gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading A Wani Gida Complete Hausa Novel by Nabeelert Lady Chapter 4 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fadin ashe halin da kasa kanka kenan Fahad? Dama na dade ina zarginka ashe zargina gaskiya ne.

Ka cuci kanka, kuma kanka zaka lalata ma rayuwa, tun kana yaronka zaka bata hun hunka da hayaki. Cikin kuka Fahad yace dan Allah Yaya kada ka fada ma Malan. Murmushi Farouk yayi yace Malan kadai kake tsoro ko? Baka tsoron Allah.

Kuma baka tsoron lafiyarka. Shikenan, bazan fadama kowa ba, duk abinda kayi dan kanka. Hamza muje anfara kiran sallah. Fahad yace Yaya dama anan kake? Farouk yace E, kuma ka tabbatar ka koma makaranta.

Juyawa sukayi suka nufi makaranta, zuciyar Farouk kamar zata fashe wai Fahad ne yake shaye shaye? Dama yasha zarginshi akan hakan, dan wani lokacin idan yadawo da dare se yarika jin warin sigari ajikinshi.


Hamza ne yace dan Allah Farouk kada kabari wannan abun ya dameka, tabbas nasan akwai ciwo,amma hakuri shine zefi, kuma kamar yanda kace ba zaka fadama Malan ba, wannan ba shawara bace.

Domin ba'ayin shiru a irin wannan yanayin, Fahad yaro ne, idan har ba a dauki matakin hanashi wannan shaye shayen ba to tabbas idan ya girma abun zefi haka. Gara kabata dashi akan kace zaka rufa mashi asiri dan yaji dadi.

Farouk yace ina tsoron yanda Malan ze dauki maganar ne, Malan yana da zafi, kawai zan fadama Mama nasan zata iya shawo kan matsalar. Hamza yace amma Malan zefi yimashi ta zafi akan Mama.

Farouk yace baka san halin Malan bane, kawai kabari zan fadama Mama. Hamza yace to Allah yasa ya gane, kuma Allah ya shiryeshi. Farouk yace amin. Haka suka nufi makaranta.

Fahad kuwa gaba daya hankalinshi yatashi, tsoro yake kada Farouk yafadama Malan, wani abokinshi ne yace haba abokina, meye na wani damuwa? Ai tunda kaga be dauki wani mataki sosai ba shima be rasa afawa.

Koda ya fada agida kawai kace masu ka dade da denawa, amma taya zasu hanaka jin dadinka, kai bakaji yanda kakeji ba idan kana sha? Nima lokacin da aka kamani agidan mu inasha kawai dan fada ne akamun.

Kuma na nuna masu nabari, shikenan kuma se aka koma ana jidani. Haka suka yita yima Fahad hudubar banza, kafin subar wajen seda wani yakara kunna mashi yabashi yasha sannan suka koma makaranta hankalinshi kwance.

****** *****

Lokacin da akayi hutu malamin su Farida ya bama Fatima takarda ta kawo ma Malan, saboda an kama Farida da wani yaro da dare acikin class suna 'yan tabe tabe, alokacin malamin shi kadai ya kamasu, haka ya zanesu kuma yace seya kaisu wajen Principal.

Kuka suka rikayi suna bashi hakuri, seda ya farfasa masu jiki sannan yace suyi mashi alkawarin bazasu kara ba, haka sukayi alkawari suna kuka. Lokacin da akayi hutu shine ya rubuta takarda ya bama dan uwan kowa yace su kaima iyayensu.

Yasan idan yaran yaba bazasu kai ba, duk da be fadama kowa ba seyai tunanin ai kama iyayensu domin sukara ja masu kunne, kuma yafada masu idan suka sake korarsu za'ayi.

Bayan Malan ya dauko su sam Fatima ta manta da takardar, haka su Fahad da Faisal suka dawo, gidan kowa se murnar ganin dan uwanshi yakeyi. Farida tace shikenan yanzu batare zamu rika dawowa da Yaya Farouk ba? Mama tace Yaya ai yana gidan biki.

Farida tace ina ne gidan biki kuma? Mama tace Isa Kaita mana. Farida tasa dariya tana fadin N.C.E zeyi shi kuma? Mama tace shida Malan sukace sun amince, base yaje yayi tayi ba.

Kude ku dage kutafi jami'a. Fahad ne yashigo yana fadin Mama ina abinci na? Mama tace Oh! Ni, yanzu ya akayi cikinka ya bude haka? Da de baka da cin abinci, ko kun dawo makaranta se kowa yaci kake cin naka.

Fahad yace yo Mama mutum ya kwaso yunwar makaranta ba dole ya nemi abinci ba. Mama tace to kaje kacire kayanka kayi wanka sekaci, dan Allah kalleka kamar ba senior ba, duk kazama kazami wallahi.

Dariya Farida tasa, kafa Fahad ya kai mata yana fadin zanci Uwarki wallahi. Dukewa Farida tayi tana kuka dan taji zafin harbin da yayi mata a cinya. Mama tace bana son sakarci fa, ya daga dawo warku zaku fara fada abinda bakuyi ada.

Tun dazu take son kadawo kuma shikenan kana dawowa zaka hauta da duka, wai meyasa yanzu kake da saurin zuciya ne Fahad? Kuma ko kunyata ba kaji zaka zagi Uwarta, to bayan ni akwai wata Uwar da kuke da ita ne? Juyawa Fahad yayi yana fadin wallahi Mama duk kece kike bata yarinyar nan.

Wallahi idan kikace zakimun wannan rashin kunyar taki Uwarki zanci, fita yayi yana zaginta. Rike baki Mam tayi tana mamakin canjin halayen Fahad, ada yafi Farouk son Farida, amma yanzu shine yake dukanta hada zagi.

Fatima ce da Faisal suka shigo tana rike da hannunshi suna ta dariya tana fadin Allah Yaya seka bani alawata, ai Yaya Saleem ni yace akawo mawa. Faisal yace ai nafada maki sekin biyani zan baki. Kwace hannunshi yayi ya ruga dakinsu itama ta bishi da gudu suna dariya.

Wani bakin ciki ne ya kama Mama, kallon Farida tayi tana fadin yi hakuri kitashi kiyi wanka kici abinci. Farida tace ni da nayi wanka ma gidan Hajiya zanje. Mama tace a'a kibari se gobe, yanzu kizauna ki huta.

Farida tace kai Mama, nide kibarni intafi. Mama tace kinsan de yanzu Malan ze dawo kuma nemanku zeyi, ki bari kawai se gobe. Farouk ne yashigo da sallama hannunshi dauke da jaka.

Farida ce tasa ihu tana fadin ga Yaya oyo oyo. Murmushi yayi yana fadin Farida yan mata, ashe har kundawo? Amsar jakar tayi tana fadin tun dazu ma. Murmushi Mama tayi tana fadin ashe kaima kana hanya? Farouk yace wallahi kuwa.

Gani nayi duk an tafi week end shine nace nima bara inzo nasan 'yan makaranta sun dawo semu gaisa. Mama tace sannu da zuwa, yace yauwa na sameku lafiya? Tace lafiya lau. Shiga ciki inzubo maka abinci.

Yana shiga Faisal yace la! Yaya yaushe kadawo? Farouk yace yanzu nashigo, ai nasan zaku dawo hutu shiyasa nace bara indawo mugaisa. Fatima tace Yaya sannu da zuwa, yace yauwa Fatima ya karatu? Tace Alhamdulillah.


Zaune Farouk yake a dakin Mama bayan yagama cin abinci tana ta tambayarshi yanda makarantar take,Farouk yace lafiya lau Mama, tace to wa yake maka girki kuma? Farouk yace ai na iya tun ina Faskari, Mama tace da kyau.

Dukar da kai kasa Farouk yayi yana wasa da hannunshi. Mama tace wai ni tun dazu nake ganinka kamar baka da lafiya, ko wani abun ne yake faruwa? Kwallace ta cika idon Farouk. Kara matsowa Mama tayi tana fadin kafada mani mana.

Fatima ce tayi sallama, amsawa Mama tayi tana fadin lafiya? Shigowa Fatima tayi tana fadin dama Malaminsu Farida ne yabani takarta yace inkawo ma Malan, shine na manta dazu a mota ban bashi ba.

Mama tace kinji gulma kai, ba anjima Malan din ze taraku gaba dayanku kowa yakawo takardunshi ba, bazaki iya ajewa anjima ki bashi ba? Fatima tace ai batawa bace ta Farida ce. Mama tace ita meyasa be bata ba? Se ke uwar rawar kai? Dukar da kai Fatima tayi kasa. Domin ta karanta abinda yake cikin takardar, kuma ta nuna ma Faisal.

Shine ma yace kada tabama Malan ta kaima Mama dan yasan Malan ze iya dukan Farida, sosai sukayi mamakin abinda Farida tayi, Faisal yake tambayar Fatima yace dama kinsan tanayin haka ne? Fatima tace nide naji ana maganar tana yawan cewa tana son maza.

Amma gaskiya bansan lokacin da tayi wannan abun ba, kuma ma kaji malamin yace be fadama kowa ba. Faisal yace Allah ya kyauta, ina fatan kede ba ruwanki? Fatima tace wallahi ni ba ruwana da kowa.

Cikin tsawa Mama tace to Uwar me kika tsaya kinayi, kitafi kibani waje, idan Malan din yadawo seki bashi. Farouk ne yadago kanshi yace kawo nan mugani, mika mashi tayi ta fita. Mama tace ai da baka amsa ba.

Bude takardar yayi Mama tana fadin karanta mani inji abinda yace, lokacin da Farouk ya fara karantawa seda hawaye suka zubo mashi, kasancewar da turanci malamin ya rubuta yasa Mama bata fahimci duk abinda ya karanta ba.

Sede ganin yana karantawa yana kuka yasa tagane akwai matsala. Mama tace bade korarta sukayi ba ko? Girgiza kai yayi yace wai meyasa komai yake zuwa mana a haka ne? Mama tace wai me yake faruwa? Farouk yace malamin su Farida ne yakawo karar ta.

Mama tace kamar ya? Nan Farouk ya fada mata abinda yace, sosai hankalin Mama yatashi, amsar takardar tayi ta yaga tana fadin baza'a fadama Malan din ba, nida kaina zan ja mata kunne.

Wannan bala'i dame yayi kama? Farouk yace shikenan kowa da tashi kaddarar, shi Fahad ga halin daya jefa kanshi, ita kuma ga abinda take aikatawa. Mama tace bangane ba? Cikin kuka Farouk ya fada mata halin da Fahad yake ciki.

Sosai hankalin Mama yakara tashi, kuka kawai takeyi, wannan wace irin jaraba ce tashigo mata gida? A fili tace Allah ya isa tsakanina dake Inne, burinki ya cika kin lalata mani yara. Farouk yace haba Mama, me kuma Inne tayi maki? Inne bata da laifi laifinsu ne.

Mama tace wallahi banyarda ba. Kuma inaso kaja bakinka kayi shiru, wallahi idan kabari naji wannan maganar a wajen wani sena bata maka rai, kasan de yanda Malan yakejin haushinsu Fahad, idan yasamu wannan labarin shikenan sun zama abun kyama awajenshi.

Ka barni nasan matakin dazan dauka, bazan bari Malan yaji wannan maganar ba bare ya maida mani yara saniyar ware. Nasan halinshi sarai, shi kullum wanda yakeyin abun kirki shine mutum awajenshi, dan haka bazan bari yasan komai ba.

Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[4/5, 4:22 PM] nabilalady5: 🏡🏡 A WANI GIDA🏡🏡
😭😭😭

Nah
Marubuciyar Zamani

NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)

www.NabilaLady5@gmail.com
Facebook...Nabeela Ladeey

Part 65 ⏩ 70

Zaune su Farida da Fahad suke adakin Mama, da ka kalli fuskar Mama kasan ranta abace yake. Dago ido tayi ta kalli Farida, gyaran murya tayi tace Farida tashi kije gidan Maman Sultan kice ta bani kayana da na bari jiya agidan ta.

Bayan Farida ta fita Mama ta kalli Fahad, dama bata son tayi mashi magana agaban Farida ne shiyasa ta aiketa. Fahad! Dago jajayen idonshi yayi ya kalleta, ganin fuskarta babu alamun wasa yasa yakara nutsuwa.

Meya sami idonka yayi ja haka bayan kuma baka da ciwon ido? Dukar da kai kasa yayi yace wani abu ne ya fada mani a ido. Mama tace bana son karya, kafada mani abinda kake sha? Fahad yace yoni me zansha.

Mama tace kwanaki kuna makaranta kun hadu da Farouk? Saurin dago kai yayi yana kallonta. Tambayarka nakeyi kun hadu? Fahad yace E, awane waje kuka hadu? Mama makarantar mu yaje fa.

Amma ba cikin makaranta ya ganka ba. Shiru Fahad yayi yana zare ido. Fahad irin rayuwar daka daukar ma kanka kenan ko? Yanzu ba kajin kunya su Faisal su san halin da kake ciki? Bakasan zasuyi mana dariya ba.

Me kake tunani idan Malan yaji wannan magana? Kuma kasan yana jin haushinka saboda yanzu baka maida hankali akan karatunka ko? Yanzu Fahad duka shekararka nawa da zaka fara shaye shaye? Kuma ba sigari kadai kake sha ba.

Bakasan kwakwalwarka zata iya samun matsala ba? Kuka Mama tasa tana fadin so kuke bakin cikin ku ya kashe ni? Kai ka fada shaye shaye, ita kuma Farida ta fara bin maza. Haba Fahad, kai ne wanda kafi kowa sona duk cikin yara na.

Meyasa yanzu kuma zaka zamo wanda zesani cikin damuwa? Dan Allah Fahad ka rufa mani asiri kadena wannan halin banzan, idan baka sani ba nasan kana mani dauke dauke. Fahad yace ni gaskiya Mama bana sata.

Mama tace bana son gardama, idan ma ba kayi to kasani shaye shaye babu abinda baya sawa, kuma se yanzu na gano dalilin da yasa kake da zafin zuciya yanzu, halinka ya canza Fahad, ka daure ka canza wannan halin.

Kuka Mama takeyi sosai. Fahad yace Mama kiyi hakuri daga yau na dena duk abinda nakeyi. Mama tace Allah yasa Fahad. Tashi kaje kuma bazan fada ma Malan ba, banaso ya kara jin haushinka. Dadi Fahad yaji jin tace bazata fada ma Malan ba, aranshi yana fadin da sauki ma.

Bayan Fahad ya tafi Farida ta dawo daga aiken da akayi mata. Haka Mama ta sata gaba tana tambayarta metayi amakaranta, Farida Kamar zatayi kuka tace Allah Mama babu abinda nayi. Mama tace amma ya akayi Malaminku ya aiko da takarda abama Malan? Farida tace wallahi ba wata takardar daya bani.

Mama tace ai Fatima yaba, kuma Farouk ya karanta mani duk naji abinda kikayi. Farida tace wai fa Mama daga yazo same mu nida kawata a class munje wajen wani dan ajinmu bayan antashi daga pref muka tsaya ya nuna mana aikin da aka bamu shine fa Malamin yazo yace wai iskanci mukeyi.

Mama tace kenan bake daya bace? Farida tace mu 3 ne fa. Kuka Farida tasa tana fadin kin gani ko za'a jamani sharri, dama Malamin ya tsaneni yafison Fatima saboda wai ni bana mashi magana.

Tsaki Mama tayi tana fadin ai dama nasan karya ne, na sanki bazaki iya aikata abinda akace ba, dama Fatima akace zan yarda domin ba tada abokan wasa se yan gidansu Amira.

Kuma ba tajin kunyar taba namiji. Farida tace damma bakiga yanda sukeyi da mazan ajinsu ba, wai se su zauna suce karatu sukeyi basa komawa daki da wuri. Mama tace ki rabu da ita, in Allah ya yarda seta debo ma Malan da Inne abin kunya.

Bade ita yakeso yanzu ba, kibarshi ai duniya zata koya mashi hankali. Abinda nakeso dake ki kara dagewa kada kibari wannan karon akara maidoki baya. Farida tace zan dage sosai, itama Fatimar ai kawarta ce take bata satar amsa. Mama tace kirabu da ita ai duk nasan komai, ba kokarin ta bane.


Zaune Faisal da Farouk suke a kofar gidansu saman benci suna fira, Farouk yana ta bama Faisal labarin makarantarsu. Faisal yace ai nima idan nagama makaranta duk makarantar dana samu tafiya zanyi.

Kaga yanzu ka huta, nasan akwai abokanka da yawa da suke zaune basu tafi makaranta ba saboda basu sami wadda suke so ba. Farouk yace da yawa ma. Shide Mannir yaci sa'a ya samu Federal University Dutsinma, muna haduwa dashi wani lokacin.

Faisal yace haka Abba yake fada mani, bakomai kowa da rabonshi, kuma kasan kowa yana tafiya da sa'arshi, se kaga wani yafika da wani abun kaima kuma seka fishi da wani abun. Farouk yace hakane. Amma gaskiya ko na gama makaranta zanyi kokarin neman aiki a katsina.

Faisal yace meyasa? Farouk yace kawai ni banajin dadin zaman gidan nan yanzu. Jinjina kai Faisal yayi yace amma kana ganin Malan ze barka? Kuma ma a Katsina wajen wa zaka zauna? Farouk yace kaide Allah ya kaimu in gama, amma gaskiya bazan zauna garin nan ba.

Kaga wannan dinkin hular da nakeyi ba karamun samu nake ba, kuma tun yanzu nafara tara kudi, kafin ingama insha Allah nasan zan tara kudade masu yawa. Faisal yace Allah yasa, amma ko ni bazan zauna garin nan ba.

Fahad ne yataho yana wani cika yana batsewa, domin tunda Mama tace Farouk ne yafada mata abinda yake aikatawa yake jin haushinshi, kuma ko da yafita daga gidan seda yaje yayo shaye shayenshi sannan, yanzu haka daga can yake.

Ko kallonsu beyi ba yashige cikin gida. Girgiza kai Farouk yayi bece komai ba. Faisal ne yace Yaya nikam akwai abinda na dade inaso in fada maka, sede bansan yanda zaka dauki maganar ba. Farouk yace maganar Fahad ce ko? Faisal yace E.

Murmushi Farouk yayi yace nima nasani, domin agaban idona nagashi yana shan wiwi, Faisal yace bayan sigari yanzu har wiwi yakesha? Farouk yace to wama yasan iyakar abinda yakesha, nide abinda nasani kenan.

Faisal yace amma Yaya ai be kamata ace anyi shiru ba. Farouk yace nayi mashi magana, kuma na fadama Mama kuma tace zatayi mashi fada. Faisal yace amma baka ganin yakamata Malan yasani? Farouk yace Mama tace kada afada mashi.

Kuma kasan halin Malan ze iya zaneshi kuma yace babu ruwanshi dashi. Faisal yace haka ne, Allah ya kyauta. Farouk yace amin. Faisal yace yaushe zaka koma Yaya? Farouk yace gobe. Tashi Faisal yayi yana fadin bara inje gidansu Amira kafin akira sallah. Farouk yace kai da Amira kode? Murmushi Faisal yayi yace kawai de mun saba da ita ne. Farouk yace to Allah yatemaka.


***** *****

Haka hutunsu yakare sam Fahad be dena abinda yakeyi ba, sema karuwa da abun yayi, dan da an bata mashi rai to seya sha, kwata kwata yadena zama gidan sosai, komai yace yatafi gidan Hajiya, itako inde yaje seta bashi kudi.

Gashi yanzu son kudinshi yayi yawa, ga roko duk inda abokan Malan suke seyaje ya gaishe su, sata kuwa sede idan ba'a aje ba. Malan tun yana mashi fadan kai dare awaje har yadena, domin duk lokacin da yayi mashi fada to aranar se sunyi fada da Mama.

Farida ma babu abinda ya canza sema abinda yayi gaba, haka suka shirya suka koma makaranta, danshi Faisal daga wannan dawowar sede yazo sallah amma se sun gama zasu dawo gaba daya.


Lokacin daya koma makaranta shida Nura haka Saleem ya sashi gaba yana ta tambayarshi Fatima, Faisal se yanga yake mashi yana fadin seka bani cin hanci zan fada maka.

Seda Saleem yayi kamar zeyi kuka sannan Faisal ya bashi wani zobe da Fatima ta bada akawo mashi Saleem yace dan rainin wayau, Faisal yace wallahi zan anshe. Faisal yace ina Lubna fa? Saleem yace nima bansani ba.

Faisal yace kada kasani, Nura yace Saleem Amira zaka tambayeshi, dariya Saleem yayi yace ka kyaleshi, mun rasa ma wane fanni yake, maganarshi dama bata wuce Fatima, Amira se Lubna.

Faisal yace ai dole in fadesu domin su 3 suna da matukar muhimmanci agareni. Fatima de kanwata ce wadda duk duniya babu wanda nakeso sama da ita, kai kanka saboda yanda kake nuna kulawarka akanta yasa na amince maka.

Amira kuwa jini na da nata ne a hade, bansan irin shakuwar da mukayi da ita ba. Lubna kuwa itace wadda ta debema Fatima kewa kuma ta nuna mata yanda rayuwa take. Wannan dalilin ne yasa nake son su gaba daya.

Nura yace kila de Mata biyu zak aura. Dariya sukasa Faisal yace kutashi mutafi masallaci an kusa kiran sallah. Saleem yace tunda anyi maganar aure ai dole kace atafi masallaci, bayan saura minti 15 akira sallar. Faisal yace E naji koma me zakuce.



Zulai ce ta kira Mama tana tambayarta ina ne gidansu gata tazo Mani, cike da Farin ciki Mama tace da gaske? Zulai tace wallahi da gaske nakeyi, biki mukazo katsina ni kuma na tambaya akace mani babu nisa shine na taho.

Mama tace yanzu kina ina? Zulai tace gani nan an sauke ni atasha, Mama tace samu me mashin ki bani shi. Bayan Zulai ta samu me mashin ta bashi wayar. Kwatancen gidan Mama tayi mashi yace yasan gidan, dan babu wanda besan Malan ba.

Da sallama Zulai ita da wadda suke tare suka shiga gidan Mama, fitowa Mama tayi tana fadin sannunku da zuwa, ashe ma ku biyu ne? Zulai tace wallahi kuwa nida kanwata ne. Mama tace kushigo.

Bayan takawo masu ruwa da abinci sunci nan suka fara gaisawa. Mama tace amma naji dadin zuwanki Zulai. Ban dauka zaki zoba. Zulai tace ai nafada maki sena rigaki zuwa, ke kam tunda kuka dawo nan ai nasan bazaki kara zuwa Faskari ba.

Dama kuma baki taba zuwa ba. Mama tace wallahi inda wani abu babba ya faru da ke da kin ganni, Zulai tace sede haihuwa ko biki, kuma babu wanda zanyi. Mama tace kai Zulai bazaki kira mu zuwa suna ba.

Zulai tace rufa mani asiri, dama ni ba wasu yara gareni da yawa ba. Mama tace ai kin huta, ya sunan kanwar taki? Zulai tace Suwaiba, itace autar mu. Mama tace Allah sarki ba tayi aure ba kenan? Zulai tace kinsan itace auta seda tayi karatu sannan.

Mama tace ai taji dadinta, yanzu se aiki ko? Zulai tace tana aikin ma, ai agidan Yayanmu take zaune anan Katsina, to anan tasamu aikin koyarwa. Mama tace Allah yakawo miji nagari to. Zulai tace amin.

Wai ya naji gidan shiru ina yaran suke? Mama tace ai duk suna makaranta. Zulai tace haka fa, amma ai Farouk ya gama ko? Mama tace yagama har yatafi wata makarantar. Zulai tace lallai Maman Farida kin kusa hutawa, ace babban danki har yashiga jami'a.

Wane gare yake? Mama tace na'am, E, a jami'ar Ummaru Musa yake. Zulai tace lallai ya more, kinga nan da wani lokaci kema zaki fara cin albarkacin 'ya'ya. Murmushin yake Mama tayi tace ai kuwa.

Sam ba taso Zulai tasan Farouk ba Jami'a yake ba, dan bataso a rai nata. Zulai tace ina kuma su Fatima? Mama tace munafuka tana makaranta, Zulai tace amma yanzu takara girma ko? Mama tace sosai ma, baki gantaba, yarinya tun bata gama secondary ba amma ta koma kamar wata uwar mata.

Sam bata da kirar mata, ni tsoro ma nakeji kada afara tanka mana gida, kuma gashi Malan yace se sunyi karatu zasuyi aure. Zulai tace kada taje tajawo maku abun kunya fa.

Mama tace wallahi kamar kin sani, yanda take ganin ta girma tazama budurwa se shige ma maza takeyi, shiyasa yanzu na hana Farida taje kusa da ita dan yanzu zata iya canza mata hali.

Zulai tace kede ki kula da diyarki, idan ta kwaso abun kunya ki korama uwarta ita. Mama tace dama waze zauna a juye mashi abun kunya agida. Mama tace amma de Zulai nan zaku kwana ko? Zulai tace dama cewa nayi kwana zamuyi musha fira.

Mama tace amma naji dadi, sallamar Malan ce ta katse masu firar da sukeyi. Tashi Mama tayi tana fadin sannu da zuwa Malan, murmushi yayi yace yauwa baki mukayi ne? Mama tace wallahi Zulai ce da kanwarta suka kawo mana ziyara.

Tazo biki Katsina shine tazo, nan ma zasu kwana dan sun gama bikin. Malan yace lallai ta kyauta, muje mugaisa ko. Malan yana shiga suka hada ido da Suwaiba, seda gabanshi ya fadi, lokaci guda yaji ta burgeshi.

Zulai ce tace Malan sannu da zuwa, zama yayi yana fadin yauwa Zulai sannunku da zuwa, tace yauwa ina wuni? Yace lafiya lau, ya megidan naki? Tace lafiya lau yana gaisheka.

Ai suna cewa sunyi kewarka. Suwaiba ce ta dago kai tace ina wuni? Murmushi Malan yasaki yana fadin lafiya lau, kunzo lafiya? Tace lafiya lau. Mama tace autar su Zulai ce, itama malamar makaranta ce.

Malan yace da kyau, Allah yatemaka, a Faskarin take itama? Zulai tace a'a a Katsina take, Malan yace Allah sarki, acan take aure ko? Mama tace ai batayi aure ba karatu tagama.

Murmushi Malan yayi yace yayi kyau, tun da angama karatu har ana aiki ai se ayi aure ko, Zulai tace kaima de ka fada, har yanzu Suwaiba taki tsayawa ta fitar da miji. Washe baki Malan yayi yace to ai aure ba'ayi mashi gaggawa, gara ta tsaya tafitar da wanda ranta ya kwanta dashi.


Mama tace wannan haka yake, domin abunda yake kawo yawan mutuwar aure hada rashin tsayawa a gama fuskantar juna. Tashi Malan yayi yace bara inje indawo, yau muna da manyan baki ai dole mu karramasu.

Ai mijinki Zulai mutumin kirki ne. Mama tace ai dagashi har ita haka suke, shiyasa duk a unguwar munfi shiri da ita. Zulai tace mungode. Mama tace baza kaci abinci ba sannan? Malan yace bara indawo. Tashi Suwaiba tayi tana fadin zanyi sallah.

Mama tace to kishiga ciki dauki kayan akwai bandaki aciki. Tana tafiya suka cigaba da firarsu, sam babu wanda yatashi domin yin sallah.

*** ****

Washe gari tunda safe Malan yace ma Mama zeje katsina, Mama tace lafiya de? Malan yace inaso inje induba wani abokina da aka kwantar a asibiti. Mama tace to ko su Zulai su shirya kawuce dasu, kaga nima se inje mu duboshi kada kutafi ku kadai nasan bazakaji dadi ba tun da baku saba ba.

Malan ya daure fuska ganin zata rushe mashi plan, danshi saboda Suwaiba ya shirya wannan tafiyar. Mama tace dan Allah Malan katafi dasu kaga zasu rage kudin mota. Malan yace sede inbasu kudin mota.

Mama tace toshikenan hakan ma yayi. Saurin kallonta yayi danshi latsa ta kawai yayi dan kada taga yayi saurin amincewa. Harta juya yace naga kamar kin bata rai? Mama tace wallahi ni ban bata rai ba. Malan yace wallahi kin bata rai, Mama tace a'a.

Ai nasan halinka ba kason tafiya da matan da baka saba dasu ba, shiyasa nace inshirya mutafi tare. Malan yace

Please Login or Register in order to submit comment