gtag('config', 'G-VDLWYD7FHB'); Reading Taki Zaman Aure Sirrin Zuciyar Mace by 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 Chapter 4 | ArewaNovels
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da nake son sani ne akansa a iyakar gaskiyata domin haka mutane suke yawan fada akansa shiyasa ake cewa yana da kudi sosai. Sai dai yanayin yadda na ga ya dago ya kalleni ya razanar da ni, ni ko a ganina tambaya ce kawai na yi domin hausawa sun ce waka a bakin mai ita tafi dadi. Matsowa yayi kusa da ni ya raba hannayensa biyu ya daga kujera da nake zaune yana kallon cikin idona.

“Noor shekararki nawa?”

Na yi saurin sauke idona kasa na kama jikina sosai zuciyata na bugawa.

“Ka ba ni tsoro”

Sai yayi murmushi ya dauke hannayensa ya matsa baya.

“Aa sheri suke min kin san mutane akwai hassada, hassada ce kawai”

Ni dai na yi shiru domin jikina na bani da farko kamar tambayar ta wa bata masa dadi ba, ko kuma ya fahimta a baibaiye ne.

“Kin san me yasa na tambaya shekarun ki?”

Yana tambayar yana kallona, na girgiza kai ina jin kamar duka na zai yi duk kuwa da kasancewar murmushi ne a fuskarsa.

“Saboda my ex kamar ke take, zata yi tambaya any how, zata fadi duk abun da ya zo mata a bakinta, bata tunani irin na mutane ita a komai nata tunanin dabam yake, yanayin surutunki mu'alamarki sakin jiki da kowa duk haka take, ina son ki zama kawata shiyasa na tambaya shekarunki”

Sai a lokacin hankalina ya kwanta, sai na yi dariya na mike tsaye.

“Idan na zama kawarka hakan yana nufin idan na zo asibitin nan, kyauta za a duba ni, kuma a duk lokacin da ba ga dama zan tafi restaurant dinka na ci abin da nake so ko na karba ba zaka ce komai ba”

“Huh?”

Ya furta yana kallona cike da burgewa, sai na daga masa kai.

“Eh shi ne abotai ai”

“Shikenan na yarda”

Ya furta cikin sanyi murya, yana kada kai a hankali. Farinciki ya cika ni har na kasa ce masa komai sai murmushin dake tattare da dariya nake.

“Mu tafi ko?”

“Toh”

Na bi bayansa domin tuni yayi gaba ya bude min kofar.

“Ni daman na san sheri suke maka ai da kana zubar da ciki ba zaka haifi wannan yarinyar ba, matarka zaka fara zubarwa...”

Ban karasa ba na ji hannunsa ya rufe min baki, dayan hannunsa kuma a wuyana ya saka ni gaba yana turani kamar wata akuya, aiko sai na duke na subuce na juyo na kalleshi rai a bace.

“Ya kana min haka sai aje ce an ga Noor wani Kato na taba ta”

Ya nuna kansa.

“Ni ne Katon? Beside neman mata ba halina ba ne, kowa zai iya shaidata da wannan bana neman mata, kuma na rufe bakinki ne saboda karki fadi wata maganar wasu su ji”

“Na gane”

Na amsa a hankali sannan na jera tare da shi muna tafiya, kana gani kasan ni kanwarsa domin ya fi ni tsayi sosai. Da kaina na Bude Motar na shiga shi ma ya shiga bangarensa a yanzu kam na gane dalilin da ya saka ba ayi masa fada ba a lokacin da ya faka mota a kofar emergency. Ban sake cewa komai ba domin na lura kamar surutuna ya fara effecting dinsa.

“Noor ya na ji ki shiru, ko maganar ta kare”

A lokacin da na juyo na kalleshi sai na ga kallona yake da da abun da ya zame masa wajibun wato murmushi a fuska.

“Na ga ai baka son surutu ne?”

“Inji waye? Ni ina son surutu sosai, shiyasa na sake da ke ba, ni mutum mai mai son wasa da dariya mai son nishadi, shiyasa kika burge yau din nan domin ina son mace da ko iska ya wuce sai ta bani labari yadda ya wuce, shiyasa nake son Ex dita amman na lura ke kamar ma kin fita”

“Ex din mutuwa ta yi?”

Ya girgiza kai ba tare da ya kalleni ba.

“Tana nan”

“To ka auro ta mana, ka aje ta a gidan ka, ka ga matarka ma ba zata sake fasawa baki kai ba saboda kishi”

“Ta yi aure ai, ina miki zancen baya ne”

Na yi kwafa.

“Wallahi ba dan haka ba da zai na zugaka ka kara aure, ni Wallahi da ni ce kai aure zan kara matar nan ta bata min rai daga tambaya? Kamar ta ji kowa kishi”

Wannan karon dariya yake min.

“Matata bata kishi, babu wani abu mai alaka da kishi a tsakanina da Matata, kawai dai kin zo a rashin sa'a ne, ko dai kin mata rashin kunyar kamar yadda ta fada, kawai an rubuto jininki zai zuba a yau ne”

Takaici ya hana ni cewa komai, wato bangaren matarsa zai dauka har yana yarda da zancenta ya watsar da nawa. Har muka isa restaurant din ban sake ce masa komai ba.

“Me za a kawo miki?”

Na dan kalleshi ina turo baki gaba.

“Ai da kunya ba komai zan iya fada a nan ba, ni dai zan shiga na karba ka fada musu”

Yayi shiru yana kallona kamar ba zai ce komai ba, sai kuma yayi murmushi ya daga min kai, sannan ya ciro wayarsa ya kira wadda ban san waye ba, ya fada masa wata zata shigo yanzu ya bata duk abun da take so.

“Zaki iya tafiya, amman ba sai kin fadawa kowa tare muke ba, ba a taba ganina da mace ba”

“Zaka iya tafiyarka ai, ni ma ba a ganina da maza, ni ma ba yar iska ba ce ba wai kai ne kadai na kwarai ba”

Ina fada ina yatsina fuska domin na lura so yake ya nuna shi na kwarai ne, ni ce yar iska.

“Ban ce ke yar iska ba ce, kawai ina son na kai ki gida ne cikin mutunci saboda na yi ma iyayenki bayanin yadda kika ji rauni, waya sani idan ban tafi ba za su iya dukanki”

Na kalleshi da sauri na tuni ma na manta da rauni.

“Eh Wallahi musamman ma Baba, bari na je na dawo to”

Na bude motar na fita ina jin kaina kamar wata yar shugaban kasa, ahh a rayuwata fa ban taba shiga mota mai kyau mai tsada irin wannan ba, kuma ina fitowa motar na shiga restaurant na karbo kayan dadi, wayyo Allah ina ma yan unguwar mu za su gan ni a yau. Sai da na kusa shiga reception din sai kuma na tuna da wani abu na dawo baya da sauri na kwankwasa gilashin motarsa sai ya sauke bakin gilashin yana kallona.

“Dan Allah ko zaka min alfarma idan na fito daga sai ka rufe idonka ko kuma ka fita motar har sai na saka abun da na karbo tukuna”

A bakin gaskiyata nake fada masa, domin kar na kwaso kaya da yawa ya ji babu dadi ai da kunya ko, daga kyauta na wuce gona da iri kuma yana gani.

“Ki ce karya min jari zaki yi ko?”

Yanayin yadda yayi maganar da kamar tsoro sai ya saka dariya ta subuce min, na yi bayabaya ina tafiya da baya baya ina dariya, shi ma murmushi yake yana kallona har na juya. Ni dai iyakar abun da na sani ba zan bar wannan banzar ta wuce ni ba, ba zan yarda na fito ba tare da na dauko abun da nake so ba, waya sani ma ko ba zan sake zuwa ba, ai Yaya ba zai bari na sake zuwa ba, kuma hausawa sun ce waman taraka bati sidda fa huwa wawa au sakare, wai duk wadda ya ga bati ya bar shi shi wawa ne ko sakare.

Ina shiga gurin na fada musu abubuwan da nake so, snack kala kala da naman kaza da farfesun kifi da na kayan ciki, har da wata yar tsutsa da na taba ganin turawa suna ci a tv sai da na saka aka hado min da ita yau dai ni ma zan dandana kayan masu kudi na ji me ake ji. Haka na riko leda biyar na fito ina boye ledodin a bayana dan kar ya gani, yace ba ni da hankali na kwashe masa kayan shago. A lokacin da na iso gurin motar sai ya bude min bayan motar na saka komai a ciki na rufe sannan na bude gidan gaba na shiga. Cingan na tarar yana ci yana kokarin juya motar

“Ka ga me na zo da shi?”

“Ba kin ce kar na kalla ba? I respect that”

Ya amsa ba tare da ya kalleni ba. Hakan ba karamin dadi yayi min ba. Sai na saki jiki ina fada masa inda zai bi har muka isa unguwarmu.

“Kwanar gidan mu mota bata shiga, ka aje motarka a nan ka raka ni a kafa”

“Ko dai na kira Yayanki ya zo ya tafi da kai?”

“Aa ko da shi ya yarda Babanmu ba zai yarda ba, kara dai kaje idan aka kira Babana ka masa bayani shi ne zan tsira, dan Allah ka min wannan alfarmar ba zan sake damunka ba daga yau na maka alkawari ba zaka sake ganina ba”

Ya daga min kai, sannan ya kashe motar. Har na bude na fita sai kuma na dawo ya leka shi.

“Amman ka zauna a motar sai na yi nisa sai ka biyo ni”

“Saboda me?”

“Saboda Saurayina idan ya gani zai ji haushi ransa zai bace yana da kishi sosai zai iya maka duka ma”

Yayi murmushin kasaita.

“Ni mai dukana ai sai ya shirya, zai dai yi kishi amman ba zai ina nuna min yatsa ba ma”

“Yana da karfi”

Na fada masa dan ya san Zafeer dina ba rago ba ne.

“Yana da kudi?”

“Aa”

“Toh ba shi da karfi”

“Ba zaka gane ba ai”

“Ke ce dai ba zaki gane ba, saboda ke yarinyar ce baki san yanayin kasar nan ba”

“What ever ni dai karka jera da ni, kuma zan bar maka ledodin a mota sai ka dauko min idan mun isa ka bawa Yayana ya shiga da su?”

“Na dauko kuma?”

“Eh ai ni mutanen unguwa za su iya fadawa Zafeer sun gan ni da ledodi manya, amman kai babu wadda ya san ka ai, ko kuma idan mun tafi ka kira Yaya ka ce ya zo ya dauki ledodin”

“Toh sai dai haka”

“Da nine kai ma cewa Yaya zan yi ya tafi gida yayi kwana biyu”

Ya kalleni.

“Saboda ya wulakanta kanwarsa, ai idan ni yarka ce ba zaka so ayi min haka ba right? Kuma ya bijirewa umarninka be kamata yayi haka ba”

“Haka ne”

Na fita na rufe motar na kama hanya ina fakar idon mutane, sai da na yi nisa sannan na juyo na kalleshi, bawan Allah ashe yana bayana daga can nesa yana bin sawuna. Sai da na isa bakin kofar gidanmu sannan na ja na tsaya har ya iso.

“Ka aika yaro kace kana Sallama da Babanmu”

“Okay”

Tsakanin amsawarsa da okay da yayi da kuma fitowar Baba da ban yi zaton yana gidan a wannan lokacin ba ban san wadda ya riga wani ba. Na ja baya da sauri na koma kusa da ogan kamar zan shige jikinsa.

“Toh Yar iska marar mutunci ina kika dauko wannan kuma?”

Kamar yadda nayi tsammani kalma marar dadi ce ta fito daga bakin mahaifina a izuwa gareni a gaban mutumen da mahaifina be san waye ba.

“Ayi hakuri ranka ya dade, dan akasi aka samu ta bugu a kai shi ne na ce bari na zo na yi muku bayani”

“Ai dama mutuwa ta yi, wannan yarinyar bata da amfani a garemu, wawuyar banza yar iska, ta maka hauka ko?”

Ogan Yaya ya juyo ya kalleni kamar mai mamakin jin furucin mahaifina akaina, ni kuma kunya da bakincikin suka saka na sauke kaina kasa ina taba yatsuna.

“Aa kareta ta na yi ba da gangan ba, ina tare da mota ne bata lura ba ni kuma burkin be tsaya ba sai na ji mata rauni a kai kadan, shiyasa na ce zan so na yi bayani a gidansu kuma na bada kudin magani, amman ayi hakuri dan Allah ba laifinta ba ne”

Baba na jin zancen mota da kudin magani sai fuskarsa ta sauya ya dan saki fuskar kadan.

“Babu komai, ita ce ai bata jin magana”

“Sunana Kareem Ibrahim Kalil, ni ne mai gurin da yaronka Nabil yake aiki”

“Maa Shaa Allahu, ashe ma abun duk gida ne, sannu da zuwa, bari na kira shi shi ma be dade da shigowa gida ba ai”

Kamin mutumen ya sake cewa komai Baba ya juya ya shiga gida. A lokaci ne ya juyo ya kalleni.

“Ki yi hakuri da abun da mahaifinki ya fada, wata kila ransa ne ya bace”

Na kalleshi ina murmushi.

“Na saba ai, Babana yana yawan cewa ba ni da sa'a babu alheri a tare da ni”

Da dare na karasa maganar irin dariyar dake tattare da bakinciki, shi kam kallona kawai yake kamin ya juya daga ni har shi mu kalli Yaya da ya fito daga cikin gidan. Cikin rawar jiki da girmamawa Yaya ya gaishe shi sannan ya kalleni.

“Noor ina kika je? Na iso gida Mama tace baki zo ba, dole na koma nemanki”

Na yi shiru ina turo baki, babu zato balle tsammani na tsinkayi muryar Ogan nasa yana karanta masa cewar ya zauna gida yayi kwana biyu.

“Ranka ya dade laifi na yi? Ko... Ko.. Noor ta yi wani abu ne”

Yana tambaya jikinsa na rawa.

“Kai ne dai ka yi laifi a wane dalili zaka tafi kai dabam ita dabam? Yanzu idan wani abun ya same ta fa? Kuma na baka umarni cewar ka tafi da ita ta dauki abun da kake so baka yi haka ba? Ban isa da kai ba kenan?”

“Dan girman Allah ka yi hakuri oga... Dan Allah ka yi hakuri”

“Ba korarka na yi ba, amman dai ka zauna sai Monday zaka koma aiki”

Wallahi ji na yi kamar na daka tsalle na dire saboda muryar lallai wannan mutumen mai saukin kaine sosai mai jin maganar mata.

“Mu je mota ka karbo mata sako, Noor Allah ya tsare gaba”

Ya karasa yana kallona.

“Ameen”

Na amsa sannan na shige cikin gida ina jin kaina kamar wata sarauniya a yau.
https://chat.whatsapp.com/ExyBEuiZZ0J1ivlVK5lIOx


Assalamu Alaikum...
Ina talata muku
KHADEEJA CANDY STORE 🥰🙌
Muna siyar da Atamfa, Laces, Mayafai, Talkami da Jaka, Akwaituna, Kayan Kitchen, Zanen Gado, da kuma kayan kawata gida ko falo.

✧✦ 𝗧𝗔 Ƙ𝗜 𝗭𝗔𝗠𝗔𝗡 𝗔𝗨𝗥𝗘 ✦✧


𝗕𝘆 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆


𝐂𝐡𝐚𝐩𝐭𝐞𝐫 -5


KAREEM POV.

After ya mika masa tsarabar Noor ya bude motar ya shiga sai Nabil ya rage tsawonsa yana bashi hakuri.

“Ranka ya dade dan Allah ka yi hakuri, Wallahi ba zan sake bijirewa umarninka ba, kuma idan wani abun marar dadi Noor ta yi maka da ya saka ya kanye wannan hukuncin dan Allah ka yi hakuri”

Kareem ya kirga 10k ya mike masa.

“Noor bata min komai ba, kuma a yanzu ina jin hakan da na yi yayi daidai domin be kamata na baka umarni ka saba ba, ba wai na koreka ba ne noo zaka zauna ne a gida har Monday”

“Toh ranka ya dade”

Har Kareem yaja gambo zai rufe motar sai kuma ya kalli Nabil

“Shekarar kanwarka nawa?”

“Wannan watan zata yi 15”

‘Fresh one, shiyasa kanta be tsaya ba, tashen balaga take’

Ya fada a ransa a zahiri kuma sai ya sake tambayar Nabil.

“Kai kuma fa?”

“19 ranka ya dade”

“Okay, amman tana karatu?”

“Bata karatu gaskiya, bata son makaranta”

“Why?”

“Haka nan kawai bata son karatun, kanwarta da kusan suke tawaye tana karatu sosai amman ita bata son makaranta”

“Kuma aka zuba mata ido? Baku tsoron future dinta ya lalace?”

“Toh ya za'ayi ranka ya dade ai ka ga yadda take, Baba ne kawai zai iya da ita shi kuma karatun ba damuwarsa yayi ba”

“Allah ya kyauta”

“Ameen mun gode”

Ya rufe motar ya juya, ya fice daga unguwar. Ba gida ya nufa kai tsaye ba restaurant dinsa ya sake komawa a gurin yayi sallah La'asar yana fitowa Masallacin abokinsa Hafiz na fakawa kusa da motarsa, Kareem ya karasa gurinsa ya mika masa hannu suka gaisa.

“Dazun na ga motarka, na so mu yi magana amman ban san fitarka ba”

Kareem yayi murmushi tunawa da Noor.

“Wata bakuwa na yi mai kiriniya ita ta saka ni zuwa nan kuma na kaita gida”

“Bakuwa?”

Hafiz ya tambaya domin be taba jin abokinsa yayi zancen wata mace ba bayan Safeena da matarsa, ko siblings dinsa iyakarsa da su gaisuwa, sai kuma fada idan sun yi ba daidai ba.

“Yeah wani yaro na ne, da yake aiki nan ya zo duba ni sai ya zo da kanwarsa to kanwarsa ce rikitacciya”

Yana maganar yana murmushi maganarsa da ita yake tunawa a lokacin da take fada masa abincin restaurant dinsa yayi tsada.

“Kuma ka kawo ta nan ka kaita gida? Ko dai...”

Kareem yayi hanzarin katse shi yana girgiza kai

“Noo kai yarinya ce irin fresh yaran nan yanzu take girma, kuma ni bayan Safeena babu kowa a raina”

Hafiz yaja tsaki jin ya ambaci sunan matar da ya fi tsana a duniya fiye da kowa, matar da ta sauya dabi'u da mu'amalar amininsa zuwa wani dabam da ba shi ba.

“Ya jikinka?”

“Alhamdullahi na ji sauki sosai”

“Amman baka shiga aiki ba yau, domin na shiga ban same ka ba, na tambaya aka ce baka shigo ba”

“Na shiga da yamman nan na kai Noor na mata treatment”

“Wace Noor me ya faru?”

“Yarinyar da nake baka labari yanzu ita ce Noor, Yusura ce ta buga mata abu akai kan ya fashe jini ya zuba shi ne a kaita asibiti”

Da mamaki Hafiz yake kallon abokin nasa.

“Yusura ta fasa mata kai kace fa? How?”

Kareem ya dan tabe baki yana jingina da motar Hafiz.

“Yusura tace wai ta fada mata magana ne, amman ita yarinyar tace Yusura kishinta take saboda ta ga kyakkyawar budurwa”

Yana maganar yana dariya, Hafiz ma yayi dariya.

“And she got lucky ka kaita asibiti”

“Daman wa zai kaita asibiti ba ni ba, matata fa ta fasa mata kai, a asibitin ma tambayoyi take min har da na banza wai ance ina zubar da ciki”

Hafiz ya tintsire da dariya.

“Kirikiri?”

“Wallahi a gida ma haka ta gama ba ni labari wai restaurant dina yana da tsadar abinci, amman bata san ni ne mai restaurant din ba sai daga baya”

“Zan so ganin yarinyar nan”

“You better not babu ruwanta take zata fara maka maganar da ta zo bakinta, kuma ka san kai ba irina ba ne zaka iya fusata, amman labarin cikin nan ya ba ni mamaki”

“Kareem kenan, ka yi kaurin suna kowa ya san kwarewarka akan iya aiki da daukar komai babu wasa, so dole makiya za su nemi hanyar da za su yada wani abun kyama game da kai”

“Toh ai ni taimako kawai nake, bana cirewa sai wanda na san akwai matsala, amman masu cikin shige ni bana zubarwa”

“Duk yadda zaka yi ba zaka gujewa mutane ba, wata ma cikin banza zata dauko ta zo tace maka mai matsala ne ka burke mata ta zubar”

“Aa sai na yi bincike nake yi ai, ni ba shashasha ba ne irin Noor”

Hafiz da sai a lokacin ya rufe motarsa ya kalli Kareem.

“Muje ka bani labarin yarinyar nan there is something special about her...”

Kareem ya jera da abokinsa suna tafiya ya zuba hannayensa duka biyu aljihu. Har suka isa office labarin abun da Noor ta yi masa yake ma Hafiz, and Hafiz was so excited domin ya dade yana jiran irin wannan labarin daga gurin abokinsa.

“Amman be dace mahaifi ya furtawa yarsa haka ba, ko da daga ita sai shi ne balle kuma har a gaban wani”

Hafiz ya fada bayan ya zauna. Kareem ya daga kafadunsa.

“Ni ma shi na gani, irin haka ke sa yaro ya lalace, ni ma ban jidadi ba balle kuma ita, amman tace min ita ai ta saba, duk sai ta ba ni tausayi Wallahi, gata karamar yarinya she's just 14 no 15 this month”

“Kasan fa wasu iyayen idan talauci ya halbo su ido rufewa yake”

“Baka da kirki Barrister amman fa akwai alamar haka, domin daga ganin gidan nan da unguwar ma ka san suna fama da talauci ko'ina kwata”

Ya fada yana ciro wayarsa dake ringing ya duba, ganin sunan Safeena ya saka shi dan shakkun dagawa a gaban Hafiz domin ya san ba karamin abu ba ne su yi fada saboda kiran, but babu yadda zai yi dole ya daga domin ba zai tana iya rejecting kiran Safeena ba kuma ba zai ga kiranta ya kasa dagawa ba.

“Hello...”

“Kareem guess what?”

Safeena ta fada daga dayan bangaren.

“Ina guest's House dinka”

“Safeena i thought mun yi magana idan mijinki yana nan ba zamu ga juna ba? Dazun nan ma ba mun yi maganar nan ba?”

“Na kasa rike kaina ne, kuma i have surprised for you shiyasa na zo, kawai magana za mu yi”

“Shi ke nan gani nan zuwa”

Ya amsa da kamar yanayin damuwa, sannan ya sauke wayar.

“Yanzu baka ko jin kunya barina zaka yi a nan ka tafi ka gurinta”

Cewar Hafiz cike da takaici. Kareem yayi murmushi.

“Kamar baka san tsakanina da Safeena ba? Tana son ganina and i can't say No”

“Ka ji tsoron Allah Kareem, kana mu'alama da matar aure macen har da yayanta hakkin ai sai ya maka yawa”

“Shiyasa na ce idan mijinta yana gari ba zamu rika ganin juna ba”

“Yanzu idan wani ya kwanta da matarka ya zaka ji? Amman kai kana yi ma matar wani?”

“If wani ya aikata matata haka, kashe shi zan yi, ba zan iya jurar komai ba, ko da kuwa Yusura ce da bana so balle ace wadda nake so”

“Amman kake aikatawa matar wani? Idan kuka mutum a wannan halin kace me? Waya sani ma ko ita ma tana tare da Ex dinta”

“Ex dinta yana can kasar waje, ba dan an cilasta mata aurena ba, da yanzu tana can tare da shi suna rayuwa ni ma da yanzu da Safeena nake rayuwa, amman ya zamu yi kaddarar mu ta zo a haka”

“Ka yi sabon Allah kace kaddararka ce a haka? Kareem ka raina wayon mutane Wallahi”

Kareem ya busar da iskar bakinsa.

“Wai da duk wannan abun why not ta kashe auren ka aureta?”

Kareem ya girgiza kai da sauri saying no to Hafiz question.

“Har abada, ba zan iya aurenta ba, idan ta fito gidan mijinta wa zai rike mata yayanta? Ni dai yadda nake da kishin nan kasan ba zan iya rike yayan wani ba, kuma...”

Yayi shiru.

“Kuma me? Ba zaka aureta ba saboda kana jin ba da kai kadai take tare ba?”

“Da ni kadai take tare a yanzu na sani, amman daga lokacin da zan aureta ba ni da wannan tabbacin, what after na aureta ta koma tana mu'amala da tsohon mijinta kuma? Ko wani? Daga lokacin da na fara kaiwa jikin Safeena sai aka tsinke igiyar aminci a tsakanina da ita, for now na san ni kadai ne, amman idan na aureta ba zan samu aminci ba”

“Kenan haka zamu yi ta zama har bada?”

“Not har a bada, ina fatar canjin”

“A hakan?”

Hafiz ya tambaya yana masa wani kallo. Kareem yayi dariya grabbing his phone ya mike tsaye ya fice daga office din.

“Allah ka tsare mana imaninmu ka tsare mu da auren mata irin Safeena”

Ya fada yana juyawa ya bi kofar office din da kallo. Kareem na shiga motarsa ya dauki hanyar gidansa da ya gina da kansa saboda Safeena da kuma irin tsarin da take so, sai dai kaddarar rayuwa bata ba su damar zama ma'aurata ba, sai suka zama ma'aikatan aikata zunubi. Yana yin horn mai gadi ya bude masa gate sai ya shiga ya faka motarsa, yana ganin motarta ya tabbatar tana gidan kamar yadda ta fada masa. Ya bude motar ya fito ya nufi kofar falon ya saka key ya murda ta bude ya shiga. Yanayin arba da ita sai murmushi ya baibaiye fuskarsa ta taso da sauri tana kamshi turare mai karfi ta rumgume shi.

“I miss you so much”

Ta fada tana shafa fuskarsa, bakinta ya sumbanta ya rike bayanta.

“I miss you too, kwana biyun nan da baki kusa kamar na yi hauka”

Ta yi dariyar jindadi.

“Ba ga matarka ba?”

“Matata ai kin san once in a month ne, amman ke kullum ne, kin san yadda nake sonki ai”

Ta sake yin murmushi ya kai bakinsa cikin nata, sun dauki lokaci a haka kamin ya cire bakinsa.

“Yau kam ba zamu wuce nan ba, Safeena ina son ki rika jin maganata, na fada miki idan mijinki yana nan ba zamu rika haduwa ba”

“Na sani, yanzu kawai na zo maka da abun mamaki ne kuma abun Farinciki”

“Surprised din me ne?”

Ya tambaya yana kokarin raba jikinsa da nata, sai ta yi baya ta nufi jakarta ta bude ta dauko abu sannan ta boye a bayanta.

“Rufe idonka”

Ya rufe idon yana murmushi har sai da ya ji matsowarta kusa da shi ta ce ya bude

Please Login or Register in order to submit comment