google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zane kamin tace "yaron Hajiya a ba shi da lafiya shiy..."saurin katseta tayi da wata tambayar "mai kyau ? Anna ba dai mai kyau na bisa bene ba?"yadda take maganar take dafar ƙirji yasa Anna kallonta na wani ɗan lokaci kamin tace "to kar naji kar na gani kin fita daga gidan nan ,na san ki da shegen karanbanin tsiya"anna ta faɗa tana mai cire kayan jikinta tayi ɗaura gaba.Ta faɗi haka ne saboda sanin halin AMIRA na ƙididdiga da son sanin abinda yafi ƙarfin kwanyarta.






Washe gari ta kama asabar,tun da wuri ta gama aikin gida kafin ta shirya cikin shigar makaranta kamar kullum.
Yau ba su yi ƙosai ba hakan yasa taci ɗumame kamin su fito ita da anna wace ta shige gidan su AMAR ita kuma ta tafi makaranta.
Tun kafin ta shiga aji zuciyarta ke tsinkewa sakamakon ganin malam NURA na bada karatu,sallama tayi ta tsaya bakin ƙofa tana jiran izini da hannu yayi mata alama ta shigo.








Tun shigowar ta malam NURA ya koma ɗari-ɗari hatta ɗalibai sun kula da haka a tsorace yake karatun kasancewar tun radda abun ya faru shugaban makarantar yayi mashi bayani a kanta kuma bata sake dawowa ba sai yau.Wurin da ta saba zama ta zauna ta kafe malam NURA da ido,shi ma ta wutsiyar ido yake kallonta ganin direction ɗin shi take kallo ya gane kenan kallon shi take tunda niƙaf ɗin ta ba ta fiddo ido waje.Ya na gama darasi ya tambayi ɗalibai sun gane suka ce eh "toh masha yanzu wa zai tashi yayi mamu jawabi tare explique' abinda mu ka yi?"cewar malam NURA yana mai addu'ar Allah sa kar AMIRA tace zata iya tunda an bashi labari ilimi gare ta,addu'ar shi bata karɓu ba dan ko ita ɗaya ta ɗaga hannunta bai da wani zaɓi doli yayi interrogé ɗinta.
"يجب الغسل من ثللثة أشياء wanka na wajaba akan abu uku الجنبابة janaba والحيضda haila والنفاسsai kuma biƙi.
Uwannan su ne ke sa ya wajaba ga mutum dan haka doli mu kula musamman wajan janaba sau tari wani kan samu janaba ba tare da yayi la'akari ba domin wasu sukan kasa banbanta maniyi da mazayi musamman mata ba wai doli sai ta hanyar jima'i ba kawai ke samun janaba,ta hanyar tunani,kallo,shafa duk ana iya samu san..."ganin mutane duk sun maida illahirin hankalin su kanta yasa ta ƙyale ba dan komi ba dan mafi akasarin ƴan ajin ƴan mata ne sun girme mata wasu ma suna shirin aure,"malam ta cigaba"cewar ɗaliban malam NURA da yayi tsaye yana kallonta cike da mamakin yadda aka yi take koro jawabai dan shi bai gaye su ba,izini ya bata ta cigaba ai kam kamar jira take"um...akwai banbanci tsakanin maziyi da maniyi.
_ *Maziyi* wasu tsinkakun ruwa ne da ke fita gaban mace a yayin ƙaramar sha'awa,ya kan fito ta hanyar tunanin wanda kake so,tunanin aure to a nan wanka bai wajaba sai dai in har sha'awar ta wuce ƙarama kamar miji yayi wasa da matar shi ta fitar hayyaci ba tare da ya sadu da ita ba to a nan wankan ya wajaba domin babbar sha'awa ke haifar da fitar maniyi.


_*Maniyi* wasu ruwa ne tsinkaku fatsi-fatsi masu kabri da ke fita a farjin mace yayinda saduwa ko wasa da wasu sassan jikinta.Wanka kuma na wajaba a mace in azakarin namiji ya taɓa farjinta ko da kuwa bata fitar da maniyin ba"tana kawowa daidai nan ta zauna "Masha Allah barakallahu feeki lokacin récréation yayi ku fita ku ci abinci"cewar malam NURA yana mai zama kan kujera har AMIRA zata fita ya kirata gabanta ne ya faɗi ta dawo tayi tsugunne gaban shi,sai da duk ɗaliban suka fita sannan yace "AMIRA wa ya koya maki wannan karatun?"ajiyar zuciya ta sauke ta zata wani laifi tayi "cikin wayar Anna naji wani malami na faɗa kullum in tana gyaran kaya shi take kunna to daga nan na riƙe a kai"cewar AMIRA tana wasa da ruwan da ake goge tableau hannunta ya kalla wanda yake fari sol mai zaratan yatsu sun sha jan lalle,ɗan nisawa yayi kamin yace "AMIRA shin zaki aure ni?"........








💞💞💞💞💞




Shiri ya ke ya na tsuki ya rasa ko mi ke mashi daɗi,kallon LAURAT yayi wacce ke kwance kan bed tsirara tun bayan da suka gama sex ba ta tashi ba sai ma wani mayen kallo da ta take bin ya da shi.Wata sha'awar shi ce ke taso mata ganin ya shirya tsaf cikin jeans blue da riga fara ya shace gashin shi sai ƙyalli ya ke,agogon hannun shi ya gyara kamin ya ɗauki key yayi waje ba tare da yace da ita komi ba.




Motar shi ya ma key bai tsaya ko ina ba sai gidan su RAINA ,a ƙofar gida ya zauna cikin mota sai gashi ta fito cikin riga da wando ta baza gashi kamar baturiya.
Tun da ta fito ya kafe forme ɗinta da ido yadda cinyoyinta suke manya sai kuma suka ɗan lanƙwasa wajan ƙugunta kamar ƙwarya hakan ya ƙara ma shap ɗin ta kyau wanda ya ke kamar coca cola,mota ta buɗe ta shiga gidan gaba ko kafin ta kai ga gaishe shi yace "yanzu sabida Allah RAINA a haka kike fita salon duk a kalle mani ke?"yadda yayi maganar zaka tsinci ya na kishi sosai,langwaɓar da kai tayi tace "ayya masoyi kawai da kwalliya nayi maka kuma layin mu bai cika jama'a ba"cewar RAINATU sai wani fari take da ido .
Lumfashi ya furzar yana jin duk jikin shi ya mutu sanadiyar shaƙar turarenta da yayi bisanin yaji kan shi na juya mashi, murmushi tayi réaction ɗin shi kawai ya tabbatar mata aiki yayi kyau "nace ba?ya kuka yi da Ammy ?"ɗagowa yayi daga duƙen da yake ya dubeta sannan yace "na gaya mata saura dadyna""to mi kake jira ka kira shi yanzu kace Ammy ta gaya mashi maganar auren"kamar jiran umarninta ya ke haka ya kira dady shi kam bai yi wani mamakin auren ba dan ya san gadon shi ABDALLAH yayi "ok son kar ka damu in naje gida mu tattauna yadda komi zai kasance"cewar dady bayan ABDALLAH ya sanar da shi "please dad nan da 1week nike son auren"murmushi dady yayi "ok ba damu bari nace ma MUSSA ya haɗo maka kayan lefen"cike da murnar da bai taɓa ji ba ABDALLAH ya yanke kiran, rungume shi RAINA tayi cike da murna.






***Abu kamar wasa sai gashi har an kai kuɗin aure kuma juma'a mai zuwa za a ɗaura aure amarya ta tare asabar.
Tunda aka kai kuɗin auren MARYAM ta fara zazzaɓi kuma taƙi yarda a kaita asibiti sai da ABDALLAH ya tausheta yayi mata allura da ɗuren magani da abinci.
Duk tausayinta ya kama Ammy wai a haka ma bata san wacce ABDALLAH zai aura ba ne.Lipton Ammy ke bata dan shi kaɗai take iya sha ya zauna cikinta ko mi taci sai ta amayar ga zuciyata da ke faman yi mata ciwo duk in ta tuna ABDALLAH aure zai ƙara tafi jin zafin wannan fiye da lokacin da tayi na LAURAT.






Rana ba ta ƙarya a yau aka ɗaura aure RAINATU NASIR da angonta ABDALLAH AHAMED ɗaurin auren ya samu mutane kasancewar a masallaci aka yi shi.
Wani sanyi ne ya ratsa zuciyar ABDALLAH lokacin da aka ɗaura auren sai yaji kamar an janye mashi wani dutsi bisa zuciya can kamin auren ji yake kamar yayi hauka tunanin auren kawai ke cikin ranshi ko lokaci bai ba LAURAT dama-dama MARYAM in yaje wajan Ammy yana ɗan tsayawa kallonta wani sa'in romance duk da ta na ture shi.








Da murna ya shigo gidan amman lokaci guda ta ɗauke jin kukan Ammy tana bubuga ƙofa da sauri ya ƙarasa inda take,ɗauke shi Ammy tayi da mari "wlh wlh wlh kaji na rantse maka ko?in har ta kashe kanta wlh kaima sai na kashe ka kowa ya huta"tana gama faɗin ta bar gun ajiya zuciya ya sauke lokacin da wata dubara ta zo mashi "haba Ammy ya zaki ce haka wlh saboda son da nike ma baby na fasa auren nan yanzu haka ana can ana rigimi wasu sai zagina suke,yauwa ga dady nan ma je ki tambaye shi yadda aka yi"yana maganar ne ƙwarai ta yadda MARYAM zata ji ai ko kunne ta kashe tana saurare.Bubaga ɗakin yayi "babyna zo ki buɗe min kinji wani lab..."tun kamin ya ida ta buɗe wuf ya shige ɗakin tare da maida key.Jawota yayi ta faɗa ƙirjin shi jiƙaken gashinta ya fara shafawa alamu yanzu da tayi wanka ta wanke shi,goshin su ya game yana dogara mata tsinin hancin shi kamin ya lalubi lips ɗinta na ƙasa ya ɗan ciza.




Ba tare da yace mata komi ba,ya ɗan fara bata kulawa ta mata da miji ta yadda zai kwantar mata da hankali.Ya ci nasara kuwa dan sosai jikinta ya saki,sai ya ɗauke cak ya aza kan bed kafin ya tsugunna gabanta yana kallonta cikin ido.
Baki ta turo gaba alamun jin haushi, murmushi yayi ya dawo kusa da ita yana mai ɗan janyo ta jikin shi.




Wata sanyayar ajiyar zuciya ta sauke lokacin,ba tayi ƙoƙarin hana shi abinda ya ke dan ita ma tayi kewar shi,cike da soyayyar da suke ma juna suka raya sunnah cike da kewar juna.
A tare suka yi wanka MARYAM sai wani kumbure-kumbure take da shagwaɓa,dariya ABDALLAH yayi yace "yarinya ta sha daɗi amman da alamu bai ishe ta ba"matashin kai ta buga mashi tana dariya shi kuma ya tsaya kallon kumatunta yadda suka lotsa dimple ɗinta ya fito sai hushiryar ta wadda tafi komi burge shi.
Tsagaita dariya tayi ta ɗaga gira "ya a kayi ne kallon fa na minene?""na kin ji daɗi ne kuma baki so a faɗa "ya bata amsa yana mai daidaita fular kanshi, murmushi tayi ta kwanta tana latsa waya shi kuma ya mata kiss a goshi ya fita.




Contact ɗinta ta shiga sai lambar RAINA ta lalubo ba ɓata lokaci ta danna mata kira har sai da ta kusa tsinkewa sannan ta ɗaga "ƙawalliya ke baki nemana ko yau wajan 2week ba mu ga juna ba"cewar MARYAM tana dariya "ba ita ba ce tana can wajan lalle ta bar wayar"cike da mamaki wai RAINA da kullum suke faɗa akan mata lalle tace bata so shine ake mata a yau"lalle kuma RAINA ce ta yarda aka mata lal..."saurin katseta wadda ta ɗauki kiran tayi da cewa "eh lallen bikinta ne ko ba ta gaya maki yau aka ɗaura aurenta ba?"kamin ta bata amsa crédit ta suka ƙare hijab ta saka ta fito falo tana mai cewa "Ammy wai RAINA ..."goron da ta gani gaban dady ya hanata ƙarasawa,tasowa Ammy tayi ta zaunar da ita "kiyi haƙuri baby tun can dama Allah ya ƙaddarta miji guda zaku aura ke da RAINA tun farko na ɓoye maki wacce zai aura ne dan kar ki shiga damuwa,ki sani babu wani abu da Allah ya gindiya zai faru ga bawa face sai wannan abun ya tabbata"wasu hawaye masu ɗumi ne suka sauka kan kuncinta uwanda ta rasa na murnar yau RAINA tayi aure abinda kullum take da burin gani (don RAINA ta kasance mai yawan sha'awa kuma tunda take babu saurayin da ya taɓa cewa yana sonta duk da ta nada kyau,wani sa'in zuciyarta na ruɗarta ga fara zina amman MARYAM ke hanata)ko kuma na kishin mijinta "allahuma ajirni fee musibatih wa'alkhlifini khairin minha"shine abinda MARYAM ke nanatawa kamin ta mike tsaye wani jiri taji ya ɗibeta luuu tayi zata faɗi Ammy ta tareta.Ganin bata lumfashi yasa suka talalabeta a ruɗe suka kaita asibiti ,jini Ammy ta gani a jikin kujerar mota ga saura a zanenta wani irin ihu Ammy tayi wanda bata san tayi ba kamin ta fara nanata "innalillahi wa'inna ileyhi raji'un".




Ɗan jim kaɗan nurs ta fito ta ba su ordonnance na maganin da za a siyo,dady ya amsa yayinda Ammy ta fara zarya cikin asibiti.An ɗauki lokaci mai tsayi kamin a turota cikin gado na maras lafiya aka kaita wani room,farar takarda Dr ya miƙa ma dady kamin yace "ina mijinta ne ?"sai yanzu suka tuna da ba a ma shaida ma ABDALLAH ba "bai nan wani abu ne?"Ammy ta tambaya "tanada shigar ciki ne na sati guda da ƴan kwanaki sai dai sanadiyar firgici yasa cikin fara zuba mun yi nasara tsaida shi in ta tashi zamu sake yi mata scaning in kuma mijin ya zo ace ina neman shi dan shi ma yanada laifi mace mai ciki ba ko da yaushe ake zuwan mata ba,in yayi ganganci cikin na iya zubewa"......












Jikar Rabo ce🌚
[18/07 à 15:40] Matar Sadauki💞: *ƁOYAYYEN SIRRI*💞


By Chamsiya Laouali Rabo






Page 38-40




Kanta Ammy ke shafawa tana tofa mata addu'a bayan ta sanar da ABDALLAH suna asibiti,kamar an jefo shi ya shigo ɗakin dady na bayan shi."Ammy mike damunta?"cewar ABDALLAH yana mai zama bakin gadon da take kwance "mi fa zai dameta in ba wannan auren naka da ka tsiro ba garai babu dalili,wlh sa'ar ka guda likita yace cikin bai zube ba da ba zan sake maka magana ba"ido ABDALLAH ya fiddo yace "cikiiii?ciki Ammy ?"yadda yayi maganar a ruɗe ya ba Ammy mamaki da kuma haushi sai tace "ka tashi Dr na nemanka inda kana son cikin ai da ba zaka yi ganganci haka ba"sama-sama ABDALLAH ke jinta baby kawai yake kallo yana duba tafin hannunta ganin dagaske cikin dai ne gareta kawai sai ya rungumeta ya sumbaceta a baki,caraf MARYAM ta riƙe mashi lips ta shiga tsutsa sam ya manta da su Ammy ya biye mata.
Da sauri ya cire bakin shi yana fitar da lumfashi ya fara kallon ɗakin wayam babu su Ammy,ƙuri suka yi ma juna dan a lokacin ta tashi.Hancinta ya ja kamin ya ɗora hannun shi kan mararta yana shafawa yana jin son cikin jikinta har ƙasan zuciyar shi,ta ido suke magana sarai ya gane kallon mi take mashi na irin miyasa ka aureta ba tare da ka gayamin ba? sun ɗauki lokaci a haka Dr ya shigo,sérum ɗin ya ƙara ma gudu ya tambayeta abinda take tace babu sannan yayi ma ABDALLAH jawabin abubuwan da bai kamata tayi ba sannan ya ɗaga mata ƙafa har cikin yayi ƙwari.
"Amman Dr nan da 1week ai yayi ko?"turo ƙofa a kayi da sauri duk suka juya Ammy ce take wurgo ma ABDALLAH wani kallo ashe duk abinda ake tana ji "ka shiga hankalin ka in ba iskanci ba kai ma ba likita ba ne ai ka san abinda ya dace "sosa ƙeya ABDALLAH yayi yace "ammyyyy" hararen shi tayi tana mai ƙarasowa gun MARYAM da ke ƙoƙarin tashi,taimaka mata tayi ta jingina a jikin bango.




Kiran sallah la'asar yasa shi fita,a can masjid ɗin ne bayan sun gama sallah Dr ke tambayar ABDALLAH"dama kai na A.A ?"kai kawai ya ɗaga mashi yana murmushi"yau ne na fara aiki a cikin asibitin sai yanzu naji Nurs na firar an kawo Mrs ABDALLAH,to miyasa baka gayamin kai ne ba"cewar Dr "na zata ka sani ne dan ranar da kazo na ga kun fito da Dr LAWAN (abokin dady ne shi ke ɗaukar sabbin ma'aikata)na zata ya gaya maka"cewar ABDALLAH yana murmushi dan sam bai da girman kai irin na ɗiyan masu kuɗi,"ina fa ya gayamin sunan naka ma dan ya kasance sunan asibitin ne"dariya ABDALLAH yayi kamin su wuce ciki suna tafe suna hira.








A ɓangaren RAINA kuwa bayan an gama mata lalle INNANE tai aiko kiranta ta fara gwada mata wasu garin magani yadda za tayi aiki da su saura kayan mata sauran kuma na gidan boka "na cikin robar tun gobe zaki yi amfani da shi ki matsa shi a gaban ki,muddin ya kusance ki ba zai ƙara jin daɗin wata mace ba"cewar BALARABA wacce bata daɗe da zuwa ba tana kwance bisa gado daga ita sai ɗaura gaba kamar gidanta ta wani saki cinyoyi ga fili.Kai kawai RAINA ke ɗagawa dundu INNANE ta kai mata "ba ki magana ne zaki wani rinƙa ɗaga min kai kamar ƙadangare"cewar INNANE "haba irin kunyar nan ce ta amare ki ƙyaleta ƙawa" BALARABA ta faɗa daga can kwance,ita dai RAINA bata ce komi ba ta kwashe kayan ta maida cikin leda,cikin trolly ta sa ledar ta fice waje.




Da sauri INNANE ta yo kan BALARABA tana shafar ta "haba ƙawa irin wannan ai sai kisa na zauce gaban yarinya"ta faɗa tana haɗiyar miyau kamar mayya "dan Allah ki barni na huta duk a gajiye nike zuwa dare sai muyi "cewar BALARABA tana gyara zanenta,wani mugun kallo INNANE ta jefa mata kamin tace "wane irin in bari da dadare?kan ki guda kuwa?ko kin mance da sharaɗin?"INNANE ta faɗa tana mai yaye zanenta suka fara masha'ar su.Sun ɗauki lokaci kamin su tsagaita , rungumeta INNANE tayi tace "nayi missing ɗinki sosai ko ranar nan da kyal nayi barci da ban same ki ba,dan Allah nan gaba kar kije da MOCTAR in zaki fito"ɗan tureta BALARABA tayi tace "ni jarabar kice ban so na kusa gama aikina na rabu da wannan banzan auren da aka jona mani"tana maganar ne tana mai sabka daga gadon,duk da INNANE taji zafin maganar dannewa tayi tace "ina ne zaki wai?"
"Wanka zani yi in yi sallah"cike da mamaki INNANE tace "yaushe kika fara sallah ban sani ba?ko kin musulunta ne?"cikin jin haushi BALARABA tace "yo da kafira ce ni?"
"A'a ban ce amman miye matsayin wanda rabon shi da ya dubi gabas an fi shekara..."hayayaƙo mata BALARABA tayi "ko ma dai minene ai ke kika ja min ni wlh duk cikin abinda aka gindiya min ba abinda yafi ɓata min rai kamar na barin sallah"ta ida maganar cikin tausayi,dariya INNANE ta sheƙe da ita "toh in banda abun ki ina kika taɓa ganin wanda aljanu zasu biye maka suna maka abinda kake so kuma su yarda kayi alaƙa da Allah ?"ɗan shiru BALARABA tayi tana nazarin maganar INNANE kamin ta fice.






