You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
ko mutuwa ta yi ta dawo ba za ta manta mai ita ba. Tana tsaye jikin kofa, harde da hannayenta a kirji, yar gaye da ita kyakkyawa sai murmushi ta ke. Ta kara tsayi da haske, ta murje sumul fiye da sanin da Saade ta yi mata.
Idanun Saade suka bubbude gabadaya, ta saki dryer din hannunta kasa, kafin ta tafi da mugun gudu ta rungume RAHEEMAH.
Fulani ta shigo, a bayanta wata mata ce da akalla za ta girme ta. Kyakkyawa da ita, da ganinsu ka ga mazauna kasar sanyi, sai kannen Rahima su biyu Sarina da Jamila. Kallo daya Saade ta yi wa matar ta gane mahaifiyar Rahima ce sabida tsabar kamannin su, wadda Rahima kullum ke kira da “Mama”.
Ta saki Raheema ta tafi ga Mama za ta tsugunna, Mama ta yi saurin riko ta a jikinta, sannan ta rungume ta. Cewa ta ke,
Masha Allahu, yau ga ni ga Saar Raheema, Saadatu Saar Mata!
Ta kama su ita da Raheema ta rike a jikinta, Sarina da Jamila sai murmushi suke mata. Ta tafi gare su suka rungume juna don dai ita duk wani ahalin Raheema tana sonsa a kan dalilin da zuciyarta har yau ba ta sani ba.
Raheema shi ne ki ka gudu daga El-Kanemi babu ko sallama, babu notice? Na shiga damuwa Raheema, zaman makarantar ya fice min a ka saboda rashinki. Na dade kafin na saba da rashinki Raheema, nayi kewar ki yadda harshe na ba zai iya bayyanawa ba, don Allah kada ki sake tafiya ki barni Raheemah. Sai kuka.
Raheema tana share mata hawaye da tafukanta, ta ce, har yanzu kina nan da kukan wofin kin nan ko? Is o.k Saadatu. Im here now, da ni za a sha shagalin biki, ba zan tafi ba sai na raka ki dakinki.
Ni ma ba da son raina muka koma Italy ba, kuma ban samu damar dawowa El-Kanemi don in miki sallama ba. Ki yi hakuri.
Sannan ne suka zazzauna a kasa, iyayen na daga gefen gado suna kallon su withaffection.
Nan Fulani ta gaya wa Saade labarin da ya girgiza zuciyarta, cewa ita da Raheema yan uwa ne na jini, da mahaifinta da mahaifin Raheema uwarsu daya ubansu daya.
na dade da gane hakan ban dai gaya miki bane tuntuni, don in Baban Rahimah ya san ke ce ba zai bar ki hannu na ba.
Saade sai ta ji duk wata damuwar duniya ta yaye mata. Feeling din da mutum ke ji idan ya san cewa yana da dangi na jini kuma na halali. Lallai da ake cewa wani farin cikin ya fi gaban kuka, sai dariya.
Ta zama kamar wata karamar zararriya don murna. Ta rungume Raheema, ta saki ta rungume Sarina, ta saki ta kamo Jamila ta rasa inda za ta sa su don kauna, su kuma sai dariya suke mata, don sun riga ta jin labarin tun suna Italy.
Maimartaba ya kira Fulani a waya ya gaya mata ta sa a rako Saade da Rahima falon saukar bakinsa ta gaisa da Babanta, wato Alhaji Kyari Babagana. Tare da Fulani suka tafi har falon ganawa ta musamman da bakin Maimartaba Sarkin Askira.
Kallo daya ta yi mishi ta hango kamanninshi da mahaifin ta Malam Hashimu, saboda jini ba ya buya. Har kasan kafafunshi ta je ta zauna ta gaishe shi a ladabce. Shi kuma ban da kallonta da tasbihi ba abin da yake a fili, tamkar Bilkisu ta yi kaki ta tofar, ko kadan ba ta debo dan uwansa Hashimu ba ko da da kalar fata ne. Sai yanzu ya tuna kallon sanin da yayi mata a ganin sa na farko da ita a El-kanemi. Ashe fuskar Bilkisu ya hango cikin idanun ta.
Alhaji Kyari ya ce, Madallah da yata mai albarka, Allah ya sanya alkhairi da albarka cikin aurenki. Allah ya hada hankulanku, Ya bada zaman lafiya.
Ba ta iya ta amsa wannan adduar ba, saboda nauyin da ta yi mata a zuciya da kwakwalwa. Idan ta ce, ameen, Allah ya amsa adduar fa? Aurenta da Yarima ya zama tabbatacce ba mafarki ba kamar yadda ta ke kallonsa? Duk da Yareema Sageer ya tabbatar mata cewa, reality ne, ta hanyar da bata taba zato ba, kuma ba shi da alamun ja da baya daga hukuncin iyayensu?
Don haka ya rage nata ta cigaba da yaudarar kanta da kanta, da cewa mafarki ne.
Sun dade yana mata tambayoyi tana ba shi amsa a kan marigayi da rayuwarsu a Tsanyawa, karatun da ta ke yi a yanzu a NTNU da kuma burin ta na yanzu wato barin karatun ta zauna a gida.
Daga shi har Askirama suka hada baki wajen tambayarta,
Saboda mene za ki bar karatunki Saadatu?
Ko shi Yareeman ne ya ce ba ya so?
In ji Maimartaba, sounding worried da hukuncin Saaden, duk da ya san hakan mawuyaci ne a matsayin Yareema Sageer na malamin jamia cikakke ya ce ya hana matar sa karatu.
Saade ta bude baki a hankali kamar mai ciwon makogaro, ta ce,
Saboda na fi son in ci gaba da zama a Askira, bana son komawa Abuja Alanguburo.
Fulani ta ce, Babbar magana, mijinki yana wani gari ke kina wani gari, a dalilin me?
Maimartaba ya yi saurin cewa, Ya isa Fulani, Saadatu za ki zauna a gidan Yarima na Askira har ki kare hutunki? Inyaso daga baya sai mu raka ki Abuja da kanmu ni da Fulani ki koma makaranta, kin amince?
Askirama ya yi maganar cikin lallashina uba mai tsananin kulawa.
Kaunar da Mai Askira ke nuna mata da yawan alkhairinsa gare ta ya fi gaban ya yi hukunci ta ce, aah. Sauran zai kasance ne tsakaninta da Yarima, tunda shine bai ce shima baya son auren ba, yayi uwa ya yi makarbiya ya amshe auren, ita ta fada a ce ta yi rashin biyayya, da kyar in Fulani bata bubbuge mata baki in ta fada hakan a gaban Askirama ba, amma tsakaninta da Askirama babu jayayya.
A hankali ta gyada kai alamar ta amince, idonta kuma ya cicciko da kwalla. Amma ta yi kokarin maida su sabida Askirama. Ko yayan da ya haifa ba ta taba jin ya raka gidan miji ba ko ya je gidajen auren su. Amma ita ya ce shi da kansa zai kaita. What an honour! Wannan ba karamin girma ne da kulawa ya ba ta ba.
A wannan daren daga Raheema har Saade sai goshin asubahi suka kwanta. Labarin juna suke bai wa juna. Inda Raheema ita ma ta sanar da ita ta samu miji a Damaturu suna karatu tare a jamiar Heartfordshire, U.K. sunansa Usman Bello Jajere. (Jajere garin fulanin Damaturu ne suna da kyau farare ne kuma suna karatu sosai yan garuruwan Jajere da Kollere. Yan Jajere kan yiwa kan su kirari da Jajere garin jajaye in ka ga baki to bako ne), amma aure sai ta gama karatu, shi kuma ya dawo gida ya yi service.
Ba abin da Saade ta tuna a lokacin sai Saidu, da yanzu ita ma yaro dan makaranta kamarta za ta aura, ina ma ta bawa Saidu damar da yake nema tuntuni tana gwasale shi? Yanzu gashi girman kanta ya sa an dauki mijin wata an ba ta wanda a haihuwar kauyensu Tsanyawa ya haife ta. Allah kadai ya san irin farin cikin da Usman zai sa Raheema, ita kam yanzu sai dai ta je ta yi ta fama da yar giya
Wannan tunanin ya fiddo hawaye daga idon Saade, wanda Raheema ta nace sai ta ji dalilin saukarsu. Don bata ga dalili ba.
Saade ta tuna cewa, wannan Raheema ce, mai kaunarta da zuciya daya tun tana bakauyiyar ta, kuma yar uwar da ba ta da kamarta a yanzu. Babu wanda ya dace da sanin halin da zuciyar ta ke ciki a halin yanzu ya kuma fahimceta ya bata shawarar data dace kamar Rahimah.
Don haka Saade ta gyara zama, ta warwarewa Rahimah komai a kan rayuwarta gidan Yareema Sageer, da halin da matarsa ke ciki, irin kyautatawar da yake mata, girmansa da ta ke gani, har da labarin Said sai da ta bata. Amma ta rasa dalilin da ya sa ta kasa ce da Raheemah Aunty Sultana na yawan cewa Sageer yana neman mata. Maganar ta yi nauyi sosai a bakinta tunda ba ta taba gani da idonta ba, shaidar zina kuwa sai ka kwana a ciki in ba ka yi taka-tsan-tsan ba.
Ta gaya wa Raheema damuwarta shi ne ba ta taba jin wani abu a zuciyar ta a kan Yareema ba, bayan na kasancewarsa guardian dinta a Abuja. Ita a wurin ta Uncle Yarima Yayanta ne mai kula da alamuran karatun ta.
Rana daya ta ji labarin aurensu daga bakin Fulani bagatatan kamar saukar aradu, ita ta fi son in auren ne ma a aura mata Saidu ba za ta damu ba, shine tsaran auren ta daidai da rayuwar ta ta yar talaka. Amma ina zata kai YARIMAN ASKIRA???
Raheemah Kyari, ta yi wani irin lallausar murmushi. Ta kama hannayen Saade ta rike cikin nata.
“inda kowacce mace take kai mijin ta Saadatu! Ina ma ni ce ke Saade! Ki yarda ba tun yau ba cewa you are among the luckiest. Auren matured men shi ne aure, wadanda suka san ciwon kansu, ki rabu da samarin nan yan rawar kai ki kama mijinki da iyayen ki suka zaba miki kin ji? What is your own business da rayuwar matar sa?
Kuma tunda Fulani ta ce ya raba muku gida, kuma ya amince, ina ruwanki da matarsa? Wannan rayuwar su ce shi da ita bai shafe ki ba.”
Saade ta zumburo baki, Raheemah ba za ki gane ba. I have no feelings a kan Yareema Sageer, na dauka zaman auren sai da feelings din soyayya yake yiwuwa???
Raheema ta girgiza kai, ta ce, inji wa? Saadatu, ki gode wa Allah kawai, ki kuma hada da addua, ki roki Allah ya sanya miki soyayyar mijinki, kuma zabin iyayenki. Soyayya da kike ambato shirme ce, cike take da unbearable challenges, aure daban soyayya daban, sai kin yi auren soyayyar in gishiri ya sauka daga kan kaza za ki gane shayi ruwa ne.
Above all kin ce kina ganin girman Yareema, to magana ta kare. Along the way soyayyar za ta zo, irinki in ku ka tashi soyayyar ma mahaukaciya ku ke yi, kuma makauniya, tunda kin ce ba ki ga alamun shi yana kin auren ba.
Muryar Saade abin tausayi ta ce, Sai ma kin ji bakar maganar da ya gaya min da na ce ba zan koma Abuja ba zan gudu kauyenmu he was like (in yi ta gudu, in fi ruwa gudu, giya in shirya sha tare da matarsa) meaning bai dauki maganganun nawa da wani muhimmanci ba.
Raheema ta yi dariya sosai, ta ce.
I would like to see Yarima Sageer. Sister you are blessed for having him as a husband, ina son brave men, wadanda suka yarda da kansu, cika baki ko rikicin mace ba ya razana su su ja da baya a kan soyayyar su. Ni ma sai in ce,
Sai kin dawo, a gaida mutanen Tsanyawa.
Saade ta kai mata bugu ta goce tana mata dariya. Muryar ta abin tausayi tace.
Wato dai Raheema kema kina bayan in auri mai mata ko? Ta je bar ta dawo ta yi min dan karen duka?
Dariya sosai Raheema ta sake yi, ta ce, Tunda ki ka ce ga inda ya auro ta kuma ga asalinta me ye abun mamaki don ta sha giya? Su fa yadda muke shan soft drinks, haka suke shanta don baki taba fita ketare bane, canjin addininta ba zai sa ta iya dainawa farat daya ba, tunda dai ba shi yake sha ba shi kenan falillahil hamdu, ki yi mata addua Allah ya sa tana da rabon dainawa.
Sai kiran sallar asuba suka ji a kunnuwan su, dole suka mike don bada farali. Daga nan kuma suka kwanta, Hanne sai barcinta ta ke hankali kwance bisa katuwar katifa ita da danta Naziru.
*****
Washegari aka tashi da event na farko, wato sakun lalle. Masarautar ta cika ta batse da yan uwa da abokan arziki da baki da aka gayyato daga masarautu daban-daban, ga kuma alummar garin Askira wadanda ma ba a gayyata ba. Da ma in dai biki na gidan sarki ne ba sai an gayyace su ba, kwansu da kwarkwatarsu suke tahowa daga gidajensu zuwa gidan Sarki.
To balle auren Yareema Sageer kuma wanda Maimartaba da kanshi ya shelanta gayyatar ga kowa da ke Askira, bayan saukowa sallar jumaa a babban masallacin jumaa. Don haka ba a taba ganin taron bikin da ya hada jamaa irin na yau ba a masarautar gabadaya. Tun daga kan auren su Yaa Maira har zuwa kan na yar sarki ta karshe da aka aurar Najaatu.
An saka amarya a lalle lafiya, Raheema da Hanne da kanwar Raheema Sarina sune kawayen amarya. Washegari alhamis aka yi NIYA wato ranar yin royal snacks su nakiya, alkali, dubulan, bakilawa da sauransu daro-daro don raba wa mutane.
Ranar jumaa aka yi WUSHE-WUSHE. A babban filin dake cikin fada aka kira decorators suka tsara shi yayi kyau sosai. Wushe-wushe shine wuri daya da Yareema da Sa'ade Zasu hadu a duk tsawon bikin su, makada ne aka gaiyyato daban daban daga garuruwa daban-daban ciki har da HajjaGumsu da yaran ta da suka zo daga Maiduguri. Sai da aka taru ana kade-kade ango ya zo cikin manyan kaya da abokan shi karkashin rakiyar Awaisu Ibrahim Waziri da kuma sisters din shi mata su Mairam Murjanatu, Yaa Maira and co.zagaye da shi cikin laffaya mai hasken sararin samaniya suna rike da kaskon turaren wuta suna turara shi, makadan fada na biye da su,suna kide-kide da bushe-bushe suna wake Yarima da amarya Saadatu har su ka kai shi mazaunin da aka tanadar musu shi da Saadatun.
Abokanen shi kuma aka yi musu shimfidun kilishi na alfarma daga gefen sa, sannan su yan uwan shi mata su kuma suna zaune inda aka tanadar musu.
Sai aka cigaba da wasa da kide-kiden cikin zakuwar fitowar amarya, wanda yawanci sai an dan ja lokaci sosai kawai dan a ja wa ango rai, haka aladar bikin masarautar Askira ke gudana a kowanne bikin dan sarki.
Saade an shirya ta cikin laffaya an rufe ta ruf har kai. Sannan kawayen ta su Rahimah da Hanne sun saka ankon dongasho da su murjani sun rike kaskon turarukan wuta suka sako ta a tsakiya kamar yadda aka koyar dasu.Maman Rahimah da Innar Hanne na rike da ita cikin rakiyar kide-kide har aka kai ta aka zaunar a gefen Yarima Sageer, wanda a lokacin da Saade ta zauna a gefen sa sai da ya dauke numfashin sa na wucin-gadi. Kawayen ta kuma by her side akan shimfidundake kallon na abokan ango.
Daga nan sai aka cigaba da kide-kide da wasanni.Saade bata yarda sun hada ido da Yarima ba duk kokarin sa ga son faruwar hakan, bata ma bude fuskarta daga cikin laffaya ba, duk kokarin Yarima Sageer na son gano halin da kwayar idon ta ke ciki a wannan lokacin hakan bai yiwu ba.
Tana jin sanda Uncle Sageer da yan uwan sa mata da maza da abokai suka yi ta yi mataruwan liki. Har tsakar dare ana wannan shagalin kafin taron wushe-wushe ya tashi. Kuma Yarima bai samu damar ganin Saadeprivately ba har su Maman Rahimah suka kama ta suka koma cikin gida.
Ranar asabar kuma aka yi KELATUL wato aka wanke wa amarya gashi aka yarfa mata kitson bare-bari kanana-kanana sun kai guda dari uku. Da yammacin ranar kuma aka yi biji-ginata inda aka shimfida manyan tabarmi aka ajiye amarya a tsakiya ana kida ana wakoki irin na barebarin Askira. Bayan an yi mata kwalliyar masarauta.
Ranar lahadi aka yi kaulu na amarya da na ango da safe. Kaulu shi ne za a ajiye miyar yauki a gaban amarya bayan an mata kitso da kwalliya. Baaba suka goya amarya suka kai ta filin da ake yin kaulu. Yan uwan Yareema na ciki daya da na sauran dakunan suka dinga dibar wannan miyar yaukin suna shafa mata, sannan daya bayan daya suka zo suna ajiye mata kyaututtuka na bajinta haka sauran matan Maimartaba.
Da yammacin ranar aka yi dubdo, wato wunin biki a harshen Hausa. Biki ya yi biki ba ka jin komai a masarautar Askira sai kade-kade da bushe-bushen algaita. Duk wadannan events din da ake yi ango bai ga fuskar amarya ba, kuma Fulani Bilkisu ita ke da alhakin yin miskero, wato abincin da ake kai wa gidan amarya. Kuma ita ke ciyar da ango da amarya dadadan girke-girke masu kara lafiya da kuzari.
In ta girka sai kuyanginta su kai sassan Yareema su ci shi da Awaisu. Korafi kam Awaisu ya sha shi gurin Yareema, kan cewa shi fa bikin nan ya ishe shi hayaniya ta yi masa yawa. A ba shi amaryarshi kawai su kama hanya. Shi ba auren fari ba to wadannan aladun duk na menene?
Awaisu sai dai ya yi murmushi don ya gama gane Yareema Sageer ya karbi auren nan da hannu bibbiyu. Har fiye da auren sa da baturiyar sa mai kananan ido. Auren da yake kira na soyayya kuma babu ya shi. Abin da bai sani ba, kuma yake matukar son sani shi ne, da ma can Yareema yana son Saade ne ko sai da aka ce an aura masa ita ya fara son ta??
Sai da Baaba (kannen Maimartaba mata) da kannen Ya Gumsu suka shigo tafiya da amarya ne idonta ya karasa raina fata. Domin a baya kallon komai take matsayin almara ko mafarki. Saadatu ta kankame Fulani tana ihu sosai ita ba inda za ta je ta bar Fulani.
Sai yanzu ne ta tabbatar da gaske an yi mata aure, kuma ba da kowa ba da Yariman Askira, Uncle Yareeman da ta ke girmamawa fiye da kowa in ka dauke iyayenta, Dr. Sageer a NTNU, kuma mijin Aisha-Sultana.
A karshe Baaba sai goya amarya suka yi tana kuka tana komai, kannen Yareema mata su Houdda sai tsiya suke mata, ko irin nasihar nan ta uwa Fulani ba ta samu damar yi mata ba sabida kukan da ta ke tun safe ya daga mata hankali. Su Mama (Babar Raheema) da su Raheeman suna gidan amarya tun safe inda ake aikin jere da kafi.
Duk wasu furnitures da aka zuba a sassan Saade dake gidan Yarima Alhaji Kyari ne ya taho da su tafiyayyu daga kasar Italiya, wadanda Maimartaba ya yi mata an wuce mata da su Abuja.
******
SAADE A GIDAN YAREEMAN ASKIRA
Daga ita sai Hanne da Raheema a bedroom din da aka zaba aka shigar da ita, wanda shi yafi kowanne kayatuwa, sai kuyangi da bayin Fulani da ke ta kintsa duk inda aka bata. Fadin dukiyar da Askirama ya dankara a gidan Yareema Sageer bata baki ne, ki sa a ranki gidan Yariman Askira mai jiran gado, shi ke nan zance ya kare.
Gida ne ginin sarauta (royal mansion) wanda aka yiwa zubi na zamani,turawa suka zana shi suka kuma zo suka gina daga Amsterdam, da aka yi wa sassan matan aure har hudu, komai da ke cikin wannan sashe shi ne a wancan sai bambancin kalar fenti. A sashen kowacce mace manyan faluka ne bi-da-bi har guda Uku da dakunan barci Uku. Babun ce kawai babu a gidan Yarima Sageer Yusuf Askira.
Sassan Aisha Sultana shi ne na farko, sai na Saade sannan wasu guda biyu a rufe. An ware bangaren bayi da hadimai daga can karshen gidan.
Sassan Yarima kuma yana upstairs wanda girmansa ya yi a hada sassan matan nasa guda biyu. Komai da ke cikin sassan Yarima ya zo da shi ne daga Amsterdam kuma duk bayan shekaru biyu ake fidda komai na gidan a sake, a yo odar wasu. A raba wa talakawan gari, ko bayi da hadimai.
A can gidan Wazirin gari Ibrahim a dakin Awaisu Yarima Sageer ne tsaye jikin mudubin dogon yaro yana sanya links din hannun farar shadda kal da ya saka, sai tashin kamshin invictus dakin Awaisu ke yi. Awaisu ya kasa danne dariyarsa ganin irin kwalliyar da Yareema ke yi wadda ko ranar da zai raka shi dakin Aisha-Sultana bai yi irinta ba, ya karkata hula ya sake karkatawa yafi sau biyar, ya ga bata yi kyau ba ya cire ya sake canza wata, [to wancan aure ne da aka riga aka kwashe albarkarsa tun a waje]. A ransa Awaisu godiya yake wa Allah yana kuma adduar Allah ya sa auren nan ya zamo karshen duk wasu matsaloli na dan uwansa Sageer.
Amma dai sai gobe za mu je sayen baki ko? Ka ga yanzu dare ya yi sosai, na san duk sun yi barci bai kamata mu tada amarya ba tana barcin gajiyar biki irin wannan.
Inji Awaisu cikin seriousness.
Wata harara da Yarima ya juyo ya zuba masa sai da ta sa Awaisu durkushewa a inda yake yana dariya. Kafin ya dago daga dariyarsa Yarima ya gama saka takalmansa ya fice yana fadin.
In ka ga dama kada ka je, da ma ba ni na gayyace ka ba, aure dai ka sani ba yau na fara ba balle ka ce rawar kafa na ke yi.
Awaisu bai bar dariya ba da ma gwanin ta ne, ya saka takalmansa ya bi bayan Yareema Sageer yana cewa,
Ko don in bata maka lokaci kafin ka shiga dakin Sa'adatu dole in bi ka.
Yarima ya girgiza kai jin abinda Awaisu ya ce, ya ce, Awaisu! Mind your language. Saadatu is my step-sister rainon ta na yi wa uwarta alkawarin zan yi, kuma shi zan yi din. Zan ba ka mamaki, jibi-jibin nan zan koma wurin mata ta.
Awaisu don dariya har da hawaye, ya ce, Aah Yarima, kada wata tara ta cika kuma mu zo bikin radin suna, wannan rainon in dai kai za ka yi shi Saadatu ba za ta taba girma ba.
Suna ta barkwancinsu na aminai har suka karaso gidan sarki, don Yareema ya ce sai ya je ya yi wa Ya Gumsu sai da safe, ya kuma nemi albarka kafin ya karasa wajen Saadatu.
[Da ya san abinda