You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zuwa taga Mammah. Sai kawai ta saka a ranta tunda weekend za'a shiga zasu zo ita da Ruky. Isowar su gate ɗin nasu gidan sai taji ƙaguwar a buɗe, dan badan Dada bane a motar da tuni ta ɓalle murfin ta shiga da gudu. Amma jikinta sai tsuma yake ta yanda har shi ma ya gane. Aiko Dabo na tsayar da motar ta buɗe ta fice dan haƙurinta yakai maƙura. Dada ya bita da kallo kawai, dan kamar ƙyatawar ido har taje ƙofar falo.
Kansa ya ɗan girgiza yana miƙama Dabo daya buɗe inda yake laptop ɗin daya rufe. Daga haka ya sakko ƙafafunsa ya fito gaba ɗaya. Sauran kayan Dabo ya tattauro, dai-dai kuma isowar maigadi da malam Buba dake noƙewa a baya wajen. Cikin girmamawa suka fara gaida Dadan. Dada ya janye idanunsa daga kallon da yay ma malam Buba na seconds, kafin ya amsa gaisuwar tasu. Suka ɗora da nuna farin cikin dawowar Nimrah, sunata ambaton godiyar ALLAH. Shi dai wajen yay ƙoƙarin bari. Amma sai maigadi ya miƙo masa abinda ke hannunsa yana faɗin, “Af naso na manta. Ranka ya daɗe dama ga saƙo yanzun nan babu jimawa wani ya kawo shi a baka. Dan zanje nakai ciki ne ma kuka iso na dakata buɗe muku ƙofa.”
Received at 12:22 PM
reacted with ❤ Idanu Dada ya ɗan zubama hannun maigadi, sai kuma ya miƙa hannu ya amsa batare da yace komai ba. Yana barin wajen Malam Buba ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi da har sai da maigadi ya kallesa. Kamar zai yi magana sai kuma yay shiru suka koma bakin gate. Sanda da ya shige ɗaki wufff tun buɗe gate da akai ya fito shima sum-sum yana leƙa hanyar sashen Mammah da har Dada ya shige....

Yanda Dada ya samu falon ya kacame da murnar ganin Nimrah sai yama tsaya kawai yana kallonsu. Dan Ruƙayya na rungume da ita tana kuka ana lallashinsu. Su duka biyun suna jikin Mammah. Mu'azz ma sai sharar hawaye akeyi na farin ciki. Shigowarsa tasa su Bilal dake zagaye da su maido hankalinsu kansa. Sai kuma duk suka zaburo cike da farin cikin ganinsa suma. Mammah kanta yau ta kasa dannewa kallonsa take farin cikinta a bayyane. Gwaggo Alawiyya tazo ta kama hannunsa tana faɗin, “Sannu kaji Haysam, ALLAH yay maka albarka. Maza zo ka zauna ansha fama kwana biyu”.
Murmushi kawai yayi yana kaiwa zaune. Ya gaida Mammah sannan su Gwaggo Khadijah. Suma su Ja'afar suka gaisheshi. Kafin wani lokaci Aunty Mimi ta kawo masa ruwa. Dan suma duk suna gidan daga asibiti suke duba Lailah. Mammah tasan duk yanda suke son jin yanda aka samo Nimrah bazai faɗa ba, dan haka ta tambayesa a shirya masa abinci ne. Miƙewa yay yana amsa mata da zai yi wanka tukunna. Ya ɗan kalli Nimrah da Ruƙayya ke bama abinci a baki itama yana bata ya wuce abinsa. Dai-dai Ammar na sakkowa daga kai kayansa ɗaki da Dabo ya kawo. Umarnin kawo masa coffee ya bashi yana wucewa...........✍️
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels

WhatsApp Number: 09017242889


Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************

[16/02, 10:58 pm] null: KIƊA A RUWA 3

12

.........“Aunty wlhy Dada ya dawo”.
Zimbur Nabeeha ta tashi daga barcin da take yi tana kallon Rayhana mai maganar. Dan yanzu babu jimawa suka zo gidan ita da Amima. Iske Nabeeha na barci yasa sukai zamansu a falo suna kallo bayan sun saka mai aiki da suka zo da ita yanzun nan shiga kitchen ta musu abinci batare da ko matar gidan sun bari ta san da zuwanta ba. Momy ce tace su kawota kasancewar Nabeehar tayi mata complain a jiya game da aikin gidan. Tasan ragwantar Nabeeha sarai, ita kuma a wannan lokacin bata son a samu matsala kodan First Lady shiyyasa tai gaggawar samar mata da mai aikin, ko muce First Lady ta samar.
“Aunty badai can ɓangaren zakije ba?”.
“To mi kike so nayi Rayhana. Kin san dai mugayen can bazasu faɗa masa na dawo ba. Gara naje da kaina ya ganni.”
“Hu'umm da dai kin bari ya kawo kansa wlhy. Amma kije ai babu aji, bayan kin san shegiyar yarinyar nan tare suka dawo. Ƙilama babu wani saceta da akayi shiyya ɗauketa yaje yasha shagalins.....”
Kallon da Nabeeha ke mata ya hanata ƙarasa faɗa, sai kuma tace, “ALLAH ya baki haƙuri. Amma magana ta gaskiya yanzu fa ba da bace Aunty. Dole ne ki gyara wasu abubuwan musamman zumuɗin nan akansa.” tana gama faɗa ta fice a ɗakin. A ranta kuwa tana saƙa abinda ya daɗe a zuciyarta ne. Dan wannan karon tayi alwashin zatayi yaƙi domin kanta. Bazata iya haƙuri da ciwon dake ranta ba. Sai dai ayi ɗayan biyu. Kota samu, ko kuma kowa ya rasa...
Nabeeha kuwa ƙwafa tayi kawai. Ta nufi bathroom. Babu jimawa ta fito fuskarta jiƙe da ruwa alamar wankota tayi. Gaban mirror taje ta fara gyara fuskar da kayan kwalliya, sannan ta cire kayanta ta canja da wani arnen lass da yay masifar ƙyau ta saka turare sosai a jikinta. Koda ta fito daga Amima har Rayhana da kallo suka bita. Amima data saki baki na mamaki ta ce, “Aunty ina zuwa haka da rana tsaka?”.
“Sashen Mammah”.
Ta bata amsa a taƙaice tana ficewa abinta. Kallon juna sukai ita da Rayhana, Rayhana ta taɓe baki da faɗin, “Kin san bata da wayo sam.”
“To ALLAH ya ƙyauta wannan ai zubar da mutunci ne”. Cewar Amima...

()<>()<>()<>()<>()

Tunda Nabeeha ta shigo falon kowa ya saki baki yana kallonta. Mammah kam kallo ɗaya tai mata ta ɗauke kanta. Koda ta gaisheta ma a haka ta amsa hankalinta akan Nawal ɗin Aunty Mimi. Su Ma'aruff da suka zo wuya zasuyi magana Gwaggo Khadijah tai musu gargaɗi da idanu. Dole sukai shiru. Sarai Nabeeha ta lura da yanayinsu, amma ta danne dan a ganinta basu bane a gabanta. Idanunta akan Mu'azz ta tambayesa ina Dada yake.
Mu'azz ba komai ya sani game da lamarin Nabeeha ba. Duk da dai da wayonsa tabar gidan amma ba komai ya sani ba. Da hannu kawai ya nuna mata sama. Bakuwa ta sake magana ba, ba kuma kunyar kowa balle jin nauyi ta nufi stairscase ɗin tana taku ɗai-ɗai cike da gadara ita ga matar boss.
Aunty Ummi dake jin kamar ta amayo zuciyarta dan takaici taja hannun Aunty Mommy suka shige kitchen bayan tama Mimi signal da ido. Fakar idanun su Mammah tai itama tabi bayansu.
Basu wani jima ba suka fito, hannun Aunty Mimi da tray an haɗa kayan abinci akai. Cikin sa'a dai-dai nan Nimrah da Ruky da Biebah ke fitowa. Nimrah tayi wanka ta canja kayanta. Kuma wando ne fari daya kwanta a jikin nata da riga iya gwiwa Pakistan style na yadi mai taushi. Sai siririn gyale kalar yadin rigar. Babu wata kwalliya a fuskarta sai rosy lips data shafa daya saka lips ɗin taushi da santsi, yay pink sosai, ko daga nesa kake da ita zakaga hakan....
“Yauwa Nimrah zoki miƙama Dada abincinsa”. Aunty Mommy ta faɗa kai tsaye. Ɗagowa Mammah tai da sauri, ta buɗe baki zatai magana Gwaggo Alawiyya ta katseta da faɗin, “Dama yanzu zan yi magana kuwa. Amsa kinji ƴar albarka. Ruƙayya ke kuma zo nan na sakaki aiki”.
Haɗa ido Mammah da Gwaggo Khadijah sukai, Mammah tayi yanayin kai ƙara gareta, amma sai Gwaggo Khadijahn ma tai mata murmushi alamar tana goyon bayan abinda ƴan ta kife ɗin ƴaƴanta ke shirin yi. Kanta ta girgiza kawai tana kallon su Ma'aruff, a mamakinta suma duk sun washe fuskoki ba kamar yanda suka ciskule ba tun shigowar Nabeeha.
Received at 12:22 PM
reacted with ❤ Nimrah dai da ba sanin abinda ya faru sukai ba tuni ta shagwaɓe fuska zata fara langare. Aunty Ummi ta balla mata harara dole tazo ta amshi tray ɗin. Wucewa tai tana ɗan tuttura baki, dan harga ALLAH tana son yin ɗan nesa da shi har sai taji amsar tambayiyinta akan batun nan ɗaya tak daya zame mata ƙayar kifi a maƙoshi....

A wannan lokacin da Nabeeha tuni ta iso ƙofar ɗakin na Dada bayan ta hauro taci karo da Afeef dake fitowa a ɗakinsu shi da Mu'azz ta tambayesa ya nuna mata. Knocking tayi a hankali, sai dai shiru babu motsi balle ta samu amsa. Sanin halinsa yasa ta sake yi har sau biyu, daga nan ta buɗe Kofar kawai ta shiga dan ta kasa daurewa. Da wani irin ƙamshi ta fara cin karo, dan ƙamshin turaren wutar SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. na Maman Abdull ya gama kama lungu da saƙo na sashen Mammah. Sai da ta lumshe idanu ta buɗe tana sauke ajiyar zuciya kafin ta ƙarasa shiga ɗakin. Ko ina fes a gyare, babu tarkace kamar yanda ta sanshi mutum mara son hayaniya. Jin motsi a bayi yasata zama a bakin gadon tana murmushi, babu abinda take hangowa sai yanda zaiyi mamakin ganinta da farin ciki. Ta sake gyara zamanta da ƙyau. A dai-dai lokacin kuma Nimrah data iso itama tai knocking ƙofar. Sai dai jin shiru da sanin halinsa na in ba shi yaso ba bazai tanka ba yasata murɗa handle ɗin ƙofar kawai ta tura ta shiga da sallama.
Wani kalar zubo mata idanu Nabeeha da zuciyarta tai zallo cikin ƙirjinta tayi. Ta buɗe baki zatai magana tana ƙoƙarin miƙewa kawai aka buɗe ƙofar bathroom. Dada da bai san dasu ba su duka biyun ya ɗan yi tsaii yana kallonsu.
Nimrah kam jitai ƙirjinta ya buga, a lokaci guda tai saurin duƙar da kanta. Gaba ɗaya ji take ta daburce, a hakan ma ALLAH ya sota bathrobe ce a jikinsa ba towel ba. Sai dai kuma abinda bata taɓa gani bane daga garesa dole ta rikice. Dan bathrobe ɗin ma dai kaɗan ta wuce gwiwarsa.
Har cikin ransa bai ji daɗi ba shima. Idan Nabeeha ta ganshi a haka normal ne ai, amma Nimrah ina, da sauran lokaci. Jallabiya ya ɗauka batare da yayi magana ba ya juya cikin bayin. Babu jimawa ya sake fitowa da ita a jiki. Abinda ya bashi mamaki har lokacin Nimrah na'a inda ya barta. Kanta a ƙasa ga kaya a hannu kamar wadda aka dasa. Yayinda Nabeeha ke mata wani mugun kallo sai dai itama bata iya tayi magana ba saboda wani curarren abu daya dunƙule mata ƙirji ko numfashi bata fitarwa da ƙyau. Zuciyarta tsara mata take taje ta fisgi tray ɗin abincin ta kife mata shi a jiki, sannan ta kamata da shegen duka har sai ta daina numfashi. Kai itafa da tana da dama ko macen sauro bazata sauka mata a jikin miji ba..
Tana can tunanin ya kwasheta kawai sai hango Dada tayi a gaban Nimrah. Itama Nimrahn daba sanin isowarsa tai ba jin an riƙo tray ɗin hannunta ta ɗago da sauri alamar dawowa hayyaci, dan ya fahimci tsayuwar da tayi tunani ta tafi mai zurfi.
“Kina lafiya?”.
Ya faɗa cikin zurfin lafazi daya sakata jin wani sanyi ya dira tsakkiyar kanta yana bin jijiyoyin jikinta yana sauka har ƙafafunta. Slowly ta ɗago idanun da suka kaɗe sosai da ja a ciki, kasancewar shima ita yake kallo sai suka shige cikin nasan har sai da yaji wani dummmm a ƙirjinsa. Dai-dai lokacin Nabeeha ta matso kusa da shi, cike da salon daya ƙona ran Nimrah kawai ta rungume shi ta baya tana kwantar da kanta a faffaɗan bayan nasa. Cike da shagwaɓar iskanci ta furta, “I miss you baby”.
Gefe Nimrah tai da fuskarta tana lumshe idanunta da suka cika da ƙwalla. Dan wani suka da ƙirjinta yayi zata iya rantsewa tunda tasan kanta bata taɓa jin irinsa ba. Gaba ɗaya taji duniyar ta mata ƙunci, wani irin tsanar Nabeeha da haushin Dadan suka zagaye ƙirjinta batare data san dalili ba. Bata motsa ba a wajen da take balle nuna alamar zata fita tabar ɗakin kamar yanda ta fahimci Nabeeha naso, sai ma ji tai a ranta saita baƙanta mata rai itama, sannan wlhy bazata bar ɗakin nan ba yau sai da su zauna su ukun, in banda iskanci da ballagazanci miye na wani rungumeshi a gabanta, ai ko ba komai shi uba ne, yakamata itama ta mutunta kanta a gabansu dan su bata irin darajar da suke bashi koda bata da ita
Received at 12:22 PMa zahiri kamar shi. Amma tunda tace ita ta iya yanzu zata nuna mata shege ma da ubansa ba aruwa ake shawosa ba. ALLAH saita gogema matar nan hadda yanzun nan. Idan ita mijinta ne ai suma Babansu ne.........✍️

Tofa Madam Nimrah mutum da matarsa. Tunda kin yarda ita mijinta ne ku babanku ne basai ki fita ki barsu su jiƙa kansu ba🥱. Anya kuwa kikaji shine mijin ba akwai yaƙi ba? To bari muga ya wasan zai kaya a yanzu💃💃🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️☺️.
Received at 12:22 PM
[16/02, 10:58 pm] null: KIƊA A RUWA 3

13

.........Dada shi kansa jiyay wata kunya mai tsananin ta rufeshi. Haba shi girma abin a riƙe ne ai. Baiyi ma Nabeeha magana ba amma ya zame jikinsa daga nata, yana nufar kan center table ya ajiye tray ɗin abincin. Yazo ya sake raɓasu ya wuce gaban mirror, wayarsa ya ɗauka ya sake gittasu dai again ya koma kan sofa ya zauna.
Nimrah dake ƙoƙarin controling ɗin kanta ta kalli ƙafafun Nabeeha dake tsaye itama kamar an dasata, da alama abinda yay ɗin ya ɓata mata rai ne ko wani abu oho mata. Kawai sai taji murmushi na neman kufce mata sakamakon abinda zuciyarta ta ayyana mata akan matar. Amma sai ta danne shi ya tsaya cikin ƙirjinta. Dada dake ƙoƙarin kai waya kunnensa ya ɗago ya kallesu, shi sai ma suka nema sakashi yin dariya. Ya dai gimtse baiyi ba, dan saima ƙara ɗaure fuska da yay cikin bada umarni ya furta, “Kiddo zoki bani abinci”.
Duk da wani haushinsa da take ji saboda rungumar da Nabeeha tai masa sai ta jinjina kai tana nufarsa, dan kurama ai tasan gidan mai babbar sanda. A kusa da shi gab takai duƙe gaban table ɗin, ta bubbuɗe kwanikan abincin sannan ta kalleshi, duk da waya yake da Imran dan taji ya ambaci sunansa bata fasa faɗin, “Dada mi za'a zuba?”.
Yanda tai maganar cikin raɗa da masa nuni da hannu tana wara masa idanunta manya ya sashi ɗan zuba mata nasa idanun. Sai da ta sake waro natan sosai ta ce, “Dadaaaah”. Sannan ya farga da abinda yake ya janye yana nuna mata da hannu. Ta jinjina kai ta fara zubawa, sai dai ta raba hankalinta a kallon Nabeeha da har yanzu ke tsaye inda suka barta tabbacin ta shaƙa da abinda yay mata. A cikin zuciya Nimrah tace (Tun banyi komai ba aunty masu miji) a zahiri kuwa sai da ta kammala zuba abincin tsaff kawai ta saka murfin kwanon tangaran ɗin da aka zuba salad ciki baki-bakin table ɗin da gangan ta kaɓoshi ya wantsalo ƙasa sai kuwa akan ƙafarta. Duk da dai tayi dabarar saka hannu sai da ya taɓa bisa tsautsayi. Zabura tayi cikin gigita sai kuma hannunta ya tsumbula cikin kular farfesu. Aiko ta fasa ƙarar data saka Dada sakin waya ya juyo kanta...
Itako tuni ta miƙe a zabure ƙafar damƙe a hannunta ɗaya tana tsalle da ɗaya, hannun daya shiga miya kuma tana yarfa shi har tana neman faɗawa kan abincin nasa. Ba arziƙi ya tarota gaba ɗaya sai kawai ta faɗa saman cinyarsa. Anan kam harga ALLAH bata san kansa take ba, dan da gaske zafin ya ratsata har cikin kai, gashi bibbiyu hannu da ƙafa, dama ga Nimrah da shegen ragwantaka.
Rasa ina Dada zai kama mata yayi, dan ita kanta Nabeeha sai da ta zaburo, sai kuma taja ta tsaya tuna wacece da kuma yanda ya riƙota jikinsa. Tai bala'in waro idanunta waje ganin ya kama hannun Nimrah kawai ya saka yatsun data saka a farfesu cikin bakinsa. Ɗayan hannun kuma ya riƙo ƙafar tata.
Itama kanta uwar haɗa wajen tsittt tayi a karo na farko, dan abune da yazo mata a matuƙar bazata, bazatar ma mai gigitar da zuciya. Dan yanzu kam ta fahimci an sauka daga layin abinda tai niyyar aikatawa an tafi wani layin sabo data gagara bama suna ko kalma. Dada da shima sai yanzu ya fahimci halin da suke ciki sai ya runtse idanu, kafin ya buɗesu a hankali kan fuskar Nimrah data zuba masa nata idanun cikin yanayin ruɗani. Sai kawai suka sarƙe cikin juna, kamar kuma waɗan da aka hana motsi kowanne ya kasa janyewa suka shagaltu. Shagala a kallon juna irin yanda basu taɓa yi ba cikin idanu dai kamar haka.....

=============

“Baƙo kuma?”.
Hajiya Hasiba ta faɗa da mamaki tana kallon maigadi. Kansa ya jinjina mata. “Eh Hajiya. Kuma kamar ma baɗan ƙas.....”
Ya kasa ƙarasawa sakamakon shigowar Adeel falon. Miƙewa Hajiya Hasiba tayi, dan ita kaɗaice a gidan su Amima na gidan Nabeeha. Cikin in-ina maigadi ya ce, “Ya....ya..yauwa Hajiya ai gama shi nan ya shig.....”
Hannu ta ɗaga masa. Sai kuma tai masa nunin ya fita. Babu musu ya nufi hanyar ƙofa yana waigen Adeel. A ransa faɗi yake (Yau gani ga Balarabe ikon ALLAH) sai da ya kusa cin tuntuɓe ya dawo hayyacinsa...
Received at 12:22 PM
Adeel dake kallon Hajiya Hasiba fuska a ɗaure hannayensa duk a cikin aljihun wandonsa ya kai zaune cikin kujera cike da isa da gadara. Sai wani bin falon yake da kallo a yatsine. Duk da kuwa ba laifi falon ya haɗu, kuma a gyare yake tsaff ga ƙamshin air freshener na tashi. Sake maida idanun nashi yay a kanta. Da sauri ta fara gaishe shi murya na rawa.
Maimakon amsa mata sai yaja siririn tsaki. Cike da wulaƙanci ya furta, “K! Nine zakima ƙaryar kinyi tafiya?”.
“Wlhy ba ƙarya nake maka ba. A cikin satin nan na dawo. Kuma na nemeka amma ban samu ba. Ban san ka dawo ƙasar nan ba shiyyasa nake neman layin Abu-dabi.”
“Mtsoww!” ya sake jan tsaki. Sai kuma ya sake watsa mata kallon banza. “Nayi alƙawari dake kin saɓa. Kince mijinta na prison na bincika ance ya fita. Baki zo kin min bayani ba saboda kina ɗaukata wawa....”
“Wlhy ba haka bane Sir! Idan baka manta ba nata ƙoƙarin mu haɗu kafin kayi tafiyar farko. Amma hakan bai samu ba. Lokacin daka dawo nan ma naso hakan amma baka ɗaga kirana ba, sai daga baya nake jin ka wuce a wajen First Lady”.
“Wannan kuma damuwarki ce. Na baki kwana bakwai ku koma Dubai da ita. Idan ba haka ba zan yi abinda naga dama. Sannan duk abinda na baki komin ƙankantarsa ne babu sai kin cika. One week”.
Daga haka ya miƙe abinsa ya nufi ƙofar fita. Cikin rawar jiki Hajiya Hasiba ta yunƙuro zatai masa magana. Hannu ya ɗaga mata tare da watsa mata kallon daya sakata dakatawa da sauri. Sai da ya fice ta bugo musu ƙofar ta zabura gefe.....

(Idan kwaɗayi.....🥱🏃🏼‍♀️)


>>>>>>%<<<<<<

A ɓangaren Daddy Imran da ƙarar Nimrah ta tayarma hankali tun yana kiran hello! Hello! Har ya haƙura ya yanke kiran. Vibration ɗin kiran daya sake yi da yanda Nabeeha da ke jin kanta na juyawa kamar zata sume a wajen ta nufo inda suke a matuƙar fusace jikinta har yana rawa ya dawo da Dada da Nimrah hayyacinsu. Hannu Nabeeha ta kawo a zafafe zata cakumi Nimrah. Amma sai aka riƙe hannun nata caraf a bazata. Ido cikin ido suka kalla juna ita da Dada. Da wani kalar kallon dake tabbatar da gargaɗinsa da barazanar da bata taɓa gani ba ya furta,
“Kada ki taɓa koda mafarkin tsallaka wannan layin a karo na biyu. Dan tabbas bazaki ajiye ƙafarki kan ƙasa tana tare da gangar jikinki ba. Ni mai RIKICI ne akan wannan ANANAR. Ba lallai na iya kauda idanun TAƁATA ba koda akan kaina ne.”
Sosai zuciyar Nabeeha ke bugawa da sauri-sauri a cikin ƙarjinta. Lips ɗinta na rawa ta buɗe zatai magana.....
“Shiiii!!!” ya faɗa cikin ƙatseta yanama bakinsa alamar zipping da nuna mata hanyar ƙofar fita.
Nabeeha dai tasan halin kayanta, ta kuma san mi zai iya. Ta kuma san fassarar gargaɗinsa da umarni musamman idan har ya buɗe baki yay magana akan abinda ke ransa. Ita ko tsuntsuwar tasa bama ta fahimci inda kalaman nasa suka dosa ba. Hasalima ba maida murtani ga Nabeeha datai niyya bane a wannan gaɓar damuwarta, kasancewarta akan cinyarsa ne tashin hankalin ta. Gashi ya riƙeta ta yanda ta gagara koda motsi. Sai da Nabeeha ta buga ƙofar da ƙarfi Nimrah ta zabura, tsalle ɗaya tai ta wantsalo ƙasan lallausan carpet ɗin wajen jikinta na tsuma, ga zuciyarta na wani kalar bugawa diff-diff-difff. Dada ma idanu ya runtse da ƙarfi, sai wani motsa yatsunsa yake kamar mai kiɗa akan hannun kujerar. Sai da ya tabbatar ya samu nutsuwar da yake buƙata sannan ya buɗe idanun tare da yin gyaran murya yana sake tsuke fuska tamau.
Cikin dakewa a ainahin Dadan sa ya furta, “Naga hannun”.
Nimrah dake jin kamar tayita kwarara ihu saboda kunya, har idanunta sunyi jawur ta ɗan kallesa. Sosai taji shakkarsa da kwarjinin sa na sake mamayeta. Dan duk da ba dariya yake mata ko surutu ba ƴar sakewar da yake da ita na sakata jin sauƙi. Amma yanda yay ɗin yanzu ita tasan wargi ma waje yaka samu. Sai da ya ƙarema yatsun kallo, ya kamo ƙafarta itama ya duba, duka farcinan sunyi ja daga na ƙafar harna hannun. Baiyi magana ba ya miƙe zuwa fright ɗin ɗakin, ice ya ciro babba ya dawo inda take ya zauna.
Received at 12:22 PMIta dai binsa take da kallon mamaki, handkachiff ɗinsa dake ajiye a saman kujerar ya ɗauka ya saka ƙanƙarar a ciki. Kai tsaye ya kamo hannun nata ya ɗora a wajen data ƙone ɗin duk da baiyi alamar tashi ba. Tako sauke ajiyar zuciya da har sai da ya lumshe idanu ya buɗe. Sai da ya saka mata kusan

Please Login or Register in order to submit comment