ma ki, kodai ki auri Samual abokina ko kuma ki fita salin alin kibarmin gidana dan bazan iya ci gaba da ri™e ki ba tunda na lura ke me farar ™afa ce, daga lokacinda Allah ya haWa ni da ke na fara fuskantar matsaloli a cikin rayuwata."""

"Šif na ji jina ya Wauke na tsawon lokaci, kwanyata ta shiga maimaita min maganganun Abba da ya ce ni me farar"

"™afa ce, daga lokacinda Allah ya haWa shi da ni ya ke fuskantar matsaloli."

"""Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un, Hasbunallahu wa ni'imalwalkil, Allahumma ajirni fi musubati, Abba maimaita min"

"maganarka dan Allah ko zan daina kokonto akan abin da zuciyata ke raya min, Abba da gaske ne abin da kake faWi Allah haWaka da ni yai, kenan ba kaine ka haifeni ba ko, dan girman zatin Allah ka amsa min."""

"Tsit Abba yai ya na jin babu daWi akan yanda na fassara maganarsa, harga Allah ba haka ya ke nufi ba, bai zata"

"hankalina zai kai ga waWannan kalaman da suka suSuce ma shi ba, kafin yasan abin yi muka jiyo muryar Umma da ta shigo yanzu ita da su Habiba ta na faWin."

"""Yo Allah na tuba Mubeena miye banbancinki da tsintacciya, ai wallahi baki da maraba da waWanda ake kaiwa gidan"

"marayu waWanda ake yasarwa a kan kwalta, akaWa a raya Abban dai shine ubanki wanda za ki yi ta™ama da alfahari da shi, domin kuwa ya yi ma ki sutura tunda ya kasance uba agare ki."""

Saurin katse zancen Mama ta yi gudun abin da kan iya zuwa ya dawo idan aka tsawaita zancen.

"""A,ah Umman yarah kece tafe da la'asar sakaliya, lalle marhaban da isowa, Biba Sumayya ku shigo daga ciki manah kun toge a bakin ™ofa kamar wasu ba™i."""

TaSe wawakeken bakinta Umma tai tare da jifar Mama da wani banzan kallo sannan ta cire yalolon mayafin cikinta

ta sagaleshi a igiyar shanya sannan ta turo Wan kwalinta gaba ta na faWin.

"""Wallahi ko Zainabu kinganni nan yanzu nai ra'ayin isowa, kuma babu wanda ya isa ya mayar da ni, ya muka same ku?."""

Cikin rashin jin daWin yanda Umma ke gwasaleta idan tai ma ta magana ta ce.

"""Muna lafiya lau Alhamdulillahi."""

"""A,ah kaga uwar gida me Capacity, Hajiya Halima ikon Allah, anbuga da ke ambarki ma™iyanki fadawanki, ke ce Waya rak amintaciyya a zuciyar Ibrahima, yo in banda ™addara da jaraba irin tawa mi na gano a wajen sauran mata da na"

"nace akansu harda fa ™aro ma ki kishiya, oh ni Iroro jikan Me ™osai, In sha Allah daga Zainabu na kulle bazan sake yo maki kishiyaba da yardar Allah."""

"Abba yai maganar ya na zuro kanshi ya na le™a cikin jakar Umma wacce ya ke hango wal™iyar ´an dubu-dubu sababbi dal, kamar wuyanshi zai Salle saboda le™e."

Ita kuwa Umma sai wani fari ta ke da idanuwa tare da ™ara buWe bakin jakar dan Abba ya samu damar ganin kuWin da kyau.

Cikin rashin jin daWin abin da Umma ta yi wa Mama ta tashi tare da jan hannun Mubeena da ke du™e cikin

mawuyacin hali ta nufi Wakinta da ita.

"Habiba da Sumayya ne suka shigo su na yatsine fuska a fizge suka gaisarda Abba, cike da fara'a ya amsa ya na musu"

sannu da hanya.

"""Mama bazan iya ci gaba da jurar waWanan munanan kalaman daga bakin Abba ba, Mama ki tausayawa halinda nike"

"ciki ki faWamin wacece ni? shin dagaske Abba shine wanda ya haifeni, ko kuma ni Win ba ´arsa ba ce, miyyasa ya ke banbanta ni da Yaya Babiba da Yaya Sumayya?."""

"Nai maganar ina me tsareta da rinannun idanuwa waWanda launonsu ya koma jah saboda kuka, ji nike gaba Waya"

"rayuwar ta ficemin, duniyar tai min zafi, banajin daWin komi, ga zafin zuciya ga zafin dukanda Abba ya yi min."

PAID BOOK NE AKAN 500 ONLY

TA KU HAR KULLUM

MARYAM STAR

³AR BAIWAR JAJIRTATTU WRITERS

5ØÜ5ØÜ5ØÜ5ØÜ5Ø
Ü 5ØÜ5ØÜ5ØÜ5ØÜ

LABARI ME CIKE DA

"BAN TAUSAYI, "

"MATSANANCIYAR DAMUWA, KUNCIN CUZIYA, "

"SADAUKARWA, "

ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.

WRITING BY

MARYAM STAR YAR BAIWAR JJRT.

MARUBUCIYAR

RAYUWAR SAMHAD DAFIN MACIJI

A DAREN AURENA AND NOW

ZAFIN WUTA

*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341

&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v

*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*

*(J.W.A)*

"_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ™asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau™i_. "

"""Jajirtattu mu ne ™arfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faWuwa. Mu ne tarihi"

"da ake ginawa!"" "

THE NOBLE WRITER'S TEAM

( DEDICATION IS OUR STRONG )

Typing...

PAID BOOK 500 ONLY

Season two

Chapter 10-15

"Gudu ya ke shararawa a cikin dajin da babu komi sai kukan tsuntsaye da halittu masu firgitarwa, bai tsaya a ko ina ba"

"sai nesa kaWan da wajen wani kogon dutse, kashe motar yai tare da fito a firgice ya tsaya daidai wani waje inda aka aje wasu tsofaffin ™orai, cikin rawar jiki ya cire kayan jikinshi tas yai tsirara haihuwar uwarshi sannan ya jefarda kayan a saman ™oran ya rufe idanuwanshi tare da juyawa ya na karanto wasu damatsilan tsafi ya isa gaban kogon, a zahiri kogon baida wa ta ™ofa sai wa ta ´ar huda ´ar ™arama wacce wani bakin haya™i ke fitowa, ci gaba da karanto damatsalan yai har wannan ba™in haya™in ya baibaiye inda ya ke tsaye, Sat ya bace daga wajen bai samu kanshi ba sai a gaban wani shirgegen ba™in mutum me tsananin muni wanda ya ke tsirara haihuwar uwarshi babu ko ™yalle a jikinshi sai wani jan abu da ya naWe al'aurarshi da ita, a hankali matashin ya fara ruWe idanuwanshi bayan jin saukar"

"wani ruwa me yau™i akan jikinsa, buWe idonshi yai tare da yun™urawa cikin zafin nama yai Sujjada tare da kirari ga"

wannan ™aton zindi™in bokan.

"Wa ta arniyar dariyace ta cika kogon wanda ke zagaye da abubuwan ban tsoro iri daban-daban, bayan Waukewar"

sautin dariyar matashin ya Wago tare da sharce guminda ke tsatstsafo ma shi sannan ya maida hankalinshi akan bokan.

"""Kamar dai yanda aka saba sadaukarwar wannan karonma tayi kyau, Zuka ya ji daWin jininda aka bashi yanzu a shirye"

"ya ke dan ganin ya biya maka dukkanin bu™atunka."""

Boka yai maganar bakinshi na amayarda tururin ba™in hayaki harda tartsatsin wuta a lokacinda ya ke magana.

"""Ina godiya Boka uban bokaye, hatsabibi uban hatsabibai, Mutum uban Aljannu, zaka dawwama kana juya duniya"

"da mutanen da ke cikinta ta ™arfin ikon ka."""

Wani mumunan murmushi Bokan ya saki wanda ya sake bayyana munin halittar fuskarshi wacce sam babu kyan

gani.

"""Kana tare da sa'a da nasara saboda biyayyarka agaremu, tabbas akwai shahara a tare da kai burukanka da yawa"

"zasu cika saboda ™arfin iymanin da ka yi da mu."""

"Nan matashi ya zube tare da kwararo godiya sannan ya shiga lissafo abubuwanda ya kawoshi, bayan ya gama"

"jawabinshi Bokan ya Waga hannunshi sama tare da karanto wasu kalmomi, nan take hanun ya shiga buWewa har wani dun™ulallen abu ya bayyana, Wayan hanun nashi me kama da icce ya Waga tare da shafa abinda ya bayyana, nan take ya shiga warwarewa yana buWewa gamida bada tsawo da faWi, wani madubine ya bayyana."

"Mutum ne a kwance kamar gawa, babu abin da ke motsi a jikinshi, babu ko tufafin kirki a jikinshi sai wani farin gyalle"

"da aka lulluSe iya al'aurarshi, jikinshi kamar babu tsoka saboda tsabar yanda ™asusuwa suka firfito miraran, fatar jikinshima duk ta ta™une ta yamushe kamar tsoho, wani abin mamaki kuma gashin kanshi na nan kwance luf kamar ba™i ™irin kamar na larabawa ko indiyawa, wani tururin haya™i ne ke fitowa daga ™ofofin gargasar da ke jikinshi."

Wata iriyar dariyace matashin ya kece da ita tare da faWin.

"""Fauzan Shareef Abdallah kaga abin da taurin kai da binciken ™wa™waf ya janyo maka ko, ka ga abin da nike mama gargaWi akashi ko, indai ZAFIN WUTAR tsafi ne yanzu aka fara, sai na ™one gangar jiki da ruhinka da ZAFIN WUTA wannan itace makomar da ka zaSawa kanka, duk wannan iko da dukiyar da kake ta™ama da ita sai na yi sanadiyyar ™arewarsu, sai rayuwarka ta WaiWaice ta wula™anta, sai na maidaka abin tausayi a cikin mutane, dole ne in nuna maka nafika tantiranci da hatsabibanci."""

Cike da mugunta ya kalli Bokan bayan ya gama magana a fusace ya ce.

"""Ya shugabana Boka uban Bokaye ina so ayiwa Aljani Zuka albishirin jinin jinjirin da ™anwata zata haifa, ina so ya"

"sake ninka azabar da yakewa wannan kafaffen Fauzan Win azaba me tsanani ta yanda hatta makusantanshi zasu ji tsoron kusantarshi, so nike asa wuta ta dinga ™ona gangar jiki da ruhinshi, ina so hannu ya gagara taSa jikinshi, ina nufin a ™one duk wanda zai taSa shi, sannan ina so a hana gangar jikinshi saurin ™onewa saboda banso ya mutu da wuri, ina so ya WanWani u™uba da azaba me raWaWi."""

"Dariya Boka ya kece da ita tare da dun™ule madubin sannan ya shafa, nan take ya Sace hannunshi ya dawo daidai, har zuwa lokacin be daina mumunar dariyarba wacce ke kama da saukar aradu saboda tsananin munin muryarsa."

TAKU HAR

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment