gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading A Wani Gida Complete Hausa Novel by Nabeelert Lady Chapter 7 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tasha wahalar Mama, dan haka bazata kara yarda da duk matar da Malan ze kawo ba, idan ada tana yarinya anyi mata abubuwa yanzu babu macen da zata kara dukanta. Allah yakawota lafiya,wai zeje ma Yaya visiting, dama can rashin sone yasa baya zuwa amma kaji zeje wai laifin Mama, kawide dan yaga yanzu mun girma shiyasa yakeso yajawo mu ajiki, ganin Malan ze dameta da surutu yasa ta kwanta.



A kofar gidan Malan ya ajeta, domin yasan gidan Alhaji, kuma yace ta gaishe mashi da Inne, sannan tace mata tayefe mashi. Ita de Fatima ta amsa ne kawai, haka tafita tabarshi dan har yanzu bata saba dashi ba.


Ihun su Khairat da Ansar ne yasa Inne tayi saurin fitowa. Tsayawa tayi tana kallonsu yanda suka rungume Fatima, kara murza idonta tayi dan ta tabbatar da abinda take gani. Da gaske itace. Ya akayi Malan yabarta tazo? Kuma ai Fatima batasan gidan nan ba.

Matsawa tayi ta kamota tana murmushi tace da gaske kece Fatima? Fatima tace nice Inne, kuma tare mukazo da Malan, amma yatafi. Inne da ta cika da mamaki tace mushiga ciki.


Bayan Fatima taci abinci ta bama Inne labarin abubuwan dasuke faruwa agidansu, hada labarin abinda Farida tayi amakaranta, kuma ta bata labarin abunda su Fahad sukayi har aka koreshi, kuma ta fada mata auren da Malan zeyi. Sosai Inne tayi mamakin Fahad.

Dama kuma duk cikin yaran Mama shine yakeda wata zuciya, kuma shine tafi sangartawa. Inne tace Allah ya kyauta kuma ya shiryasu, ashe su Hauwa za'a samu wata kishirya kuma. Fatima tace yanzu Inne kozaman gida Fahad bayayi, gashi da anyi mashi abu yayita zagin mutum, bakiga irin dukan da yayima Farida ba.

Inne tace kede ba ruwanki dashi, Fatima tace ni dama bana shiga harkarshi, Inne tace ina Farouk fa? Fatima tace Allah sarki Yaya me kirki ba, yana makaranta wannan karon bezo week end ba. Inne tace ai zan samu numbershi ince yazo mugaisa, haka sukayi tafira, abubuwa kala kala Inne takawo ma Fatima, da yamma kuma suka shiga kitchen tare.

Lokacin da Alhaji ya dawo shima yayi mamakin zuwanta, anan Inne tabashi labarin da Fatima ta bata, hada maganar auren Malan, sosai shima yayi mamaki, addu'a yayi shima yace Allah yashiryasu. Allah yasa kuma su Fatima suji dadin matar daze aura.


**** ****

A na gobe daurin auren Malan Farouk yazo gida sunyi hutun mid semister, dan yanzu suna a second semister ne, sosai yakara girma, gashi yakara hankali, bayan sun gaisa da Mama yaci abinci take fada mashi halin da ake ciki.

Sosai yayi bakin cikin abinda yafaru, yace kin gani ko Mama, shiyasa tun wancan lokacin naso kibari afadama Malan, domin Fahad yana jin tsoron Malan yanzu ga irin abinda yajawo ma kanshi.

Mama tace dan Allah kada ka bata mani rai, shege me hali irin na Ubanshi, abun bakin ciki yasamu Dan uwanka amma ka tsaya kana fadar maganar banza, to de abun kunya ba akan Fahad aka farashi ba.

Kuma ni nasan wadda tayi mashi haka, kasa ido kayi kallo wata rana akan yaranta asirin ze koma. Farida tace Yaya yanzu kana dinkin hular? Hararar ta yayi yana fadin bansani ba, sakarai ya kawai, inda Fatima ta fiki kenan.

Kina kallon mutun bazaki iya mashi sannu da zuwa ba bare ki gaisheshi, seyanzu zaki tambayeni abinda be shafeki ba. Mama tace tashi kabani waje, Fatimar taje tayi ta finta seme? Ai de har abada bazaka canza Farida ba.

Kuma Fatima bazata taba zamowa jikinka sosai ba, domin rabin jininka ce, Farida itace take cikakkar jininka. Fatimar da kake fadi yanzu ma tana ajen Uwarta, kaga kuwa dole ka rungumi Farida tunda a inuwa daya kuke zaune.

Sakarai wanda baya kishin yan uwanshi da ni kai na, wallahi idan kace irin wannan halin zaka kawo mani zakasha wuyata, domin bazan lamunci karika tsanar yarana kana fifita wasu banzaye can ba.


Tashi Farouk yayi rai abace, saboda halin Mama yasa ko week end bayason zuwa, mutum yadawo daga makaranta yana farin ciki amma daga zuwanshi ko hutawa beyi ba an fara zaginshi, ya kamata ace yanzu tadena zaginshi agaban Farida.

Shiyasa da akayi hutun waccan semister yayi zamanshi makaranta, dan dinkin hularshi yafiye mashi yazo gida, seda ana saura kwana 3 adawo sannan yazo gida. Dakinshi ya wuce yaje yayi wanka lokacin Malan yadawo yashiga suka gaisa.


Sosai Malan yaji dadin ganin Farouk dan duk wanda yaganshi seyaga nutsuwa atare dashi, komai cikin nutsuwa yakeyi, anan Malan ya mashi maganar Fahad kuma yace meyasa be fada mashi ba. Farouk yace kayi hakuri Malan.

Naso infara fada maka se Mama ta hana, Malan yace ai shikenan, amma daga yanzu duk abinda yake faruwa banaso karika boye mani, nafiso kome zaka fada kataho wajena muyi magana, kaga kaine babba idan ba ka sakin jiki dani kana fada mun komai ai sauran yan uwanka bazasuyi koyi da kai ba.

Farouk yace haka ne, kuma insha Allah zan gyara. Malan naga anyi mana dakuna, Allah yasaka da alkhairi mungode. Malan yace bakomai, wancan dakin ma gobe za'a kawo amaryata. Farouk yayi murmushi yace Malan aure zakayi? Malan yace ko na tsufa? Farouk yace a'a, amma Mama bata sani ba ko? Malan yace zata sani amma se an kawota. Farouk yace Allah yasa alkhairi.

Malan yace amin, kaima Allah yayi maka albarka, nan Malan yafada amshi ya bude shago, haka suka yita fira, daga karshe yajashi suka fita dan yaga shagon.

***** ****

Washe gari wajen karfe 12 Malan yashirya cikin babbar riga se kamshi yakeyi ko sallama beyima Mama ba haka yatafi dauri aure, Mama bata san wainar da ake toyawa ba, hatta da mazajen unguwar sunje daurin auren amma babu wadda ta fada mata.


Salamatu da Momyn Teema sosai wannan aure yayi masu dadi, Maman Sultan ma batasan zeyi aure ba dan mijinta baya gari.


Bayan angama daurin aure kowa ya nufi wajen da za'a ci abinci, domin suna gamawa zasu dauki amarya su taho da ita, dan yanzu andena daukar amarya da dare. Kowa yaga Malan yasan yana cikin farin ciki. Bayan sun gama reception sukayi la'asar sannan aka basu amarya.


Farouk ne yashigo dakin Fahad domin tun da yadawo basu zauna dashi ba, dan har yanzu Fahad yana jin haushin Farouk, ko magana baya mashi, har Mama seda Farouk ya fada mawa, amma babu abinda tace se cewa tayi tunda kaima ka tsaneshi ba dole ze kyaleka ba, jin abinda Mama tace yasa Farouk ya kyaleta.

Warin wiwi yaji daga bandakinsu, fita waje yayi yana jiranshi yafito. Fahad yana fitowa ya jawo dakinsu dan fita zeyi. Koda yaga Farouk be kalli inda yake ba haka ya nufi hanyar fita.

Farouk ne yace wai kai Fahad meyasa bakada hankali ne? Yanzu dan rashin mutunci acikin gida zaka rika mana shaye shaye? Duk irin abinda yafaru da kai be zamar maka darasi ba? Yakamata ace kaji kunyar abinda ka aikata har yasa aka koreka daga makaranta.

Wallahi inda nine kai daga ranar da aka koreni daga ranar nabar shaye shaye, domin shine silar jefani cikin halin da nashiga. Amma dayake kai ba kada tunani shikenan seka dawo kabude sabon iskanci agida.

Fahad yace na bude dan Ubanka, ai gidan banaka bane, nima ina da gado aciki, kuma naje nasha wiwin, idan dakinka nashiga nasha se kayi mani mgana. Da aka koreni kuma ai ba kai aka kora ba zakazo kana zagina banza kawai, wallahi yanzu na tsaneka.

Daukeshi da Mari Farouk yayi yana fadin ni kake zagi? Dun kule hannu Fahad yayi ya kaimashi naushi a hanci seda jini ya fita.

Haka suka fara kokowa suna ta dukan junansu. Farida ce ta taho kiran Farouk, ai tana ganin an danne Fahad a akasa ana duka ta ruga da gudu tana kiran Mama. Da kyar Fahad ya ture Farouk lokacin daya watsa mashi kasa a ido.

Yana tashi ya hangi wani karfe babu bata lokaci yadaukoshi ya caka ma Farouk aciki, dede lokacin da Mama da Farida suka zagayo, hannu Mama ta dora akai ta fasa ihu tana fadin Fahad bakada hankali.

Farouk kuwa tuni ya sume awajen. Kuka kawai Farida takeyi, haka Fahad ya fice yana huci, yana fita yaga motoci suna parking akofar gidansu, ko kallonsu beyi ba yayi gaba, Malan da yake fitowa daga mota yabishi da kallo.

Mutanan unguwa se lekowa suke suna kallon masu kawo amarya, da gudu Mama tayi waje domin ta nemo wani yazo akai Farouk asibiti. Tana zuwa bakin gate ana shigowa da amarya se guda akeyi.

Tsayawa tayi tana binsu da ido, da Zulai suka fara hada ido, ko kallonta Zulai batayi ba haka suka wuce wasu mata suna fadin Suwaiba kin samu gida dankari. Daskarewa Mama tayi a wajen tana maimaita sunan Suwaiba abakinta.

Farida ce tafito da gudu tana fadin Mama wallahi jini se zuba yake a cikin Yaya, zubewa Mama tayi awajen a sume dan batama san abinda Farida take fadi ba.


Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263

๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ Ina mika godiyata agareku, kucigaba da kasancewa dani. Love u all

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment