google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Downloaded From https://tknovels.com.ng 
MASARAUTAR MU!.





3








SUMAYYAH ABDULKADIR
takorikabara@gmail.com
babbangoro2015@yahoo.com

SADAUKARWA
Ga 'yar uwar da muka rasa a TAKORITES. Allah ya jikan ki da rahma HASNA'U yasa aljannah ce makomar ki. Ya bamu guzurin tadda ke. Takorites bazamu taba mantawa da ke ba. Da zaman amincin da muka yi tare.Muna son ki Hasna.


JINJINA
Har kullum jinjinar taku ce dukkan members na TAKORI'S ONLINE FORUM whtspp, littafin MASARAUTAR MU jinjina ne a gare ku, nagode da kauna da kwarin gwiwa, ni da ku hadin Allah ne. Allah ya bar mana zumunci har gidan aljannah.

GARGADI
Ban yarda a karanta wannan littafi a kowacce kafa ta sadarwa ba batare da iznina ba, tun daga radio, youtube, facebook, whtsp idan har ban yi izni ba, yin hakan karya doka ne kuma abin tuhuma ne daga lawyer na Barrister Sadiq Rufa'i Wali.

MASARAUTAR MU 3
Cikin raunin murya marar amo da rashin karsashi kamar ta wanda ya sha duka sabida yadda tayi kasa sosai, Yarima Sageer ya duka gaban mahaifin sa Askirama tamkar zai shige cikin sa, ya soma magana cikin sanyin murya da hardewar harshe.
Allah Kawun jo (Allah ya baka yawan rai) amma me ya sa tun lokacin da na dawo daga Amsterdam din, na kuma zo da bukatar auren Sultana baa tambayi raayi na a kan Saadatun ba? Allah ya ja da ran ku da a ce kun bayyana min kudirin ku akan mu tun farko, tun a wancan lokacin, a kan zabin da ku ka yi min, zan hakura ne da nawa zabin duk son da nake masa in karbi zabin ku. Saboda na san duk wani hukunci da za ku yi a kaina alkhairi ne wanda ni duk yawan shekaru na ba zan taba iya hangowa kaina ba!!!.
Sai hawaye suka fito sharr! Daga idanun Yareema Sageer, wadanda a yanzu Askirama ya tabbatar na farin-ciki ne ba na komai ba; hawayen wani irin contentment da Dr. Sageer bai taba ji a rayuwarsa ba.
Sai ya ji rayuwarsa a yau ta cika, ta zama cikakkiya, duk wani gibi dake cikin ta ya cika, amma a baya incomplete yake jin ta somehow shattered. duk da tarin dimbin achievements din da ke cikin ta. kamar akwai wani wawakeken gurbi a can kasan zuciyar sa da a da can, yake jira a cike, gurbin da bai san ko na menene, ko kuma na wanene ba, ya samu aka cike masashi yau unexpectedly. A yanzu ya gane cewa ya jima yana jiran shigowar Sa’adatu cikin rayuwar sa, he'spatiently waiting for her to come to his life ba tare da ya sani ba, sai a yau ya gane hakan.
A can baya kafin zuwan wannan ranar jin sa yake tamkar bashi da komai tamkar bai taba mallakar komai a rayuwar sa ba, duk da ba abinda bai mallaka din ba a rayuwar tasa including ASIAN WIFE.
Amma a yanzu da yake durkushe gaban Mai Askira yana yi masa wannan bushara sai yaji tamkar Askirama ya mallaka masa dukkan mulkin matan duniya, da mulkin dake cikin duniyar, mulkin da ya fi na garin Askira girma da ilahirin El-Kanem Borno Empire, da duk wani nau'in farin cikin dake cikin duniya da dan adam ke burin samu da ya mallaka masa Saadatu diyar Bilkisu da Mallam Hashimu.

Na gode da wannan gatan Mai Askira, Nagode ZAKIN Askira, ina mai rokon Ubangiji da ya fi ni godewa, na kuma karba da hannu bibbiyu. Ina rokon Allah Ya sa daga yau ba za ku sake jin wani abu a kaina wanda ya jibinci laifuffukana na baya ba.
Hakika na sani Askirama ni Sageer mai yawan laifi ne, mai saba muku ne, mai ketare tarbiyyar da kuka yi masa, amma hakan bai sa kun yi fushi da ni ba, kullum burin ku da fatan ku shine in dawo hanya madaidaiciya, wanda hakan yasa a kullum nake cikin tuba da neman gafarar Ubangiji. Ina rokon Allah ya fidda ni kunyar ku, Ya ba ni ikon rike muku yar ku da amana.
A yi min godiya wurin Fulanin Sarki (yana nufin Fulani Bilkisu), kodayake bari in je in same ta da kaina.
Askirama sai gani ya yi Yarima Sageer ya mike cikin wata irin azama, jikin sa har bari yake, gabadaya ya zama ba cikin nutsuwar sa ba, ya rude saboda excitement din da ya samu kan sa a ciki. Wanda Mai Askira zai iya rantsewa bai taba ganin sa cikin kwatankwacin irin wannan farin-cikin ba.
Sai Askirama ya mika hannu ya kamo hannun sa, kada ya je ya yi abun kunya a gaban bayi da kuyangin Fulani Bilkisu, kuma dai Fulanin ta gaya masa Saade ta dau fushi tun jiya ta kulle kanta a daki. Wanda ke nuna ita bata murna da auren ko kadan. Kamar yadda nasa dan ke neman shidewa sabida farin-cikin hakan.
Zo zauna in kirawo Fulanin ka yi mata godiyar nan a gabana, kada ka je sassan ta yanzu har sai bayan biki. Baa zuwa. Zuwa lokacin Saadatu ta huce daga laifin da muka taru muka yi mata.
Yareema ya yi murmushi yana sosa kai, laifi? Auren sa ne ya zamo laifi ga Saade? Kodayake bai kamata hakan ya zamo abin mamaki ba a gare shi duba da cewa daga shi har ita respect ne a tsakanin su, babu wata magana bayan wannan, koda ace akwai din ita a gareta babu komai tunda bai taba furta mata ba, ko nuna wata alama da zata gane cewa he sincerely admires her tun farkon rayuwar ta a gidan sa.
A lokacin suka hada ido da mahaifin sa wanda ya kura masa ido kawai yana murmushi, yana karanto duk abinda yake son karanta. Yareema Sageer yayi hanzarin dawowa daga duniyar tunanin da ya fada cikin jin nauyin kaifafan idanun Askirama. Kada dai ya zamanto cewa Mai Askira ya gane a rude yake gabadayan sa? Kuma already a rijiya yake? A rayuwar shi babu farin cikin da ya taba ruda shi irin na yau, kai mawuyaci ne wani abu yasa ya kasa mallakar kan sa amma yau? Saadatu a matsayin matar sa! Wani al'amari ne da bai zata ba. It comes abruptly. And it touches him more than he can imagine. Wani abu ne da bai taba kawowa zai samu da sauki haka ba, duk da zuciyar sa ta dade tana buri, kwakwalwar sa na kiyasta masa, ruhin sa na kwadayi da mafarkin kasancewar hakan.
Ba don bashi da gatan samun ta ba, sai don yana ganin hes not worth enough ga mallakar ta matsayin mata, in yayi laakari da tarin aibubbukan sa.

Maimartaba ya kira Fulani ta wayar hannun sa, suka yi magana ya aje, ya dubi Yarima wanda jikin sa ke ta (tsuma) ya kasa nutsuwa a waje daya, ya zama very upset, bai taba ganin dan sa Sageer cikin kwatankwacin irin wannan halin ba.. daga haihuwar sa har girman sa. Wanda ke nufin....(already Sageer na son Sa'adatu)!!!

Ba abin da ya furta a zuciyar sa sai godiya ga Ubangijin talikai, ya ce da Sageer a hankali cikin muryar sa ta girma da sanyawa dan adam nutsuwa, yana murmushin kasaita irin nasa ta kyakkyawan gashin bakin sa da farin gemu ya zagaye;

Be a Prince!". (Wato ya koma Yariman sa).
Yareema ya dafe goshin sa yana yar dariya da jerarrun hakoran sa bakidaya a waje, wannan ma wani abu ne da Mai Askira bai taba gani ba, iyakacin sa murmushi ga duk abinda yayi impressing din sa, sannan ya kuma koma cikakken Yariman sa ta hanyar kokarin sarrafa kan sa da komawa cikin nutsuwar sa.
Sai ga sallamar Sarauniya Fulani Bilkisun Askirama cikin kwalliyar ta ta kasaita, ta shigo ta kofar da suka saba shigowa bangaren Askirama ita da sauran matan sa, kowacce akwai kofar da ta bulla unguwar ta, zuwa turakan Mai Askira. Takun ta kadai abin kallo ne ga mijin ta.

Yarima na ganin shigowar ta ya dukar da kai kamar tsohon da ya yi wa sarki karya. Surukuta sosai yake nunawa yau ga Bilkisu. Bai taba jin kunyar ta matsananciya ba irin yau. Kafin zuwan wannan ranar, jin ta yake kamar Yayar sa Yaa Maira, ba matar mahaifin sa ba.
Alal hakika yana son matar nan ba tun yau ba, sau-tari, mantawa yake kishiyar Ya Gumsu ce sabida kirkin ta, mantawa yake da duk wani sabani da ke tsakanin ta da mahaifiyar sa sabida son da yake mata da kulawar da itama take bashi. Ashe Allah ya rubuta Kakar yayan sa ce masu zuwa nan gaba cikin kudurar Ubangiji.
Jinin su ne zai zo ya cakude wuri guda ya kara binding din su together. A can gaba. Ya kara dunkule su matsayin iyalin Sarki Yusufu Mai Askira. Ya kara nutsuwa a wurin da yake tankwashe zaman Rakuma akan kafafun sa, sannan ya gaishe ta da sassanyar murya, bayan ta zauna kusa da Mai Askira tana zolayar sa.
Ango! Ango ka sha kamshi.
In ji Fulani cikin murmushi.
Maimartaba ya juya gare ta yana tambayar ta,
“Fulanin Askira Me ku ke shiryawa ne game da biki?
Fulani Bilkisu ta gyara zama,sannan ta kaskanta murya cikin yanayin ladabin da Askirama kadai take yiwa magana da shi ta ce.
Alanguburo, ai ni rabon da in ga Saade tun jiya da na gaya mata. Ta shige daka ta kulle kofarta, watakila idan ta ji mutanen Tsanyawa sun zo ta bude, kuma dai dama bukukuwan gidan nan Ya Gumsu ce ta ke tsara su ga shi kuma tana fushi da ni a kan laifin da babu ruwa na.
Maimartaba ya ce, Zan turo Yaa Maira (babbar yarsa) ku tsara komai, Murjanatu ma tana kan hanya za su zo su same ki. Wannan kiran kuma na Yarima ne ba nawa ba, shi yake son ganinki, zai bi ki unguwarki na ce ya bari in kirawo ki nan, na ga yana ta bare-baren jiki kada ya je ya yi abin kunya a gaban bayi.
Dariya Fulani ta yi, shi kuma Yarima ya kara dukar da kai, murya a raunane ya ce.

Fulanin Maimartaba, Allah ya baki yawan rai, na gode. Allah ya jikan magabata, insha Allahu ba zan ba ku kunya ba. Na karbi auren Saadatu da hannu bibbiyu. Allah ya ba ni ikon yin adalci a tsakaninsu.
Sosai Fulani ta ji dadin kalaman Yarima Sageer, suka wanke damuwarta kaso hamsin cikin dari na tunanin Yarimazai wulakanta mata Saade tunda yar talaka ce kuma yana da mata Baturiya, damuwar hakanta ragu daga ranta, don ba ta zaci haka zai karbi maganar ba with due respect, tunda uwar shi ma ba ta so. Ta ce,
Da kai da Saade duk daya ne a wurina Yarima, kamar yadda Askirama bai taba bambantata da ku yayan da ya haifa ba. Rokona daya gare ka Yarima ina so ka raba musu gida, sabida Saade ba za ta iya zama waje daya da Aisha - Sultana ba, shekarun su, tunanin su, akidunsu da halayyar su ba zai taba zuwa daya ba. Ka ga kuwa zama da juna zai musu wahala.
Ya saci kallon Askirama ta kasan idanun sa,sabida tsoron ko ya ji abin da Baggarar matar san nan ta ke fadi? Sai ya ga hankalin shi ba ya kan su sam, waya yake yi ma da yar sa Yaa Maira lokacin, wadda ke aure a masarautar Biu. Tana gaya masa cewa sun taso suna hanya har sun wuce Maiduguri.
Wani sigh of relief Yarima ya sauke da ya fahimci Askirama bai ji ta ba. A ran sa fadi ya ke na tabbata sanda aka yi miki aure da Baban Saade baki yi girman ta ba kuma kin haifeta lafiya. A fili kuma ya ce,
Insha Allah zan nema mata nata muhallin, daya bukatar kuma zan duba insha Allahu ran ki ya dade. Ai ba abinda zai gagara.
Da wannan ya yi musu sallama ya mike zai fita. Sai Askirama ya sake yafito shi.
Be a man also, after being a Prince (ka zama namiji bayan zama Yarima) wanda ba mai iya juya raayin sa, wanda ya san cewa mata da karkataccen haqarqari aka halicce su tunanin su ba kamar na maza bane, ka san yadda za ka lallaba mahaifiyarka har ta sauko daga dokin fushinta, ta karbi Saadatu matsayin diyar ta, ta sanyawa auren ku albarka. Tashi ka je ku tsara komai kai da Awaisu. Allah ya yi wa rayuwarku ku duka albarka.

*****

Yaa Maira ta iso daga masarautar Biu kamar yadda mahaifinta ya kira ta don ta zo su yi shirye-shiryen bikin dan uwansu. Haka Murjanatu ta taso dagaIstanbul tun jiya ta sauka Abuja. Zata biyo connecting flight zuwa Maiduguri yau.
Kamar yadda Maimartaba ya yi mata umarni cewa, idan ta iso kafin ta shiga koina ta fara ganinsa tukunna. Yaa Maira, ta bi wannan umarnin na mahaifin ta, ta yi saa babu kowa tare da Mai Askira lokacin da ta shiga falon ganawarsa da iyalinsa.
Ta same shi yana cin abinci. Ita dai ta ji an daura wa kanin ta Yareema aure, amma ba ta san da wa Askirama ya daura ba. Yanzu da ta ke durkushe a gabansa suna magana ta Da da mahaifi, bayan ya kare cin abincin sa sun gaisa, ta fahimci ko wace ce Maimartaba ya zaba wa kanin ta Yareema Sageer. Ba kowa bace face Saadatun Fulani Bilkisu!!!
Yaa Maira, wadda sunan ta na sarauta kenan, tana da wata baiwa ta daban kamar yadda na fada a baya ta sunsunar kaddara. Tun ganinta da Saadatu na farko jikinta ya ba ta wannan yarinyar will some day become part of them, za kuma ta zamo wani jigo a rayuwarsu. Zubin halitta da komai nata na Fulani Bilkisu ne, Bilkisun da ke juya zuciyar Maimartaba a halin yanzu. Bilkisun da babu tauraruwa mai hasken ta a idanun Mai Askira. Sai ba ta yi mamaki ba ko kadan da wannan zabin na mahaifin su domin BAGGARA matan manya ne. Abu daya ta ke so ta tantance yanzu shi ne hakikanin alakar dake tsakanin Bilkisu da Saadatu.
Mai Askira sai bai boye mata ba, ya gaya mata hakikanin alakar da ta hada Bilkisu da Saadatu.

Yar ta ce ta cikin ta!

Mamaki, alajabi da tuajjibi kamar ya zauta Yaa Maira, kodayake dama ta dade tana kiyasta hakan, kawai sai ta ji ta karbi Saade da dukkan zuciyar ta matsayin suruka. Duk da aibanta ta da Humaira ke yi duk sanda suka taru bata taba fadin wani mugun hali a tare da ita ba, in ka fahimci duka kushen Humaira akan Saade to kishi ne na son da Askirama ke mata da daidaita musu matsayi da yake yi lokacin suna makaranta. Sai ko taya uwar ta Yaa Hibbani kishi da Fulani Bilkisu. Sai kuma kyawun Saaden da take cewa irin na shegu ne.
Ita ta sani uwar Saade mai nagarta ce, cikin matan gidan kaf babu mai kirkin ta, saidai kishi ya hana aga hakan a kare da fadin aibun ta. Maimartaba ya sa mata albarka domin ta ce ta karbi amanar Saadatu a dakin su, ita ce uwardakinta daga yau, za kuma ta yi duk irin kokarin da za ta iya wajen ganin cewa mahaifiyarsu (Ya Gumsu) ta sauko ta sanya wa alamarin albarka.
Da wannan ta bar falon Askirama zuwa unguwar Ya Gumsu. Tana tafe tana saka irin lallashin da zata yi mata.
*****

Yaa Gumsu ta yi mamakin ganin Yaa Maira a daidai wannan lokacin, don dai ita da kanta ba ta gaya ko dayan su zancen auren Yarima da Saade ba saboda tsananin kiyayyarta ga auren. Yaa Maira ta kwaso gabadaya yayanta maza da mata sun taho, kallo daya ta yi wa Ya Gumsu, ta tabbatar da abin da Askirama ya gaya mata na cewa tana matukar adawa da auren, ba kuma don komai ba sai don kishinta da Fulani Bilkisu.

Ya Gumsu hakimce cikin royal chair ta babban falon ta, kuyangi na yi mata firfita da maficin gashin dawisu. Wasu na tausa mata kafafu, wasu na zubo kirari amma duka basu ishe ta kallo ba sai kumburi take kamar zata fashe. Ta daga ido tana kallon Yaa Maira da ke warware lafiyayyar laffayar jikinta don ta ji dadin hutawa, sun sha zaman mota daga Biu zuwa Askira. Take gayawa Yaa Gumsu. Ya Gumsu ta harare ta sosai, sannan a hassale ta ce.
To da ki ka kwaso bataliyar yayanki ku ka zo kuka cika min gida me ku ka zo yi? Wa ya gayyato ku? Na ayya gayyar sodi?”
Dariya Yaa Maira ta yi, ta ce,
Allah ya taimaki Gumsun Gari, mu ai ba sai an gayyace mu ba. Su Murjanatu ma duk suna hanya.
Ya Gumsu ta kara shaka sosai, amma ta ja bakinta ta yi shiru sabida kuyangin da ke zazzaune wasu a tsaitsaye, zuciyar ta na tafasa. Ta kara ganewa Mai Askira bai dauki auren nan da ya daura da sauki ba tunda har da kan sa yake gayyatar yayan sa abinda bai taba yi ba. Allah kadai yasan iya gayyatar da yayi da irin hamshaqan sarakunan da ya gayyato akan auren nan. Bata kara magana ba sabida kunar zuci. Kallo daya Yaa Maira ta yi wa kuyangin da ke wurin duk suka mike suka bar falon, suna masu yi mata kirari irin wanda suke yi wa diyan Ya Gumsu.
A tashi lafiya Yaa Mairar gida,
A gana lafiya uwar marayun Askira,
A fito lafiya cikin alheri Yaa Maira uwar diyan Yaa Gumsun Askira bakidaya..

Daidai kafafun ta Yaa Maira ta zauna suke kara gaisawa a nitse, gaisuwa irin ta Da da mahaifi, Yaa Gumsu na kokarin hadiye fushin ta, yaran duk sun bazama cikin gida, kowa ya tafi wurin saanninsa yadda suka saba in sun zo gidan. Yaa Maira ta ce da mahaifiyar ta cikin sanyin murya.
Sai muka ji abin alheri Yaa Gumsu, da ma zaman Yarima da mace daya ai ba yi ba ne, Yarima fa, Yariman Askira Mai jiran gado! Balle wadda ba ta fito daga jinsinmu ba balle addinin mu.
Na yi farin ciki kwarai da gaske don dama ni auren nan na farko na Yarima bai kwanta min ba ko kadan, babu wani biki na alaadunmu da muka yi sabida abin kunya ne ma mu fito mu fadi ga wadda ya aura a cikin masarautun da ke zagaye da mu.
Sai kuma ku yo gayya a auren shegiya mara asali? Tukunna ma kin san da wa ya daura masa auren da kike wannan giringidishin?
Subhanallah, Yaa Gumsu tofar da miyan bakinki tun kafin malaiku su rubuta. Saadatu ba shegiya ba ce, diyar Bilkisu ce ta cikinta
Tayi aure ta haife ta da mijin ta na fari kafin ta auri Askirama..!.
A razane Yaa Gumsu ta dago ta dubi diyar ta Yaa Maira. Sai Yaa Maira ta yi amfani da wannan damar data samu wajen luguiguita zuciyar ta.
Tiryan-tiryan ta soma bai wa Ya Gumsu labarin Bilkisu da yadda ta haifi Saade, sak yadda mahaifin su ya bata labari, ta kare da labarta mata Bilkisu ta boye musu Saade yarta ce sabida ba ta son gori musamman daga ita Yaa Gumsu in ta ji cewa ba a budurwa Mai Askira ya aure ta ba ta kade har ganyen ta da gori. Karshen maganar da Ya Maira ta fada shi ya kara sanyayar da jikin Ya Gumsu.
Dangin mahaifinta na hanya, wan mahaifinta uwa daya uba daya Alhaji Kyari Babagana, na tabbata kin san wannan sunan, don kuwa shi ne yake bai wa Bulama fatun da yake kai wa kasar Italiya. (Bulama kani ne ga ya Gumsu, wanda suke sanaa daya da Alhaji Kyari). Ita ma Ya Maira Askirama ne ya gaya mata hakan. A binciken da yasa aka yi masa akan asalin mahaifin Saade.
Ya Gumsu da ke ba ta son nuna karayarta, sai ta hau mitar rashin dalili.

Ban da munafurci me ye na boye mana cewa yarta ce? Ina ruwanmu don ta taba aure? Gori yana tsiro a goshi ne? Duk wata harka ta kishiya sai kin samu dunkulallen munafurci a ciki. Ashe ma a bazawara ta zo shi ne ta bi ta juye kan tsoho, kinibabbiya, haba! Ni fa in ce wannan so da Askirama ke wa yarinyar nan da walakin, ashe agola diyar mowa ce, to muna jira mu ga wan baban yarinyar da idanunmu don mu tabbatar ba shegiyar bace.
Kuma shi Yareema shi ke nan ba zai auri yar sarauta ba, auren misali sai dai ya gani a wurin tsararrakin sa? Alhalin ba gata aka fi shi ba? Daga jinsin yahudawa da masu kanan ido sai jinin talakka agola a matsayinsa na Yarima mai jiran gadon Askira?
Ya Maira ta yi kasa da murya ta ce.
Yaa Gumsu, gara talaka, agola tushen musulunci tashin musulunci a kan tubabben da aka ce daga kwalba ta ke yi a bar, sallar ma ta daina. Ki gode wa rahmar Allah Ya Gumsu alheri Askirama ke nufinmu da shi. Yariman ai ba wankakke ba ne kin fi kowa sani. 'Yar Bilkisu aka cutada auren Yarima ba Yarima ba.
Ni tun ganina da yarinyar na farko na san za ta zame mana wani jigo cikin zuriar mu. Tana da charisma mai yawa. Tana da wisdom bayyananne. Allah ne bai taba kai hankali na kan Yarima ba, musamman da ya zo ya yi auren sa daga baya. Amma na yi zaton Ashgar zaa bai wa, sai dai lalurar sa ba za ta bari ya yi aure ba,
Jiki na ya dade da bani hakan cewa bazata wuce mazan gidan nan ba koda ba daga dakin nan ba.
Yaa Gumsu Ta kyabe baki tace Mairam ki fita ido na in rufe, na bi wisdom da gudu na tattake babu takalmi a

Please Login or Register in order to submit comment