gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading DR Chapter 12 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

to."

Sannan tabar musu d'akin.

Shi kam juyawa yayi wajan khadija yana tambayarta,

"Babyna babu inda kemiki ciwo ko?!"

Kallonshi tayi sannan ta kalli yaron dake hannun shi tace,

"Laah ya Ahmad wallahi da kai yake kama ka gani kuwa?"

Murmushi yayi tare da kashemata ido d'aya yace,

"Yoo yarinya angaya miki ni d'in na wasa ne ko matsalata ai tasa yaron yayo kama dani, tambayarki nayi fa ina kemiki ciwo?"

"Jikina be min ciwo amma dai ina jin zafi awajan abuna."

Kwantar da yaron yayi kamin yajata can karshen d'akin saman gado yace,

"Kwanta in gani ko kinsami kari ne."

Bata yi mishi gadda maba domin tana jin zafin wajen sosai daurewa kawai take yi. cikin nutsuwa ya dubata yaga tasamu amma dai beda yawa befi aimata d'inki d'aya ba kuma daga waje ne, shafarta ya fara yi bayan ya gama dubawa musamman kirjinta da sun riga sun gama tsokane mishi idanu, ganin yana neman fita hayyacin shi ne ya sata fara tureshi daga jikinta sabida tasan bata da abin bashi sannan tasan shi wasan ninnan bawani yi mishi suke ba shi dai kawai yajishi in.

"Nashiga uku ni Habi babana uban me kuke yi cikin kuryar d'aki kuma daga haihuwa yau sakaran wofi kawai...? zaka fito ko saina ci maka mutunci yanzun nan?"

Zaro idanuwa yayi yana kallon khadija saida ya dai data nutsuwar shi sannan ya fito yanata murmushi tare da shafar sumarshi yace,

"Kai Mama bafa wani abu zanyi ba dubata kawai nayi yanzuma idan kin yi mata wankan zanje da ita sai nayi mata d'inki tukunna ta denaji ciwon."

Harararshi tayi kamin tace,

"To naji zoka fice waje dan Allah kabarta ta huta haba mana kadai. san yanda haihuwa take yarinya nason hutu amma ka like da wanne kakeso taji?"

Hakuri ya bata tare da sumbatar yaron shi agoshi sannan ya bar d'akin bako kunya shi yanzu har wata fitsara-fitsara yakeji sabida ya girna ya zama Abba.

***

Kullum gidan nan cike yake da mutane Ahmad sam be cikin sukuni domin idan yabar gidan tun safe to be kuma dawowa sai dare sabida mutane. sosai yayi kokarin ganin yayima khadija da yaron shi bajinta domin akwati uku yayima khadijan sannan yayi ma yaron akwati d'aya sabida shi yaron kullum cikin samun kaya ya keyi daga abokanan shi da dangi kowa ya naso yaga yayima Ahmad din wani abu da zaiji dad'i.

Sun bawa mutane mamaki domin kuwa kowa yayi tunanin zai sakama yaron sunan mahaifin shi ranar sunan sai kawai sukaji an sakama yaro suna MAHMOUD, wato sunan malam Mamuda mahaifin khadija sai dai sun saka mishi suna na alkunya wato Abba.

Har hawayen dad'i malam Mamuda yayi lokacin daya ji sunan yaron yayi farin ciki tare da godema Allah, sannan ya shiga har gidan yayima Mama godiya sai dai itama godiya take mishi hadda hawaye yayinda ta tuna irin halaccin dayayi musu a cikin rayuwar su.


BAYAN SUNA:-

"Mama inaga abarta anan kawai d'akinta zaifi tunda baba yak'i yadda ta koma can d'in kuma mani sai naga dama nan da can d'in ai duk d'aya ne ko?!"

Wani kallon banza tai mishi kamin tace,

"Babana ban san meyasa yanzu ka rainani ba wallahi, so kake yi in bar maka yarinyar mutane kasani jin kunya wataran? kaddafa ka kamanta nice mahaifiyarka na sanka ciki dabai dan haka bazan bar khadija a d'akin taba zata dawo nan d'akina kai kuma ka zauna ana kun data gama wanka saita dawo d'akinta idan tagama zaga dangi amma gaskiya bazan yadda da zamanku tare ba sabida inajin tsoran halinka babana..."

Hakuri ya bata tare da barin d'akin cikin sanyin jiki. zaune ya taddata tana bawa yaron nono shima jikinta ya shige har wani ajiyar zuciya ya sauke kamin ya fara d'an shafarta sama-sama yana jin wata irin masifar kewarta jiyake kamar yayita tsala ihu ko za afahimci abinda ya keji cikin jikinshi.

Daga shi har ita nisa suka yi,sai dai sukaji ihun yaron ashe Ahmad dinne ya kwace nonon daga bakin shi ba tare da sanin lokacin da yayi hakan ba wato shi ya maye gurbin yaron, dariya suka saka tare bayan yai saurin maidama yaron nonon cikin bakin shi.

Dariya suke yi sosai musamman khadija da harwani nuna Ahmad din ta keyi da yatsa, saida Mama ta leko sannan sukai fargai-fargai dasu tace,

"Kukan me abba keyi haka?!"

Shiru su kayi kowan ne ya sadda kanshi k'asa, hararar Ahmad d'in tayi kamin tace hala yau ba zaka fita ba ne ko?!"

Mikewa yayi ya shige ciki saida ya shirya ya fito, Maman tabashi hanya ya fice sannan taje ta amshi yaron ta goyeshi ta fara had'a kayan da zasu bukata ta dinga kaiwa d'akinta ita dai khadija nata ido kawai.

Saida ta gama kintsa komai sannan ta tasa khadijan zuwa d'akinta,

"Ke naga alamar bawani hankalin kirki gare kiba inba haka ba duka yaushe kika haihu da zaki fara biye mishi tunda kin san ba hakuri ne da shiba? koda yake bazan yi mamakiba tunda shine ya raineki babu abinda be koya mikiba ke ma kin zama shi."

Kunya tasa khadijan rufe kanta akan gado tun tanajin motsin Maman har barci ya d'auketa a haka.












*MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€
*πŸ’—DR.AHMADπŸ’—*

42

*NA MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€

Edit by *HAJJA CE*πŸ‘ˆ

*HASKE WRITER'S ASSO....*πŸ’‘
(Home of expert & perfect writer's)


*B*ayan kwana biyu masu jego sunyi shar abinsu basu da wata damuwa sabida irin kulawar da suke samu daga gurin duka side din, abba sai k'ara washewa ya keyi da wayau tubarkalla Mama bata da aiki saina kallon abba tare dayi mishi rawa ita dai Allah ya jarabce ta dason yaron wanda har bata iya boyewa.

AMINU kam kullum sai anyi daga dashi domin soya keyi ya dinga goyashi itako Mama taki yarda khadija ko babu ruwanta daya ce bani take mika mishi haka Maman zatai tamata fad'a amma bazai hana gobema taba shiba dan tana ganin bayan uban yaron to Aminu ne na biyu.

Malam Amadu kuwa tuni ya fara tsanewa atsaye duk da cewa kullum yanzu azumi yake yini dashi amma dakyar yake barci sabida kewar matar shi.

Zaune yake cikin ofis d'inshi yau tun safe babu abinda ya tsinana gashi yanzu har anfara kiran sallar azahar a wasu masallatan, wayar shi ya lalubo kamin ya dan na mata kira, cikin shagwab'a ya furta,

"Babyna..!"

Murmushi tayi kamin tace "uhumm yayana ya aikin?"

"Na kasa baby wallahi yau jinake kamar zan halaka Mama ta daina jin tausayina wai har yanzu baki fara sallah ba?"

Tunowa tayi da fad'an Mama dan haka da sauri tace mai,

"Eh ban fara ba, amma dai yau baka azumin ne?!"

"Inayi baby ya zanyi."

"Ayya toh shike nan dama cewa zanyi kai sauri ka dawo yanzu kamin Mama ta dawo ko ragewa sai kayi, tunda kuma kana azumin shike nan.."

Ai tuni ya mike tsaye tare da furta,

"Ashe batanan amma kikaki gayamin tun safe? bari inzo ganinan."

Dariya ta fara yi mai bayan ta ajiye wayar, zuwa yanzu mijin nata ya daina bata mamaki sai dai tausayi, sannan kullum adduarta gareshi shine Allah ya dauwamar da hankalin shi a kanta ya kauda idanunshi daga kallon matan banza ballema harya kaiga ta yawa.

Jikinta ta gyara da turaruka sannan ta tsaya jiran shi tana addu'ar Allah yasa kar Mama ta dawo da wuri. aiko sai gashi yau ko takan abba bebiba wata irin wawar runguma yayi mata akirjin shi kamin ya fara sunsunarta da lasarta, jikinshi harwata tsuma ya keyi yana cewa,

"Babyna yaushe rabon da ko rungumarki nayi Mama ta hana komai wallahi na kusa mutuwa da kyar nake daurewa, dan Allah da abun ya d'auke kimin magana ko sau d'aya ne nayi batare da sanin maman ba kinji matata?!"

Sumarshi take shafa ahankali cikin lallashi kamin tace,

"Kayi hakuri kaji kayiwa Mama biyaya nima ka tayani yi mata abinda take so."

Bak'aramar murza ta shaba a hannunshi ba sannan ya samu ya rage damuwar shi, Allah ya temaketa harya gama bired'ed'en shi hankalin shi be kai wajan abinba dan tasan da saiya gane ta sami tsarki ita kuma tana tsoran kar Mama ta gane tayi mata kallon wani abun.

kwance yayi agadon yana sauke nunfashi, har lokacin idanunshi alumshe yake kuma hannunshi na saman kirjinta yana cigaba da shafarta,

"Uhm! honey ya Ahmad to ka tashi ka shirya jikinka kamin Mama ta dawo ta taddaka kasan fad'a zatayi kuma sai ta gane sannan ya maganar azuminka yana nan?!"

Dariya yayi kamin yace,

"Ai kema kin san yabi ruwa na yau babyna amma dai zanyi gobe insha Allahu ai na rage zafi."

Itama dariyar tayi kamin tace,

"To yaza kai da girkin da zatayi maa anjima?"

Janta yayi jikin shi yaci gaba da tsotsar lips d'inta idanunshi arufe tsawon lokaci domin harta farajin zafi sai dai batasan ta katse shi domin samun nustwarshi itace tata.

Motsin yaron ya kwaceta dan haka da sauri ya tashi ya fara goge jikin shi ita kuma ta nufi abba dake son fara kuka.

Wucewa yayi d'akinsu yana fad'in,

"Sorry bari inyo wanka yaron baban shi sai nazo in d'aukeka kajiko?"

Tana bawa yaron nono shi kuma ya shigo ya canza kaya sai kamshi ya keyi, ganin irin kallon da take mishi yasa shi zama gefenta yace,

"Baby na can zamiki ne?!"

"A'a dadyn abba kawai dai naga kaimin kyaune sosai ina fatan zaka kauda idanunka daga kallon haramun?!"

Abba ya amsa a hannunta kamin yace,

"Ki tayani addu'a babyna insha Allah zan kiyaye nagode da kulawarki gareni Allah yayi miki albarka."

"Amin."

Wasa ya fara yima yaron kamar wani babba shiko yaro ya zubama fuskar baban shi ido.

"Kaga nidai kawoshi ka tafi kadda Mama ta dawo tayi tunanin ko wani abun kadawo mawa."

Yana mika mata yaron Mama na shigowa domin tunda ta hango motarshi taji hankalinta ya tashi, sannu da zuwa sukai mata ciki-ciki ta amsa tare da jefama Ahmad din wani kallon tuhuma,
kauda kashi yayi ga barin kallonta kamin yace,

"Mama ashe unguwa kikaje yanzu na shigo khadija ke gayamin gidan hassan naje shine nace bari na biyo daga nan in gaya miki hadda d'an-wake zakimin na bud'a baki sabida na rabu dacin shi wallahi."

Washe baki Maman tayi kamin tace,

"Au to shike nan yasu hassan d'in ai tun safe nafita dawowata kenan."

"Toh sannu rikeshi baby in wuce sai na dawo."


Kallon tausayi Maman tabishi dashi kamin ta maido kallonta gun khadija tana murmushi tace,

"Ashe yanzu shima ya dawo?!"

"Eh Mama shigowar shi kenan sai ya dauki abba toh kema sai gashi kin shigo kamar tafiyar ku d'aya."

"A'a ni yanzu na shigo Allah ya dawo dashi lafiya."

"Amin Mama."


Irin gyaran da Mama takema khadija ya sanya tuni itama tafara adduar Allah yasa Mama taje unguwa kosun samu su sake da juna dan ta tsumu iya tsumuwa, sai dai ina Mama ta tsare ta rantse sai anyi arba'in cas.

"Please Mama na kiji tausayi na tunda tayi kwanaki 40 din kibarni da ita wallahi kamar zan mutu nakeji ki tausaya min Mama dan Allah ki cetoni daga fad'awa halaka kamar yadda kika cetoni tun kafin nakai haka girma.."

"Oh ni na bani babana nadai koma abokiyar wasanka kawai, yo in ba haka ba niza ka samu da wannan maganar?!"

"To Mama ya zanyi kefa mahaifiya tace amma kin hanani ganin khadija bani da nutswa idan na gaza hakuri na dauko wani zunubin wallahi hadda laifinki ciki Mama please, yanzu bakya sona kin daina damuwa dani baki san ya nake kwana ba haba Mama ni nefa Ahmad d'inki babanki d'anki wanda kikafi so a duniya."

Tashi tayi tabar mishi d'akin cike da jin nauyin maganar shi, aiko shima afusace ya bar gidan yana cewa,

"Yaukam bazai yiwu ba wannan wahalallen barcin da nake yi ba dani ba, babu wani lemon tsamin da zanshi...."












*MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€


*πŸ’—DR.AHMADπŸ’—*

43

*NA MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€

Edit by *HAJJA CE*πŸ‘ˆ

*HASKE WRITER'S ASSO.....*πŸ’‘
(Home of expert & perfect writer's)



*K*usan duk taji abinda ya faru tsakanin Ahmad da Mama dan haka agigice ta fara lalubar wayarta tana sharar hawaye daga kwancen da take, tajima tana ringing sannan ya d'aga wayar muryarshi tayi matukar yin sanyi da kaji kasan yana cikin damuwa.

Cikin muryar kuka ta fara magana,

"Ya Ahmad kadda kai min haka dan Allah ka rufamin asiri ka dawo gida kadda ka aikata wani zunubin wanda zamu samu kamasho muma, ka dawo gida wallahi zan kwana a wajanka ko Mama bata so amma kadda kaje wani wuri kaji dan Allah?!"

A kai-akai yake sauke ajiyar zuciya kamin yace,

"To ki daina kukan yanzu zan dawo."

"Nidai ban yadda ba ka dawo in ba haka ba wallahi bazan iya zama dakai ba sabida zanfara zarginka gara ka dawo yanzu nasan ko nisa ba kaiba."

"Toh shikenan ganinan amma in taddake a d'akin mu kinji ko?!"

"Toh..."

Ta furta tare da ajiye wayar, idanu suka had'a da Maman wacce tuni tagama jin duk wata magana da suka yi.

Idanun tane suka kuma kawo ruwa kamin tace,

"Mama kiyi hakuri tsoro na keji, wallahi tsoronake Yaya Ahmad bashi da hakuri ya riga yaje makura kiyi hakuri.."

"A'a toh nikuma menene nawa khadija? ai kunfi kusa Allah ya baku zaman lafiya da hakuri da juna, amma dai sai gobe zaki koma d'akin naku ko? sabida a d'an k'ara gyara shi.

Ba yadda zatayi tace,

"Toh Mama."

Goma saura ta sulale zuwa wajan mijinta domin tuni ya isheta da kira, lallab'awa tayi ta ajiye yaron kusa da Mama tayi tafiyarta wajan Ahmad, kusan cin karo suka yi a hanya harya gaji da jira zaizo ayi yanda za ayi, tana rungume jikin shi har gado ko kofar basu tsaya sakayawa ba suka fara shagalinsu domin ba k'aramin hakuri Ahmad d'in yayi ba shi kanshi beyi tunanin zai iya hakurin ba amma dai yasha wahala fiye da yanda masu karatu zasu fahimta....

Lokacin da tafiya tayi tafiya tuni malam Amadu aka fara sambatu da kiraye-kirayen sunaye sabida ba karamin gigitashi babyn tashi tayi ba, sosai ta temaka mishi har wajan asuba suna nanike da juna koya ta motsa saiya mai da ita jikinshi, sun manta da batun jaririn su abba da yake dama yaron bawani damuwa da tsotsan dare yayi ba hakan yasa suka manta dashi.

Kasa fita sallar asuba yayi sabida wani irin matsiyacin zazzabi daya sakko mishi, koda sukai sallah kuma nad'eta yayi ajikin shi yana kyarma itako tuni tafara mishi hawaye sabida tausayin shi takeji dan har ta fara tunanin ko yanada shafar aljanu.


MAMA kam jin kamar motsi kusa da ita ya sata tashi zaune tare da haskawa,

"Lahaula wala kuwwata illabillahir aliyulazim ni Habiba nan ta kwangarar dakai kenan ta tafi wajan mijinta, oh ni yaran zamani to banda shirme aida dashi ta tafi idan da ya tashi ni zan bashi Nono ko kuwa..."

Kuma haska yaron tayi idanunshi biyu yatsa kawai yake tsotsa, hab'arta ta kama kamin tace,

"Ikon Allah zamani..."

Koda tayi sallar asuba rungumar yaron tayi jikinta tana mutmushi idan ta tuna shirmen iyayen shi.

Koda gari yayi shaaa tuni Ahmad ya fara galabaita sabida aman daya keta shek'awa dan haka arud'e khadijan ta nufi d'akin Mama tana hawaye.

A tsorace Maman ta mik'e dan dama bawani barcin kirkine ya d'auketa ba sabida tana gudun kadda yaron yai kuka,

"Lafiya khadija?"

"Mama bashi da lafiya tun dare yanzu kuma amai yake tayi harya gaji."

"Innalillahi muje na ganshi."

Saida ta goya yaron sannan suka nufi d'akin yana kudundu ne a cikin bargo ya rufe har fuskarshi, sannu Maman tayi mishi kamin tace,

"Ina wayarka akira maka ko Hassan ne ya duba ka?"

Muryarshi tai sanyi sosai yace,

"Mama tana falo."

Khadija ta kira dr. hassan da yake abokin aikin Ahmad d'in ne kuma suna abotaka sosai sannan unguwarsu d'aya, saida tayi mishi bayani sannan yace gashinan zuwa.

"K'arb'eshi kibashi nono inje inrage ayyukan kamin yazo ya dubashin."

Zama tai kusa da Ahmad domin bawa yaron nono bayan fitar Maman d'akin Ahmad ya rungumota jikin shi yana kallon yaron kamin yai murmushi yace,

"Kinga be kuka ba da dadaddare gunta zai dinga kwana ma kawai ko?!"

"Eh..!"

Ta furta a hankali kamin tace,

"Ya jikinka?!"

Kirjinta ya matsa da karfi har saida yaron ya kware da nonon kamin yace,

Koma dai menene ai kune kuka jamin tunda da kika biyema Mama akaita jamin rai."

Shiru tayi mai tak'i yin magana dan tasan tsiya yake yi mata,


"DR. ya haka?"

Cewar dr. Hassan dake dariya, shima Ahmad d'in dariya yayi kamin yace,

"Kai nifa bana san iskanci kaje kakawo min magani kawai insha."

Ficewa yayi yana dariya itama dai Maman bata kuma bi ta kan shiba dan tasan ciwon berasa nasaba da tasowar kwantacciyar jarabarshi ba.

Sai wajan sha-biyu sannan ya warware nan da nan ya fara lalubar khadija, saima lokacin ne ta tuna da zafin dataji jiya da daren domin bakaramar wahala yaba taba.

Marairaicewa tayi tace,

"Kai yayana daga warkewar ka?!"

Ko kulata beyi ba sai da ya sami nutsuwa sannan ya rungumeta jikin shi yana sauke numfashi murya k'asa-k'asa tace,

"Khadija kin sauya da yawa wallahi jinake kamar in makale ajikinki na daina fita, ashe idan mace ta haihu k'ara canzawa take yi?"

Murmushi kawai tayi aranta tana cewa inda gyara ko, ai wannan aikin Mama ne.

Aminu ne ya zabga sallama d'akin da sauri suka rufe jikinsu da bargo kamin Ahmad din yace,

"Kai Aminu ya akayi?!"

"Mama ce tace akawo shi kuka ya keyi kuma a cire mishi kayan sanyin rana ta fara zafi..."

"To kawoshi nan."

Ganinsu cikin bargo yasa aminun cogewa saida Ahmad din yace,

"Kawoshi mana a'a Maman shi barci take yi."

Daga kwancen ya karbi yaron Aminu ya fita yana waka shi kuma ya gyara mai kwanciya ajikinta yace,

"Bashi yasha sai muje muyi wankan."

*****

Babu sauran wata b'araka tsakanin ma'auratan domin Mama ta tsaya musu tsayin daka wajan ganin zaman nasu ya d'ore amataki na adalci da kyautatawa juna, haka rainon yaron kusan awajanta yake indai ka ganshi hannun khadija to nono zai sha ya saba da Mama sosai sabida yanda take kulawa dashi kullum wajata yake kwana idan ya motsa tabashi ruwa, be tab'a yi mata kuka ba.

Ahmad ya fara cuku-cukun neman karatun khadija ya sami karin girma da transfer zuwa katsina dan haka cikin farin ciki ya gayama Mama tare da shawarar komawarsu gaba d'aya can, domin Maman taso kin zuwa sai dai tun alokacin khadija ta saka kuka tare da rantsuwar itama ba zata bishiba matukar Maman baza taje ba.

_Kunjifa surukai ko masu shirin zama surukan ya kamata musan irin zaman da zamu yi da matayen 'ya'yan mu tunkamin sufara mana adduar mutuwa sabida bak'in halin da muke nunawa a garesu."_


Ckin sati uku suka koma cikin garin katsina da zama sai dai sunbar Aminu a gidan malam Mamuda sabida makaranta idan ya kammala J.s sai ya k'arasa acan. satin su biyu da tarewa khadija ta fara zuwa makaranta inda ta samu Omar musa 'yar aduwa, bata da matsala da abba domin ya fara shan kamu wanda Mama ke had'a mishi na waken suya da madara har taje ta dawo be kosawa da jiranta shima d'an albarkar....










*MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€

*πŸ’—DR.AHMADπŸ’—*

44

*NA MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€

Edit by *HAJJA CE*πŸ‘ˆ

*HASKE WRITER'S ASSO...*πŸ’‘
(Home of expert & perfect writer's)



*K*ullum shike sauketa a makarantar sannan shi kuma ya wuce wajan aikin shi, yana matukar girmama khadija da duk abinda ya shafeta bejin kiwar yi mata duk abinda take so sabida bata rageshi da komai ba musamman wajan bukatarshi koda bata so takan jure tak'i nuna mai hakan har sai ya barta dan kanshi. kullun cikim gyaran jikinta take da kayan marmari da kamshi sam bata yarda yajita da wani tashi wanda ba kamshi ba, tana matukar amfani da shawarwarin surukar tata domin wasu lokutan ma ita da kanta take murzamata kankana da madara ko kuma kwakwa da jikakken dabino ko kuma had'in kanunfari da zuma, had'i ne masu matukar k'arama d'iya mace lafiya da kuzari tare da d'and'ano mara algush shi yasa kullum mijinta yake like da ita bata ba shi damar kallon kowace d'iya mace ba awaje kullum cikin shaukinta yake ga yaronta shima tabarkalla kullum kara girma yake yi da wayau. waye yayi tunanin rayuwa zata zo musu a haka? sabida kowa yana tunanin rashin mahaifi shine durkushewar rayuwa, wannan ba haka bane domin Allah baya tab'a d'orawa bawa abinda bazai iyaba sai dai shi bawan ya d'orawa kanshi ma'ana be amince da kaddarar shiba.

Fitowarta kenan daga cikin makarantar sotake ta biya gidan wata k'awarta da keta fama da laulayi taga yau kwana biyu bata zoba taji wayarta nata ringing ko bata duba ba tasan mijinta ne domin kalar nashi daban yake dama.

"Hello.."

Ta furta cikin yanayi na rigima da gajiya yace mata,

"Babyna ya kike?!"

"Lafiya lau nake, ya aikin naka?!"

"Lafiya lau, sai kewarki data dameni baby ganinan a hanya zanzo in d'aukeki mudawo gida idan na huta zuwa anjima saina koma."

Murmushi tayi wanda har saida yaji sautin shi kamin tace,

"Toh shikenan amma ka tahomin da abu me sanyi yayana sabida yunwa nakeji sosai."

"Ok as you wish madam."

Samun wuri tayi ta zauna dan jiranshi yayinda take tuno mijin nata wai kewa sai kace da safe be taketaba amma yanzu biyu na rana harya fara maganar neman k'ari Allah ya rangwanta mai.

Har ya tsaya gefenta hankalinta baya wajen shi saida taji yana k'okarin d'aukarta sannan ta farga, gaishe shi tayi sannan ta zagaya ta shiga motar, madarar Hollandia me sanyi ya mik'a mata saida ta shanyeta tas! sannan tayi hamdala tana kallonshi,

Girarshi ya d'aga mata kamin yace,

"Kin dawo dai-dai ko?!"

"Sosai ma wallahi yunwa ba tayi ba."

"Ina fa tayi ai shi yasa zakiji almajiri d'an malam yana cewa iya yinwa zata kasheni."

Duk suka yi dariya koda suka koma gida kallo Mama tabisu dashi kamin tace,

"Ikon Allah daga ina haka ku kuma?"

Shigewa d'aki khadija tayi tana dariya yayin da shi kuma Ahmad d'in yayi tsaye gabanta yana sosar kanshi kamin yace,

"Mama ina abba ne banji motsin shiba?!"

"Hummmm Allah-Allah ya shiryaka babana amma dai ka dinga kula da aikinka kaji ko? ga abba can yau barcin rana ya keji."

"Toh Mama insha Allahu a ci gaba da yi mana addu'a."

"Muna kan yinta ai banana."

Da haka ya sulale zuwa b'angaran su,

"Baby na babu kara shine zaki gudo ki barni da Mama ko?"

Dariya tayi kamin tace,

"To ai tasan halin 'yan kayanta tsayawar me zanyi ni kuma..?!"

Tare suka watso ruwa sannan ta kula dashi saida ya sami nutsuwa sannan ya shirya yabar gidan itako nan yabarta tana barcin gajiya.

****

Bayan wata hudu:-

Rarrafe yaron keyi yanata zagaye gidan yana wasanninshi shi kadai kyakykyawa ne na gaske gashi lafiyayye yasan kowa na cikin gidan ga d'an karan b'arna kamar sun had'a kawance da b'era. da yake weekend ne sam kiriniyar shi ta hana uban barci wanda tuni ya keso yayi barcin amma wasannin da yaron keyi shi kawai ya keji akunnuwan shi.

Jikin shi ya zare daga na khadijan kamin ya tashi dogon wando ya saka sannan ya nufi tsakar gidan inda ya kejin hayaniyar yaron, nan ya ganshi ya fara tsallen a d'aukeshi, Mama dake gefe tana dariya tace,

"Ya hanaka barci ko? ai abba badai kiriniya ba."

Sama ya dinga cab'e yaron suna dariya kamin yace,

"Wallahi Mama motsinshi kawai nakeji ko barcin ranar ma ya kiyi, amma bari na kama Mamanshi kila in tabashi nono yayi bacci."

Yana farashan nonon yayi barci sai gashi su duka sunyi barcin har Mama wadda dama itama motsinshi ya sata zama tsakar gidan dan kadda yai wajen ruwa.

Cikin ikon Allah komai na tafiya tsaf yanda suke bukata basu da wata matsala kullum arzikinsu karuwa yake kamar yanda temakonsu ga mabukata yake karuwa lokaci zuwa lokaci suna zuwa malumfashi tare da charanci domin ziyarar 'yan uwan su.

****

"Wai kai dr. bazaka iya k'ara aure bane kaduba kaga yadda yarinyar nan take ta binka kaiko tausayinta ba kaji ne?!"

Cewar dr. Hassan wanda ke zaune cikin office d'in DR.AHMAD din suna hira, wani.......








*MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€
*πŸ’—DR.AHMADπŸ’—*

45

*NA MAMAN KHADIJA*πŸ™‡πŸ»β€β™€

Edit by *HAJJA CE*πŸ‘ˆ

*HASKE WRITER'S ASSO.....*πŸ’‘
(Home of expert & perfect writer's)

*KARSHE*πŸ’ƒπŸ»



*W*ani murmushin gefen baki yayi kamin yace,

"Dr. Hassan kenan, kana tunanin idanuna zasu iya kallan wata mace alhalin ina da khadija agida? To wallahi bari kaji wani abu da baka sani ba khadija ta zama wani b'angare na rayuwata na tabbata shigarta damuwa zai iya saka ni haukacewa, kowa ne bil adama daka sani yana son me kyauta ta mishi, khadija bata tab'a barina cikin halin damuwa ba kullum burinta ta gani cikin farin ciki to kana ganin nayi mata adalci idan nace zanyi mata kishiya?

Kin yi mata shine kawai sakayyar da zan mata a duniya, yanzu alhalin wahalata babu kalar wacce bata shaba, kuma kadda ka manta na baka labarin aurena da Zainab babu kalar soyayyar da bata nuna minba amma takasa iya zama

Please Login or Register in order to submit comment