gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Furar Danko Part2 Complete Hausa Novel by Billyn Abdul Chapter 6 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

“Karki tada hankalinki zamu samu mafita. Aunty tsakanina da ALLAH nake jin ƙaunarki a cikin raina, saboda kin min abinda bazan taɓa yarda a cutar dake ba. Nima halin da kike a cikin gidan nan na tada min hankali. Na kasa tunkararki da batunne saboda ina jin tsoron karki kasa fahimta ta. Sannan ke kanki kin kasa gane tamkar anyi kidnapping ɗinki ne anzo an ajiye anan. Dan gaskiya akwai manufa a al'amarin kawun nan naki a yanda nake lure da shi, na fahimci hakanne tun sanda aka zubar miki da ciki da ɗauke passport ɗin mu da yayi”.
     Lulu dake jin hawaye da wata matsananciyar tsanar Alh. Sulaiman ta cika mata zuciya ta ce, “Nima na fara jin haka a raina Ummita, sai dai gani nake mizaisa Dada a matsayinta na grandma ɗina ta aikata hakan, shiyyasa kawai nake hora zuciyata da ƙin yarda. Amma a yau zuciyata ta kasa karɓar al'amarin, cikin da suka zubar ashe bai fita ba”.
      Da sauri Ummita ta ɗago tana kallonta. Lulu ta gyaɗa mata kai alamar tabbatarwa, “Yana nan Ummita, kuma wlhy naji ina matuƙar son sa. Idan har kakata nada manufa a kaina itada Uncles ɗina dama family ɗina duka ashe bani da babban abinda ya kamata na runguma sama da wannan cikin, yafi kowa kusanci dani a yanzu, banda uwa, banda ƙani, banda yaya. Daddy na da Uncle Yousuf sun fifita soyayyar wani a sama da tawa. Wlhy a yanzu-yanzu Ummita naji ƙauna da soyayyar abinda ke cikina harda zumuɗi da fatan zuwansa duniya lafiya, a wannan karon bazan bari su taɓamin shi ba, ina son na rayu da shi, bana son na rasashi ko shi ya rasani kamar yanda na rasa mahaifiyata”. Sosai Ummita taji itama hawaye na cika mata ido. Miƙewa tai tana murmushin yaƙe dan har yanzu munafukin na laɓe, sai dai bazai iya jin abinda suke faɗa ba. Hanya ta nunama Lulu alamar su koma tana ɗan murmushin yaƙe. “Muje restroom ɗin karsu fahimci wani abu, ina son ki kwantar da hankalinki ko'a fuska kada ki nuna musu kina son cikin balle yunƙurin guduwa. Na miki alƙawarin kozan rasa raina zan taimakeki. Dan nima kin min abinda bazan taɓa mantawaba, wanda shine dalilin amsar wannan aikin da nayi a lokacin da na ganki cewar kece wadda zan zauna da ita anan”. Sosai Lulu kema Ummita kallon mamaki, amma sai Ummitan tai mata murmushi kawai. Restroom ɗin suka shiga, Lulu ma sai tai fitsari sannan suka fito. Ganin sun nufo hanyar dawowa bodyguard ɗin nan yay saurin yin baya yana sanarma Alh. Sulaiman cewar gasu nan zasu dawo da gaske restroom ɗin suka shiga. Sarai Ummita taga waya a kunnesa, hakan ya sata sake gaskata zarginta. Sun koma wajen Dr Olivia wadda suka sameta tana waya da Dada. Dan haka Lulu ta laɓe tana saurarenta. Dr Olivia da bata lura da Lulun ba ita cikin harshen turanci ta cigaba da faɗin, “Idan akace sai an fidda cikin nan a wannan gaɓar akwai babbar matsala, dan za'a iya taɓa lafiyar ta ɓangarori da dama, koma a rasata baki ɗaya. Kawai Mrs Garko kuyi haƙuri ta haifi abinta. Amma dai har na mutu bazan daina mamaki da al'ajab ɗin wannan al'amarin ba, harma na sakashi a cikin manyan record namu na ban mamaki da suka faru a asibitin nan. Sannan zanyi bincike mai ƙarfi akai dan tabbatar da daga ina aka samu matsalar”.
