You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
kinga wannan jakar, Inne ce jiya tazo takawo mani tace inkawo maki, shima Yaya Saleem ta bashi ya kaima Yaya Faisal. Dariya Fatima tasa tana fadin dagaske? Lubna tace wallahi kuwa, kuma tace kada kibari Farida tasan ankawo maki.
Fatima tace kai nagode ma Inne na, jinake kamar in watsar da wadan nan kayan ma. Dariya Lubna tayi tace ai seki watsar. Zama Fatima tayi tace ashe Yaya Saleem da Yaya Faisal abokai ne? Lubna tace emana nima shine yake fada mani.
Kullum seya dameni wai inbashi labarin shagwabarki. Dariya Fatima tasa tace lallai ma nice me shagwabar, Lubna tace sosai ma, kawai bakisan kinayi bane. Ga jakar sweet ma yace inkawo maki.
Fatima tace haka fa yabama Yaya Faisal yakawo mani da akayi hutu, nima idan zaki tafi zan siya mashi wani abu. Lubna tace to tashi mu hada kayan.
***** *****
Haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya, sosai Fatima da Lubna suke maida hankali a makaranta, lokaci guda Fatima ta maida jikinta, kuma yanzu babu ruwanta da Farida.
Koda akayi visiting Fatima bata damu da abinda Mama takawo mata ba, bayan kwana biyu kuma Inne da Alhaji suka zo gidan Principal, haka ta aika aka kira Fatima Da Luban, sosai Fatima tayi murnar ganin Inne.
Haka suka sha fira kuma takawo mata kaya masu yawa hadasu Inner wears, haka tabata kudi, Fatima takara bata wasu tace tasa mata a asusu, haka suka dauki kayan sukayi masu sallama suka tafi daki.
Tun daga wannan rana Inne take zoma Fatima Visiting a boye, kuma Farida bata gane ba, hankalin Inne yanzu ya kwanta dan tana ganin yaranta, kuma tanajin dadi ganin Fatima se girma takeyi tana kiba.
Fatima tafi jin dadin rayuwar makaranta, har bataso ace an kusa hutu, domin tanajin dadi sosai. Farida kuwa bata karatu, sede wasa da maza, gata da son aikama wani tana sonshi, yan ajinsu duk sun ganeta, idan suna zaune da kawayenta komai tayi masu labarin aure. Zinatu ce kawai take biye mata sunayi.
**** ****
A yaune Inne ta haihu, inda tasamu diya mace me kyan gaske, sosai Alhaji yayi farin cikin samun diya mace, dan yanason yara mata, su Ansar ma se murna sukeyi, ba kamar Khairat, dan tasamu abokiyar wasa. Haka Inne ta buga ta fadama su Salamatu.
Ranar suna yarinya taci sunan Amatullah, dan Alhaji yace yanason sunan, sosai Inne tayi mutane, su Momyn Lubna sune akan gaba, dan zumuncinsu yakaru sosai. Su Momyn Teemah da Salamatu ma duk sunzo.
Taro yayi kyau, Inne takara zama babbar Hajiya, tayi kyau takara gogewa tazama 'yar birn, idan ka ganta ba zakace Innen daka sani bace ada, dan yanzu ta waye sosai.
Kamar yanda Alhaji yace idan ta haihu ze biya masu makka kuma ze koya mata mota, haka yasa aka fara koya mata mota lokacin da tayi arba'in, kuma yace zasuje Makka tunda saura wata bakwai atafi, kafin lokacin Amatu takara girma, seta ajeta idan ta dawo tacigaba da shayar da ita.
***** *****
Abubuwa da dama sun faru, yara sun kara girma, Fatima tazama yan mata, tagama horuwa da aiki yanzu sam bata bari Mama tayi mata fada, sede idan Mamar taso yin fadan ne, Farida ta zama kwarkwar, gashi abun bakin cikin anyi mata repeating yanzu Fatima tana gabanta.
Duk tayi sanyi bata da sauran rawar kai a cikin kawaye, hatta da Zinatu yanzu ta wuceta. Lokacin dasu Faisal sukayi JSCE da za'azo ma Lubna visiting seda Saleem yazo, hakama Faisal seda Malan yace su shirya shida Fahad atafi dasu.
Sosai sukayi murnar ganin junansu Saleem da Faisal, Fahad kuwa sakin baki yayi yana kallonsu dan ko magana basayi da hausa, lokacin dasu Fatima sukazo sosai tayi murnar ganin Faisal.
Saleem kuwa ido ya kura mata, itama shi take kallo, Lubna tace Yaya Saleem wato baka ganni ba ko? Dariya yayi yana fadin am sorry Lil sis, ya makaranta? Faisal yace bata amsawa, kyaleshi Lubna zo kifada mani labarin makarantar ku.
Duk maganar da sukeyi da turanci sukeyi, Mama da Farida da Fahad sun zama yan kallo, sosai haushi ya gama kama Mama, dan tunda Fatima ta gaisheta suka ware dasu Faisal.
Farida kuwa kuka tayi ta mama tana fadin acanza mata makaranta, Mama hakuri tabata tana fadin kinsan de halin Malan, baze taba canza maki ba, gara ki kara dagewa, yanzu kina ganin se Fatima ta rigaki gamawa. Narasa meke damunki keda Fahad, so kuke ayi mani dariya.
Haka ta yita bata hakuri, lokacin da zasu tafi seda Fatima tayi kuka, shima Saleem seda idonshi yayi ja, wani zobe dake hannunshi yabama Fatima, su Faisal da Lubna se tsokanarsu sukeyi. Momynsu kuwa se dariya take masu, haka suka rabu cike da kewa.
Bayan koma warsu SS1 ne Fahad yafara biyema abokan banza, kuma anan ne suka fara koya mashi shan taba, tun yana sha yana kwarewa har yasaba, daga taba se kuma abun yaci gaba, kullum da dare se sunje bayan makaranta sunyi shaye shayensu kafin su dawo.
Lokaci guda ya kware, kuma ya kara zama dan iska, lokacin da akayi hutu Mama tace wai Fahad me yake damunka, duk kayi baki karame? Kallonta yayi yace mefa, kawai wahalar makaranta ce, haka ta dage tana bashi abun dadi dan yasamu yaciko.
Gashi yanzubsam yama dena kokari, kuma Malan yadena masu fada akan rashin kokari tunda Mama tace asiri akayi masu, hakan yasa ya zuba masu ido, duk zasu koma seya kawo ruwan addu'a yace surika sha, sede baya ba su Faisal, saboda suna kokari, besan kuma hakan da yake ba kara hura wutar kiyayya yake azuciyarsu, dan sun dauka bayaso suyi kokari ne shiyasa yake bama sauran.
Kullum idan Fahad yafita baya dawowa da wuri, kuma da dare ma seyayi shaye shayenshi sannan yake shigowa gida, gashi hada dauke dauke yakeyi, duk abinda yakeyi babu abinda Faisal be sani ba.
Shiyasa yanzu yake lallabashi, dan abu kadan yake harzuka Fahad, har da Farouk dambe sukeyi, Mama tarasa inda Fahad yasamu wannan zuciyar. Faisal yaso ya fadama Farouk dan yanzu suna mutunci sosai, se kuma yaji tsoron kada Mama tace sharri yake mashi.
Dan shi yanzu Farouk babu abinda yasa agaba kamar dinkin hularshi, sosai yazama gwani a dinkin hula, kuma da yayi saidawa yakeyi, sosai yake samun riba, kuma ba laifi yanzu yana maida hankali dan tun wani lokaci da Faisal yabashi shawara akan yarika maida hankali idan yasamu yagama karatun se yayi dinkishi sosai.
Tun daga lokacin Farouk yake maida hankali, kuma yana zuwa masallaci dan inde suka zauna suna fira da Faisal to seya yimashi wa'azi cikin dabara, dayake Farouk beda girman kai haka yake daukar duk abinda Faisal yake fada mashi. Amma tsakaninshi da Fahad fada ne kawai, dan yanzu Fahad sosai yakejin haushinsu.
Shakuwar Amira da Faisal ta wuce wasa, domin yanzu Amira takara girma, yanzu tana JSS3 itama, kuma takara dagewa wajen karatu, sede har yanzu akwai yarinta atare da ita saboda yanayin datake ciki.
Amma ita da Faisal abun ba'a magana, sosai yake sonta, duk abinda yasamu ita da Fatima yake bamawa, kuma ga Lubna itama sun shaku da ita, Baban Saddik har cemata yake Matar Faisal, itako tayita dariya.
Inne kuwa yanzu ta zama Hajiya Inne, motar datake tukawa kanta abun kallo ce, duk da mijinta ya aje aiki amma yana da hanyar samu sosai, ita kanta shagon saida kaya ya bude mata yazuba mata kaya kuma ya mallaka matashi, haka tasamo wani dan Uwanta a Mashi yake tsare mata, sosai tayi arziki,
Kuma ba ta manta da kawayenta su Salamatu ba, ita da Momyn Lubna sun zama tamkar yan gida daya, Ansar da khairat ma anzama manya duk sunje secondary, Amatu kuma tana nursery, sede daga ita Inne bata kara haihuwa ba.
Wata rana da Momyn Teemah ta haihu lokacin ana hutu, haka Inne ta sako yaranta amota sukazo suna, ba karamin kyau sukayi ba, lokacin da tashigo cikin unguwar kowa seda yabita da kallo.
Maman Sultan da Mama sun taho zasuje wajen sunan su kaga tsayuwar mota.Tsayawa sukayi suna kallon wanda ze fito. Inne tana fitowa Salamatu ma tafito daga gidanta.
Cike da farin ciki tace ga Hajiya Inne oyo oyo, saurin kallon Inne su Mama sukayi, tabbas itace, ido Mama ta tsura ma Inne, tanajin zuciyarta kamar zata fashe, Fatima da Amira suna zaune suka hango Inne, ai da gudu suka rugo suna murna.
Fatima tana zuwa Inne ta rungumeta, Amatu tana rike da hannun Khairat se dariya takema Fatima, dan sun saba, da ita. Daukar Amatu Fatima tayi tana mata wasa, Khairat ma ta rungume Fatima.
Su Faisal ne da Abba suka karaso yana ta dariya, Ansar ne ya rungumeshi yana fadin Yaya ina wuni? Faisal yace lafiya lau Ansar ina Abba? Yace yana gida.
Takawa Inne tayi har wajen su Mama tana murmushi, Salamatu tana binta abaya, kallonsu tayi tana fadin Maman Farida ina yininku? Maman Sultan ce ta amsa da kyar, Mama kuwa mamaki da haushi sun hanata, magana.
Murmushi Inne tayi ta juya tana fadin Salamatu muje wajen sunan ko, haka ta juya tana takawa cike da takama. Mama kuwa kasa shiga gidan sunan tayi, haka ta juya takoma gida kamar zatayi kuka saboda bakin ciki.
Kalli yanda Inne ta koma, itako gata nan yanzu kaya masu tsada ma bata dasu, tashin hankalin Farida da Fahad ya hanata yin kiba. Haka ta koma gida tana me cike da bakin ciki.
**** ****
BAYAN WANI LOKACI
Farouk yagama makaranta inda su Fahad suka zana jarabawar shiga aji shidda, dansu makarantarsu se wanda yaci jarabawa yake shiga aji shidda. Kuma akaci sa'a Fahad baci ba, hakan yasa aka mashi repeating.
Ya dawo mate din Fatima, dan itama Farida tun suna aji 2 akayi mata repeating, yanzu Fatima tana gabanta, duk da lokacin Mama taji haushi haka nan ta hakura tunda de tasamu ta rufe bakin malan da cewar Inne ce tayima yaranta asiri, kuma shima ya yarda da hakan.
Lokacin da suka gano jarabawar Fahad kuka yayi tayi yana fadin baze koma makarantar ba.Malan yace aiko be isa ba seya koma, dama ai nafada maka. Kallonshi Malan ya karayi yana fadin wai ni tsaya ma, baka da lafiya ne? Fahad ya dago jajayan idonshi yace lafiya kalau.
Malan yace amma kalli bakinka, duk yayi baki, kaima kanka kayi baki kuma ka rame.. Fahad yace kawai nadanyi zazzabi,ne. Malan yace ni kake fadama kawai? Mama tace haba Malan kayi hakuri mana, kaima daga gani ai kasan bayada lafiya, kallifa yanda yarame.
Malan yace to ai seku shirya mukaishi asibiti. Mama tace, tashi kaje Fahad, haka yatashi yana wata 'yar iskar tafiya yafita. Malan yace nifa ina zargin yaron nan. Tashi Mama tayi tana fadin a'a Malan kada kafara fadar irin wannan maganar akan yarana.
Me kake nufi da kana zarginshi? Nifa banaso kana ma Fahad haka, na lura da dadewa kafara tsanarshi acikin yaranka, to wallahi zamu fara batawa matukar kana mani haka, fita tayi tare da bugo kofar.
Murmushi Malan yayi yace Hauwa kenan, kowa yaga Fahad yasan halin dayake ciki, amma tunda bakiso infadi gaskiya nabarki dasu, na dade da sanin kina goyon bayan yaranki, amma tunda haka kikeso zan sa maki ido. Allah ya shirya.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[4/4, 2:30 PM] nabilalady5: 🏡🏡 A WANI GIDA🏡🏡
😭😭😭
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
www.NabilaLady5@gmail.com
Facebook...Nabeela Ladeey
Part 60 ⏩ 65
Kwance Mama take a dakinta tun bayan fitowar ta daga wajen Malan, zuciyarta se zafi take mata. Wannan wane irin bala'i ne haka? Yanzu Malan yadena kula da yarana kamar yanda yakeyi ada.
Tunda Inne tabar gidan nan soyayyar da Malan yake ma yarana ta fita daga zuciyarshi. Kenan saboda zaman Inne agidan yake son yarana? Meyasa ma nasa yasaki Inne? Gashi yanzu ita ta cigaba ni kuma ina nan kullum se kara tsotsewa nakeyi.
Gaba daya tafiyar Inne daga gidan nan haske ne akan yaranta, ni kuma duhu ne ya mamaye ni da yarana. Shi kanshi Malan yanzu arzikinshi ba kamar da ba. Amma kalli irin motar da Inne take hawa.
Kalli kayan jikinta, gashi ta rike 'ya'yan mijinta tamkar itace ta haifesu. Yaranta sun zamo abin so ga kowa, kansu ya bude yayin da kan nawa yaran ya toshe gaba daya. Duk kokari irin na Farida da Fahad be hana anyi masu repeating ba.
Nida naso ace yaran Inne ne ja baya akaratu, lokacin da zasu fara karatun jami'a yarana sunyi nisa alokacin kuma gashi Malan ya aje aiki. Se gashi kuma anyima yarana repeating, gashi Faisal gwamnati ce take daukar nauyin karatunshi.
Ita kuma Fatima zata riga Farida gamawa, nasan duk sauran kudin Malan akansu ze kashe, tunda zasu rigasu shiga jami'a. Allah na rokeka kasa Farouk shi yaci jami'a, koshi kadai nasamu yayi karatu nasan seya riga Faisal gamawa.
Idan yasamu aiki nasan ze kula da sauran. Hawaye ne suka zubo mata, tabbas maganar Malan gaskiya ce, yanayin Fahad ya dade da canzawa, narasa meke damunshi, gashi yanzu duk abinda na aje se inga andauke, wanda ada ba haka ake mani ba.
Kadde ace Fahad yafara sata? Saurin girgiza kai tayi tana fadin, ina, acikin yarana babu barawo, domin duk dangin mu babu barawo. To kode yafara shaye shaye ne? Kara girgiza kai tayi tana fadin hakan ma baze yuwu ba.
Domin Fahad tun yana karami baya son warin koda sigari ce. To meya samu Fahad? Tabbas nasan akwai sa hannu acikin rayuwarshi, kuma koma wanene senayi maganinshi, kuma daga yau duk abinda za'a kawo na kayan dadi nashi seyafi yawa.
Bazan zauna ina kollo yarona ya lalace ba, duk yayi baki yarame, tabbas kafin ya koma sena ginashi. Hannu tasa ta goge idonta ta tashi tana kwalama Farida kira.
Shigowa tayi tana fadin kai Mama, wannan kira kamar kin makance. Mama tace wato nice ma na makance ko? Dariya Farida tayi tana fadin ai naji kina ta kwala mani kira ne. Mama tace nasan Fatima tana can gidan su Amira.
Jeki dora farar shinkafa idan ta dawo setayi miya. Farida ta turo baki tana fadin lallai ma, ai kin sande itace take aiki taya zakice inje in dora abinci? Mama tace Farida kinga yanzu kin girma, inaso kifara koyon aiki domin wata rana aure zakiyi.
Farida tayi murmushi tana fadin ai kamar kin sani, muna gama makaranta aure zanyi nida kawata. Zaro ido Mama tayi tana kallonta, Farida tace kinsan yanzu samarina nawa? Su 2 ne, damma suna tsoron Malan shiyasa basu taba zuwa gidan nan ba.
Mama tace rufa mani baki, ke yanzu har kinsan maganar aure? To bari kiji in fada maki, yanda kowa zeyi karatu a gidan nan kema sekinyi karatu. Haba Farida, so kike bakin cikinku ya kashe ni? Kina ganin yanzu shima Fahad yadawo baya.
Kema kin koma baya, Farouk ne kawai acikin yarana yagama Secondary, so kuke wadan can yaran su zama wasu manya agidan nan, ga uwarsu ta zama babbar Hajiya, suma suzo suyi kudi, shikenan ni kuma na zama baya kenan.
To kima cire tunanin aure aranki, matukar ina raye se kinyi karatu kamar kowa. Kuma daga yau zan raba maku aiki keda Fatima, idan ma bazaki iya shara da wankin bandaki ba, wannan ba matsala bane.
Nide fatana ki iya girki, sauran ko baki iya ba badamuwa domin akwai masu aiki, amma shi girki kyan mace ta iyashi, idan na dare kikeso to, idan kuma na rana zakiyi duk daya seki zaba.
Farida tace Allah Mama bazanyi ko daya ba, tunda de Fatima takeyi kawai ki barta ta cigaba, Mama tace haba Farida, meyasa bakison farin cikina? Kuka Farida tasa tana fadin ai dama yanzu naga kindena son mu.
Gashi Malan kullum seyayi mana fada, se wadan can kawai yakeso. Kuka sosai Farida tasa tana dire dire. Jawota Mama tayi tana fadin yi hakuri, ni na isa ince bana sonku? Kawai inaso in koya maki girki ne, tunda bakiso shikenan.
Je ki kira mani Fatimar tazo ta dora, share hawayenki, bakida mesonki sama dani. Murmushi Farida tayi tace anjima zanje gidan 'yar makarantarmu daga can zanje ingaishe da Hajiya. Mama tace to jeki kira mani Fatima an jiman seki tafi.
Abinda Mama bata sani ba shine, inde Farida ta tafi wajen 'yar makarantarsu da gidan Hajiya to haduwa takeyi da wani saurayinta Salisu, yana da shagon provison, kuma hade yake da dakin da yake kwana.
Tun wata rana da Farida taje siyen sukari ashagon suka hadu, tun daga nan suke soyayya, kuma Farida tana bala'in son shi, saboda yace ze aureta, ita kuma babu abinda takeso kamar maganar aure.
Sanin halin Malan yasa be taba zuwa gidansu ba, sede tayi dabara taje shagonshi, wani lokacin ma dakinshi suke shigewa suyi fira, sosai Farida ta sake dashi, duk lokacin da taje haka yake gama tabeta ya kawo kudi da kayan zaki ya bata.
Haka take boye kudin tace ma Mama sauran kayan agidan kawarta aka bata. Ta saba da abubuwan da yake mata sosai, hakan yasa duk bayan kwana 2 setaje wajenshi, daga can seta wuce wajen Hajiya dan kada tace bata zuwa.
Kuma sosai Hajiya take jin dadin zuwan da Farida takeyi, har cewa take ita da Fahad sune yan gidanta, domin shima da gidanta yake fakewa yatafi yawon shaye shayenshi.
***** *****
Bayan sun koma makaranta first term, Faisal na SS 3, Fatima da Fahad kuma SS 2, yayinda Farida take SS 1, ba laifi Fahad ya ciko, yayi kiba kuma lokacin da zasu tafi seda Malan ya kara mashi fada sosai akan rashin maida hankalin da bayayi, kuma yace idan har aka kara mashi repeating to ze maidoshi Day.
Haka suka tafi Fahad kamar ze fashe, Mama duk bataji dadin abinda Malan yayi mashi ba, haka ta dauki fushi da Malan dan yanzu haushin shi takeji sosai, duk wata kissar da takeyi ada yanzu babu, abu kadan se fada.
Shi Malan ma dariya take bashi, shiyasa baya biye mata, idan kuma ta kureshi haka zeyi mata tass, dan shima Malan akwai fada, sanin halinshi ne yasa take jin tsoron yi mashi wani abun, koya bata mata rai ma sede ta dauki fushi dashi, idan ta gaji kuma ta sauko.
Yanzu gaba daya Malan ya canza, baya ma yaranshi fada, babu abinda yake fata kamar ya dedeta tsakaninshi dasu Faisal, dan ya dade da gano tsantsar tsanarshi a idanuwansu, sede har yanzu be yarda cewa ba Inne bace ta rabashi da su ba.
Haka sam yadena ma yaran Mama fada, ya kyalesu kamar yanda bataso yana masu. Kuma har yanzu yaki barin su Faisal suje wajen Inne, suma kuma sun dena mashi maganar, domin basu da damuwa tunda suna ganinta, shi kuma Malan ya dauka sun fiddata daga ransu.
Jarabawar su Farouk ta fito, ba laifi yaci, sede be samu English ba, gashi mark dinshi na JAMB be kai ya tafi jami'a ba, kuma duka subject 5 yaci, Math, Biology, Geography, Hausa se islamic.
Sosai Mama taji haushin rashin samun mark din daze tafi jami'a, samun Malan tayi tace abarshi zuwa shekara me zuwa se ya kara sake JAMB din kuma ya nemi English idan yaso seya tafi jami'ar.
Murmushi Malan yayi yace kina da tabbacin shekara mezuwa zeci duka abinda kikace? Mama tace amma de kasan ai Farouk ba jaki bane, duk da banso ya gama karatu tare da kannanshi ba, amma dole inyi hakuri ya sake jarabawa tare da Faisal.
Malan yace to kimayi addu'ar yasamu direct a makarantar dazan samar mashi, domin tunda naga beci JAMB sosai ba na siya mashi form din Isa Kaita Collage Dutsinma yaje yayi N.C.E, kinga yanzu beci English ba.
Kinga kuwa basa bama mutum direct N.C.E se yana da Maths and English, zanje inji idan zasu daukeshi, idan kuma bazasu daukeshi ba sede yayi PRE N.C.E.
Mama kamar zatayi kuka tace kasan Allah, Farouk bazeje wanan makaranta ba, makaranta kamar gidan biki, duk wanda yataso se kaji yace can zeje, gaskiya gara ya hakura yayi zaman shekara guda, zuwa wata shekarar se yasake jarabawa yatafi jami'a.
Tashi Malan yayi yana fadin, idan ke kike da iko dashi zaki iya hanashi tafiya, kuma wallahi iname tabbatar maki matukar Farouk betafi wannan makarantar ba, wallahi bazan kara nema mashi wata ba.
Fita yayi yana masifa. Kwallace ta cika idon Mama, Farouk kuwa da yake tsugunne yayi shiru yana sauraronsu. Mama tace Farouk kana jina ko? Duk yanda Malan zeyi kada ka amince da wannan makarantar.
Idan ka nuna kanajin tsoronshi shikenan an maidaka baya, kai ne babba agidan nan kai yakamata ace anfi daukakawa amma yanzu ace wai waccan banzar makarantar zaka tafi. Ai ko Fahad da kafi kokari bazanso yaje can ba.
Dago kai Farouk yayi yace gaskiya Mama nide zan tafi kawai, koma menene nine na jama kaina, Allah yabani kokari amma na tsaya biyema abokai muna shiririta. Da ace na dage nasan zanci duka jarabawata.
Babu amfanin inzauna jiran wata shekara, domin banida tabbacin zanci jarabawar dazan sake,nide kiyi hakuri kawai zantafi. Hannu tasa ta daukeshi da mari tana huci, hannu Farouk yasa ya dafe kuncinshi.
Mama tace tunda haka kace se kaje katafi, kuma naira 1 tawa bazata kara ciwo akanka ba, tunda yanzu kaima ka koma bayan Malan da wadan can banzayen yaran sekaje kayi tayi,wata rana kai ne zakayi kuka da idon ka.
A lokacin da Fahad da Farida zasu tafi jami'a kai kuma sede ka kare da alli kaga kayo gadon ubanka. Tashi kabani waje. Mikewa Farouk yayi yafita yana kuka. Duk abinda sukeyi Malan yana jiyosu.
Har Farouk yakai kofar gida Malan ya kirashi, sosai yaji tausayinshi, hannunshi yakama suka bar gidan. A cikin mota Malan yace Farouk duk naji yanda kukayi da Mamarku.
Kada kalamanta su tsorata ka, kuma tunda yanzu ka gane kuskurenka inaso kasani lokacin gyara baya kurema mutum har se mutuwa ta riskeshi, kuma kai namiji ne, kayi hakuri da duk abinda ze zo maka arayuwa.
Kada ka dauki wannan karatun da zakayi da wasa, kuma kada ka rai nashi, idan ka dage kayi karatun kana cikinyi ma zaka iya sake jarabawa ka nemi English din, kaga duk lokacin daka gama karatunka ko kana aiki ne zaka iya tafiya ka karo karatunka.
Shi karatu da kake ganinshi ba'a rai nashi komin kan kantarshi, kuma inaso kadage idan kashiga makarantar domin ka gyara kuskurenka, inaso kadawo da kokarinka na da. Farouk yace insha Allah. Malan yace Allah yayi maka albarka. Yace amin.
**** *****
Cikin sa'a Farouk yatafi makaranta inda suka bashi Pre N.C.E ze karanci Biology/Geography, haka Malan ya shiryashi babu abinda be sai mashi ba, Mama kuwa ko sisi bata bashi, da kyar ma tace Allah ya bada sa'a, haka yatafi yafara karatunshi.
Sosai yake maida hankali wajen karatu, kuma yana dinkin hularshi, idan yagama ya kaima Malamai, cikin lokaci guda Malamai suka sanshi dan Farouk ya iya dinka hula, sosai yake ciniki a cikin makaranta har ma da wajen makaranta.
Kuma acikin aji sosai yake dagewa, duk abinda akayi masu baya bacci seya karantashi, gashi yanzu yana son addini sosai, sam baya wasa da sallah.
Wata rana sunje cikin gari shida wani abokinshi Hamza da yamma, yaje siyo kayan dikin hularshi, haka suka taho akasa se sauri sukeyi dan ankusa magriba, da yake ranar asabar ne babu class.
Ta wajen makarantar su Fahad suka biyo dan babu nisa daga makarantarsu zuwa tasu. A gefen katangar makarantar sukaga wasu 'yan makaranta kusan su biyar a jikin katangar makarantar, hayaki ne kawai yake tashi daga inda suke.
Hamza ne yace dan Allah Farouk kalli wadan can kamar ba 'yan makaranta ba, ace wai yaro tun yana secondary ya bude hun hunshi da hayaki, zuwa gaba kuma me kake tunanin zasu zama.
Juyawa Farouk yayi danshi bema kallesu ba. Karaf idonshi ya sauka akan Fahad ya daga wata farar takarda daya kunna yana zuka yana fesar da hayakin sama se daruya suke mashi.
Murtsike ido Farouk yayi domin ya tabbatar da abinda idonshi ya gane mashi. Tabbas ko a amafarki yaga Fahad ze iya ganeshi, wasu hawaye ne yaji sun zubo mashi, Hamza yace Farouk lafiya de? Hannun Hamza Farouk ya kama suka nufi inda su Fahad suke.
Daga sama Fahad yaji muryar Farouk, dede lokacin ya zuki wiwi dinshi, ido yazaro lokacin da sukayi ido biyu da Farouk, zumbur ya mike tsaye, kwarewa yayi hakan yasa hayakin yarika fitowa daga bakinshi.
Saurin wurgar da sauran wiwin yayi yana kara kallon Farouk, sauran abokanshi ma duk suka mike. Kwalla ce kawai take fita daga idon Farouk, Hamza ne yace wai Farouk ka sanshi ne? Share idonshi yayi yace Fahad din gidammu ne.
Cike da mamaki Hamza yakara kallon Fahad din. Fahad cikin sanyin jiki yace Yaya? Girgiza kai kawai Farouk yayi ya juya baya yana
Support ArewaNovels
Your support helps us maintain the platform and build a sustainable reward system for writers.Enjoying this story? Help us keep ArewaNovels growing.
Your subscription keeps the platform running and helps us support the writers who create the stories you love.
Choose how you want to support
You can continue reading free, or subscribe to help us grow and unlock premium access.
Weekly Support7 days of premium access
₦500Monthly Support · Most Popular30 days of premium access
₦1,500