***


Shiri ake kamar za a kaita wajan gasa,wata fitinaniyar gizner ce fara sol wadda aka mata aiki na jan zare da perle,sosai ɗinki ya amshi jikinta.
Ƙamshin jikinta kawai ni'ima ce dan ɓarin turare INNANE tayi mata kamin su taru ita da BALARABA suyi mata nasiha wacce da ita da babu duk ɗaya dan babu zancen kiyi ma mijin ki biyayya ko ki zauna lafiya da abokan zaman ki sai dai akasin haka.






Motoci kan amarya wasu vide ma suka tafi dan INNANE ba tada yarda balle har tayi wasu mutane dayawa.Gida na gani na faɗa ne aka kai RAINA ƙawayenta ƴan ƙarya sai ɗaukar hotuna ake ana azawa a statut .




Bayan kowa ya watse aka bar amarya ita ɗaya,cilli tayi da mayafi ta je bakin madubi tana kallon kanta kamin ta cire kayan ta shiga toilet.Wanka tayi ta shirya cikin wasu arnan kayan barci wanda da su da babu duk ɗaya,feshe jikinta tayi da turarukan boka sannan ta hauda parfum tare da shafa man da BALARABA ta kawo mata na matsi.
Turo ƙofa aka yi tare da yin sallama sai dai bai ƙarasa yinta ba sauran ta laƙe a maƙoshi sakamakon arba da idon shi suka yi da kyakyawar surar RAINA,yawu ya haɗiye ya ida shigowa ciki yana mai ajiye ledar hannun shi.




Tsaye tayi ƙiƙam tana kallon réaction ɗin shi kamin ta fara takowa tana girgiza jiki,suman tsaye ABDALLAH yayi lokacin da ta tsaya gaban shi tana zagaye bakin shi da yatsa.Ajiyar zuciya ya sauke jin turarenta mai kashe jiki da sanyaya zuciya masoyi, juyawa tayi ta nufi ƙofar fita yabi bayanta da kallo yadda shap ɗinta suka fito.Dawowa tayi da ƙaramin tray a hannunta,ledar da ya shigo da ita ta jawo ta juye gasasun kajin Madougou sai turiri suke,abinda ango ya kamata yayi ma amarya ita tayi ma angon shine ciyar da shi da hannu har suka ƙoshi.




Tana lura da yadda yake samun canji amman ta share sai ma wanke bakinta da tayi ta haye bed, ABDALLAH ya koma kamar wani sakarai ya kasa taɓuka komi da kyal ya rage kaya ya shiga wanka.






Dariya RAINA ke yi ƙasa-ƙasa ganin yadda towel ɗin jikin shi ya toni asirin shi na halin da yake ciki,sallah ya so suyi amman sam bai ji zai iya daurewa ba.Hutar ɗaki ya kashe ya zo ya kwanta yana mai jawota a tare suka sauke ajiya zuciya,lumshe ido RAINA tayi tana karɓar saƙonnin da ta daɗe tana jira kamin ta fara maida mashi .Sosai ya samu nutsuwa sai sa mata albarka yake kamin ya fara rarashinta, munafukar luf ta laye cikin ƙirjin shi tana shasheka wani barci yayi awon gaba da su.(🥱asubah ta gari)










***
Kallo guda zaka yi mata ka gane tayi kuka kuma tana buƙatar yin barci sai dai hakan ne taƙi samuwa"ina kwana Ammy "ta furta da muryar ta da bata fita murmushi Ammy tayi kamin ta amsa mata tana mai haɗa mata lipton wanda yasha karamfani,karɓa tayi tana kurɓawa a hankali har ta shanye ta kwanta bisa salon Ammy kuma ta koma kitchen.




