gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading MASARAUTAR QAMAR Sirrin Sarauniya Book 2 By Khadija (KMU) Chapter 11 | ArewaNovels google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shiga rayuwar mutane ba ita haka Allah yayita kuma batasan ana shiga rayuwarta saida mi bazata iya zama tana kallon ana Neman kashe Wasba





Shiga cikin gidan tayi sannan tazo saitin matar tana watsa mata wani kallo da idanunta masu kwarjini cikin tsiwa da gadara matar tace ke kuma daga ina shegiya la anarna halan kema zuwa kikayi domin ceton ta Tau bari kiji inagaya maki wanda suka fiki ma sun barni don ba wanda ya isa ya kwaci wannan tsintarciyar magen cikin gidan nan tana rike kugu tana watsa ma Hurriya wani kallon banza



Hurriya batace kala ba tana kallonta har tagama kumfar bakinta





A hankali Hurriya tazo saitin wasba tana kallonta duk ta rame ta fita hayyacinta Hurriya sam bazaka iya karantar abinda ke fuskar taba



Dagota tayi sannan tace sannu kinji bata gama fadar sannu ba taji anja mata gashi abinda kam tafi tsana arayuwarta kenan wani ya tabata hakan yana triggering dinta wanda har monster in her mutum zai iya gani A hankali ta juyo domin kallon isasshen saidai ko mamaki babu uwar rikon wasba ce kallon hannunta Hurriya takeyi wanda yake rike da gashinta tana mamaki is she kidding her dayan gashin Hurriya ta fara ja wanda ya sanya Hurriya Tayi saurin janyewa tareda dauketa da kyakyawan mari rike tana watsa mata wani kallo me ma anoni



Rike kuncinta tayi tana lailayo wani ashar ai bata ida kai aya ba Hurriya ta kara wanka mata mari





Kallon bukitin da ta cika da ruwa Hurriya tayi aiko ta dauko ta sheka mata shi duka wanda ya sanya ta faduwa tana shesheka





Hurriya bulalar da ta yadda ta dauka ta fara zabga mata ita ko ina ajinkinta da tsantsar mugunta da keta ihu takeyi kota ina tana Neman taimako acece ta Amman shiru ba wanda ya lekota saida Hurriya ta tabbata tayi mata blue and black sannan taje wurin wasba har zata tada wasba wata roba ta dauki hankalinta



Robar yaji ta hango aiko ta nufi yajin sannan tazo saitin fuskarta ta zazzage mata shi ihu take tana kiran sunan makwabtan ta Amman ba wanda yayi yunkurin taimaka mata





Hurriya riko wasba tayi wanda zata iya cewa abinda bata taba ba all her life kenan wasba kam murmushi tayi tana kallon Hurriya tanajin kamar taga mahaifiyarta har sunzo zaure Hurriya ta tuna da har yanzu bataga jini na fita a jikin matar nan ba anya zata iya bacci yau batare da taga jini na fitowa ba cewa tayi dan zauna sannan ta koma ciki



Hurriya Kallonta tayi ko motsi batayi alamar ta suma Amman a haka Hurriya taje ta take mata hannu tare da murzawa yadda ko bata kare ba tasan akwai gocewar kashi ko babu gocewar kashi akwai targade tafison tayi jinya kamar yadda ta sanya wasba jinya







Ba inda ta tsaya sai dakinsu sannan ta kalli wasba tace ta kwanta ta huta zata samo mata abinda zataci wasba murmushi kawai take tana binta da kallon kauna



Kitchen Hurriya ta shiga bata iske inna hanne a kitchen din ba saidai haule reza don haka Hurriya wurinta ta nufa tace mata ta zuba mata abinci ba bata lokaci haule reza ta zuba ma Hurriya abinci da yake tana yinta sosai amsa Hurriya tayi batare da tace ta gode ba ta nufi dakin ta kalli wasba tace tashi kici ahankali wasba ta tashi sannan ta karbi abincin a hannun Hurriya tayi bismillah ta faraci taci abinci sosai Hurriya cikin kayanta ta lalubo wani magani da aka bata farkon zuwanta masarautar Qamar ta mika mata tace ta sha .amsa tayi tana yamutsa fuska alamar batasan magani Ganin irin kallon da Hurriya takeyi mata ne ya sanya ta hadiye maganin hade da ruwa.









A hankali yake saukowa daga saman bene ba abinda bai Ganin ba ta CCTV camra inda akayi mashi barbade yana kallonsu da duk abinda suke cewa jin takunshi da isowarsa ya sanya kowa ya shiga taitayinshi



Takunshi wanda yake bayyanar da kamala kuma da taurin kai sai kuma aura dinsh da take zagaye dashi



Tunda suka ji takunshi kowa ya shiga tsananin fargaba da shakku don ya cika ko ina a parlon da kwarjini da girman shi fuskar shi babu alamun sassafci ko sauki idon shi rufe da glasses mai kyau da tsada sai walking stick dinshi wadda ta kara fito da dressing dinshi





Dukansu dukawa sukayi har yazo katon dining dinshi kallonsu Dukansu ya shigayi yana karantarsu bude kulolin yayi na different varieties na abinci sannan ya tsaya a dake ya dage table din baki dayanshi banda karar fashewar Abu ba abinda kakeji a wurin plate da abincin suna tararatsewa komai yana zubewa kasa cikin tsananin bacin rai yake kallon duka munafukan fuskokin su da suke kallon kasaa ya buga masu wata muguwar tsawa yace how dared you ba wanda acikinsu hanjin cikinshi bai kada ba saboda tsawar da ta ratsa ko ina na falon ida juye komai yayi kara kawai kakeji wani abu ya danna aiko nan da nan sai ga cheif of security ya shigo kallonshi yayi sannan yace they re all fired kuma kayi punishing dinsu according to my rules how dared they messed with their future king .chief of security ya dukar da kanshi yace yess your league cikin bacin rai ya koma kasa don ko abinci bai bi takanshi ba







Kuyangin suka biyo chief of security din banda kyarma ba abinda sukeyi don sun san kashinsu ya bushe don Allah ya taimakesu ba Khalifha Qamar dakanshi yayi masu hukunci ba





Ba inda suka tsaya sai babban prison din dake cikin palace din chief of security sai kamewa akeyi duk inda ya gifta don shima kamar boss din nashi yake fuskar nan tashi kullum babu dariya anan aka watsa su sannan ya bada dokokin yadda Khalifha Qamar yakeson ayi masu azaba .





Hurriya kam tsayawa tayi tana kallon wasba wadda tana gama shan magani bacci ya dauketa kallon yadda take sauke ajiyar zuciya tayi sannan ta fita wurin Bintu ta nufa inda take zaune tayi uban tagumi kallonta Hurriya tayi sannan tace mike damunki a firgice ta juyo ta kalleta sannan ta turo baki fashewa Bintu tayi da kuka tana kallon hurriya zama Hurriya tayi kusa da ita tana sauraren kukan da takeyi har saida tagama sann Hurriya ta kalleta da ayar tamabayar miye ya sanyata kuka





Bintu kallon Hurriya tayi tace ina cikin damuwa ina tsoron kada wani abu ya sameki Hurriya har yanzu banda sukuni tun ranar da naga kina kokowa da numfashin ki. Hurriya shafa kanta tayi sau daya wanda kamar ta shafa kashi don tana shafawa ta sauke hannunta murmushinta mai sanyi wanda ke fiddo mata da aininhin kyau da kuma wata boyayyiyar charisma da kwarjini tayi hakoranta farare tass da kuma Gold dinta dake tsakankanin hakoranta gefe da gefe





Bintu kallonta kawai takeyi tana fatar Hurriya ta kasance a irin wannan yanayin a har abada ba irin yanayin da zata rinka daure fuskaba



Murmushin daga zuciyarta ya fito wanda ya kasance har cikin ranta kuma zata iya kirga murmushin da ya fito daga zuciyarta irin wannan tunda ta baro masarautar Heral wannan shine na biyu ko kuma







Kallon Bintu kawai takeyi Bintu har ta bude baki zatayi magana saiga wasu kuyangu biyu sunzo wai Gimbiya zinariya na kiran Hurriya .

[5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: <Masarautar Qamar

The mysterious palace



By Khadija (KMU)



37&38



Hurriya kallon wasba tayi wadda har ta fara warwarewa inna hanne ta samo masu aron katifa inda Hurriya ta kwana jiya da yau kwana biyu da suka wuce taje kiran da zinariya tayi mata

saidai yadda matar ta rinka kallonta kamar zata cinyeta ne ya bama Hurriya haushi Sosai don har saida ya zamana cewar Hurriyar ta gaji da kallon da take mata tayi tafiyarta zinariya kam abinda ya bata haushi sosai itadin wacece face kaskantatciya wadda bata da gata









Hurriya kam tafiyarta tayi don bata ga amfanin tsayawa inda akeyi mata irin wannan lusful look din ba



Don kawai bata bukatar wani ya kara tabata a masarautar nan da sunan duka da ba abinda zai hanata ta buge idon zinariya yadda idan ance ta kara kallonta haka gobe bazata

Kara ba saidai tasan girman abun da take tunanin aikatawa ne don as a maid how could she messed with someone like her shiyasa don haka duk hukuncin da akayi mata bazata iya retaliating ba bata cikin yanayin buge idon kawai ma shiyasae don this is not an excuse to her because she doesn t give a damn at all yaushe ta fara tunanin abinda zaije ma ya dawo saidai idan bata ga damar yin abun ba sunanta fa Hurriya Faisait Hamood murmushi tayi kadan sannan ta cigaba da kallon wasba wadda dan kwalinta yadan zame





Kallon cikakiyar sumarta Hurriya tayi wadda take da yawan gaske da cika saidai gashin yayi dukun dukun ga dukkan alamu ba a kula dashi



Ahankali ta taba gashinta wanda itama takejin ya takura ma rayuwarta don tana bukatar aski idan ta aske nata sai taba ma wasba itama ta aske nata don gashin yayi masu yawa









Khalifha Qamar zaune yana kallon masu aikin da ake shigowa dasu yanzu kusan batch na bakwai kenan Amman har yanzu ba wadanda sukayi mashi



Don idan ankawo sai ya tashi yayi analyzing kowacce acikinsu saidai Dukansu ji suke suna cikin wani bala i da masifa saidai kwata kwata baya saukakawa kowanne acikinsu don duk wanda aka kawoshi chamber din Khalifha Qamar to ba ason shi ba a kaunar shi fitinar shi da izzarshi ta ishi kowa





Cheif of security wanda ya shigo da kuyangu kusan guda goma kallonshi yayi yana jiran command daga wurin oganshi kuma uban gidanshi saidai baice kala ba ya tashi ya hau sama



Yasan nufin shi har yanzu basuyi ba cikin rashin gajiyawa da halin yarima ya korasu sannan ya fita zuwa nemen wasu







Khalifha Walking stick dinshi ya canza da wasu kaya masu matukar kyau sannan ya fito yana takunshi mai girgiza makiya har ya iso inda convoy dinshi suke kallon security s dinshi da suna Ganinshi suka fara dukar dakai alamar gaisuwa yayi ya dade yana kallonsu





Alama yayi da sandar shi da abude mashi mota da sauri aka bude mashi farar limousine dinshi ya shiga da tsantsar mulki hade da lumshe ido yanajin kamshin da ya mamaye ko ina a motar sannan suka fara tafiya







Da wani irin mugun gudu suke tafiya kowa basu wuri yake don a yadda suke tafiya basu keda asara ba sai wanda ya haye masu







Wani katon fili ne inda wurin yake dauke da manya manya mutane daga masarautoci daban daban zaune ana kallon polo din da ake bugawa wanda a shekara sau daya akeyinshi





Jiniya ce wadda sarki kawai akeyi ma irinta tohm irinta tawagar Khalifha Qamar sukeyi don wata irin kara jiniyar takeyi wadda saida hankalin kowa ya dawo kansu





Kowa ya saki baki da kunnuwa yana jiran yaga wani issashen ne haka



Mai martaba sarki Faizan Qamar wanda yake zaune akan kujerar girma ta mulki ya kalli motocin da suke shigowa wurin da wani irin mugun gudu murmushi yayi yana kara gyara zama The Devil is back Don basai an fada mashi kowaye ba makahon Kaninshi ne ya dawo wanda hakan bai bashi mamaki ba ko kadan don an sanar dashi zuwanshi don yana sane da duk abinda ke faruwa a chamber dinshi murmushi yayi na kasaita

Saidai abinda ya bashi mamaki mi ya kawo Khalifha a filin polo don tunda ya fara makanta shekara goma bai taba zuwa ba sai yau



Akwai kallo kenan koma miye a hannun rigarshi yana jiran yagani







Bude mashi kofa akayi sannan ya sauko da kafafunshi.

girman hallitar shi da kuma annurin sallahr fuskarshi ya fito sosai wanda ya sanya ma masu kallonshi shakkar shi



Brass Nautical folding stickc ce rike ahannunshi na dama yana dogarata cike da mulki



Ba wanda zai kalleshi yace mashi makahone don ko lokacin da yayi makanta ba lallai Kagane cewar shidin makaho bane saboda yadda ba wanda yake taimaka mashi da hanya kuma da alamari na Rayuwa



Ya fito a cobra dinshi dangerous and poisonous don aura dinshi ta cika ko ina





Ba inda ya tsaya sai inda wurin da taron manya mutane suke zazzaune kallon kujerar da yayanshi yake zaune yayi



While yayan shima idonshi akan Khalifha murmushi Khalifha Qamar yayi wanda mutane suka fi bama irin murmushin suna Devil smirk



Girmamashi ake ana gaishe shi duk inda ya wuce wata kujera akazo aka ajiye mashi ya zauna suna kallon polon





Kusan kowa a wurin a ranshi yake tambayar mai ya kawo Khalifha Qamar nan wurin miyake yi yana makaho wanda bai gani saidai ba wanda ya bari maganar ta fito







Murmushi Khalifha yayi don haka yayi ma chief of security dake gefenshi alama aikam da sauri ya matso





Chief of security yana gama magana da Khalifha ya nufi wurin wani wanda ke rike da usur magana yayi mashi a kunne.









Manage this please ba yawa pagae din yau. Very busy



Share ,comment and like



Love you all

[5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: <Masarautar Qamar

The mysterious palace



By Khadija (KMU)



39&40



Announcement din da akaji coach din nayi ne ya sanya hankalin kowa ya karkata ya koma wurin shi fargaba ce ta mamaye mai martaba sarki Faizan wanda yake zaune kan kujerar mulki







Wurin shiru ya dauka kamar babu kowa a wurin cikin karfin da Allah ya bashi ya mike zuwa filin polo din hannunshi rike da sandar shi



Wani kosasshen doki ne aka fito dashi fari Mai wani irin kyau da daukar ido chief of security ya mika ma sandar shi sannan ya haye dokin





Wanda yaci wasan polon daga masarautar kano ya fito don haka idonshi akan Khalifha Qamar wanda yake makaho mizaiyi yanzu kuma bayan angama wasa kuma ya za ayi ayi wasa tsakananin mai gani da makaho gaskiya kilan barcin rashin ido to yana da tabin hankali na musamman don ba wanda ya taba cinshi a fagena wasan polo bare kuma makaho



Gaskiya an mutunci shi da kuma kimarshi saboda a rasa dawa za a hadashi wasan sai makaho





Tun kafin aje ko ina zaiyi maganin shi,

Khalifha kallonshi yayi sai kuma ya maida hankalinshi wurin dokin



Tambayar su akayi sun gama shiryawa dayan yaron ya bada amsa while Khalifha Qamar yayi shiru





Ganin kallon da Khalifha yayi ma chief of security aiko nan da nan chief of security din yace yerima ya shirya da wani irin zafin nama Khalifha ya fara gyara dokin shi





Mabusa aka hura masu wanda yasanya acikinsu kowa ya fara buga wasanshi





Ba wanda hankalinshi bai karkata wurin wasan ba saboda abun da mamaki makaho da buga wasan polo



Fargaba da tsoro ya cika zuciyoyin mutane da dama wanda aciki harda Danuwanshi wato Sarki Faizan Qamar







Zuciyoyin mutane da yawa sun buga jin ana announcement na cewar Khalifha yaci wannan wasan



Rabonshi da irin wannan wasan shekara Goma kenan kuma ko a shekara gomar da suka wuce Khalifha Qamar bai taba faduwa wasan polo ba don duk inda yayi sai yaci







Yanayin sarki Faizan ya canza Sosai ba abinda fuskarshi ke nunawa irin zallar bacin Rai da damuwa Anya Khalifha bai warke ba abinda ya tambayi kanshi kenan





Ya akayi yaci wasan?to ai Khalifha Qamar da zuciyar shi yake gani bada ido ba don ba abinda bayayi duk da baida ido polo ne kawai ya Daina wannan kuma ba wanda yasan dalilin hakan

Sarki Faizan tausar zuciyar shi ya farayi a hankali yace haba dai kadaina irin wannan tunanin Khalifha shida ya gani kilan har abada amman ina







Galadima ne yadan karkato yayi mashi rada wanda a wani irin duniyance launin fuskarshi ta canza ta dawo mai dauke da murna





Saukowa yayi daga kan dokinshi sunanshi kawai ake kira wato Khalifha Qamar Dan sarki Qamar yadda yake tafiya zai tabbatar maka dacewar shi din sarki ne don kwarjinin shi bugun xuciyar makiya da yadda yake tafiya kamar yanajin tsoron taka kasa Amman acikin tafiyarshi zaka hango karfi kuma da jarumtar da Allah yayi mashi









Sarki Faizan ne ya sauko daga kan kujerar mulkin shi yana mai jin faduwar gabar haduwar shi da Khalifha dan Karamin kaninshi kuma da ya zamar mashi babban kalubale a rayuwarshi





Gardawan Guard din Khalifha ne suka zo da sauri suka tarbe saitin da sarki Faizan yazo tare da kareshi suna fitoda manya idanunsu waje da bindugu





Shiru wurin ya dauka kowa idanunshi bude suna kallon ikon Allah sarki fa dakanshi





Black Americans ne Guard dinshi Giant Kamarshi wanda daga gani they are loyal kuma sun san aikinsu





Ba wani alama ta girma da suka bama sarki Faizan abu daya suka Sani cewar bai isa ya gifta layin da suka ja ba kuma tabbas idan ba Khalifha ko chief of security yayi masu magana ba bazasu taba barin shi ya wuce ba





Da sanda Khalifha yayi ma chief of security alama da subar shi yazo aiko yana masu magana Dukansu suka matsa





Murmushi sarki Faizan yayi tare da zuwa wurin Khalifha ba wani bata lokaci ya rungumeshi Khalifha shima rungumeshi yayi back tare da cewa it s being a long time brother I miss you inji sarki Faizan Qamar





Khalifha Qamar wani Devil smirk yayi tare da cewa nazo na amshe sarautar masarautar Qamar Rest assured kaga bazaka kara missing dina ba tunda muna cikin masarautar Qamar



A hankali yayi maganar yanda ba wanda ya isa yaji face sarki Faizan Qamar



Murmushi sarki Faizan yayi sannan yace banda abun Khalifha ka taba ganin inda makaho ya sarauci Al-umma





Ko kallo Khalifha bai kara bin sarki Faizan dashi ba bare yayi tunani amsa ya nufi hanyar motar shi don shikam ya gama magana idan kuma yariga ya gama magana to ba wanda ya isa ya sanya shi ya maimaita miskili ne sosai



Manya manya mutane ne sukazo wurin Khalifha da niyyar yi mashi magana amman security s dinshi suka dakatar dasu ta hanyar daga masu hannu da nuna masu bindgogi







Tashin kurar mota kawai kakeji a wajen wanda hakan ya sanya mutane dayawa cikin alhini da fargaba







Sarki Faizan Qamar har baya Ganin gabanshi saboda tsananin bacin ran da yake ciki da kyar ya samu ya lalubo murmushi a fuskarshi yayi ma manya mutanen dake wurin sallama





Khalifha Qamar cikin motane ya saki wani murmushin mugunta sannan ya kwanta akan kujera tare da lumshe ido.





Wanda sukayi polo da Khalifha kam ya raina kanshi sosai don daga baya ya gane cewar Khalifha jarumi ne.







Hurriya kam Al-Amarin zinariya yanzu ta rasa mi zatace saboda kullum akwai abubuwan da take badawa akai mata na duniya duk abinda ta bada kuma haka zata sanya a maidashi ba tare da ta kallah bare kuma har ya burgeta





Wasba kam ta samu wuri don ba karamin son Hurriya take ba kuma dawowa datayi a wurin shine babban abu najin dadi data samu a masarautar Qamar Don tunda ta dawo wurin Hurriya komi za a kawo ma Hurriya indai na ci ne tohm sai ta rage tukunna Hurriya ke cin abinci koda Hurriya kam bataci komai ba Allah ya sanya mata kaunarHurriya don tanajinta kamar wani bangare na jikinta







Kullum sai ta nuna ma Hurriya tayi Bacci don haka Hurriya na kwanciya zata matso gefenta ta kwanta sannan tayi mata addu a da taga ta fara motsi sai ta koma katifarta ta kwanta





Hurriya kallon abubuwan da zinariya ta sanya a kawo mata da safe tayi shrugging kafadar ta tayi tare da tafiya inda take wanki don yanzu aikinta daya a masarautar don kwata kwata ta daina zuwa shashen zinariya aiki



Wankinta takeyi tare da zura earpiece a kunnenta tanajin wakarta mai dadi tana cikin yin wankin uwar bayi tazo tare dayi ma kowa magana Dukansu suka matso wurinta domin jin mai zatace



Yawwa Zamuje sashen Gimbiya subira da kuma yerima Khalifha saboda suna da bukatar masu aiki Don haka ku kiyaye nan ta fara gaya masu irin Dokokin na Subira da Khalifha duka Dokokin are strict Amman ya zasuyi dolensu ne tunda abinda ya kawosu masarautar kenan.







Acikin duka mutanen data tara ba wanda bai shiga cikin damuwaba da tashin hankali ba saboda inda zasuje aikin





Hurriya kam duk da earpieces ne a kunnenta tanajin duk abinda suke cewa



Uwar bayi bata ce mata komai ba don tasan gaba da gabanta aljani ya taka wuta tasan very soon zata shiga hankalinta ta daina wannan jiji da kai din da izzar don mutum biyu mararsa sauki a masarautar sun dawo.







Uwar bayi tayi gaba a hankali suka bi bayanta har zuwa sashe magajiya Zama wato subira tafiyace mai nisa Amman kwata kwata Hurriya yanzu ta daina ganin tafiya saboda har ta saba





Bayan sun iso kowa ta nemi wuri ta tsaya domin jiran Gimbiya subira don ta fito taga idan sunyi mata







Zaune take a wata matsiyaciyar kujera mai kyau sanyi da kamshin turaren wuta mai dadi da tsada sai kafafunta acikin wani ruwan mai kumfa mai matukar kyau da daukar ido



Idonta sanye da wani haddaden designer glasses mai matukar kyau da tsada itadin kyakkawace ta ajin farko don wani irin luminous skin gareta wanda yake brightening kamar sunshine skin dinta kam flawless ga smooth skin dake fidda wani uban glow tanada wani irin dogon gashi wanda yake bude anyi mata gyaran ponytail gashinta brown hair ne mai matukar kyau wanda kallo daya zakasan ana kashe mashi kudi wurin gyaranshi





Tana da dogon hanci mai kyau wanda ya fito kamar biro idonta sun hadu don wani irin double eyelid gareta wanda suka fita sosai eyeballs dinta wani kalan dark brown ne mai shining Itadin mai kyau ce kuma tasan da haka





Kallo daya idan kayi mata zakasan bratty ce ta ajin karshe don yadda take wani yamutsa fuska kamar kashi pedicure akeyi mata wanda har angama soaking kafar gyaran kafar za a fara







Gyaran nails akeyi mata nails dinta masu bala en kyau very cautions matar takeyi mata saidai subira da wayarta na a hannunta tana dariya sai kam hannun matar ya goce tare da yankarta kadan





Duk abinda ke wurin tsayawa yayi domin sun san rashin mutuncinta





Saukar kyakkawan marin da sukaji ne wanda ya sanya kowa shan jinin jikinshi



Dukar da kanta matar tayi wani irin matsiyacin kallo subira take aikawa matar da ta kusa haihuwarta shiru wurin ya dauka



Tashi subira tayi tsaye anan naga komai nata itadin doguwace saidai ba Sosai ba don baza a sakota cikin jerin gajeru ba tanada wani irin figure mai daukar hankali don everything about her is screaming perfection





Ture matar tayi sannan ta takata bayan takawar da tayi mata jawo kanta tayi baki daya ta sanya shi cikin ruwan kumfar da aka wanke mata kafar sannan ta fito da kan tana watsa mata kallon banza





Numfashin matar yana kawowa yana daukewa Amman batausayi bare tausayawa

Ta kalleta shekeke sannan tace ke kidahumar inace da sauri ta dukar da kanta tace don Allah kiyi hakuri Allah ya taimake Gimbiya kiyi hakuri don Allah





Wani uban tsaki taja sannan ta haye sama kuyangunta na bayanta



Ruwan wanka mai dumi aka hada mata fitowa kuyangar tayi tareda cewar Allah ya taimake ki nagama sannan ta fita subira batace komai ba don wayarta ke a hannunta cire bakin glass dinta tayi ta aje tareda shiga toilet din





Saidai tana taba ruwan da aka zuba mata a komin wanka ta fara kwala ma kuyangar ta kira da sauri saro tazo tana durkusawa ruwan komin ta diba sannan ta watsa mata a fuska saro bata ida dawo hayyacinta ba ta kara watsa mata ruwa mai zafin gaske a fuska wani irin ihu ta kwalla tadiyeta subira tayi da tsantsar mugunta da gadara saida ta fadi akasan tiles din









Saro yau taga bala i a rayuwarta Sosai don saida ta hada mata ruwa ya kai sau ashirin tukunna akasamu yayi ba irin zagin da batayi mata ba yau ,zagin na cin mutunci ma da wulakanci kuka Saro ta rinkayi data fito duk wanda ya ganta kawai hakuri yake bata.







Hurriya suna tsaye kusan awa dinsu ta uku kenan ga sanyi ita kadaice ma ta samu wuri ta zauna tanajin wakarta hankali kwance ta riga da tace idan har aka kara minti biyar ba a

Please Login or Register in order to submit comment