          Shiru alamar tana sauraren Dada itama, sai kuma ta nisa da cewa, “Shike nan sai kin shigo ɗin”. Daga haka ta yanke wayar. Haɗiyar zuciya Lulu ta dingayi cikin wani yanayi, kafin ta saita kanta da ƙyar ta nufi cikin office ɗin. Murmushin da Dr Olivia ta gani a fuskar Lulu ya ɗan sata jin relief, ta rubuta mata magunguna da abubuwan da ya kamata taci dan inganta lafiyarta data abinda ke cikinta. Lulu tai mata godiya ta fito akan zata cigaba da zuwa awo. Koda suka fito a asibitin sai da suka tsaya sukai ɗan shopping sannan suka wuce gida. Sun samu Tajuddeen yazo, amma kamar yanda Lulun ta saba kallo ɗaya ta masa ta kauda kanta tare da wucewarta ɗaki tana amsa masa gaisuwar da yake mata a taƙaice. Tajuddeen da yake jin kamar ya fasa kuka ya sauke numfashi mai nauyi tare da dafe saitin zuciyarsa dake harbawa da sauri-sauri, da gasken gaske yake ƙaunar Lulu, soyayya yake mata mai zafi wadda shi kansa wani lokaci yana jin abun na neman fin ƙarfinsa. Bai taɓa jin koda ɗigon sonta ya ragu masa a rai ba duk da cin kashin da take masa. Hasali ma duk abinda tayi sai ya zama shi birgeshi take yi tare da ƙara jin sonta a ransa. Burinsa ya mallaketa matsayin matar aure, ta zama uwar ƴaƴansa, randa yaji ta ɗauki cikin wani ba nasa ba har hawaye yayi, dan ƙarshe ma sai da ya ga likitansa.........✍️




_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣1️⃣



.......Kasancewar Tajuddeen a gidan ranar ya hana Ummita da Lulu sakewa, dan itama dai Ummitan irin mutanen nan ne masu tsantseni akan addini da rayuwa, balle kuma itama ɗin dai tanada tabo irin na Lulu, koma muce ya zarce na lulun tunda ita an riga an keta mata nata mutuncin a sanadin fyaɗen ma harta haifi ɗa sai dai a yanzu babu shi a raye, abin takaicin kuma mijin yayarta data riƙeta ne wanda ta taso tanama kallon tamkar uba ta aikata mata hakan. Sannan tanada matuƙar wayo da lura akan al'amura na rayuwa. Lulu data rufe kanta a ɗaki saboda kasancewar Tajuddeen ɗin tana shiga saman gado ta kwanta tai shiru cikin nazarin abubuwan da suka faru a yayin fitar tasu yanzu. Sai kuma kamar wadda aka tada ta tashi zaune zuwa gaban mirror ta nufa, kanta ta ƙurama ido na tsawon lokaci, kafin takai hanunta ta ɗage rigarta gaba ɗaya ta ƙurama cikinta da ya ɗan turo kaɗan idanu, sai kuma ta kai hannunta saman shi a hankali ta lumshe idanunta hawaye na ciko mata su, ɓul-ɓul taji ya harba tamkar abin shiri, da sauri ta buɗe idonta da hawaye suka cika taf tana kallon saitin daya motsa ɗin, sai kawai ta saki dariya mai haɗe da kuka. Dan abu uku ne ke mata kai-kawon. Wai ita Mawaddat Isma'il Ibrahim Jiƙamshi ce ɗauke da ciki na haihuwa, abinda bata taɓa kawowa a jerin tunaninta ba na rayuwa. Duk da kuwa tanada masifar son yara a rayuwarta, amma bata taɓa kwatantasu gareta anan kusa ba ace matsayin ga nata ba a dalilin tsanar maza da tayi a rayuwarta. Sai kuma wata hikima ta UBANGIJI da ikonsa gashi a yau itace aka tabbatarma zata haihu ɗan mutum matsayin mallakinta. (Mallakinku dai ke da ubansa) wata zuciya ta ayyana mata. Idanunta dake a rufe tai saurin sake buɗewa, dan abinda zuciyar tata ta tsikaro mata yay matuƙar dakar ƙirjinta. (Aliyu) ta sake ayyanawa a zuciyarta tare da kaiwa zaune a kujerar mirror ɗin tamkar cikin gajiyawa. Sai kuma a fili kamar wadda aka tunzuro ta furta, “Ai har abada bama zai san da cikin ba balle zuwansa duniya ko rayuwarsa Mtsowww!!” ta miƙe a ɗan hasale. Kokawa ta shiga yi da zuciyarta akan abinda take ta ƙoƙarin sake tsikaro mata game da Smart ɗin. Cikin tsawa-tsawa kamar zararra tace, “Please and Please bana son damuwa a beg”. Ta ƙara jan tsaki ta shige toilet. (Ni sai ma taban dariya sai kace wadda keyi da wani a gabanta😂🤳).
          A haka Lulu ta ƙarasa wannan yini cikin wani irin yanayi mai wahal fassara a gareta ita kanta. Sai dai jaɗan-kaɗan hannunta na saman cikinta, yayinda zuciyarta ke cigaba da kawo mata al'amari mai nauyi dangane da kakarta da kawunta da sukaso rabata da shi batare da ko sau ɗaya sun taɓa tunkararta da batun tana da ciki ba ko tunanin zata so abinta. A ganinta wannan babban taka hakkin ɗan Adam ne ai, sannan bataga minene dalilinsu na zubar mata ɗin ba. Dole tana son tasan dalilinsu musamman ma Uncle Sulaiman data rasa dalilinsa na shishshigema rayuwarta a yanzu. Tunda a baya ita dai takan ma haɗa watanni bata ganshi ba. Ganin damuwa na neman cinkushe mata rayuwa ga kayan shaye-shaye sun gagareta sha a yanzu balle tasha ta manta damuwarta ya sata tattare tunanin ta ajiye gefe. Sai ma wani ɗan murmushin takaici ko damuwa za'a kirashi data saki, tare da shafa cikin nata a fili tace, “Wato kai saika nuna min daga jinin wanda ka fito ko?, abu na farko daka fara datse rayuwata da shi shine shaye-shaye, to ya isa a tsaya iya nan inba hakaba a sha ranƙwashi dan bana son shishshigi, shima uban naka yasan ba kanwar lasa bace niɗin tunda ban taɓa raga masa ba akan shiga min hanci daya dinga yi” ta duddungure cikin da yatsanta, zafin da taji ya sata ɓata fuska da sake faɗin, “Garama ka biyo halin Ammah dai zan iya fatan haka ba wannan mutumin mai fuska a turɓune ba uwa ta shanu” daga haka ta fito zuwa falo, dan tasan dai Tajuddeen ya wuce ai yanzu. Ilai kuwa Ummita kawai ta samu a falon tana ƙara gyarawa. Cikin ɗan murmushin da ayau ne ta fara yinsa ga Ummitan ta ce, “Ɗazun mun fara magana amma baki ƙarasa bani labari ba”. Ɗan kallonwa Ummita dake murmushi tayi, sai kuma cikin yanayin signal da idanu ta mata nunin tai shiru da bakinta. Sarai Lulu ta fahimta kuwa, dan haka ta waske da cewar, “Yanzu ni kuwa dama labarin ko dai film ɗin zan nema kawai na kalla da idanuna”.
         Murmushi mai ƙayatarwa Ummita tayi tare da jinjina a kaikaice ganin uwar ɗakin nata ta  fahimci abinda take son ta fahimta ɗin cikin sauri, dan haka itama ta fara bata labarin wani Hausa film da take kallo a YouTube kawai. Sai daga baya Ummita ta ajiye mata ƙaramar takarda. Ɗauka Lulu tayi tana dubawa dan cikin littafi ta saka mata yanda ba za'a gane ba.
        _“Aunty dole fa sai munyi taka tsantsan, dan inaji a jikina an saka mana recorder a cikin gidan nan da take recording duk wani magana da muke iyayi koda bata shafi komai ba, maybe ma harda cctv camara”._
      Lulu ta jima tana kallon takardar da Ummitan ta ajiye tare da shiga dogon nazari akan abinda tace ɗin dama abubuwan dake faruwa. Wanda ya kamata dama tun farko ta nazarcesu a matsayin ta na Lawyer. Sai dai rashin fahimtar dalilan da zata iya hangar abubuwanne kawai yasa bata kai can ɗin ba, da kuma halin rashin lafiyar da take ciki shima. Zaram ta miƙe daga falon zuwa bedroom ɗinta, tamkar wadda akaima allura ta fara kaikawo tare da tsunduma cikin gidauniyar nazari. Komai take bi dalla-dalla, tun daga randa Dada ta ɗakko ta da ga gidanta har zuwa zamanta Abuja na kwana biyar a hannun Hajiya Shuwa batare da Dada ta barta ta nufi gidan Uncle ɗinta Khamil ba. Zuwansu Canada da kai-kawon da Uncle Sulaiman keyi anan ɗin shi da Tajuddeen. Yunkurin zubar mata da ciki da ɗauke mata passport da yayi daga ita har Ummita, bibiyar ta da taga anayi da canja security ɗin ƙofar gidan da akaiyi da bata isa fita ba daga ita har Ummita sai da izinin Dada, amma kuma ai shi Tajuddeen kai tsaye yake zo musu. Maganar da Dr Olivia tayi yau da Dada, zancen Ummita akan recorder da cctv camara da take hasashe. Tsaf Lulu ta haɗe waɗan nan abubuwan waje guda tare da tattara hankalinta a jikinta ta saka rigar lauyanci. Tana zaune a gado pen da book a hannunta tana rubuce-rubuce akan haɗa wancan da wannan ya bata ma'ana Ummita ta shigo ɗakin da sallama ɗauke da kofin kunun gyaɗa da ya zama abincin Lulu. Sai tururi yake da ƙyamshi mai daɗi. Ummita ta ajiye mata saman coffee table da ɗan kaiwa tsugunne a gabansa ta fara tsiyaya mata a ƙaramin kofi. Cikin raɗa-raɗa ta ce, “Aunty karfa ki tada hankalinki akan maganar nan da kikaga na rubuta tunda bawai mun tabbatar bane ba ko gani da idonmu. Amma ina son daga yanzu mu sake taku a gidan nan musamman akan wannan cikin na jikinki. Aunty duk da ban san miye dalilin son zubar da shi da ake ba ina son ki gane muhimmancinsa a gareki kamar yanda kika faɗa a ɗazun. Dan da ace bai kasance mai muhimmanci ba baza'aita kawo masa hari irin haka ba na san salwantar da shi gaba ɗaya. Sannan ina son ki nutsu a matsayinki na lawyer ki fahimci wanene kawunki da ɗansa da manufarsu, dan tabbas a nawa guntun nazarin na fahimci kamarfa suna amfani da Dada ne kawai a wannan al'amarin, kai shi kansa Tajuddeen ɗin kamar uban amfani yake da shi a kanki kawai wlhy”.
       Tunda Ummita ta fara magana Lulu ta zuba mata idanunta ne kawai. Dan gaba ɗaya lissafin Ummitan yazo dai-dai ne da nata. A hankali itama ta furta “Ummita duk ya akai kika san wannan?”. Murmushi Ummita tayi da ya ƙara fidda ƙyawunta da gogewar data sake yi na zama a turai. Cikin nisawa ta ce, “Aunty kenan. A kanki zan iya yin fiye da hakan, dan ke wata madubi ce ta rayuwata data haska min kaina da ga ruɗanin munana zuwa na MACE MUTUM mai daraja”. Hannu takai ta share hawayen da suka sakko mata, sai kuma tai murmushi mai ciwo. “Aunty ki bari zamuyi magana amma ba'a gidan nan ba, sai dai ki yarda aikine tuƙuru a gabammu wlhy, amma bana son muyisa cikin gaggawa in har muna son kuɓuta da ga wannan tarkon cikin ƙoshin lafiya batare da an rasa wani a cikinmu ba.” ta miƙe a hankali ta nufi ƙofa. Da kallo kawai Lulu ta bita cikin wani irin yanayin sake shiga firgici, dan har wata ƴar zufa-zufa ke tsatstsafo mata a goshi. Sai kuma ta lumshe idanunta dai-dai sanda Ummita take ficewa a ɗakin gaba ɗaya ta zame ta kwanta. A karan farko ta saki lallausan murmushi irin wanda ke tabbatar da Lulu ƙamshi ta dawo kenan da ga barcin daya figeta na wucin gadi ba Mawaddat ta yanzu ba mai yawan karaya da yin sanyi. Dan tabbas a yau Ummita ta zame mata tamkar wata fitilar tochlight data haska mata wajen ajiye ƙafa da ɗaukewa, sannan allura mai ƙarfin gaske da ta zaburar da ita tare da wanke mata idanunta da ke lulluɓe a ɗan watannin nan cikin yanayin barci ruɗani. Laulayin cikinnan da daina shan abubuwanta ya so maidata wata sabuwar Mawaddat ba Lulu ƙamshi ba. Idanunta ta sake buɗewa a hankali ta ƙure p.o.p ɗin ɗakin da kallo. A zuciyarta ta ce, (Tabbas Ummita gaskiya kika faɗa, yanzu ba lokacin gaggawa bane ko burin guduwa. Lokacine na cigaba da kwantar da kai matsayin MAGE MAI KWANCIYAR ƊAUKAR RAI har sai nasan SIRRIN DAKE ƁOYE. Dolene na fara sanin manufar Uncle Sulaiman a kaina tare da tantance Dada kafin a fara wasan) ta saki wata ƴar siririyar dariya da faɗin, “Mutanen nan wato har yanzu baku san wacece ainahin Lulu ƙamshi ba ko? Karku damu saura ƙiris ku sani har ma ku bama wasu labari. Hhhh” ta sake sakin dariya tana kai hannunta saman cikinta da cigaba da faɗin, “Idan na gama da su kaima zan dawo kan naka UBAN, dan ajiyarka da yay anan ta ƙarfin tuwo bai sha a banza ba duk da yamin sakin dana buƙata salin alin”. Wani ɓul-ɓul cikin yayi kamar ɗazun har sai da ta zabura alamar tsorata, sai kuma ta harari cikin da faɗin, “Idan ba kayi ko kikayi ba ai ba'a tabbatar min jinin gadararre bane. Dan haka a nutsu bana son iyayi okay”........✍️

     _(😂Smart ɗanka ko ƴarka sun higa uku, duk tsiyar da ake maka da alama zata dawo kansu yanzu😂. Tofa dangin Smart kuma sai ku shirya MATA bisa kanku, dan akan cikinku zamu huce komai da kukai mana ehe🚴🚴🚴🥱)._



_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣2️⃣


.........*_LONDON_*

     A kwana a tashi ba wuya wajen UBANGIJI. A ɓangaren Smart komai na tafiya dai-dai da fatansa dama na duk masoyansa. Sosai ya ƙara canjawa a komai na halittar jiki, gogewar fatarsa da sake zamansa tsayayyen namiji ƙyaƙyƙyawan, ƙiba dai kam bai ƙara ba, sai ma canji wajen zama dana abinci da ya saka shi ɗan ramewa kaɗan dan yasha wahala kafin ya saba ci, yanayin ramar tasa sai ya sake fidda masa ƙuruciyarsa. Harma wani zai iya ɗauka shekarun da yake amfani da su a ƙwallon sune nasa na gaskiya. Kamar koyaushe Lulu na nan daram a ransa, sai dai ɗammarar da ya ɗaura akan tattara al'amarinta da duk wani wanda ke kusa da ita ya sashi dakewa tamkar a yanzu babu komai dake gaban nasa sai harkar ƙwallo da ibada da sam baya sakaci da ita. Abu ɗaya ke damunsa a kanta shine duk dauriyarsa a kowane dare kafin barci ya ɗaukesa daren nan mafi daraja daya ratsa a tsakaninsu ya dinga masa kai-kawon kenan, wataran har takan kaisa ga mafarkinta a wannan yanayin har sai ya kaisa ga wanka kafin sallar asuba. Wani lokacin kuwa har mafarkin gasu a tare yake da ciki a jikinta kotana shayarwa. Duk randa yay irin mafarkan nan yakan tsinta kansa a cikin nishaɗi duk da yana ganin abune mai wahala da yuwuwarsa ba lallai ba, bai kuma taɓa hasashen zata iya kasancewa da cikin na a haɗuwarsu ɗaya kacal, dan duk da ƙarfafashi da zuciyarsa da su Ammah keyi baya jin hasashensa zai iya tabbata akan sake kasancewar su inuwa ɗaya da ita balle har a kai ga haihuwa kuma. Dan ya jima da fahimtar Lulu nada taurin kai dana zuciya matuƙa akan abinda take ƙi ko take so....
       A yanzu haka su Smart sun fara wasan da suka kwashe tsahon watanni suna training akai. Wasane da gaba ɗaya ƙasar Unitet Kingdom hankalinsu ke akansa, kasancewar ya shafi kowa-da-kowa. _Smart Mawashi no. 9_ da ya kasance wannan ne wasanshi na farko a cikinsu tun a wasan farko ya fara bada mamaki. Inda ya zama mutum na farko da ya jefa ƙwallo a raga. Ba'a ɗauki dogon lokaci ba ya sake na biyu. Babbar magana kenan, dan kuwa fa a wannan rana gidajen jaridu da na tabijin harma da rediyo da yanar gizo na ƙasar ta UK a duniyar ƙwallo ka-ce-na-ce ake akan wannan sabon yaro na Queen City, dan ya girgiza zukata fiye da tunani. Farin ciki da Coach ɗin su ya shiga tare da Teammate ɗinsa da fans a wannan rana ba'a magana. Shi kansa yana cikin farin ciki mara misali, dan daga ƙwallon farko har ta biyu da ya jefa sai da yay sujida wa UBANGIJI. Bayan gama Home mach da sukaci 3-1 sati mai zuwa suka tafi away mach, a wannan rana ma al'amarin sai godiyar ALLAH, dan ranar ma dai Smart ya zira ƙwallo sau ɗaya duk da dai ansha wahala matuƙa da gumurzu. Tofa, abinfa ya fara zama babban al'amari. Dan al'amarin Smart Mawashi ya fara ratsa zukatan turawan ƙasar England. Wasan link ya cigaba da tafiya fiye da yanda Smart ke fata, dan matuƙa team ɗin nasu na taka rawar gani, saboda sune na ɗaya a tebiri, dan sunada maki kusan talatin da biyu, sun kuma bama team dake bimusu tazarar kusan maki goma sha biyu. Suna taka rawar gani ta yanda a duk randa zasu buga wasa zakaga stadium ɗin ta cika maƙil fiye da kowace rana. Smart ya jefa ƙwallaye goma a wasa goma sha biyu da suka buga, sunci wasa goma, sunyi drow a biyu. Haka dai wasa ya cigaba da tafiya cikin nasarori daban-daban tare da ƙalubale. Ranar da za'a buga wasan daya kasance kamar na dabi ko hammaya tsakaninsu Model Unitet cika iya cika stadium ɗin tayi. Dan duk wani masoyin ƙwallo na ƙauye dana birni a wannan ƙasa dama maƙwaftan ƙasar sun taru domin ganin wannan wasa na da sabon ɗan wasan dake lokaci da Queen City zata buga da Model Unitet ɗin da kowa yasan akwai hamayya mai ƙarfi tun shekarun baya tsakanin team ɗin guda biyu. Bayan kammala al'adu irin na ƴan wasa su Smart suka shigo cikin fili. Bakinsa ɗauke yake da addu'a kamar kullum, yayinda yake sake jin wani irin karsashi da himmar ganin yanda ya tara masoya a ƙasar daba tashi ba. Wasa ya fara gudana yanda ya kamata, sai dai a mamakin kowa yau Smart sai wani jan jiki yake yi, gashi shine lamba tara da kowa zai iya taɓawa. Kaɗan-kaɗan masoyansa dama na team ɗin sa suka fara ƙananun maganar yau kuwa lafiya?. Shi kansa Coach nasu hankalinsa ya fara tashi ganin yanda Smart ke gara ƙwallon a kasalance, sai dai abin jin daɗin sun tare ko'ina har yanzu suma abokan hamayyar tasu basu zira ƙwallo ko guda ba, sunata dai kai hari. A haka har aka je hutun rabin lokaci babu wanda ya zira ƙwallon. Dabaibaye Smart da tambaya Coach yayi akan ko baida lafiya ne yau. Amma sai yay murmushi ya ce lafiyarsa ƙalau kawai dai a haka wasan yazo. Sake jan hankalinsu Coach yay akan karsu bari suyi wahalar banza bayan nasarorin da suka kwararo a baya, saboda in har suka bari Modal Unitet sukaci galaba a kansu zasu sanyaya gwiwar masoyansu ne, dan shi dai yau bai gane komai ga Smart ba. Tofa wasa ya canja salo, dan ana dawowa kowa ya nuna da zafinsa ya dawo. A mamakin kowa sai akaga Smart ya ware kamar bashi ba. Abinka da rainon gero da masara a tsaye yake kan ƙafafunsa babu jin gajiyawa ko nuna rauni, gara ƙwallo yake a fili da iyakar ƙarfin zuciya dana ƙwanji. Cikin mintuna biyu da dawowa su Smart suka zira ƙwallo ɗaya, sai dai bashine ya zira ba. Wannan zira ƙwallo ya sake saka wasan ɗaukar zafi suma Model Unitet team ɗin suka rama a mintuna goma da dawowa. Tamkar an tsirama Smart allura ne shi da Teammate na shi a wannan gaɓar. Bata kashi ake na gaske kowa nason ganin ya sake nasara da kai ɗan uwansa ƙasa, amma hakan bata samu ba sai a kusan mintuna ukun ƙarshe da za'a tashi cikin amincin ALLAH Smart ya saka ƙwallo a raga. Wani irin ihu stadium ɗin ya ɗauka tamkar garin London zai tsage kasancewar yau wasan na cikin gida ne, dan Model Unitet ɗin suma ƴan nan cikin London City ɗin ne. Sakanni ashirin da huɗu saura Smart ya sake jefa ƙwallo ta biyu uku kenan da ɗaya. Ya arrahaman zokaji yanda stadium ɗin ke girgiza saboda matsanancin ihu da masu kallo suka ɗauka. Yayinda teammate ɗin Smart suka wani irin rungumeshi a tsakkiya bayan ya ɗago daga sujidar daya zube ƙasa ga hawayen farin ciki sun wanke fuskarsa. Dolene yay farin ciki, a cikin mintina ukun ƙarshe saura a tashi kacal da kowa ya gama fidda ransa za'a tashi 1-1 amma ya zira ƙwallo har sau biyu, wannan abun yayi kukan farin cikine tabbas..   
       Wannan itace mafarin nasarar tabbatuwar cikar mafarkin Smart a harkar ƙwallon ƙafa. Dan gaba ɗaya ƙasar England da kafafen yaɗa labarai suka ɗauka. Tako ina ƙasar ta ɗauki zance akan wannan sabon yaro da Queen City ta samo a wannan karon. Wanda daga fara wasan link zuwa yanzu ya zira ƙwallaye ɗai-ɗai

Please Login or Register in order to submit comment