"Yanzu yana can rungume da ita ƙila ma yana mata wanka dan na tabbatar ABDALLAH ba zai ɗaga mata ƙafa ba tunda daman shi ko can bai kwanan banza"MARYAM ta faɗa a zuci tana mai goge hawayen da suka zubo mata,sai kuma tayi murmushi"RAINA burin ki ya cika kin auri irin mijin da kike so na san mijina ya haɗa komi abu guda da baki so kuma shi Allah ya bashi shi dayawa gashin ƙirji"duk a zuci ne take wannan maganar kamin kuma ta miƙe zauna "Allah sa kar ta aske shi "ta faɗa a fili ,fitowa Ammy tayi tace "magana kike?ko a baki abinci kamin nayi maki taiba ɗin?"kai ta girgiza tana mai tashi ta nufi ɗaki.
Wani tausayinta ne ya kama Ammy sai taji ƙwalla ta cika mata ido.




Ɗaki ta shige ta kwanta kan bed ta rungume matashin kai a ƙirji tana jin wani irin son mijinta da kishin shi na taso mata,a haka barci yayi awon gaba da ita.
Gashin kanta wanda yake a barbaje taji ana shafawa a hankali ta buɗe idonta ta sauke su kan ABDALLAH wanda ke zaune cikin ƙananan kaya ,da sauri ta tashi zaune shi kuma ya jawota jikin shi yana shafar bayanta.Ɗan janyewa tayi daga jikin shi ta ɗora hannunta ga rigar shi ta shiga ɓalle maɓalen bai dakatar da ita ba har ta gama,ajiyar zuciya ta sauke tana mai zura hannunta cikin ƴar farar ƙaramar rigar shi ta ciki "ina son wanga abun please kar ka aske shi"ta faɗa muryar ta na rawa,"na sani shiyasa na hana ta askewa"da sauri ta kalle shi "har tace ka aske ko?"
"A'a ta dai ce bai burge ta"hannunta ta fiddo tana shirin sabka ya maidata "kwanta ina son ganin lafiyar bébé junior"kwantawar tayi ya ɗaga rigarta yana shafar cikinta daga bakin ƙofa suka ji Ammy na cewa "wannan shirun yayi yawa ABDALLAH uwar mi kake da baka fito ba?"kallon juna suka yi kamin yace "Ammy gamu nan zuwa"ya faɗa yana mai maida mata rigarta daidai.
Falo suka dawo Ammy ta gabatar masu da abun karyawa,shi ke ba MARYAM a baki har ta ƙoshi.










A ɓangaren RAINA kuwa ba ƙaramin haushi taji ba da ABDALLAH ya banzatar da maganarta da tace mashi ta tsani gashin ƙirji sai bai ce mata komi ba yayi kamar bai ji ba ma,abun ƙarin haushi ko ƴar kyautar nan ta amare bai bata ba.
Fitar shi ma tun da safe taji haushinta sai dai babu yadda zata yi, INNANE ta kira bugu biyu ta ɗauka bayan sun gaisa ne INANE ke gaya mata zasu zo ita da BALARABA ganin ɗaki........












💞💞💞💞💞




Ƙyaƙyaf da ido AMIRA ta fara yi sai hawaye sharrr,shashekar kukanta ce tasa malam NURA sanin kuka ne take da sauri yace "tashi ki tafi"AMIRA na fitowa bata zarce ko ina ba sai gida.






A zaune ta tarar da Anna tana gyara waken ƙosai na gobe,ba sallama ta shigo gidan tare da cilli da hijab da niƙaf ɗinta ta fashe da kuka.Cike da tashin hankali anna ta fara tambayar ta lafiya "na gaji!na gaji anna doli ki gaya min wacece ni ko kuma wlh na bar maki gidan ki"dafe ƙirji anna tayi "AMIRA c'est une longue histoire ta yaya ta ina kike so in fara ki bari har ki ƙara girma kinji ƴata"anna ta faɗa tana shirin dafa AMIRA amman ta goce tayi hanyar waje"ki dawo zan baki ciwon da bai barin ka ai gwara ya kasheka ka huta"dawowa AMIRA tayi ta zauna kan tabarma, "AMIRA zan gaya maki kaɗan daga cikin abinda na sani"




*Asalin labarin....*




A damagaram an yi wani shahararren malami mai fatawa mai kuma riƙo da

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment